da ya ji fatar.
Yana ɗauke hannun ya miƙa wani wajen tun da gabaɗayan su a kan katifar suke, duk sun
cushe, tun da su biyar a kan katifa ɗaya, yana ƙara miƙa hannun ya sauke a kan ƙafafun
samarin nan shafawa ya yi sai ya ji wani gautsin fata, don har ya shafo kaushi da faso a ransa
ya ce
'Kai jama'a har yanzu dai ina ta dawurwuri a jikin ƴan ƙasar nigeri'a Allah ka kaini a kan daidai
wato in taɓo fatar balarabe' Ya faɗa yana jin tausayin kansa.
Samarin nan kuwa jin an taɓo musu ƙafafu, kowanne sai numfashinsa ya tsaya cak! Tunanin
su fatalwar da Liman ya gani ce za ta yi awon gaba da su. Juna suka ƙara ƙanƙamewa
kowanne yana ta ƙoƙarin warto addu'a a zuciyarsa domin ya kuɓuta, sai dai a cikinsu babu
wanda ya yi nasarar ambatar kowacce addu'a don ruɗanin ya kai ruɗu.
Gwiwarsa ya ja bargonsa yana ƙamale a kafaɗarsa idanunsa a rufe, ya miƙa hannunsa bai
masa masauki a ko ina ba sai a kan mazaunan Ya Sheik, laushi luɓus ya ji, hakan ya sa ya
miƙa ɗaya hannun ma ya zamana hannayensa biyu a kan mazaunan don yana son tabbatar da
cewa tabbas a kan fatar Ya Sheik ya sauke hannunsa, amma fa duk abin nan da yake bai san
cewa a kan mazaunan Sheik ya sauke hannu ba. Sheik kuwa jin an taɓa masa mazaunai a
lokacin ya ƙara gane mazaunansa a tantagarya yake babu rufi ba ma wannan ba lalumen da
Mai Gari yake yi nema yake ya wuce gona da iri a wajen Sheik domin kuwa hannunsa yana
neman taɓo mafitsarar Sheik, Sheik wanda tunaninsa ya fara bashi cewa fatalwa ce take
lalumen jikinsa sai ya ƙara tsorata ya shiga ruɗu, da tunanin kar dai fatalwar mai ƙusunbin tana
so ta tsinke masa mafitsarar ne gabaɗaya ma, wani sashen na zuciyarsa yana bashi cewa ko
dai shayi ake son a masa(Kaciya,sallatu) Idanu ya zaro bai san lokacin da ya buɗe baki ba
gabaɗaya ya manta sa ƙalƙalar sa yake yi ta larabci wajen yin magana, wato yadda ko hausa
yake sai ka ɗauka ɗan koyo ne.
Wanann karo da hausa sak irin yadda bahaushe yake magana babu gargada ya ce
"Wallahi na rantse da Allah an mini kaciya, don Allah kar a cire mini mafitsara" Ya faɗa a fili
ɗakin har yana ɗaukan amsa kuwwa. Don ya fara tunanin kar a je ko dai a tsinke masa
mafitsarar ko dai a je garin masa kaciyar a yanke fiye da rabin mafitsarar a bar masa ƴar
guntuwa. Yana faɗa wani hawayen tausayin kansa ya cigaba da zubo masa domin ya fara tuno
matansa su Lami da ya baro a ƙauyansu ya san duk inda fatalwar kakan Mai Gari ya gabce
masa rabin mafitsara, ko ta cire masa gabaɗaya to in har ma bai mutu ba kenan, ya san
shikenan sai dai kowacce ta ce ya bata takardar saki, tuno da wannan kuma ya san yana son
matansa sai ya ƙara ware murya duk da yana cike da tsoro ya ce
"Wallahi ina son matana, ba zan sake su ba wani ya aura" Mai Gari tun maganar da Sheik ya yi
ta farko wato inda ya ji Sheik yana batun kaciya da cire mafitsara, bai san lokacin da ya ɗauke
hannuwansa salin alin da sauri ya koma wajensa da ya taso ya kifa kansa yana ambaton
'Lahaula wala ƙuwwata ' A zuciyarsa, don shi ya san dai ya ji an yi magana amma ko za a saka
masa wuƙa a maƙoshi ba zai gane ga wanda ya yi maganar ba, sannan ruɗanin da yake ciki bai
bari ya gane cewa Sheik ne ya yi maganar hausa sak ba, babu ƴar ƙalƙalar larabcin.
Malam Liman jin ana ambaton kaciya sai ya fara tunanin ko dai fatalwar ta yanke shawarar
yayyanke musu mafitsara ne hakan ya sa ya saki towel ɗin da ya rufe kansa da shi, ya mayar
wajan matse matsin ƙafafunsa a nufinsa ya yi shirin ko ta kwana, saboda kar a masa sakiyar da
ba ruwa.
Gabaɗaya kowa da zaman jiran tsammanin da yake, Sheik ya yi ƙarfin halin jan bargon ya
rufe mazaunansa, yana jin da na sanin zuwa garin ma baki ɗaya, sai dai shegen kwaɗayi da
son abin duniya ba za su bari ya bar garin ba, ya yi wa kansa alƙawarin zama daram sai ya ga
abin da ya turewa buzu naɗi.
Mai Gari ya jiƙe da gudmi sharkaf ga gwiwarsa ta ƙafa da ya tsunduma a fitsarin Liman, amma
dai yanzu a matsayinsa na Mai Gari gashi kuma yana tsoron mutuwa dole zai yi ƙoƙarin yin
magana don a samu mafita, tun da tana ganin duka manyan garin ne a ɗakin, idan kuwa
fatalwar mai ƙusumbi ta musu fata-fata to gari yana cikin garari.
Su kaɗai suka san gari lafiya lau yake, amma shi Sheik har yanzu tunaninsa wani gudun
famfalaƙin tsoron ne ya sa suka yi hijira daga cikin gari zuwa gidansa.
Da muryar kuka kuma muryar a shaƙe kai daga ka ji maganar ka san mai yinta ƙarfin hali yake
Mai Gari ya ce
"Ya Sheik, muna buƙatar taimako, muna buƙatar addu'a kar fa a mana ɗauki ɗai-ɗai, ka yi
addu',a mana, mu baƙaƙen fata muna cikin wani hali kaima babban malami kana...
Tun Mai Gari bai kai aya ba Sheik ya daure ya yi ƙarfin halin saita ƙalƙalar hausar larabcinsa
ya fara cewa
"A'uzubillahi minash shaiɗanir rajim, Bismillahir rahmanir rahim" Tun da ya sanu nasarar yin
a'uziyyar nan shikenan yake maimaitawa don shi ita kaɗai ya iya kamowa, don haka bai damu
da cewa yana ta maimaitawa za su ce wani abu ba. Mai Gari da yake jiran ya fara jin ana
zayyano addu'o'in larabci masu yawa bayan gama a,uziyya da bismillah sai ya ji ba a fara ba
ana ta maimaita abu ɗaya. Can ya ce
"Haba Ya Sheik ka fara addu'ar da muke ji ana karantowa a ƙasar makka mana" Ya faɗa yaba
ɗan ɗaga muryarsa da take ta zillo tana rawa, tare da saurin gyara fuskarsa daga inda ya nutsa
ta a jikin katifa jin ya danne hancinsa numfashi yana neman gagararsa shaƙa, amma fa duk
maganar nan da ya yi Sheik bai ce uffan ba kuma bai fasa faɗar abin da yake faɗa ba, saboda
shi a ganinsa ya samu makamar ceton kansa.
Liman da samarin nan jin muryar Sheik ta karaɗe ɗakin yana faɗin
"A'uzubillahi minash shaiɗanir rajim, Bismillahir rahmanir rahim" Cikin muryar larabawa tamkar
wanda wani balaraben gaske yake yi, basu san cewa Sheik sai da ya daɗe yana yi wa
muryarsa training a kan ƙalƙalar kafin ya zo garin nasu ba.
Liman da samari basa bambance abin da yake faɗa, don yadda yake maganar tamkar wata
doguwar sura ce yake karantawa sai suka shiga mishi amshi da faɗin
"Allahu akbar!" Idan ya faɗa sai Liman ya ce
"Attakabir" Sai samari su ce
"Allahu akbar!" Mai Gari ma tuni ya bi yarima yake shan kiɗa, don ya lura shi kaɗai ne muryarsa
bata fitowa a cikin ɗakin, yana tsoron abin ya zama shi kaɗai zai samu.
Sun kwashe sama da awa suna a haka, sannan ne Sheik ya ji ƴar nutsuwa, ya buɗe ido ɗaya
ya ƙyallara ya ga dai ɗakin babu kowa, wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke, yana tunanin abin
da ya faɗa ne ya sanya fatalwar ta fita daga ɗakin.
Daƙyar ya ɗago daga gohon ya zauna, ganinsa babu towel ɗin nasa, sai ya ƙura ido a
mafitsararsa yana son ganin ko an masa shayin, amma sai ya ga yadda take haka take, sai dai
ta yamushe a waje guda ta tattare saboda wahala. Har lokacin bakinsa bai yi shiru da abin da
yake faɗa ba, hannu ya kai ya fisge towel ɗinsa na wajen Liman, Liman da dama bai riƙe towel
ba kasancewae hannuwansa suna matse a matse matsinsa, sai ji ya yi an buɗe masa kansa,
hakan ya sa ya ƙara runtse ido haɗe da bada ƙaimi wajen ƙara danna hannuwansa don ganin
ba a yi kaciyar nan da shi ba, har lokacin yana faɗin
"Attakabir" Da sauri Sheik ya ɗaura towel ɗin ya ɗan muskuta ya koma kan sallayar da take
shimfiɗe, tare da miƙa hannu ya ɗakko hirami a jakarsa yana gyra zaman hularsa da gemunsa,
sai da ya zauna yana kallon gabas , ya rufa hiramin yana ta cigaba da a'uxiyya.
Dakyar ya samu nasarar warto suratul fatiha a bakinsa, ya shiga karantowa, sai da ya yi sau
uku, sannan yana zaunen ba tare da ya juyo ba ya ce
"Alhamdulillahi, na samu nasarar korar fatalwa, komai ya dawo daidai" Ya faɗa cikin muryarsa
ta balarabe. A hankali suka fara tashi zaune kowa yana ɗan ƙyallara ido, ganin babu fatalwa a
ɗaki, sannan Sheik yana kan sallaya ya rufa hirami sai suka fara hamdala Mai Gari faɗi yake
"Allah mun gode maka da ka kawo mana babban malamin larabawa da yau ya za mu yi?" Ya
faɗa yana kallon gwiwar ƙafarsa, da ta jiƙe, shi kuma Sheik bai ma san inda gudawarsa ta yi ba
domin yanzu ba ya ma ji.
Malam Lima cewa yake
"Ai ba ƙaramar sa'a muka yi ba" Ya faɗa yana ɗan satar kallon wandonsa da ya jiƙe ya ce
"Wannan yara an yi yaran banza, yanzu a cikin ku aka samu wani marar imanin ya zage wando
ya mini fitsari a jikina?" Ya faɗa yana kallon samarin nan da suke sharkaf da gumi. Ɗaya ya
buɗe baki zai yi magana Mai Gari ya yi saurin cewa
"Kai ba a son wani tone-tone ku bashi haƙuri" Haka suka bashi haƙuri ba don son so ba, sai don
ba yadda za su yi kuma dai ga wandonsa ya fi nasu jiƙewa tun da shi ya yi fitsarin su dai kawai
sun shiga lemar ne.
Liman daɗi ya ji a ransa ganin girmansa bai zube ba. Nan suka kalli Sheik da ya juyo daga
kallon gabas yana gyara zaman towel ɗin da hiraminsa, gumin da yake yi tamkar ya dawo daga
filin tsere.
Mai Gari yana kallonsa ya ce
"Sannu Ya Sheik lallai ka yi artabu" Sheik a zuciyarsa ya ce
'Artabun yau ka gani, da ka ga na jiya da na sha da ina ga wano zancen ake ba wannan ba'
Amma a fili sai ya ce
"Kai wannan ai ƙaramin abu ne, ai ina tabbatar muku kuna zuwa cikin gari za ku ga aljannu sun
lafa komai ya daidaita" Da mamaki suke kallonsa jin yana batun cikin gari, Malam Liman ne ya
ce
"Cikin gari babu lafiya ne dama?" Shiru Sheik ya yi yana tambayar kansa a zuciyarsa cewa
'To da uban me ya taho da ku da gudu idan ba tashin hankali kuka baro a cikin garin ba?' A fili
ya ce
"Dama cikin garin lafiya, na ɗauka ai babu lafiya da na ga kun shigo gidan nan a kuɗime" Mai
Gari ya ce
"A'a gari lafiya ƙalaw dama zuwa muka yi, mu ga ko lafiya mun zo da asuba kiranka a yi sallah
amma aka gaji da bugawa shiru, to shi ne muka samo samarin nan muka ce su ɓalle ƙofar a
duba lafiyarka, da aka tura ƙofa kuma sai muka hango ka taho a guje da takalmi ɗaya a ƙafa jiki
duk kumfa, wannan dalilin ne ya sa mu ma muka ga tun da har kana gudu to akwai gagarumar
matsala gwara mu bika mu tsira ka ji dalili amma gari kowa yama sabgar gabansa lafiya" Wata
ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke, yana jin wani mugun haushin su, da suka firgita shi, shi a
nashi tunanin garin ne a ruɗe suka taho ashe dai shi ya ruɗa su.
Cike da ƙarfin gwiwa ya sheƙo wata sheƙeƙiyar ƙarya don kar a ga gazawarsa ya ce
"Ai nake faɗa musu ina cikin banɗaki ina wanka, nan na ga wani aljani mai ƙaho bakwai ya
tsaga bango ya fito, yana fitowa ta sheƙe da dariya yana cewa, wai yanzun nan za su saki
manyan aljannun da za su rikita gari, kai har cewa ya yi mai gari ma ɗauke shi, za su yi,
wannan dalilin ne ya sa ina nuna shi da yatsa wani hayaƙi ya tashi da shi sama, ya bi iska ya
ɓace, to ni kuma tuno halin da garin zai kasance shi ne na fito hankali a tashe domin na kai
muku ɗauki cikin gari, ganinku a guje kun shigo ya ƙara sanya hankalina ya tashi, saboda bana
son jama'a su shiga damuwa, sai yanzu bayan na gama addu'ar nan na gano ashe dai aljanin
nan ne ya shiga jikina ya haifar da tsuma da ruɗu da tsoro, don kar in taimaka muku, shi ne fa
muke rige-rige tsakanin ni da ku wajen samun maɓoya" Ya faɗa yana dafe goshi alamar
damuwa.
Mai Gari har da ƙwallar farin ciki ganin ba ƙaramar ƙauna Sheik yake yi wa garin nasu na
Ƙundu ba, sannan ba ƙaramin taimakon su yake yi ba, bai san cewa Sheik kasuwanci ya zo yi a
garin nasu ba, don ba a aikin banza a ko ina.
Cike da girmamawa ya ce
"Allah saka da alkairi Malam ashe kana ta fafutuka ne a kan garinmu, silar haka har aljani ya
shiga jikinka ya saka muke tsere, bawan Allah dama na yi mamakin ganin muna ta neman
mafaka tare da kai ashe dai ba da kai muke nema ba, da aljani ne" Ya faɗa yana kallon Sheik.
Liman ya ce "Ai ni na yi mamaki dama, malamai ai magada annabawa ne" Sheik ya ce
"Ina ai ƙaryar aljani in ji tsoronsa, su kansu sun sanni" Ya faɗa amma yana ɗan rage murya
saboda tuno kunnen jaririn da aka jefo a banɗaki.
Liman ya ce
"Allah mai baiwa, ku dai Allah ya baku" Sheik aka wani gyara zama gudun kar towel ya kunce
ya ce
"Ai aljanin ya yi niyyar hanani yin addu'a ma lokacin da fatalwa ma ta shigo hatta bakina sai da
suka so riƙe mini, yanzu ma sai da na sha fama na hau sallayar nan, so suka yi kar in yi addu'a"
Gabaɗaya suka ce
"Allah ya fi su"
Nan dai aka sa samarin nan su fita da katifa su gyara ɗakin, a nan ne ma Mai Gari ya ƙarewa
Sheik kallo ganin idanunsa luhu-luhu alamar ko dai kuka ko rashin bacci ya ce
"Ya Sheik ka ga idanunka kuwa, hatta fuskarka a kumbure take" Sheik tuno artabun da suka
sha jiya da jarirai da aljannu har ya hau bishiyar kuka, sai ya ɗan yi gyaran murya ya ce
"Haba Mai Gari wanann tambayar ma ai ɓata baki ake yi, ni da na zo taimako ina ni ina bacci, ai
ni nan da na gama cin abinci kawai alwala na yi na hau sallaya, nake salloli ina addu'a ban tashi
ba sai da aka fara kiran assalatu, shi ne na sake alwala na yi shirin fita masallaci, sai kuma na
tuna ku ne za ku zo mu tafi tare, to dai ni ban ji zuwanku da asubar bama don ni nan na yi
sallah da nafiloli, wataƙila aljannu sun saka mini auduga ne a kunne shi ya sa ban ji bugun naku
ba" Ya faɗa yana kai hannu ya share zufa a goshin sa.
Sosai suka jinjina masa, daga nan suka ce za su je a kawo masa abin kari, nan ya ce wainar
ƙwai da dafaffan ƙwai sai a biredi da shayi me kauri. Mai Gari sai da gabansa ya faɗi, jin
abubuwan da ya zana, sai dai har da wasu sunayen abubuwan larabci da shi kansa Sheik bai
san mene ne ba, ya zayyana sai da Mai Garin ya ce vasu san abubuwan ba sannan Sheik ya
ce a barsu dama abincin su ne na ƙasar larabawa.
Bayan samarin sun gama gyaran suka tafi da su Mai Gari. Lokacin ya saka jallabiya, ya ce zai
yi wanka, suna tafiya ya gabansa yana faɗuwa, amma haka ya je ya garƙama sakata ya ɗauki
ruwa ya tuɓi ya yi wanka a tsakar gidan, don ba zai iya komawa banɗakin a lokacin ba. Yana
gamawa ya buɗe ƙofar gidan saboda masu kawo abincin don an ce masa mutane za su fara
zuwa neman magani yanzu gidan zai cika maƙil in ya gama cin abinci.
Juyowar da zai yi ya yi arangama da wani ƙaton hanci yashe a tsakar gidan, amma girman
hancin ya yi kan mutum da gudu Sheik ya doshi ɗaki towel a hannu don da ya kunce gani ya yi
bashi ma da nutsuwar tsayawa ya ɗaura.
Yana shiga ɗakin ya banke ya jingina da jikin ƙofar yana mayar da numfashi, a fili ya ce
"Ko a ni ko a ku aljannun garin nan, wato kun ga ana girmamani hassada da tsana suke
damunku, yadda zan ke shan ganimar girki, da kuɗaɗen magani ana biyana yasin babu inda
zan gudu, ba hanci da kunne ba kai ko karo zan ke ci da mafitsara kuna jefowa aradu sai dai na
gudu ɗaki amma dai arziƙi sai na dagwala a garin Ƙundu" Ya faɗa yana ƙarasawa ya zauna, ya
shiga shafa mayukansa, sai da ya gama tsaf a saka kayansa ya samu turarukansa masu
ƙamshi ya shafa saboda su kashe warin mayukan bilicin yake yawan amfani da turaruka.
Yana gamawa ya kabbara sallah, sai lokacin ne ya yi sallar asuba, a lokacin kuma Audu yake
rafka sallama, gyaran murya ya yi, sai da ya sallame sanann ya amsa, amma da ya leƙo bai ga
hancin nan ba, haka ya buɗewa Audu ɗakin ya ajiye masa kayan abincin bayan ya gaishe da
shi, ya nuna masa kwanukan jiya ya ɗauka, har ya jiya zai tafi Sheik ya ce
"Mu manyan malamai ba a gutsure mana cinyar kaza ko wani sashe na jikinta, yadda aka ba
mutum saƙo ya ji tsoron Allah ya kawo daidai" Da rashin fahimta Audu ya kalle shi amma sai ya
ce
"Malam ban gane ba"
Sheik ya ce
"Jiya kazar nan da ka kawo bata da cinya ɗaya" Mamaki ne ya kashe Audu jin wai shi da aka
bashi abu har lissafawa ya yi, hakan ya sa ya ce
"Wallahi ni ban ɗauka ba, sai dai ko a gidan Mai Garin ne da aka dafa suka ɗauka suka rabawa
yara" Maganar Audu ta nunawa Sheik asalin gaskiya ya faɗa masa, don haka sai yayarda ya ce
ya tafi.
Tun da ya buɗe kwanukan ƙamshin wainar ƙwai ya cika ɗaki, ya cinye tass ya sha shayin
bayan ya saki gatsa ya ce
"Bari in yi shiri na san yanzun nan masu buƙatar magani za su fara zuwa, ni ko buhun hatsi ma
zan ce Mai Gari ya bayar a kawo min? Saboda in ke zuba kuɗin sadakar magungunan da zan
ke bayarwa" Ya faɗa a fili yana ciro hular kansa ya shiga taje ta da brush kumb ta kwanta sosai
ya ɗauko wani mai me sheƙi ya shafa a take ta shiga walwali. Ajiyewa ya yi a gefe ya buɗe inda
kuɗinsa yake ragowar kuɗin saniya, ya shiga ƙirgawa, yana cikin hakan sai ya ji tashi hayaniya
an shigo gidan, sai ya ji ana masa wani kira kamar na ƴan farauta ana cewa
"Sheik ka fito gari babu lafiya, aljannun mai farfaɗiya sun tashi, ƙartai goma aka tara suka riƙe ta
amma ta watsar da su" Gaban Sheik ne ya harba da ƙarfi wai me farfaɗiya, kuma ƙartai goma ta
watsar kenan yanzu shi kuma in zai mata maganin ya zai yi?.
Bai yi magana ba kuma dama ɗakin nasa a rufe, sai ya ji wani ya shigo yana cewa
"Innalillahi wallahi matar nan mai farfaɗiya ta ɗaga Mai Gari da hannu ɗaya hannunta na dama,
hannun hagun ɗin ta ɗaga Malam Liman, Sheik ka fito da gaggawa ,a ta hau saman kukar
bulukiya da su" Gabaɗaya idanun Sheik sun ciko da ƙwalla, hankalinsa ya tashi gabansa ya hau
dukan uku-uku. Dakyar ya yi ƙarfin halin faɗin
"Ya subhanallahi, mai farfaɗiya a yi haka kuma, ki ɗaga Mai Gari da Malam Liman, jama'a gani
nan zuwa" Ya faɗa yana zufa, sai dai abin da ya bashi mamaki wanann hular tasa wacce ita ce
rufin asirinsa, wacce ya cire ya taje gashin ya ajiye a gefe yana lissafin kuɗi, babu ita babu
dalilinta, wato hula dai mai gashi da gemo da saje ta yi ƙafa don bai ganta ba.
Hankali a tashe ya kai hannunsa biyu saman kansa yana shafo tsakiyar kansa zuwa fuskarsa,
hankali tashe, jin ya shafo ƙwal kwabon kansa da kuma fuskarsa da babu saje babu gemu lallai
yau akwai cakwakiya, ya ake so ya yi wajen fita zuwa ruƙiyyar.
Wani ƙaramin mudubi ya ɗakko a jakarsa ya duba fuskarsa yana ganin tabbas idan ya kuskura
aka ganshi a haka ya kaɗe har ganyensa, don za a gano ba balarabe ba ne.
Wani mai ƙarfin hali ne ya takarkare ya ce
"Sheik ka fito su Liman rai a hannun Allah, tana hawa kukar nan ɓacewa za ta yi, don idan
aljannu suka ɗauke ta sai ta yi wata biyu ma ba a ganta ba" Ya faɗa a ruɗe ganin Sheik bai fito
ba.
Wannan furucin ya sake sanya shi diriricewa yana ƙara shafa sallallan kansa ya ce
"Gani nan zuwa ai ƙaryarta ta sha ƙarya"
*Mu haɗu a gaba don jin ya SHEIK zai yi wajen fitowa babu hula, shin ina hular tashi? Ko
dai aljannun ne suka saci don su ga ƙarshen ƙarya?*
Yanzu muka fara ku dai ku biyo ni don jin ya za ta kaya✍️
MAMAN AFRAH
09025576222
*Dan Allah masoya ina neman alfarmar addu,arku gareni da bakunanku masu albarka, Allah
kaɗai ya san bakin wani, ina nema domin Allah🤲 ko a zuciya ne ki mini addu'a NGD sosai ana
tare😍* 🤝
[7/4, 4:00 PM] Mom mashkr & Afrah: https://chat.whatsapp.com/EBurrU2vz6OFGbE37xLhPS
👳🏻♂️ *MALAMIN BOGI*👳🏻♂️
NA
MAMAN AFRAH
First Class Writer's Asso.📝
Daga marubuciyar:
Ƙazamin miji
Bonono Rufin ƙofa...
Ruɓaɓɓiyar igiya
Ƴar zaman wanka
Ƙara'in inna delu
Beelal
Ƴan adaidaita sahu
Ungozoma
Jalli joga
Da sauran su.
*09025576222*
BOOK1️⃣
PAGE 5
*ƘAUYEN MAI MANGWARO*
A fadar Mai Gari dakyar aka dakatar da Jummau daga kukan da take tana ta faɗar cewa yau
sai an biya ta saniyar marayu. Ita ma Lami tana faɗin sai Jummai ta biya ta kuɗin adashen ta,
tun da ita ma saniyar ba ita ta siyar ba don haka sai dai ta biya ta kuɗinta in ya so idan Ibra ya
kawo kuɗin sai ya bata, sai dai Mai Gari ya tsawar musu sannan suka yi shiru.
Isowar Kakar Ibra Inna Tasallah fadar Mai Garin na Mai Mangwaro tana sakin ɗan kuka tana
face hanci shi ya dakatar da kowa aka ɗago ana zuba mata na mujiya, wuri ta samu ta zauna
har lokacin tana ɗan matse hawaye ita takaicin ta ɗaya jarin kayan miyar nan idan ta bayar ina
za ta samu?
Mai Gari ne ya yi gyaran murya ya fara magana kamar haka yana mai cewa
"Tasallah shin kin san kiran da na aika aka miki?" A maimakon ta bashi amsa sai ta ƙara gudub
kukan nata, kasaƙe ya yi yana kallon ta, sai da ta ɗan tsagaita kukan ta ce
"Yo na sani mana Mai Gari, ai Idrisu da ya je ya kwashe komai ya faɗa mini, to zuwa wajenka
kuwa ai ya zame mini farillah tusa a masallaci, in da sabo na saba a kawo ni ƙara wajenka, yau
a ce Ibra ya cinyewa yarinya me tallah ƙosai, gobe a ce ya warci sandar rake a dandali, har ta
kai ya fara kame kajin mutane yana yankewa ya cinye, yau kuma saniya sukutum ya gudu da
ita wallahi albasa bata yi halin ruwa ba"Ta faɗa tana rungume robar kayab miyar ta tamkar wani
ya ce zai ƙwace.
Jummai ce ta yi tsoma baki ta ce
"Wallahi in har ya saba cin ƙasa ya kiyayi ta shuri, in har tun yana ƙarami yana wartar kayan
jama,a ana ƙyalewa kawo samartakarsa, to yau ya taɓo gidan rina don ko sama da ƙasa za su
haɗe sai kin biyani saniyata" Haɓa Inna ta dafe ta ce
"Haba Jummai kema kin san alamar ƙarfi tana ga mai ƙiba, in ba tada zaune tsaye ba, ni yanzu
a kan kuɗin ƙafar kaza ma sai a harbe ni, bare wata saniya, ni ban ci nanin ai nanin bata ci ni ba
ko?" Ƙirji Jummai ta buga tana hayayyaƙowa Inna kamar ta kai mata duka ta ce
"Ai dama ɗan kuka shi yake jawa uwarsa jifa, nima dai kayan marayu ne, don Inna ko kan ki za
ki kai kasuwa a yi cinikin ki masu yankan kai su saye ki yasin sai kin siyar kin biyani kuɗin
saniya" Da wani kuka mai jiniya Inna ta fashe jin ana batun ta sayarwa ƴan yankan kai kanta ta
biya kuɗin saniya, Mai Gari ne a fusace ya ce
"Wai shin ni zan yi hukunci ko kuwa ku za ku yi, idan har ku za ku yi babu amfanin zuwanku,
kuma nima babu amfanin zumana a wajen nan" Mutanen fadar Mai Gari suka haɗa baki wajen
faɗin
"Wannan gaskiya ne ranka ya daɗe, Allah ja zamaninka mai gudumar dukan talauci" Wani zama
ya gyara yana gyara babbar rigarsa, don maganar da ya yi ba iya su Inna ya katsewa hanzari
be har da Lami da ta ƙunso nata maganganun amma sai ta ja bakinta ta ƙunshe.
Mai Gari ne ya shiga faɗin
"Tasallah yanzu magana tana hannunki amma dai kafin nan sai na fara da Jummai, ke Jummai
me ya sa kika cinyewa Lami kuɗi har dubu ɗari biyu?" Ƙeya Jummai ta sosa irin ta mararsa
gaskiya sai ta ce
"Tsautsayi zagin mahaifi" Wani kallo ya mata ya ce
"To in har cinye kuɗinta tsautsayu ne to ke ɗin ma ɗaukan saniyarki tsautsayi ne" Ɗagowa ta yi
tana kallonsa da sakakken baki, sai kuma ta kalli Lami da take aika mata harara kamar idanunta
za su faɗo.
Bai jira cewarta ba ya ce
"Kowa
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 4 Chapter of 14