Share this page
miyana sun ƙare duka don cikin ribar na ɗauki naira talatin na saya mangwaro in sha a ruwan raina shi ma sai ya zama ana mini baƙinciki, mutane bakwa so ku ga mutum duniya tana gara masa, wato kun fi so ake zaman kashe wando... Wata harara Lami ta aikawa Inna ta ce "Inna tsakani da Allah ko ana yi wa wani baƙinciki wa zai miki, ni wallahi a sana'ar kalwa da barkono da kuka ban ga abin baƙinciki ba" Kamar Lami ta yi saɓo haka Inna ta zaro ido ta ce "Kina wasa da maƙiyi, maƙiyi ai shi ko alawa kake siyarwa sai ya maka baƙinciki, yanzu ni a wajena ai cigaba na samu tun da gashi a cikin ribar har ina shan mangwaro" Ta faɗa tana gutsuro fatar mangwaro, Lami a zuciyarta ta ce 'Yanzu zan rikita miki lissafi, yanzu za ki kiɗime don na tabbatar baki san da abin da nake tafe' A fili kuma sai ta ce "Inna saƙon kira ne aka bani wajenki" Sai da ta suɗi mangwaron ta ce "Kai zaƙu har cikib kaina wallahi, wannan mangwaro da zan samu iri ai da na shuka, to ke waye yake kirana in ka ji kira ai samu ne" Baki Lami ta damƙe cikin dakewar murya ta ce ",Inna, ina ce dai kina sane yau kwana ukun da Mai Gari ya ɗauka a kan maganar saniyar da Ibra ya tafi da ita" Tari ne ya sarƙe Inna jin wata gagarumar matsala sabod ita kwata-kwatanta manta don maganar ta kwanta mata , sanadin tarin da ta yi mangwaron hannunta ya suɓuce ya faɗi a ƙasa amma ko ta kansa bata bi ba ta ce "Lami waye ya faɗa miki wannan magana, yanzu haka ma Mai Gari ya manta da zancen nan amma saboda ke ce mai tada zaune tsaye kika je kika tado da maganar ko?" Lami ta ce ",To ba ni ɗin ba ce, Jummai ce tun da sanyjn safiya ta je faɗawa Mai Gari cewa kwana uku sun cika amma Ibra bai dawo gari ba, to da ta je da safen Mai Gari ba ya nan sun yi asubanci sun je wani ƙauye gaisuwa, shi ne yanzu ta koma da yamma, tana can ma fadar Mai Gari cike maƙil da mutane, yanzu ma daga can aka aiko ni kiranki, saboda kowa ya hallara amma ban da ke" Idanun Inna suka yi rau-rau tana tunanin abin yi sai ta ji hankalin ta ya tashi domin ita ta manta da wannan maganar kwata-kwata ashe dai yau wa'adin kwanakin zai cika. Ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi ta ce "Kai jama'a ba dan na shiga ban ɗauka ba bata fitar da ɓarawo wallahi da babu abin da zai kai ni fadar Mai Gari, saboda bani da kuɗin saniya, ban ajiye ba " Lami ta ce "To Inna ni ina zan gane wannan yaren naki, Mai Gari za ki yi wa bayani" Banza ta yi da Lami ta wanke hannunta, ɗaki ta shiga ta haɗo kan kuɗin kayan miyan da ta sayar, akwatin ƙarfen ta ta buɗe tana zaune a gaban akwatin ta fito da atamfofi guda uku ɗinkakku, wanda a wanke suke tas sun sha linki takaicin ɗakko atamfofin take ji a ranta amma haka ta zuba a ledar Viva ta fito ta ɗakko wata samira irin ta ƴan da mai hawa huɗu duk sun yi lamba a jiki, ta ce Lami ta riƙe mata, ita kuma ta yafa gyalenta ta ɗauki ledar atamfofin ta rufe gidan suka kama hanya a ranta tana cewa 'Ba saniya ba ko giwa ce Ibra ya gudu da ita in na bada kayan nan ba zan ƙara komai ba' Ta faɗa tana kallon setin samirarta da yake kan Lami... MAMAN AFRAH 09025576222 [7/9, 3:38 PM] Mom mashkr & Afrah: https://chat.whatsapp.com/BcJ4LIJJQlfHRgfiJUnBJo?mode=r_c 👳🏻‍♂️ *MALAMIN BOGI*👳🏻‍♂️ NA MAMAN AFRAH First Class Writer's Asso.📝 Daga marubuciyar: Ƙazamin miji Bonono Rufin ƙofa... Ruɓaɓɓiyar igiya Ƴar zaman wanka Ƙara'in inna delu Beelal Ƴan adaidaita sahu Ungozoma Jalli joga Da sauran su. *09025576222* BOOK1️⃣ PAGE 9 *SHEIK* Jin kamar dai babu alamun wani da zai taho daga ƙofar gidan ya kawo masa ɗauki, wato ya tabbatar muryarsa bata isa waje ba, don haka yanzu kam matar ta cim masa ba zai iya ma bari ta cigaba da azabtar da shi ba, dakyar ya ƙwace kansa ta shiga binsa da gudu suna tsere a ɗakin bai ankara ba sai ya ji ya kama rigarsa daga baya a haka yake gudun tana jansa tana rinjayarsa kasancewarta ƙatuwa ta fishi ƙiba, sai ya zamana dakyar yake iya gudun kasancewar rigarsa jallabiya ce a zuciyarsa ya ce 'Ina ganin ikon Allah, in ban da maluntar nan da na ɗakko ta larabawa ina dalili mutum zai kafa fama kullum da doguwar jallabiya kana tafiya tana taɗe ka' Ya faɗa a daidai lokacin sun zo saitin ruwan da ya ajiye, wanda yake kwalfa yana ba mutane, ruwan ne suka ture ya zube, tsautsayi ya sa suka shiga ciki gabaɗaya Sheik ya yi gaba ya yi baya ji kake tim santsi ya kwashe shi ya faɗi, ya yi zaman ƴan bori a cikin ruwan ita ma tana ɗora ƙafarta sai ta zame ta tiƙu da ƙasa. A reran ta je ƙasa, ganin haka Sheik ya yi ta maza ya daure ya matso don ba ƙaramin buguwa mazaunansa suka yi da ledar ba, qulhuwallahu ahad ya shiga karanta mata yana tofa mata sai dai wannan karon ba tofi ƙarami yake yi ba tsabar bala'in da yake ganinsa a ciki, yawu kawai yake tofa mata ba kaɗan ba. Karkarwa ya ga jikinta yana yi kuma ya fahimci kamar jikinta ya yi sanyi alamar aljannun za su sake ta, da hanzari ya janyo hularsa ganin ta ɗan leƙo daga bireziyar da ta saka ta a ciki, bai sake bi ta kanta ba sai ya shiga suturta kansa wato ya saka hularsa da gemun, mukullin ya gani a inda ya faɗi daga hannunta ya ɗauka ya buɗe ƙofar yana mayar da numfashin wuya, jin maganar wani mutum yana rafka sallama sai Sheik ya ɗauki wata ƙatuwar bulala da take ajiye ya ɗaga ya tsulawa matar nan da ƙarfi ta ce "Zan fita" Gabansa ne ya faɗi sai yanzu ya fahimci ashe aljannun basu saka ta ba, sai ya ji mutumin nan na waje yana cewa "Ah ashe dai ruƙiyya ake yi wa matar nan, shi ya sa ta daɗe ta bar mutane a layi ana jiran fitowarta, bari in fita in faɗawa jama'a halin da ake ciki" Ta haka Sheik ya fahimci cewa mutumin da ya shigo ya zo ne ya ga dalilin daɗewar matar. Can kusa da katifar ya koma yana raɓe, har sai da ya ga matar rana sakin atishawa wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke ganin yana sha n wahala a maluntar nan ta BOGI amma ƙarfin hali da sa kai wanda ya fi wauta ciwo ya hana shi barin maluntar bogin. Duk da ya san yana amfani da maluntar yana damfarar jama'a bayan ya san shi jahili ne babu abin da ya sani, ko surorin qur'ani da yake karantawa izun ƙasa ne, tun lokacin yana zuwa makaranta kafin ya kangare da ya kangare kuwa ai makarantar ma ba ya zuwa. Ko karatun bokon ma ko secondary bai gama ba. Zaune ta tashi tana kalle -kalle ta ce "Waye ya kawo ni nan" Sheik ya ce "Magani aka miki maza tashi ki je gida, kike shan sauran ruwan alwalar la'asar da magriba, sauran aljannun kan naki za su kama gabansu" Shiru ta yi ba don ta gama fahimta ba, ta muskuta ta tashi tana ganin yadda duk ta jiƙe, fita ta yi Sheik a fili ya ce "Gwara in faɗa miki bogi ki tafi yo ina na ga nutsuwar baki magani ma ki je ki ƙara shaƙo ni, ni na rasa mai hular gashin nan nawa ta yi wa aljannu da mutane, duk abin jikina ba a kaiwa komai farmaki sai hula ta" Ya faɗa yana gyara zaman hular, yana tuno artabun da ya sha da aljannu suka ɗauke masa ranar nan. Dakatar sa masu shigowa ya yi, ya sauya jiƙaƙƙiyar rigarsa ya goge ruwan, a haka ya cigaba da karɓar mutane suna bashi kuɗin yana tarawa ransa fari ƙal yake ji idan ya kalli kuɗin nan yana zaune yake samu. Sai da ya gama da jama'a ya ce sai kuma gobe za a cigaba da karɓar mutane. Tun daga wannan rana Sheik ya zama limamin garin Ƙundu, shi yake jan sallah, sai dai waɗannan ƙananun surori na ƙasa su ne kullum yake jan sallar da su, idan yana jan sallah ya ƙara maƙe murya ya lanƙwasa sai ka ɗauka cewa a masallacin makka ne ake jan sallar amma dai a wajen mutanen Ƙundu, saboda su ne basu gama tantance asalin karatun balaraben mutum da kuma Sheik baƙar fata wanda mayuka da sabulai suka wanke masa fata. Idan za a yi sallah mutanen ƙauyen kafin Sheik ya zo masallaci sai masu manyan wayoyi adroid su zo su kunna recording su ajiye wayoyin, daga an yi sallah an idar, sai ka ga idan sun fita daga masallacin suna samun wuri su kunna, suke ji sai ka zo wucewa ka ga mutum ya duƙufa da earpiece a kunna sai dai ka ji yana faɗin "Allahu akbar, uhmmm, ma sha Allahi, Allah ƙara lafiya babban malamin ƙasar larabawa" Sai ya zamana hatta mata masu waya sai su ba mazajen su, wayar in za su je masallaci su ɗakko musu sallar Sheik. Wanann dalilin ne ya sa Mai Gari ya ce Sheik ya musu karatun qur'ani wanda za suke saurara a waya, na izu sittin irin wanda ake turawa na su Ahmad Sulaiman da yake Mai Gari yana da irin su a waya. A nan ne fa gizo yake saƙa, don Sheik ya san dai bai sauke qur'ani ba hakan ya sa ya ƙaƙalo ƙarya kamar yadda ya saba ya ce "Ai an fi so mutum yake sauraren abin da ya iya, wato tun da basu sauke qur'ani ba ba za suke saurara, na fi so kuke sauraren izufin ƙasa saboda kuke biyawa yadda za ku ƙara ƙwarewa a hadda" Ya faɗi haka don ganin ya tsira daga tarkon wannan, hakan sai ya sa Mai Gari ya gamsu Sheik ya musu rukodin ɗin iya surorin ƙasa da ya iya, suke saurare. Batun magani kuwa duk waɗan da Sheik ya ba magani sai suka zo suke godiya da saka albarka a cewarsu magani ya musu amfani, saboda Sheik yana zama ya yi wa'azi a kan cewa ba a ƙaryata malami ko a tuhume sa, hakan ya sa ko da mutum bai ga amfanin magani ba sai yaja bakinsa ya yi shiru, sannan ma dama duk abin da aka baka a matsayin magani in dai ka yarda cewa zai yi to ko ba maganin bane yana maka magani. Bare kuma Sheik da yawanci matan dama kissa ce yake faɗa musu, da kyautatawa mijin kuma ko wanda ya ce mata suna gudunsa saboda muninsa da ya je ya yi abin da Malam ya ce na bayar da kuɗi ga budurwa sai gashi ya samu mai son sa har an ɗaura aure, hakan ya sa kowa ya ƙara yarda da maganin Malam. Sanann masu aljannu yana cewa suke karanta nas da falaƙi kullum wanann ya sa suke samun kariya tun da sun yi amfani da ayar qur'ani, idan kuma aljannun wanda ya fitarwa suka aara tashi, sai ya ce dama ciwo na ɗaya rana ne sauƙi sai a hankali. Duniya ta yi wa Sheik daɗi yana cin karensa babu babbaka, gabaɗaya ya ƙara ƙiba saboda cin kayan daɗin da yake, duk da cewa yanzu Mai Gari yana sanyawa a masallaci ana haɗa sadaka to da su yake amfani wani lokacin ana ciyar da Sheik, sannan wasu ma suna kawo gudunmuwar kaji, wasu zabbi wasu ma dama idan daga rugar da suke maƙotaka da Ƙundun za su zo magani da kaji da nono suke zuwa a matsayin abin sadaka. Wata rana ana zaune Sheik yana faɗakarwa, Liman sai muzurai yake don shi yanzu bashi da maƙiyi sama da Sheik, tun da an ƙwace masa Limancinsa wanda tun yana saurayi yake yi. Duk da a ganin Liman ɗin Sheik ya fishi ilimi kuma yana karatu irin nasu na larabawa amma dai duk da haka yana jin haushi. Wani ne ya ɗaya hannu ya ce "Ya Sheik ni ina so a fassara min Assalamu alaikum, kuma a fassara mini karatun cikin suratul fatiha wacce ake karantawa a kowacce sallah, ina so in san me yasa a kowace sallah sai an karanta ta?" Ƙululuuuu cikin Sheik ya bada wani sauti a hankali ba tare da kowa ya ji ba. A zuciyarsa ya ce 'Na shiga uku yau an ƙure ni?' A fili kuma sai ya ce "Ma sha Allah, su'alun mai kyau" Ya faɗa yana ɗan lashe baki. Gabaɗaya waje ya kaure da cewa "Yawwa ni ma ina so in sani" Kowa sai ya ce yana son ya sani har Mai Gari. Da gangan Shei ya tsiri wani tari yake yi ba ƙaƙƙautawa daga tarin ya lafa sai ya ce "Ma sha Allah ya ikwan... Sai kuma ya sake fara tarin alamar tarin ba zai bar shi ya yi magana ba, nan aka shiga masa sannu aka kawo masa ruwa amma ya ƙi dainawa saboda dama da gangan yake tarin saboda bai san amsar da zai bayar ba. Ganin haka sai Mai Gari ya ce Sheik ya je gida ya huta, daga haka maganar fassarar ta sha ruwa. Wata rana da daddare Sheik ya fita daga gida ya saci hanya, gidan wani matashi da yake babu nisa da inda aka sauke shi ya je, ƙogar gidan ko kara ta ba a yi ba kasancewar sairayin yana shaye-shaye idan ya dawo daga yawonsa a buge sai ya shiga ya kwanta. Can Sheik ya shiga ya ga sausayin kwance a tsakar gida a ƙasa yana bacci. Machine ɗin saurayin ya ɗauka ya fito daga gidan, sai da ya ɗan tura machine ɗin ya wuce gidan saurayin, ya tada mashin ɗin dama ko mukulli ba a sakawa mashin ɗin a hakanake tashin sa. Hawa ya yi ya tafi ƙauyen da malamin wanda Sheik yake karɓar maganin da yake ba mutane, ya same shi ya bashi kuɗi mai yawa daga kuɗin da yake samu, nan malamin ya bashi magungunan amma Sheik ya ce maganin matsalolin mata ya fi yawa saboda sun fi zuwa da matsaloli. Ya bashi kuɗin mayukansa da sabulai da turaren oud da sunayen su a rubuce ya ce zai dawo ya karɓa, dama malamin yana zuwa birmi. Bayan ya karɓo ya dawo gidan saurayin ya akiye mashin, ya tafi gidansa. Yau ta kama laraba misalin ƙarfe goma Sheik yana zaune a ɗakinsa yana karantar ƙamus mai larabci da hausa, yana ta haddar kalmomin larabci don ya haddace saboda sakowa a magana, duk da cewa ya san ko kwaɓa larabcin ma ya yi ba ganewa suke yi ba, Allah ma da ya taimake shi rubutun larabcin akwai inda aka yi fassarar hausar larabci. Shigowar mutane ya ji zaure gidan suna rafka sallama kamar dai ma a kiɗime suke, da sauri ya mayar da littafin ya tashi ya hau sallaya, jin suna ta cigaba da sallamar sai ya shiga jan gyaran murya alamar baya rabuwa da bauta da ibadad kowane lokaci. Jin suna ɗan surutai sai ya saurara ya ji suna cewa "Ai shikenan kuma matsalolin Ƙundu sun fara dawowa, har muna murya an maganace ashe dai da sauran rina a kaba" Didimmm ƙirjinsa ya buga, kafin wani yinƙuri sai ya ji muryar Mai Gari alamar shi ma ya shigo yanzu, ya ji Mai Gari cikin karkarwar murya yana cewa "Kabarin Hashimu da na wa hallaw?" Sheik ya ji wani ya ce "Da kabarin Fatsime" Gabaɗaya Mai Gari ya kwashi salati. Zufa ce ta fara ketowa Sheik jin ana maganar kabari shi dai duk da bai fahimci kurman baƙin ba amma dai ya san shi ne a cikin matsala tabbas. Haka ya koma ya zauna daɓas sai da ya ji ya ɗan samu ƴar nutsuwa sannan ya buɗe baki ya ce "Bismillah a shigo" Ya faɗa yana janyo dogon carbinsa mai dubu ya fara ja yana mismis da baki tsabar rikicewar da ya yi shi kansa bai san abin da yake faɗa ba. Su duka suka ɗoro ɗakin Mai Gari ne a kan gaba sai wasu mutum huɗu a bayansa. Mai Gari yana baza malun-malun ya zauna amma kana ganinsa ka san babu lafiya, yana zama ya ce "Barka dai Ya Sheik" Sheik sai da ya yi yaƙi da idanunsa wajen ganin basu bayyana taoron da yake ciki ba tsumu-tsumu don shi a duniya in dai maganar aljannu ne da maganar mutuwa to ya ƙi jinin maganar nan, ko kabarin mai Ƙusumbi da yake zaune a gidan da shi saboda, kar ya bayar da kansa a ga gazawarsa, don dai ba yadda zai iya kuma yana son samun kuɗi ba ya so ya bar garin wato ya bar cima mai daɗi da kuma samun kuɗi, shi ya sa yake wanann siyar da rai, to in ba siyar da rai yake yi ba kake tunkarar aljannu kai tsaye, bayan shi ƙasurgumin jahili ne ya shiga MALUNTAR BOGI. Amsawa Sheik ya yi yana ɗan washe bakin dole, duk gumi ya wanke masa goshi, saboda lura da ya yi da sauran mutanen nan su a tsugunne suke basu zauna ba, hakan duk yana nuni da ana cikin ruɗu da masifa. Mai Gari ya ce "Ya Sheik abu ne na gaggawa, garin Ƙundu babu lafiya, wannan ƙaiyen da muke maƙotaka da su ne maƙabartar su ta cika, to shi ne idan aka yi rasuwa sai su kawo maƙabartar garin nan su binne, yanzu wani yaro ne ya mutu a garin sun zo ya za su binne shi aka samu gawa biyu an tono su daga kabari, kuma an ce masu haƙar kabari da suka zo suka tona kabarin da za a binne yaron lokacin da suka gama kabarurrukan da aka tone lafiya lau ba a tone suke ba, sai yanzu da suka zo suka tarar da hakan, kuma sun ce ɗaya gawar da aka tone ta yi motsi bayan ta shekara nawa a binne, yanzu dai sun bar gawar yaron a maƙabartar kowa ya gudu" Mai Gari ya faɗa yana ɗago kai ya kalli Sheik. Tun da Mai Gari yake bayani ƙirjin Sheik yake fat-fat-fat, ya yi wani tsumu-tsumu tamkar an tsamo ɓera daga ruwa, dama sunkuyar da kansa ya yi idanunsa suna kallon ƙasa don kar su fallasa asirin zuciyarsa na tsoron da ya ji ya kunyata. Sheik ya ɗago da kansa idanunsa tamkar wanda aka tada daga baccin sa yake mafarkin tsoro, ya yi wujiga-wujiga, ruwan da yake gefensa a kwano ya ɗauka ya kurɓa, bayan ya ce musu da sai ruwan roba da na leda yake sha, ajiye kwanon ya yi ya ɗago carbinsa yana ja tsabar ya ruɗe ma ba ɗaɗɗaya yake jan carbin ba, wani lokacin ƴaƴa goma wani lokacin biyar kawai ja yake babu ƙaƙƙautawa, sai da ya ji zuciyarsa ta daina bugun da in ya yi magana za a harbo jirginsa na tsoro ya yi ta maza ya ce "Subhanallahi, subhanallahi, subhanallahi, wannan aikin aljannun garin ne yanzu abin har ya kai a tono gawa a kabari kai abin ya girmama, yanzu ya za a yi?" Ya tambaya har lokacin tamker ana fisgo maganganun daga bakinsa. Ɗaya daga cikin mutanen ne ya ce "Ya Sheik yanzu dai ka yi gaggawar zuwa maƙabartar nan ka rufe kaburburan da aka tone, gudun kar a yi bori da sanyin jiki su cigaba da tone sauran kaburburan maƙabar nan, tun da hatta yaron nan da ya mutu yana nan ajiye a makara ba a binne shi ba, an bar sabuwar gawa ajiye a maƙabarta" Nannnauyar ajiyar zuciya ya sauke wacce ta kasa ɓoyuwa a ɗakin ya ce "Tabbas wannan iblisan aljannu ne, da ifiritai" Mai Gari ne ya zaro ido duk da yana ganin za a magance matsalar garin amma jin wannan sunaye na aljannu ya ƙara rikita shi ya ce "Yanzu waɗanann aljannu ya za ka yi ka fitar da su daga garin nan, bayan ƙauyen ya yi lafiya amma kuma yanzu za su dawo mana da hannun agogo baya" Sheik ya ce "Kar ku damu, na taho daga ƙasarmu ne don in kawo ɗauki ga mutane masu neman taimako babu gudu babu ja da baya" Ya faɗa yana miƙewa tsaye, ganin haka sai suka fita suka bar shi, gabaɗaya ji yake kamar ya rufe ido ya gan shi a garinsu MAI MANGWARO ji yake kamar dai ya bi wata hanyar ya bar garin ba tare da sanin kowa ba, sai dai wata zuciyar tana tuna masa irin badaƙalar da ya baro a garinsu, da basussukan da ake binsa kuma dai bai akiye ba bai bayar ba ajiya, ya san tabbas in ya koma zaman banza ne zai cigaba da yi, amma tun da ya samu sana'a a nan dole ya jajirce. Ruɗin da yake ciki ya sa bai rataya hiramin a wuyansa ba kamar yadda yake saƙalawa, yau sai ya masa naɗin gwaggwaro, daga gaban goshin ma naɗin ya ɗan zamo ya karkace sai ya yi tamkar tsohuwa, ya ya ɗauki zumuƙeƙen carbinsa, ya ɗauki littafinsa na ƙamus, sai wani ruwan magani da ya karɓo cikin magungunan da ya siyoa wajen malaminsa, shi tsabar ruɗani ma ya manta ko ruwan maganin mene ne. Yana fitowa ƙofar ɗaki ya ga saka takalminsa ya ga su Mai Gari tsaye suna jiransa, fitowarsa ke da wuya duk da ruɗun da suke ciki sai suka fara magana cikin girmamawa. "Allah ya taimaki balaraben Malamin, Allah ƙara ilimi, haƙiƙa mun samu jajirracce da yau sai dai kowa ya yi hijira daga garin nan don ba za mu iya da wanann aljannun ba" Sheik a zuciyarsa ya ce 'Kwa mini kirari mana tun da kun haɗani da aikin tsohuwar gawa da sabuwa, yau ai sai ta Allah' Ya faɗa yana yin yaƙe tare da ƙara ƙanƙame littafinsa a ƙirjinsa yana jan carbin haka suka fito daga gidan bayan ya kulle ƙofar. Abin da basu sani ba shi ne, Sheik ya fi su shiga ruɗani da tashin hankali. Tun da suka fito tsakiyar garin maza suka fara tururuwa don sai lokacin, suka ji ƙarfin gwiwar fitowa tun da Sheik ya fito gani suke aljannu ba za su fafata da Sheik ba ko su ja da shi. Sheik ne a gaba mutane gari suna take masa baya, sai wani bada faɗi yake shi ala dole masanin qur'ani da addu'o'i, ana cikin tafiya, sai lokacin ya kalli ƙafarsa, idanu ya zaro ganin takalman ƙafarsa gamin bauta ne, wato takalmin ƙafar dama takalminsa ne sandal amma kuma na ƙafar hagun ne ba wai na ƙafar dama bane, don haka a juye yake, shi kuma takalmin ƙafar hagun ɗin silifas ne na wankansa, amma kuma ƙafar dama ne a hagun ɗin wato dai shi ma a juye yake a zuciyarsa ya ce 'Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, mutanen garin nan kun saka ni a masifa, da tashin hankali tun da uwata ta haife ni ban taɓa wannan gamin bautar takalmin ba, amma yau saboda kun jefani a ruɗani gashi nan, takalmin kwalliya da na wanka na saka, su ɗin ma kowanne ba ƙafar ba ce' MAMAN AFRAH 09025576222 [7/10, 4:03 PM] Mom mashkr & Afrah: https://chat.whatsapp.com/BcJ4LIJJQlfHRgfiJUnBJo?mode=r_c 👳🏻‍♂️ *MALAMIN BOGI*👳🏻‍♂️ NA MAMAN AFRAH First Class Writer's Asso.📝 Daga marubuciyar: Ƙazamin miji Bonono Rufin ƙofa... Ruɓaɓɓiyar igiya Ƴar zaman wanka Ƙara'in inna delu Beelal Ƴan adaidaita sahu Ungozoma Jalli joga Da sauran su. *09025576222* BOOK1️⃣ PAGE 10 *MAƘABARTA* Tun da Sheik ya lura da takalminsa sai ya wayince ya je kusa da Mai Gari ya masa raɗa cewar garin saurin ya zo ya ceci gari ya sako takalmi ba iri ɗaya ba, Mai Gari ya ce "Allahu akbar! Tabbas Sheik kana ƙaunar garin nan" Nan ya nuna masa babu komai ruɗun da jama'a suke ciki ma ba zai bari su lura da takalmin ba, kuma ko sun lura ma sai a musu bayani. Wannan bayanin ne ya sa Sheik ya ji daɗi tun da ya lura yanzu dai ba za a zargi cewa tsabar ruɗani ne ya sa ya sako takalmi gamin bauta ba daidai ba. Tun da suka zo dab da maƙabarta Sheik gabansa ya fi na kowa faɗuwa, amma a haka ya daure yake jan carbi, da yake maƙabartar ƙauyen ba a kewaye take ba, sai dai akwai bishiyoyi da suka mata ƙawanya, sannan akwai hanyar da aka ware don ake shiga ta wajen. Gabaɗaya jama'ar sai suka yi turus kowanne yana tsoron shiga, Sheik ne a kan gaba sannan suka mara masa baya. Suna shiga jikinsa yana karkarwa amma sai ya maje ya nuna ba karkarwa jikin nasa yake ba, mutane gabaɗaya suka tsaya suna jiran su ba abin da zai faruwa, kowa yana gefe. Ƙarasawa ya yi gaban kabarin guda biyu gabansa yana faɗuwa, kallon ɗaya da aka tono ya yi, wani yawu ya haɗiye muƙut ya juya ya kalli Mai Gari ya duk kamar a ce asss su zura da gudu, ɗan wayincewa ya yi ya ce "Babu tsoron Allah a wannan lamari, a ce a tone gawa tsohuwa da sabuwa, kai Allahumma ajirni min wannan mummunan aiki, ya subhanallah," Ya faɗa yana girgiza kai irin na malamin da ya ga an yi wani aiki marar kyau. Wani ne daga cikin tawagar mutanen ya ce "Ni fa a hanya na haɗu da masu binne yaron can, na ji suna cewa wai ji suka yi yaron ya saki kuka shi ne aka rasa mai tsayawa a cikin su... Kafin saurayin ya gama magana Sheik ya kai hannunsa mai carbi ya sharce gumi, ya ce "Alkazibu, ƙarya haramun, babu gawar da za ta yi kuka" Duka wurin babu wanda ya tona don shi Sheik sani ne bai yi ba kafin ya zo garin wataran tsakiyar dare ake jin ƙaran turmi ana daka a cikin maƙabartar ko dai a ji ƙaran injin markaɗe, abubuwa dai barkatai. Mai Gari ya kalli Sheik ya ce "Ya Sheik ko da matsala

Chapter 8 of 14