dameni ba amma tabbas ina jin ba daɗi.
Har yamma ina ta faman tunani, da kuma tsoron me Sardauna zai dawo da shi, zai sami matar ne ko sai gobe?
"Ya Allah ka sa wannan auren ya zama ƙarshen duk wata wahala, da wani tashin hankali."
Knocking na ji ana yi min, na tashi a raina ina addu'ar Allah Ya sa Bilkisu ce, sai ina buɗewa na ga Turaki.
"Ina wuni?"
"Lafiya ƙalau Nana."
Ya faɗa yana kallona, ganin shirun ya yi yawa na ce.
"Bayan nan."
"Nana komai lafiya a gidanki?"
"Lafiya ƙalau."
"Kinje wajensu Hajiya?"
"Na je."
"Amma Ra'is ya ce kin fi watanni baki je ba, me ya sa?"
"Ina zuwa."
"Nana yakamata kije ki yi magana da Hajiya, ki faɗa mata duk wata matsala da take damunki."
Yana faɗin haka ya juya ya shige ɓangarensa, haka na dawo ciki duk jikina babu daɗi, ni shikenan kullum rayuwata a babu daɗi, zaman ba daɗi, gidan ba daɗi, ni narasa wace irin rayuwar aure ma nake yi.
Waya ta na ɗauka na kira Hajiya, na yi sa'a kira ɗaya ta ɗauka. Bayan mun gaisa nake ce mata bani da lafiya ne kwana biyu.
"Me yake damunki?"
"Hajiya na yi ɓari ne."
"Allah Ya ƙara lafiya."
"Amin Hajiya, ya mutan gidan?"
"Nana kowa yana lafiya, Ra'is ya ce kun yu waya kwanaki, Nana duk wanda na ce ya zo gidanki sai ya ce bazai zo ba mijinki, sai da wancan ɗan Albarkan Turaki ya zo na yi masa magana, nasan yanzu ma shi ya yi miki magana ko?"
"Eyh Hajiya shine."
"Nana ki dinga addu'a kin ji."
"In sha Allah Hajiya."
*****
Wayar da na yi da Hajiya ta rage min wani abu daga cikin damuwar da nake ciki, yamma lis sai ga Bilkisu ta zo itama a kiɗime, al'amarin mahaifinta ya ta azzara akan auren da ya ce zai yi mata.
Itama gaba ɗaya ta yi wani sukuku, ta fita hayyacinta.
"Bilkisu to ke ki duba cikin masu zuwa wajenki mana."
Na faɗa dan dai nasan Bilkisu ba zata taɓa rasa masu zuwa wajenta ba, domin dai tana da kyanta yadda yakamata, ga ilimi kuma yar gayu ce sosai da sosai.
"Nana bazaki gane ba kwata kwata, duk masu zuwa wajena ba na aure ba ne, burinsu na basu haɗin kai su ɓarar mun da mutunci su cuceni."
"Ya salam, Allah Ya tsare ki."
"Amin amin, ku yanzu kun sami matsaya?"
"Eyh mun samu, aure kawai Sardauna zai ƙara kamar yadda suka umarta."
"Allah Sarki Nana gaskiyya kinyi namijin ƙoƙari Allah Ya baki haihuwar nan."
"Amin Bilkisu, Allah Ya kawo miki mafita."
Itama ta ce Amin, nan muka zauna kowa na jajantawa kowa har Sardauna ya dawo ya sameta, sai bayan ya dawo ta tafi.
A yanayin Sardauna na yau dai babu wata sabuwar matsalal, kuma na ji daɗin hakan sosai da sosai, haka washe gari ma babu wata matsalal. Al'amuran kamar sun sauƙaƙa wajen kwana biyar, sai ranar kwana na huɗu Sardauna ya dawo cikin tashin hankali, Hajiyarsa ta ce lallai lallai ya sake ni idan har bai fito da mata ba cikin kwana biyu, a kiɗime na ce.
"To baka ce musu kana dubawa ba ne?"
"Nana wa zan duba, har yanzu fa ban ga wata da na ji zan iya haɗa ta dake ba, Nana mata basu da kama ko kaɗan, bazan iya auren wacca zata hulaƙanta ki ba ko kaɗan Nana."
"Kar ka damu Sardauna, ni zan iya zama da kowace muddin kana nan kuma kana ganina a matsayin da kake ganina yanzu, Sardauna ka auri duk wacca ta yi maka."
"Nana anya kuwa kina kishi na?"
Kallonshi na yi, sannan na kalli ƙasa.
"Tayar maka da hankali shine kishi? Sardauna indai sai na ɗaga maka hankali na saka a damuwa bayan wacca kake ciki shine kishi to ni bana kishi, hasali ma babu zuciya a tare da ni, ina sonka a kowanne irin hali, zan ci gaba da sonka a kowanne irin yanayi Sardauna."
"Nana bana jin zan iya neman wacca zan aura, ina neman alfarma a wajenki guda ɗaya dan Allah."
Ya faɗa yan goge ƙwallar da take idonsa, bai bari na yi magana ba ya tsugguna a gabana, tare da riƙe min hannuna.
"Nana! Dan Allah, dan girman ma'aiki ki ta ya ni duba wacca zan aura, Nana kowa kika kawo indai kin aminta da ita to zan aura Nana, dan ke zan yi auren kuma ina so ki nema min waccan zan aura da kanki da hannunki Nana."
Wani irin nauyi na ji ya danne ni kamar an ɗauramin gungumen dutse. Tabbas wannan alfarmar da Sardauna ya nema a wajena da girma take, ta ina zan fara?
"Nana dan Allah, mutuncina da darajata duk suna hannunki a yanzu ki tallafa min Nana."
"Ka tashi zaune dan Allah."
"Nana ki yi min wannan alfarmar dan Allah."
"Tom na yi ka tashi zaune ka ji."
"Na gode Nana."
Ya faɗa tare da zama kan kujerar, ya ƙureni da ido sannan ya ce.
"Nana!"
"Na'am."
"Na ga kin rame kamar bakya cin abinci?"
Kallon jikina na yi, ni banga wata rama ba amma tabbas nasan a jikina ina jina falai falai kamar wata takarda.
"Nana kamar ba kya cikin ni'imar aure, matar Ta Ambo ce a haka Nana?"
"Ba wata rama da na yi fa, kawai strees ne."
"Name?"
"Abubuwan da suka dagule mana, komai ya rincaɓe."
"Nana ai komai yazo ƙarshe ko? Komai zai yu sauƙi tunda a yanzu za ayi auren kuma ai shikenan ko?"
"Eyh shikenan in sha Allah."
"Yawwa Nanaty, zan ci abinci."
Tashi na yi ma nufi wajen dinnig ɗin, shi kuma yana biye da ni a baya, alkubus da miyar taushe ne na yi, ya zauna ya ci sosai nima kuma ya matsamin sai na ce, yadda ya ci haka na ce. Ko majalisar ma baije ba ya kwashe ne muka yi ɗaki, duk ranar da Sardauna ya ɗaukeni da kansa ina shan wahala har nagane, shi ya sa bana so ya ɗaukeni nafi son mu tafi ƙafa da ƙafa.
Tun daga wannan lokaci Sardauna ya sani a wata duniyar ta daban, kullum aikina tunanin wace za ta da ce da Sardauna, dan ya zama dole na nema masa a ƙasa da kwana ukun da ya ambata. Ƙawayena Malaika ta yi aure tana kano, Fauziya ta yi aure, Amina Aminu ma ta yi aurenta daman su kenan, Yaya Radiya kuma Yayata ce babu aure a tsakaninsu, Anty Adiza kuma matar aure ce, ni kuma su kaɗai ne mutanen da nasani, sai dai ko Bilkisu ita kuma aure ne ba ta so a yanzu.
"Ni fa ina ganin can yaje danginsu ya nema, zai fi mana sauƙi."
Na faɗa a fili kamar ina magana da wani ko wata, ko da ya dawo ma baiyi min maganar ba kuma nima bance komai ba, washe gari ma haka na yi ta faman tunani, sai gab da yamma na shirya naje gidan kitso wanda daman na tambayeshi, tun zuwana unguwar gidan kitson kawai nake zuwa shima sai na yi wata nawa banje ba. A hanya na yi ya kallon 'yan mata ko akwai wacce za ta da ce da Sardauna, amma bansamu ba. Haka a gidan kitson ina zaune ina kallon mutane sai hira suke, a ɗauko gulmar waccan a sauke a ɗauki ta waccan har layi yazo kaina ni dai ban tanka musu ba.
"Baiwar Allah a wane gida kike?"
Wata mata ta tambayeni.
"Nan baya."
"Ina ne baya ko ba anan kike ba?"
Wata daban ta yi tambayar.
"Eyh ina Takur Site C ne."
"Eyh kam da dan nisa gaskiyya, amarya ce?"
"A'a na shekara biyu."
"Allah Sarki Allah Ya sanya alheri."
"Amin."
Na faɗa daga nan ban sake ce musu komai ba har aka gama yi min na tashi na tafi, a raina na ce.
"Ina fita zaku hau yi dani."
Illai kuwa ko ƙarasa fita ban yi ba na ji muryar wata ta ce.
"Wai ita matan Takur sai wani shan ƙamshi ake."
Murmushi na yi na ƙarasa ficewa ta, ba su san ɗimbin damuwar dake damuna ba ne shi ya sa ma suke wannan zancen.
Har na ƙaraso gidana ina kallon 'yan mata hanya sai dai Allah bai sa na ga wadda zata da ce da mijina ba, haka na dawo gida shiru. Nan dai na yanke shawarar tamnbayarshi na ji ko akwai wata yarinya da yake burgeshi haka, ko yake yawan ganinta.
Banyi masa maganar adawowarsa ta farko ba, sai da ya dawo daga Majalisa sannan na ce.
"Na yi tunani a iya matan da nasani, amma kafin nan kai babu wata yarinya da ka sani ko kake ganin tana da hankali."
"Nana bayan ke bansan kowa ba."
"Ko a wajen aikinku, ko a family?"
"Nana bayan ke bansan kowa ba."
"Ka na ji, ko a unguwarku da kuna ƙanana?"
"Nana unguwar da na taso ba irin Yalwawa ba ce, Unguwa ce da ba ruwan kowa da kowa, unguwa ce ta masu arziƙi babu talaka ko ɗaya a unguwar dan haka babu 'yar wanda nasani Nana, ba kamar ku ba cike da yara wani gidan na cin wani gidan, yara su shiga wancan gidan su fita wancan, mu duk ba haka muke ba."
A maganar sai na ji kamar gori, na yi mishi murmushin yaƙe sannan na ce.
"Ba haka nake nufi ba ranka ya daɗe, irin ko a makaranta haka?"
"Nana, zaki yi min ko bazaki yi ba? Idan bazaki yi ba just tell me, ba sai kina haɗani da ƙazamar rayuwa marar daraja ba, rayuwata ba irin wannan ba ce Nana. Ina ga har yanzu bakisan su waye Familyn mu ba Nana."
"Ka yi haƙuri, baka fahimce ni ba."
"A'a ba wani ban fahimce ki ba Nana."
"Ka yi haƙuri."
Ta shi ya yi ya shige ɗaki ba tare da ya ce dani ko ƙala ba. 'Oh ni yau me yake damun Sardauna ne?.' Na tambayi kaina a zuci.
Washe gari ma haka ya tashi yana faman cicin magani ko breakfast ma cewa ya yi wai ba zai ci ba.
"Dan Allah me ya faru?"
"Nana kinfi kowa sanin duk abinda ya faru."
"Bansan sani ba, bansan wani abu da ya faru wanda yasa ka canja baki ɗaya."
"Hhm! Nana sai na fito fili na faɗa miki cewar ki nemo min aure?"
"Ai akan wannan maganar muke kai kuma ina kan dubawa."
"Su wa kika duba?"
"Duk cikin ƙawayena kowacca ta yi aure."
"Duka babu marar aure kenan?"
"A na kusa dai babu, shi ya sa nake so kara faɗa tunanina don bincikawa."
"Nana yau ne fa ranar ta ƙarshe da Hajiya ta bani."
"Nasani kuma in sha Allah yau komai ƙare."
"Nana ki yi duk abinda kike tunanin zaki iya, dan Allah."
"In sha Allah, to muje ka yi breakfast ɗin."
Muka nufi dinning ɗin, muna cikin breakfast ɗin Sardauna ya ce.
"Nana! Ko zan samu ki wanken kayana ko guda biyu ne, na ji daɗin wancan da kika yi min."
'Ashe Sardauna ya kula na yi masa wanki? Amma ko a ido bai taɓa nuna min ba, ko da yake gashi yanzu ya faɗa.' Murmushi na yi masa sannan na ce.
"Babu damuwa, ko ban yi yau zanyi gobe."
"Me ya sa sai gobe."
"Idan ba mafita na samu akan wannan maganar ba bani da nutsuwar da zan iya yin wankin da zai burgeka ya yi maka kyau."
"To shikenan, Allah Ya yi miki albarka Nanaty."
"Amin amin."
Tin fitar Sardauna nake tunanin inda za a sami mafitar ƙarshe, kwatsam Bilkisu ta kirani a waya, bayan na ɗaga muka gaisa na ce da ita.
"Ya Abban naku?"
"Nana ya ƙaramin one week ɗazu, na ji daɗi sosai wallahi Nana zan duba yanzu duk wanda yazo zan bashi fuska."
"Ma sha Allah Bilkisu, Allah Ya kawo na gari."
"Amin Nana, na gode miki da nuna kulawa, zan je ofis mu yi magana anjima."
Bayan ta kashe wayar kawai tunanin haɗa ta da Sardauna ya faɗomin.
"Zaman Sardauna da Bilkisu zai yi ɗaya kuwa? Tsakanina da Bilkisu akwai fahimtar juna, akwai soyayya to amma Sardauna fa?"
Legendspen
08129553971.
*SARTSE*
-Amanar-Janafty-
*Sayyid Legendspen*
MAH/2026/001
Sadaukarwa.
RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA
(Mai Dambu)
Shafi na ashirin da biyu.
(22)
‘Sardauna baya son karatu? Bilkisu har aiki take yi, shin Bilkisu za ta iya barin aikinta sabida Sardauna, ko kuwa Sardauna zai iya haƙura ta yi aiki, ya ce kuma yana da kishi ba zai iya jurar matan shi na yawo a titi ba suna cakuɗuwa da maza, amma tabbas Bilkisu za ta dace da zamanmu a wannan ƙadamin, tun da itama mahaifinta ya bata lokaci kamar yadda Hajiyar Sardauna da Big Daddy suka ba shi?’
“To Nana hakan ba matsala?” Na ji wani ɓari na zuciyata ya faɗa a fili kamar wani daga wajene ya faɗa. ‘Sardauna yana sona, kuma Bilkisu tana sa ilimi zata zauna da ni da Sardauna lafiya, ni bani da wata matsala indai Sardauna na nan kuma yana kallona a matsayin mata ina ƙarƙashen inuwar aurensa.’
Waya ta na ɗauka na kira Bilkisu amma ba ta ɗauka ba, ƙila bata ƙarasa ofis ba sai kawai na tura mata text.
“Bilkisu dan Allah ki kirani, akwai mafitar da nake tunani wacca za ta kawo ƙarshen komai in sha Allah.”
Na tura mata tare da emoji na kuka da na roƙo, ina turawa na nemi lambar Yaya Rumaisa dan tabbas sai na sanar da wani nawa. Bugu ɗaya ta ɗauka tare da faɗin.
“Manya yau a gari?”
“Ina wuni Yaya?”
“Lafiya ƙalau Nana, ya gidan?”
“Alhamdullah Yaya, dan Allah wata magana zan faɗa miki amma bana son Hajiya ko wani ya sani.”
“Wace magana ce haka Nana?”
“Ki yi min alƙwari dan Allah.”
“Nana ya za ayi na yi alƙwari akan abinda bansani ba?”
“Dan Allah ki yi min, ba wani abu ba ne na cutarwa kawai labari zan baki.”
“Shikenan Nana na yi miki.”
Na sauke ajiyar zuciya sannan na ce.
“Zan ƙarawa Sardauna aure.”
“Bangane abinda kike nufi ba.”
“Yaya a gidansu aka bashi zaɓi guda biyu, tun da ni bana haihuwa mahaifata ba ta gama ƙwari ba ko ya sake ni su aura masa wata ko kuma ya ƙara aure.”
“Ke bana son rashin hankali, uban waye ya ce miki ba kya haihuwa?”
Ta faɗa cikin jarababbiyar muryarta.
“Munje asibiti sabida na yi ɓari har sau biyu, shine aka ce ba ta yi ƙwari ba.”
“To da zai sake auren shine ke zaki ƙara masa?”
“Yaya ya bani zaɓi ne akan na nema masa matar.”
“Wannan shine kuskure na biyu da zaki yi a rayuwarki da Sardauna, na farko kin zaɓi miji sama da kowa, sai da ya raba ki da ‘yan uwanki da duk wasu mutane a kusa dake shine zai ƙara aure? Nana wai uban me kike sha?”
“Yaya Umarni ne daga gida, shi ya sa ma ya bani damar zaɓa masa wadda zai aura.”
“Lallai Nana mahaukaciya ce ke? Dan mun yi alƙwarin bazamu sake shiga al’amuran gidanki ba, amma dai sai na zo har gidan na ci ubanki na ci uban mijin, banza marar hankali wace yarinyar kika zaɓa masa?”
“Wata maƙwafciyar mu ce.”
“Jaka! Nana bansan ki lalace ba sai yanzu.”
Tana faɗin haka ta katse kiranta, ni nama manta da halin faɗa irin na ta har na kira ta, gashi ta zageni ta zage mijin nawa gaba ɗaya, ita daman bata da haƙuri ba abinda ta iya sai faɗa a rayuwarta.
“Mitcheww.”
Na ja tsaki na kwanta akan kujera, banda rainin hankali irin Yaya Rumaisa mutumin da baya son auren ƙarshe ma yaban zaɓi shine za ta ce wai ya rabani da kowa shine zai ƙara aure. Duk sai da na yi danasanin kiranta, daman ita ba a fiya yin abun arziƙi a kwashe duka da ita ba, haka na yi ta faman ɓacin rai har yamma, yau indomie na yi wa Sardauna dan ba abinda zan iya sabida wani irin ciwon kai da na tashi dashi bayan na kwanta da yamma.
Fuskarsa babu yabo babu fallasa haka ya shigo cikin gidan.
“Sannu da zuwa.” Bai amsa ba ya ajiye jakarsa, yanayin da nake ji ma bazan iya tashi na bishi ba, yanda ya shiga ɗakin haka ya fito.
“Baki da lafiya ne?”
“Jiri nake ji.”
“Sannu, bama ki yi girki ba kenan?”
“Na yi.”
“Bari na ci.”
“Tom, akwai magana.”
“An samu?”
Na gyaɗa masa kai.
“Faɗamin to.”
“Ka fara cin abincin.”
“A’a faɗan.”
Sai da na tashi zaune na riƙe hannunsa.
“Kasan dai bazan zaɓa ma abinda zai cutar da ka ba, dan Allah ina son ka amshi zaɓin da na yi maka da hannu biyu biyu, kuma kasa a ranka alheri ce a garemu duka.”
“Nana duk jikina ya yi sanyi, wace ki faɗamin dan Allah.”
“Bilkisu! Wannan ƙawar ta wa ta kake ɗan ganinta.”
Shiru ya yi sai kuma can ya ce.
“Wata fara haka?”
“Eyh ita.”
“Anya Nana?”
“Dan Allah karka ce a’a.”
“Nana zan yi shawara.”
“Tom, amma da matsala guda fa?”
“Kinji ko? Wace matsalal?”
“Tana aiki.”
“Wane kalal aiki kuma?”
“Aikin Ofis, kuma ka ce ba zaka iya jure ganin matarka na cakuɗuwa da maza ba, shine nake so dan Allah ka yi haƙuri ka barta.”
“Nana sai na yi tunani gaskiyya, bari na ci abincin.”
Yana faɗin haka ya tashi ya nufi dinning ɗin, da kanshi ya zuba ya ce kuma bai yi magana akan indomie ɗin ba, ko da yaga ban jindaɗi ne?
*********
Yau Sardauna bai fita majalisa ba, da na tambayeshi sai ya ce bani da lafiya dole ya yi jinyata kuma gashi yana son ya yi tunanin akan al’amarin nan. Haka dai na yi bacci na barshi yana faman tunane tunane.
Washe gari bayan munyi breakfast zai fita ya ce da ni.
“Nana na yi tunani duba da yanayin da muke ciki na matsi Hajiya da Big Daddy na amince zan barta ta yi aikin na ta, amma gaskiyya bana so.”
Har cikin raina na ji daɗi.
“Alhamdulillah, Allah Ya sa albarka, yanzu sai na yi mata magana nasan zata amince itama.”
“Wannan ya rage naki.”
Ya faɗa yana ficewa, ni kuma na koma kan kujera na zauna, na ɗau wayata na fara kiran lambar Bilkisu, amma bata ɗauka ba, gashi message ɗin na jiya ma ba ta dawo da amsa ba. Sake kiranta na yi har ta gama ƙarar ta ba ta ɗauka ba, haka na ajiye wayar da tunanin an jima zan sake kiranta idan ba ta kirani ba. Har yamma ba ta kirani ba kuma nasake kira ba ta ɗauka ba, na yi ta addu’ar Allah Ya sa lafiya dai. Da ddaddare na faɗawa Sardauna na ce ya bani wayarsa na kira ta sai ya ce na sake kiranta dai. Ina kira kuwa ta ɗauka.
“Nana ki yi haƙuri, yau na yi busy da yawa wallahi, ina ta ganin kiranki ban sami zama ba.”
“Ayyah ba komai Bilkisu, ya gida ya aikin?”
“Alhamdullilah, ya mai gidan?”
“Lafiya ƙalau, na ce ya ake ciki da maganar Abban naku an da ce kuwa?”
“Tun da ya ƙaramin sati ɗaya bamu sake maganar ba, kuma kamar naga saƙonki ko? Kince kin sami mafita?”
“Eyh Bilkisu na samu wacca nake ganin za ta yi amfani wa ni dake.”
“Nana ai matsalal mu ba ta da alaƙa da juna.”
“Eyh Bilkisu sai dai kamanceceniya, Abbanku ya matsa miki, nima Hajiyar Sardauna ta matsa me zai hana Bilkisu mu haɗu a rufawa juna asiri, ki auri Mijina.”
“Nana kina da hankali? Kinsan abinda kike faɗa kuwa? Na auri mijinki Sardauna?”
“Is for the best Bilkisu Please.”
“Nana bazan iya ba, a yadda kike son mijinki na shiga ciki? Ki rufan asiri Nana.”
“Bilkisu ke ce last hope ɗina, aure na ma tangarɗa yake ki taimaka.”
“Lallai Nana, dan Allah ina so ki a ranki bamu taɓa wannan maganar ba dan Allah.”
Tana gama faɗin haka ta kashe wayar, na kalli Sardauna da yake zaune yana sauroro.
“Nana akawai wata bayan ita?”
Na girgiza kai sannan na ce.
“Ita kaɗai ce.”
“Nana to ya za ayi?”
“Ita ɗin dai, nasan za ta fahimta in sha Allah.”
“Nana banga alama ba, ki na ji ta ce yadda kike son mijinki ba za ta iya shiga tsakaninku ba.”
“Hhhm, idan ba ta shiga ba rasa ka zanyi gaba ɗaya.”
“Nana ki daina wannan tunanin ba zaki taɓa rasani ba, Nana a yadda nake jin ki a rayuwata idan babu ke nima ai babu ni.”
“Nima nasan ba zan rasa ka ba, amma biyayya ga iyaye dole ce idan muna neman albarka a rayuwa.”
“Nana bari na je gidan Hajiya na gara kiranta yanzu.”
“Tom Allah Ya tsare hanya.”
“Amin Ya Allah.”
Ya faɗa yana tashi, yana fita na sake kiranta a waya amma bata ɗauka ba, message na hau rubuta mata.
‘Salam, Bilkisu dan Allah ki fahimceni, ina so ki aure mijina Sardauna sabida ki tsira daga auren dole da zaayi miki, shima ya tsira daga auren dolen da za ayi masa ki fahimta dan Allah.’
Na tura mata amma har Sardauna ya dawo ba ta yi min reply ba, washe gari da safe ma na sake tura mata wani amma shima ba ta ce dani komai ba.
“Honey ya kuka yi da yarinyar?”
Kallonsa na yi sannan na ci gaba da haɗa mai tea ɗin, sai da na gama sannan na ce.
“Ba ta sake cewa komai ba, amma dai zan ƙoƙarta zan sake magana da ita.”
“Shikenan Nana, nasan zaki iya, Allah Ya yi miki albarka.”
“Amin Amin.”
Bayan mun kammala breakfast ya tafi, na dawo na ci gaba da kiran wayar Bilkisu amma bata ɗauka ba, ganin ba zata ɗauka ba na shiga fito da wankin kayan Sardauna na hau yi, da ƙarfi nake dirza kayan sabida ina son su fita su yi haske yanda zai ji daɗi, sai wajen la’asar na gama wankin na shanya su s abun shanyar mun na bayan kitchen, ina dawo na ga missed call ɗin Bilkisu, jikina har ɓari yake na ɗau wayar na kira ta, ina kira ta ɗauka, cikin rawar baki na fara magana.
“Bilkisu!”
“Na’am Nana.”
“Bilkisu kinga messages ɗina?”
“Nagani Nana, ni bansan abinda zance miki ba shi ya sa ma ban miki reply ba, kina magana kamar wata ‘yar ƙwaya.”
“Hhm Bilkisu ba zaki gane ba ne, amma dan Allah ki taimaka, ki taimakeni ki taimaki mijina.”
“Nana babu wata hanyar taimako da zan ia yi miki bayan wannan? Gaskiyya wannan abun yafi ƙarfina, ki barni da matsalal Abbana kawai.”
“Bilkisu dan Allah ki biyo ta gidana mu yi magana.”
“Nana bana jin zan sake zuwa gidanki, tun abinda kike son ƙullamin kenan? Ace na zo gidanki na aure miki miji, duniya ta yi ta zagina.”
“Haba Bilkisu ya zaki ce haka? Dan Allah kizo ko ba zaki aureshi ba nasan akwai shawarar da zaki ban.”
Shiru ta ɗanyi na ‘yan mintina sannan ta ce.
“Shikenan, bari na zo yanzu.”
“Tom Bilkisu na gode sosai.”
“Sai na zo.”
Ta faɗa tana kashe wayar, na koma na zauna. ‘A halin da Bilkisu take ciki na yi tunanin zata amshi wannan tayin hannu biyu biyu? Ko dan mafita da take nema, amma taƙi! Lallai Bilkisu ta cika mutuniyar arziƙi.’
Ta shi na yi na duba kayan Sardauna dana wanke, na fara kawahe waɗanda suka bushe na shiga dasu ciki, ina fitowa itama ta shigo ɗakin, ban bari ta zauna ba na fara mata magana.
“Haba Bilkisu, ahalin da kike ciki na yi tunanin wannan mafita ce a garemu duka?”
“Nana mafita ce mana, amma da ace wani ne ba mijinki ba, Nana da wane ido zan kalli duniya? Da wani ido zan kalli mutane zan kalli makwafta, zan kalli ‘yan uwanki, ace ina ƙawarki na zo na auri mijinki, zagin da zan sha Nana ba ƙarami ba ne, Nana tsinuwa zan sha a bakin jama’a, ta yanda babu yadda zaayi na kare kaina, tun da gani a gidan naki, Nana a dinga duba ana saran gatari.”
“Bilkisu mu zauna.” Na faɗa ina kama mata hannu, zaman ta yi sannan na ce.
“Ina ruwanmu da surutun wani? Waye zai sani? Waye zai san mi dake ƙawayene, Bilkisu ko sun sani mene a ciki? Ba dai mu muna zaune ba, nasani Bilkisu zaki zauna tare dani cikin aminci, mu kula da mijinmu, to ina ruwanmu da zancen mutane? Su yi ta yi kar su daina.”
“Idan ke kunnenki zai iya jurewa, to ni nawa ba zai ya jurewa ba. Nana bakisan mene bakin mutane ba, idan suka sa ka agaba wallahi duk wata albarka dai ka nemeta ka rasa, Nana idan ke kin fahimta ina ‘yan uwanki zasu fahimta?”
“Kishiya ce fa Bilkisu! Kuma ba Kaina farau ba ko karau? Mijina ne kaɗai ya taɓa ƙara aure?”
Hannuna ta kama sannan ta ce.
“Nana, ki yi haƙuri abar wannan maganar, kamar zata fi amfani Nana, idan duk na ce na ji nagani shi mijin naki fa? Yana sona? Zai soni? Zaman alfama Nana bazan iya ba dan Allah.”
“Salamu alaikun.”
Muyar Sarauna ta ratsa ɗakin, ban maji ko warn ɗinsa ba, kawai sallamarsa na ji.”
“Sannu da zuwa.”
“Yawwa sannu.”
“Sannu da zuwa.”
Bilkisu ta faɗa kanta yana ƙasa.
“Yawwa sannu.” Yana amsawa ya shige cikin ɗakin, bai ƙara sa shigewa ba Bilkisu ta miƙe tare da faɗin.
“Nana, zan tafi.”
“Bilkisu bamu gama magana ba.”
“Nana ni dai nagama yanke hukuncina.”
Tana faɗin haka ta fice, hannuna na ɗora a goshine tare da faɗin.
“Hhhm, Ya Allah.”
Ɗakin da ya shiga na bi shi, ina zuwa na tarar da shi zauna a kan gado, idanunsa sunyi jawur alamun ya ci kuka ya gode Allah.
Legendspen
08129553971
*SARTSE*
-Amanar-Janafty-
*Sayyid Legendspen*
MAH/2026/001
Sadaukarwa.
RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA
(Mai Dambu)
Shafi na ashirin da uku.
(23)
“Ya salam! Me ya faru Sardauna?”
Wasu hawayen ne suka fara fitowa daga idanunsa, waɗanda suka ƙara ɗagamin hankali, ya riƙe hannu.
“Nana
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 16