kansu akan san zuciya wacce ba komai bane a ciki sai tsantsar buri da halaka dake cikinta?"
Umma ta kalleta tace " Haka rayuwar ta maidamu Khadija, ni kaina ina dana sanin abinda zuciya ta sani na aikata, a koda yaushe ina takaicin abinda na aikata."
Khadija ta d'ago ta kalleta tace " Umma!"
Kallanta mahaifiyar ta tai tare da maida hankalinta kanta.
Khadija tace " me yasa kike yadda akan duk abinda Abba yace? Mai kyau ko mara kyau? Haram ko halal?"
Umma idanunta ne suka canza kala tana kallan Khadija, tace " ban taba yimai musu ba haka kuma ban taba bijerima abinda yake so ba, shine ginshikin yan uwana, da abin hannunsa suka zama abinda suka zama yanzu."
Khadija tace " saboda abin duniya? Saboda 'yan uwanki suji dadi kike yarda da duk hukuncinsa? Ba kya tunanin kema kinada kamasho na laifufukan da ya aikata?"
Umma ta mike tare da kokarin maida kwallarta tace " Khadija! Kada ki kuskura kiyi rayuwa irin tawa, kada kisa 'yan uwa da iyayenki gaba da maganar Allah, wannan shine babban kuskuren da muke tafkawa idan Mahaifanmu,mijinmu ko 'yan uwanmu suka samu abu, bama tunanin dacewarsa ko kaucewarsa a addininmu sai muyi kokarin aikatashi dan musu biyayya da faranta musu."
Ta kalli Khadija wacce ke hawaye tace " khadija me kika sani? Me kika ji wanda ya tada hankalinki haka, kin canza, kin rame tunda kikazo ko abinci baki ci ba sannan neman barin gari kike yi, menene kikaji da yasa ko kallan iyayenki bakyasan yi?"
Khadija ta runtse ido wasu hawaue suka fito tace " menene ribarku akan kai Ya Abdulmajid gun Umma Magajiya?"
Gaban Umma ne ya fadi ta kalleta a tsorace, Waziri da tun dazu yake tsaye yana jinsu duk gab'obin jikinsa sunyi sanyi, jin wannan magana ta khadija yasa ya kalli kofar d'akin da sauri, cikin tsananin tsoro.
Khadija tace " kuna tunanin wannan sirri bazai taba fitowa ba? Idan Abba yayi hakan dan samun karfin mulki da juyowar mulki daga zuri'ar jinin sarauta zuwa nashi, kefa?"
Umma kallan Khadija kawai take batasan hawaye na zubo mata ba.
Hisham juyawa yai jiki a sanyaye yai waje zuwa masarauta, dan bazai iya jin naganganunsu haka ba.
Umma ta tsugunna a inda take tare da dafa kanta, Khadija kuka take dan bazata iya fadar dayan abinda taji ba dan ta tabbata Umma batasani ba, sai yanzu ta fahimci tsantsar dalilin dayasa Turab ya canza mata, ba shakka ba yanda za'ai sanda yake mata yai tasiri in har yasan sirri nan, bayan ita din jinin Hisham ce bawai rikonta akai a gidan ba.....
************
A cikin fada kuwa Sarki na zaune akan kujerarsa ta mulki cikin nad'i na sarauta, Galadima da Barde su kadai aka kira sai alkalin cikin gida.
Sai dogarawa dake tsaye a gefe, Turab ne ya shigo ya zauna a inda ya kamata, shiru sukai suna jiran Hisham dan isowarsa.
Galadima ne ya kalli agogo yace "Ranka ya dade minti 15 ya wuce daga lokacin daka bashi."
Sarki yace " a kara mai minti biyar."
Minti biyar ce tai, Barde yace " minti biyar tayi ranka ya dade."
Sarki ya kalli Alkali yace " wannan alama ce ta ya aikata abinda ake tunanin ya aikata ko?"
Turab kam addu'a kawai yake akan Allah yasa ya zo.
Alkalin zaiyi magana aka sanar da isowar Waziri.
Wani irin dogon numfashi Turab yaja na jin dadi.
Wannam shine shafin farko na d'aukan mataki akan abinda Magajiya ta aikata musu, shi, mahaifiyarsa, Sarki, Abdulmajid da Khadija.
Bazai so wani abu ya jawo rashin zuwan Hisham ba.
**********
Mairo kam duk ta rasa me ke damunta, ba shakka tunanin halin da Abdulmajid yake ciki shine ya dameta, yaci abinci? Ya sha ruwa? Karfa tun abincin data bashi har yanzu bai sa komai a cikin sa ba?
Mikewa tai zaune daga tsintar wanken da bata san ma me takeyi ba.
Tace a fili, zanje in dubashi ne bawai dan na damu da halin da yake ciki ba, sai dan zuciyar muslunci da tausayi.
Kai ta d'aga tace " ai duba mara lafiya ma babban aikin samun lada ne, dan haka dubiya zanje bawai dubiya zani saboda Abdulmajid ba....."
😄😄😄😂Nace anya kuwa Maryama????
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*80*
Kowa da ke cikin gurin ne ya zuboma Hisham ido, jiki a mace ya shigo ya zauna.
Galadima ya kalleshi sheke ke ya tuno abinda dansa ya sanar dashi, ba shakka ko waye ya ji dolene yasan da hannun Hisham a wannan lamarin inba haka ba ta yaya ya san inda aka kai Abdulmajid?
Gyaran murya da sarki yai ne yasa kowa ya nutsu, Takawa ya kalli Hisham sannan ya kalli Alkalin yace " a fara."
Nan alkalin ya ciro takardar ya fara karantawa kamar haka.
" A jiya ranar lahadi ne aka kawo karar Hisham wanda akace ya nemi da a kama Abdulmajid wanda hakan ya jawo masa karaya a kafarsa da kuna manyan ciwuka a gab'obin jikinsa."
Kallan Hisham yai yace " Hisham kana da abin cewa a game da laifin da akace ka aikata?"
Kalaman Abdulmajid ne suka fad'omai ya kalleshi yace " ta yaya zan so wani abu ya samu d'an kanwata? Ni fa na kasa fahimtar takamaimai me na aikata"
Galadima yace " ina muka san manufarka?"
Turab ne ya d'ago sannan ya kalli Hisham ya juya ya kalli Alkali yace " Gaskiya ni kaina na kasa gane takamaimai me ka aikata, zuwa gun d'aurin aurena dakai ka tambayeni a inda na taho? Ko kuwa jin Abdulmajid ya taho a motar daya kamata in taho da kaji hankalinka ya tashi? Ko kuma ganin da Sabi'u yama ka je ka d'auko Abdulmajid? Ni kaina Mai Martaba na Kasa gane mai Waziri ya aikata."
Hisham yace " dan na tambayeka in da ka taho gani nake ai ba laifi bane."
Turab ya jinjina kai yace " haka ne, sai Dai ya akai kasan inda Abdulmajid yake farat d'aya? Ba tare da bincike ba?"
Hisham ya d'ago ya kalli Sarki.
Sarki ya kalleshi yace " amsarka nake san ji."
Hisham ya daure yace " nima ba sani nai ba bincike nai har Allah ya kaini gun."
Galadima yace " gaskiya kam, ai hakan zata iya faruwa, amma ni a sanina Sabi'u baiga alamar bincike a tattare da kai ba."
Hisham ya kalli Galadima cikin takaici sai dai bai amsa ba.
Turab ya mike ya dawo gefen da Hisham ke zaune ya kalli sarki yace "Ranka ya dade menene dalilin daya sa Abdulmajid ya shiga motar da ta kasance mota ce wanda Ango zai shiga?"
Kallan Hisham yai yace " Waziri mai kake tunani?"
Hisham ya kalleshi dan bai fahimcu me yake nufi ba.
Turab yace "baka tunanin yaji wani abu game da abinda zai faru?"
Idanu Hisham ya zaro yace " kanaso kacemin Abdulmajid yasan abinda zai faru a ranar?"
Turab yace " ranar? Wace rana kenan?"
Hisham kallansa yai sannan yace " bansan me kake so kace ba."
Turab yace " zata iya yiwuwa, sai dai da alama bakwa tunanin abinda Abdulmajid yakeji a wannan lokacin, ace yayan mahaifiyarsa shine ya nemi halaka mai rayuwa, ko meye ribarka........"
Cikin zafi Hisham yace " kai yaro, ya isheka haka, har yaushe aka haifeka da zaka zo ka dinga d'aure magana? Hauka nakeyi da zan nemi halaka Abdulmajid? Tsautsayi ne dai ya afka ya shiga motar da bai kamata ya shiga ba, amma ni ban yarda ya ji ba, ni ina tunanin kai ne ka sashi ya shiga motar ma."
Kallan Turab sukai, Shikam bai san sanda ya sa dariya ba, yana dariya ya sunkuyar dakai yace " tuba nake ranka ya dade, bansan sanda dariya ta kwacemin ba, ni? Meye ribata in nayi hakan?"
Hisham yace " ka hau mulki ba tare da matsala ba mana."
Turab yace " kana so kace in har d'aya ya kauda d'an uwansa a tsakaninmu d'ayan zai hau mulki ba tare da matsala ba kenan?"
Hisham yace " Sai ka tambaya?"
Turab yace "ahhh na gane, amma in na kusa damu ne suka neman taimaka mana gun rage mana iri fa?"
Hisham yace " ban fahimceka ba."
Turab ya kalli Alkali yace " ina so a duba maganar Hisham kamar haka, na farko yace Tsautsayi ne dai ya afka ma Abdulmajid ya shiga motar, na biyu zuciyarsa tana tunanin halaka junanmu shine hanyar da ya fi cancanta d'ayan mu ya hau mulki, sannan bai musa ba akan shi da wani sun aikata wani abun tunda sanda na cemai Abdulmajid yaji bai musa ba akan bai san me yaji ba sai cewa dayai wai bai yarda yaji ba."
Ji sukai " Abu Turab kuka so ya shiga motar?"
rq
Gaba d'aya kallan mai martaba sukai wanda idanunsa ke kan Hisham, ya cigaba " motata dana bada ta ango ce, menene dalilin dayasa ba'a tare ko wace mota ba sai ta Ango?"
Turab Murmushi yai dan dama shi bai isa yai tambayar nan ba, fatansa d'aya mahaifinsa yai.
Hisham ya rikice ga tsananjn kwarjini na idob Sarki, kalaman Khadija ne kawai suke mai yawo, meye ribarsu?meye ribarsu? Duniyar ma nawa take?
Sarki a zafafe yace " Dakai nake magana Hisham."
Hisham ya kalli Sarki a tsorace sannan ya kallu Alkali.
Turab ya kalleshi, Hisham duk ya rikice.
Turab ganin ya gama rikicewa yai sauri yace " Waziri nine bakasan gani a duniyar? Me na tare ma?"
Kallan Turab yai yana huci yace " tambaya kake? Zuwanka duniya shine abu na farko da mukai dana saninsa."
Sarki yace " mene?"
Hisham ne ya kalli Sarki a tsorace sannan yai saurin sukunyawa duk jikinsa rawa yake, ina zai sa kansa?me zaice wanda bazai taba rayuwar Abdulmajid ba.
Turab jiki a sanyaye yace " kai da wa kukai dana sanin zuwana duniya?"
Hisham ya kallu Turab sannan ya kalli Alkali dasu Galadima da Barde wansa suka saki baki dab tsananin mamaki.
Hisham ya gama sadaukarwa yau kam tashi ta kare.
Idanu ya runtse yace " nine na aikata, ni ne nasa a kamaka, tsautsayi ya fada kan Abdulmajid."
Dolene ya fadi haka ba wai dan Magajiya ta sashi ba sai dan yasan yau kam tashi ta kare, ko ma menene dolene ya kare rayuwar Abdulmajid.
Inalilahi wa ina ilaihi raji'un.....
Abinda kowa ya shiga fada kenan a fadar.
Turab yace " kana so kacemin kai kadai ne ka shirya wannan abin?"
Hisham yace " ni kadai ne, da dani dawa nake yanke shawara ta?"
Turab yace " ni na kasa fahimtar menene ribarka a ciki in Abdulmajid ya hau mulki, dan yana d'an kanwarka? Ko kuwa da wani abun?"
Gaban Hisham ne ya fadi ya kalli Turab, tsananin tsoro ne karara a idanunsa.
Sarki a kufule yace " kai da wa kuka aikata? Magajiya?"
Kasa yau da kansa da sauri yace " ko d'aya bata ma san da wannan zancen ba, ni kadai na aikata bawai kuma saboda mulki na aikata ba sai dan ina bakincikin yanda Khadija ke san yarima Turab shi kuma yana murnar auransa."
Turab ya kalleshi a ransa yace taban ka biyo? wato so kake har karshw kar ka nuna dana sani ko? Zuciyarka ta gama kekashewa wanda ko kayi dana sanin bazaka taba sanarwa mutane da ka yi ba? Kunyar duniya ce bakasan kaji?
Ran Sarki ya baci yace " Alkali inaso a kewa Hisham daga wannan lokacin sannan ayi bincike sosai akan kaf laifufukan daya aikata inaso a sanar dani nan zuwa kwana uku."
***********
Magajiya kam ta rasa ina zata sa ranta, a zaune dai take kusa da Abdulmajid amma sam hankalinta baya gun, tashi hankalinta bai wuce sanda ta tuna abinda Abu Turab ya mata ba bayan sun rabu da Hisham.
Tana kokarin shiga d'akin taji muryarsa a bayanta yace " kin gama tsaramai?"
Juyowa tai ta kalleshi batace komai ba, sai wani kallo da take mai wanda ni kaina bansan manufarta ba.
Turab yace "shawara nazo baki, kiyi gaggawar zuwa ki sanar da laifufukan da kika aikata, dan wannan karan bazan taba bari kici galaba akaina ba."
Murmushi tamai tace "bari? Kana nufin kai kake bari nake yin nasara akan al'amurana? Sai dai ya zakayi Turab? Har karshen rayuwarka baka isa kai nasara akai na ba, ka sa wannan a ranka."
Ta shige d'akin, idanunta ta runtse sannan ta mike da sauri, bataga ta zama ba.
Kallan Abdulmajid tai wanda shi kansa a kwance kawai yake tace " zan je gida."
Bata jira amsarsa ba tai gaba.
Da kallo ya bita.
Baga dade da fita ba yaji an turo kofar, idanunsa ya maida ya rufe dan ya d'auka itace, sam baiji sallamara datai ba.
Kusa da gadon taje a hankali tace " Malam kaci abinci?"
Idanunsa ya bud'e da sauri sannan ya kalleta, ji yai wani sanyin dadi ya ratsashi sai dai yana tunanin ko ita taji sirrinsa kila kallonsa ma bazata sake ba.
Had'e rai tai tare da cewa " karma kai tunanin damuwa nai dakai nazo dubaka, asibitin nazo shine na karaso inga Khadija."
Murmushi ya sakar mata yace " ko ma menene dalili naji dadin ganinki."
Baki tad'an tabe tace " ya jikin Khadija?"
Yace " ta koma gida."
Tace " yayi, kai fa? Ka daina pretending d'in baka farfado ba?"
Murmushi yai yace " me? Kin damu ne akan rashin cin abincin da nake? Kullum ina kwance?"
Kai ta kawar da sauri tace " inji wa kenan? Tab!"
Dariya ya d'anyi ganin yanda tai saurin bashi amsa...........
**************
A can bangaren Turab kuwa, Gimbiya na zaune a kan gado ita kadai a cikin d'aki, ba shakka ya dade bai dawo ba, dan ita ma bata dade da dawowa daga bangaren Umma ba.
Jitai an kwankwasa kofar tare da yin sallama.
Amsawa tai sannan ta mike jin muryar Turab.
Kallan kofar tai a hankali taga ya shigo.
Tana ganin yanayinsa tai saurin karasowa inda yake tace " lafiya?"
Jitai ya jawota jikinsa ya rungume ta tsam.
Mamaki ne ya kamata, sai dai bata nuna ba, a hankali takai hannunta bayansa.
Ajiyar zuciya yai a hankali......
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*81*
Ya dade a jikinta kafin ya d'ago ya kalleta yace " i'm sry."
Abinda ya fada kenan yai fara takawa zaiyi waje.
Takunsa biyu yaji ta riko rigarsa, tsayawa yai ba tare da ya juya ba, a hankali ta tako zuwa inda yake itama ta sake rigarsa sannan ta kwantar da kanta a bayansa.
Yayi mamakin jin ta a bayansa dan shi har yanzu gani yake auren had'i ne tsakaninsu shi kuma bazai taba shiga hakkinta ba.
Cikin wata murya mai sanyin gaske tace " Thanks alot for showing me ur weaknesses."
Jiyai wani abu ya tsirgamai, murmushi tai mai sanyi sannan tace " ban san me ke zuciyarka ba game dani, sai dai at least nasan abu d'aya wanda inaji shikadai ya isheni zama dakai cikin farin ciki."
" menene shi?"
Kanta ta d'aga daga bayansa tana murmushi tace " nasan u are comfortable in kana tare dani."
Murmushi yai sannan ya juyo ya kalleta yace "Hmm abinda kika ce......"
Kallansa tai cikin mamakin dan yanda yai maganar alama ce ta zai musa abinda take tunani, da sauri ta juya bayanta tace " ba sai ka fad..
.."
Kansa ya sako ta bayanta saitin kunnenta yace " abinda kikace hakan yake."
Sam ta manta da kanta na gefen kunnenta ta juyo da sauri jin amsarsa.
Numfashinsu ne ya sarke dan fuskarsu tayi daf da juna, a hankali ya saukar da idanuwansa ya kalli bakinta wanda yake dan karami mai kyau, gashi tasa jan baki jaa amma bai turo ba.
Wani abu ne yaji yana tsirgamai, dif sukai kamar an d'auke wutar nefa sai shi da yake dan kokarin kara karkatar da kansa wanda ita kuma tai kasa da idanunta saboda kunya.
(mai kake shirin yi Turab? Me zuciyarka take neman saka? Ina alkawarin?)
Jisukai an kwankwasa kofa, juyasa yai da sauri ya nufi kofar ya bud'e.
D'aya daga cikin masu kula da Gimbiya ne, ta gaisheshi sannan tace "Yarima an turo Mai Martaba na banana. "
To kawai, yace yai waje.
Yana fita ya furzar da wata iska sannan ya d'anyi fifita da hannunsa yace " why am i feeling hot?"
Itama yana fita ta fada kan gado ta kwanta tare da saukar da ajiyar zuciya itama.
Bangaren Mai Martaba ya nufa, a waje yana jiran kafin a sanar ma Mai Martaba zuwansa ya kalli wani yace " Jakadiya fa?" yace " ai yau da safe tace wai yarta ba lafiya, shine aka dawo da wannan nan, ita kuma ta tafi." ya karasa maganar yana nuna mai wata.
Murmushi yai dan ya tabbatar guduwa tai, nan ya shiga bangaren Sarki.
Yana zaune ga abincin nan a gabansa da alama yanzun nan ya gama ci.
Sai da ya kara gaisheshi sannan ya zauna tare da lankwashe kafafunsa yace " gani."
Sarki ya kalleshi yace " me kake tunani game da Waziri?"
Turab yace " ban fahimceka ba..."
" na rasa me yasa nake ganin kamar akwai abubuwa da dama da kake b'oyemin."
Turab yace " me yasa kake tunanin haka? Ni kam ba abinda nake b'oyema."
Takawa ya kalleshi sannan yace " Turab? Kana tunanin zaka iya kama Magajiya da kanka?"
Turab ya d'ago ya kalli Sarki sannan yace " Abba me yasa ka ke kokonto a kaina?"
Sarki ya girgiza kai yace " Abu Turab!"
Kallansa Turab yai jiki a sanyaye, yace " Hajiya ta farfado, sannan naji abinda ya ke faruwa."
Idanunsa ne suka canza yana kallan Mahaifinsa saboda tausayawa.
Sarki yai murmushi yace " alokacin da naji abinda ya faru lokacin ne na tabbatar da Magajiya tafi karfina sannan babu ko dan d'igon imani a zuciyarta, a da nayi tunanin rashin nuna mata kulawa ne yasa ta rikid'e ta koma haka, sai dai abinda naji sam ya hanani bacci, hankalina ya tashi. Ban taba tunanin a duniya akwai wanda rashin imani zai sa ya aikata hakan ba, sannan bayan abinda ta aikatamin har ta nemi halakamin mahaifiya, a wannan rana nayu dana sani sosai na zamantowata Sarki dan da ace ni ba Sarki bane banaji duk wad'an nan abubuwan zasu faru dani."
Turab yace " Kaddarar ka kenan Abba, sai dai fatan Allah yasa kaci jarabawar da ya maka."
Sarki ya kalleshi yace " wato ita daga d'anta bata san in sake haihuwa kenan?"
A ran Turab yace " Abba shima ba naka bane."
Sarki ne ya cigaba, Turab kai Kainuwa ne dashen Allah, shi yasa duk wani makirci da kiyayya bata hanaka takawa duniya ba, bata kuma haka bud'e ido ba a duniya, wannan itama Baiwa ce da Allah ya bani wanda nake gode masa."
Turab ya d'ago ya kalli Mahaifinsa yanajin wani tsananin tausayinsa na ratsashi, cikin takaici yace "Abba wai kana sarki ke zai hana ka hukuntata daidai da laifukanta, barinta fa da akeyi shi yasa ma take abubuwan dataga dama."
Sarki ya dade kafin ya murmusa yace " Turab kenan, bakasan me nene nauyin dake d'aure akan kujerar nan ba, sannan abu ko ya shafeni dole sai na fitar da shaida sannan nai hukunci cikin jama'ar fada, sai dai matsalar itace Magajiya bata barin abinda zaisa a gane tayi abu, sannan duk wani wanda yake da hannu akan abun to fa sai ta san yanda tai ta kawar dashi."
"Hajiya fa?"
Sarki yace " wa zai yadda da shaidar tsohuwa? Sannan suruka?"
Turab yace " haka ne na tabbatar zata iya juya laifin kanta."
Sun dade suna tattaunawa kafin su rabu.
Turab na fitowa ya bi d'akin mahaifin nasa da kallon tausayi, tabbas dolene ya hanzarta sanin abinda ya kamata yai da Magajiya.
Magajiya kam tana dawowa taji labarin killace Hisham da akai, wannan abu ya tabata sosai ya kuma kara tada mata hankali domin ta tabbata Turab sai tayi da gaske akansa, wannan shine karo ma farko da aka kada ita da dan uwanta akoda yaushe sukecin riba bawai su a ci riba akansu ba.
Bayan La'asar ta aika a kira mata Basira.
Basira kam ta gama had'a kayanta kenan da Turab yace ta koma can ko sati d'aya zuwa biyu ne tayi, sannan Sarki yace za'a maida Hajiyarsa can gidan.
Jin wannan sakon yasa tai shiru kafin ta fito, dan a ka'idar mulki Magajiya ce Sarauniya wacce duk matan sarki ke karkashinta dolene ta amsa kiran data mata.
Magajiya na zaune kan kilisarta kai kace ba wani abu dake damunta sai dai zuciyarta fal take da tsoro da shakkar abinda ke faruwa.
Basira ta gaisheta sannan ta zauna.
Magajiya ta kalleta cikin izzarta tace " Basira kin san ko ni wacece ko?"
Basira ta kalleta cikin mamaki da rashin fahimtar abinda take nufi, Magajiya ta murmusa sannan tace " ba wai wani abun nace ba, tuna miki dai kawai nakeyi, ni d'in macece wacce banida yafiya akan duk wanda ya nemi tozartani, inaso kisa hakan a ranki sannan ki sanarma na kusa dake abinda na fada, daga ke har abinda kika haifa banaji kunyi kaurin wuyan da zai sani na tsugunna muku, tunani yakeyi shine yake cin galaba akaina shiyasa na kiraki ke wacce kika haifeshi in sanar dake hakan."
Basira ta kalleta sannan tace " Magajiya ni na kasa fahimtarki, Turab ne ya tozartaki kike sanar dani in gargad'eshi ko me?"
Ran Magajiya ya b'aci sai ta saki dariya tace " me? Tozartawa?au har an hallici d'an dazai tozartani a duniyar nan?"
Basira ta murmusa sannan tace "nima abinda na gani kenan, shi yasa nake mamaki danaga kin kirani kika neman sanarmin in jaa ma Turab kunne, bayan yaran nan naki ne."
Magajiya ta kalleta a ranta tace " wato kema kin rika ko?"
Basira tace " zan koma in ba wani abun."
Bakin ciki baisa Magajiya ta kara tanka mata ba.
Tana fita Magajiya tasa kafa ta ture tiren inibin dake gabanta cikin b'acin rai, sannan tai wani dan karamin kara ma takaici, me yasa yanzu sam bata iya shanye bakin ciki? Mikewa tai cikin takaici tace " ke aika a kiramin Waziri."
Baiwar ta sunkuyo tace "Ranki ya dade kin manta an........."
Matsowa tai ta kifama yarinyar mari sannan tai ciki ranta na soyuwa.
Tafiya ta kamayi a d'akin cikin b'acin rai, yanzu ba Hisham wanda sai dai tana daga zaune tasashi aiwatar mata da duk abinda take so, sannan ba Abdulmajid wanda take tunkaho dashi Yana can a kwance.
Kanta ta dafe sannan ta d'ago idanunta cikin tsananin bacin rai, tace "Abu Turab!!! Ka jirani, zan shayar dakai abinda har karshen rayuwarka bazaka manta dani ba, wannan shine zai zama fad'anmu na karshe dakai, in har nai kuskuren halaka rayuwarka to tabbas nasan tawa rayuwar zatai rawa."
Kurama kasa ido tai cikin tsananin takaici, rabon datasamu bacci mai dadi ta manta, kullum sai tai mafarkin Turab na neman illatata, tabbas dolene suyi fito na fito yakin karshe a tsakaninsu.....
(😂😂😂😂nace Allah yaba mai rabo sa'a)
Khadija kam ta gaji da jiran Mahaifinta tana zaune a waje akwatinta na gefenta, ganin yamma tayi yasa ta mike ta fito waje.
Tsayawa tai ta kira mai kula da kofar su, ta tambayeshi " ina Abba wai yaje?"
Yace "wlh ban sani ba na dai san ya fita."
Juyawa tai ta koma ciki kawai, Umma na kwance a d'aki tunda sukai maganar nan da Khadija ta shiga d'aki bata fito ba, tanaji kannan Khadija da yayyinta na shigowa su fita amma ta kasa tashi, saboda tsananin dana sani dake damunta.
Wannan kenan..........
*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*82*
Bayan tayi sallar magrib ta yafa mayafinta katon gaske, lulubi tai sosai da sosai, wanda inba kaga fuskarta ba bazaka taba cewa Magajiya bace, ta fito, tara bayinta tai ta sanar dasu zata fita sai dai batasan kowa yasan ta fita sannan ko anzo nemanta a tabbatar ance tana bacci.
Ita kadai ta fito ta nufi inda aka killace Hisham.
Tana zuwa ta sauke mayafinta sannan ta kalli masu tsaron gun tace "yana ciki?"
Kallanta sukai bayan sun gaisheta sukace " Ranki ya dade Sarki ya umarcemu akan kar kowa......."
Wani kallo data buga musu shine ya hana su karasa maganar, tace " nice kowa?"
Da sauri sukace " ba haka bane......"
"ya isheni, bud'e."
Jikinsa na rawa ya bud'e kofar ta shiga."
Hisham na zaune ya had'a kai da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 32 Chapter of 37