zuciyata fiye da wanda na ji ɗazu, ita ce ta kirashi kenan?
“Na gode sosai da kulawarki agareni.”
“Har kulawa ta bashi kenan?.”
Na tambayi kaina, dariyar da yake ce da ita ce ta katsen tunanin da nake.
“Ai nagani, shine abinda ya ƙara burgeni da ke, idan zan dawo a ƙara yi min.”
Ji na yi dama na mutu, dama na mutu da wannan baƙar ranar da nake ganin, kamar kunnuwana ba daidai suke ba, yau Sardauna ke waya da wata mace a gabana, akan idona, me ta yi masa da ya sa ta burgesa? Ƙila ma Samosar da na koya mata ne. ‘Na shiga uku ni Nana.’
Har ya kamalla wayar ina kwance ban buɗe idona ba, kusan minti ashirin yana wayar, sannan ya sake yi min magana.
“Nana tashi mana.”
Hannu yasa a jikina ya fara taɓani, ta dole na buɗe ido, amm sai na ji bana ma son ganinshi, na mayar dasu na rufe.
“Nana na dawo.”
“Har ka dawo.”
Na faɗa ina tashi.
“Har ne ma?”
“Sannu da zuwa.”
“Yawwa.”
“Nana baki tambayi yadda muka yi da ita ba”
Murmushi na yi masa wanda yafi kuka ciwo, sannan na ce.
“Tun da naga ka daɗe ai nasan kun fahimci juna.”
“Eyh hakane kam, Nana na gode miki sosai.”
“Da na yi me?”
Hannuna ya kama sannan ya ce.
“Da kika yi komai ma, Nana a yanzu an kai matakin nasara kar ki bari sheɗan ya shiga zuciyarki, ya lalata miki komai, ya ɓarar miki da ladanki.”
“In sha Allah.”
“Koma ki kwanta to.”
Ba musu na kwanta abuna, zuciyata gaba ɗaya babu daɗi, amma nasan ta bakin Sardauna ne sheɗan ne yake son ya shiga zuciyata ya haifar min da wani abu wanda zai ɓarar da lada na duka.
Abu Kamar wasa Sardauna da Bilkisu, kullum sai Sardauna ya je gidansu Bilkisu sai bayan sha ɗaya yake dawowa, gashi sai su kai ƙarfe ɗaya na dare suna waya, haka da safe kafin ya fita ma sai sun yi waya, duk abin ya dameni yadda sardauna ya fara janye lokacinsa daga kaina. A haka ma tun ba ayi auren ba, ina kuma ga idan anyi auren? Tsakanina da Bilkisu ko ta waya ba ma gaisawa ba ta sake cemin komai ba, ko kiranta na yi a waya ma bata ɗauka, gaba ɗaya na damu kamar na yi gangancin haɗa shi da ita, wani lokacin idan na zauna ina tunani sai na ji kamar ma Sardauna ko Bilkisu wani na son wani kafin yanzu, amma idan na tuna irin yadda na shiga na fita akan Bilkisu da Sardauna sai naga kowa da ta shi matsalal, yadda muka yi da Bilkisu da kuma yadda muka yi da Sardauna, sai na ji kawai Allah ne ya haɗa jininsu a lokaci ɗaya.
********
Tun safe Anty Adiza ta kirani a waya akan yau za ta zo, na ji daɗin zuwan ta sosai, haka ma Sardauna da na faɗa masa, sai da ya ce kar na kuskura na yi mata zancem ƙarin aurensa. Wajen ƙarfe ɗaya ta ƙara so, na tarbeta da murna itama haka, bayan mun gaisa ne tasha ruwa ta kalleni sannan ta ce.
“Nana duk kin rame, kamar mara lafiya ji yanayin jikinki ko kina da hawan jini ne?”
Na girgiza kai sannan na ce.
“Na dai yi Low Bp kwanaki, bayan rasuwar Alhaji.”
Domin yanzu na zama mashahuriyar maƙaryaciya akan al’amuran Sardauna, har uwata ma ƙarya nake mata.
“Ayyah Allah Sarki, amma da kin mai da hankali akan ganyayyaki da sun ƙara jini sosai Nana.”
“Tom shikenan Anty Adiza zan maida hankali in sha Allah.”
“Nana.”
Ta sake kiran sunana, na ɗago na kalleta.
“Munyi magana da Yaya Radiya, akan wasu abubuwan dake faruwa, Nana wai menene asalin matsalalki?”
“Nifa ba ni da wata matsala, bansan me suke magana a kai ba.”
“Nana duk wanda ya ganki yasan da damuwa a tare dake, ga shi ba inda kike zuwa.”
“Mijina ba ya son fita, indai ba wani ƙwaƙwaran uziri ba.”
“Hhm, Me yaja miki Low Bp.”
“Tun rasuwar Alhaji ne.”
Anty Adiza wayayyiya ce, tasan ta yadda zata kama mutum ta dole, wasu irin tambayoyi ta dinga watsomin har sai da na yi suɓul da baka na ce da ita Sardauna ne zai ƙara aure, murmushi ta yi sannan ta ce.
“Nana kenan, bayan nan fa.”
“Babu komai Allah.”
Matsowa ta yi kusa dani ta kama hannu, ta fara magana cikim tausasawa.
“Nana karki kasance sokuwa, karki kasance shashasha! Daga lokacin da miji ya fuskanci kin shashantar da kanki a kansa, zai mai dake marar amfani, zai mai da ke tsanin da zai taka ya hau kowane mataki, Nana ba a ce babu soyayya ba, ba a ce soyayya ga miji ƙarya ba ce, amma Nana ki mutunta kanki, muma duka Nana ai muna son mazajenmu, so ba ƙarami ba Nana, amma muna mutunta kanmu ta yadda suma zasu mutantamu, Nana babu mijin da ya isa ya zo sama da ‘yan uwa ko iyaye, kowa matsayinsa daban. Ki farka daga wannan baccin da kike Nana, kisan idan kika tunkara karki zauna ki lalace a haka.”
“Shikenan Anty Adiza, na gode sosai kuma in sha Allah zan gyara.”
“Shikenan Nana Allah Ya sa gyara mana.”
“Amin amin .”
Kalamanta duk sun shige ne ba ƙarya, kuma a iya hasashen da na yi gaskiyya ta faɗa min, amma ni har yanzu banga mafarkin da nake yi akan Sardauna ba, matsala ɗaya ce rashin zuwa gida kuma in sha Allah zan dinga zuwa.
Bata jira Sardauna ya dawo ba ta tafi sabida tabar yaronta a wajen masu aiki, ba ta daɗe ta tafiya ba na sake gwada lambar Bilkisu amma ba ta tafiya.
“Allah Ka sa wannan baiwar taka tana lafiya.”
Na faɗa a raina tare da ƙudiri niyar idan Sardauna ya dawo zan tambayeshi, sannan na ce idan ya je ya haɗani da ita. Ba Sardauna ya shigo ba sai bayan magariba, shima a gurguje ya shigo ya shirya ya fita ko abinci bai ci ba, sai bayan goma ya sake dawowa, hannayen shi riƙe da leda da alama shopping ya yi.
“Nana ga wannan, Bilkisu ce ta ce akawo miki.”
Karɓa na yi sannan na ce.
“An gode.”
“Munje shopping ne, kinsan an sanya ranar aurenmu wata ɗaya, shine muka je siyayya.”
Kamar ansoka mini mashi haka na ji shigar maganarsa, amma sai na kauda kai tare da cewa.
“Allah Ya nuna mana.”
“Amin Nana.”
Miƙewa na yi da niyar shiga ɗaki na kwanta, Sardauna yasa hannu ya jawo ni kusa da shi, ya riƙe hannayena duka biyun da ƙarfi, riƙon da ya yi min ya haifar min da nutsuwar dole, shi kuma ya zuba min idanuwansa waɗanda suka riga canza launi zuwa yanayin tausayi da damuwa, sannan ya fara magana cikin muryar sa mai amo ta daɗi.
"Nana... kin san irin son da nake miki, kuma kin san cewa wannan lamarin ba zaɓina ba ne, kaddara ce ta iyaye. Amma abin da ya fi komai burgeni ya haifar min da nutsuwar da ta bani damar sauke haƙƙin da nake shirin ɗauka shi ne yadda kika nuna min tsantsar girma da biyayya kika amince da wannan auren. Nana, wannan babban Aikin Lada ne kika ɗauko wa kanki."
Ya gyara zama, ya ƙara matse hannuna.
"Nana, yanzu an riga da an sa rana, komai ya fara ɗaukan harama, kuma hausawa sunce aski idan yazo ƙarshe yafi ƙaiƙayi. Ina so ki sani, Shaiɗan ba zai bar ki ba. Zai rinƙa hura miki wutar kishi a zuciya don ya rusa miki ladan da kika fara nema. Kar ki bari Shaiɗan ya yi nasara a kanki. Ki duba yadda kika jure har zuwa yanzu, don Allah Nana ki daure ki ƙarasa wannan jihadin da kika fara."
Ya ɗanyi shiru kamar mai tunani, sannan ya ci gaba.
"Idan aka kawo matar nan, ina so ki nuna mata cewa ke mace ce ta gari, uwar gida mai daraja. Ina so ki sanya ta ta yi miki biyayya kamar yadda kike mini, amma ta hanyar nuna mata ke ce babba. Ki zama uwa a gare ta, ki koya mata yadda ake girmama ni. Idan kika yi hakan, Nana, kin gama mallakar zuciyata har abada, kuma kin tabbatar wa duniya cewa ke ba mace ba ce irin ta sauran mata masu kishin hauka."
"Ina so ki nuna mata girmana da darajata a gidan nan, ta yadda ita ma za ta bi sawun ki wajen yi mini hidima. Ta hakan ne kishi ba zai taɓa samun gurbin zama a tsakaninku ba. Nana, shin za ki iya yi mini wannan alfarma ta ƙarshe? Ki zama jagora a gare ta, ki kuma kare ladanki daga sharrin Shaiɗan?"
Wani irin sanyi na ji ya ratsa zuciyata, soyayya da tausayin Sardauna suka sake lulluɓe ɓargo da fatar jikina, cike da tausasawa nima na fara magana.
“In sha Allah Sardauna, ni zan kasance mai biyayya da tausayawa a gareka har ƙarshen numfashina, Sardauna na yi niyar yaƙi da kowanne irin sheɗani da zai zo ya shiga rayuwata, zan yi haƙuri zan zauna da amaryar ko da ba ta son zama da ni, zan nuna mata girmanka da soyayyarka.”
Ya sa hannu ya rungumo ni jikinsa, sannan ya ce.
“Na gode Nanata, Allah Ya yi miki albarka.”
Na amsa da amin, ina rugume da shi. Ban sami damar yi masa maganar rashin ɗaukan wayata da Bilkisu take ba, tun da gashi har abu ta bada akawo min. Tun daga wannan rana bansake bari sheɗan ya samin wani tunani na kishi ba ko wani abu mai kama da hakan, shirye shiryen biki suna ta ƙaratowa, Sardauna ya yi matuƙar busy abubuwa kawai yake shiryawa na auren, lefe akwati set uku ya yi mata, ni kuma ya yi min set ɗaya. Ranar da aka kai kayan gidansu Bilkisu ya kama ɗaurin auren saura sati biyu cif, amma shagulgulan bikin sauran kwama takwas afara a yadda Sardauna yake faɗan. Har da wasu Events da za ayi a Abuja ma, ɗaurin auren ma acan zaayi sabida Bilkisu na da ‘yan uwa acan, ni dai nawa na yi fatan alheri ne kawai.
Lokacin da bikin ya rage saura kwanaki biyu a fara Sardauna ya umarce ni da na je gida na faɗawa su Hajiya, idan zan iya ma na kwana ɗaya acan. Na ji daɗi sosai sabida ina son na zaga ‘yan uwa da na daɗe bangani ba, duk da ya ja kunnena sosai akan kar na faɗi wasu abubuwan.
Da kanshi ya kaini har gida, bayan ya shiga sun gaisa da Hajiya sannan ya tafi, gidan bakowa sai Hajiya Yaya Radiya tana makaranta, Ra’is da Yaya Ridwan ma haka, yaran Yaya Radiya ma sun tafi makaranta. Hakan ya bamu damar zantawa da Hajiya sosai da sosai, har na faɗa mata auren da zaiyi, sai dai na ɓoye mata cewar Bilkisu ƙawata ce, na ce a familyn ɗinsu take, ta yi aure ne ya mutu.
Yaya Ridwan ne ya fara dawowa, amma bai nuna ko ya ganni ba, ya shige ɗaki sai kuma Yaya Radiya, ita ce ma muka tattauna muka yi hira sosai, sai Ra’is da ya dawo. Da daddare Sardauna ya kirani na ce da shi zan kwana anan ɗin, ya kashe wayarsa na tare da ya ce min komai ba.
Washe gari na je gidan Yaya Rumaisa, ta yi mamakin ganina a gidan nata dan tun da na yi aure bai fi sau biyu na je ba, shima duk kafin rasuwar Alhaji ne, amma tun da Alhaji ya rasu banje ba. Muna cikin hira ta ce dani.
“Shashasha, wannan yarinyar ce zaki ce mijinki ba sonta yake ba tuntuni?”
Ta faɗa tana nuna min hoton Sardauna da Bilkisu a cikin mota wanda Bilkisun ta ɗauka da kanta, na yi murmushi sannan na ce.
“Yaya ai sun amshi ƙaddara ne, sabida dukkansu ƙaddararsu iri ɗaya ce, amma aina kika sami hotonan?”
“Nana baki da hankali, a yanzu babu wasu couples da suke trending a social media kamarsu. ko wane shafi kika duba hoton su nr, mutane suna ta posting suna cewa Sardauna Ta ambo, ya sami matar da yake so, wasu a comment sai ƙare miki zagi suke, har da masu cewa ‘yar mitsiyata.”
“Hhm Yaya Wannan tunanin su ne, tun da dai muna zaune da mijina lafiya ai shikenan, duk abinda mutane zasu ce su yi ta faɗa,ni dai ina son mijina shima yana sona, ba shikenan ba.”
“Ke Nana kalle ni, wallahi Allah Sardauna baya sonki, ke ni yanzu na fahimci Sardauna auren manufa ya yi dake.”
Legendspen
08129553971
*SARTSE*
-Amanar-Janafty-
*Sayyid Legendspen*
MAH/2026/001
Sadaukarwa.
RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA
(Mai Dambu)
Shafi na ashirin da shida.
(26)
“Yaya bana son irin wannan maganar, ai daman na san kwata kwata ba kya son Sardauna.”
Na faɗa a fusace.
“Ke dalla malama rufe min baki kafin na yi ƙasa ƙasa dake anan, rashin kunya zaki yi min akan Sardaunan?”
“Ni ba rashin kunya zan miki ba, amma kema kinsan ai abinda kika faɗa bai kamata ba, miji na ne fa.”
“Au mijinki ko? To mene amfanin aure irin na Sardauna?”
“Yaya wai mene haka?”
“Duka na zaki yi Nana? Duka na zaki yi?”
Ta faɗa tana miƙewa, ganin tashin hankalin na ta ya yi yawa na miƙe da cewa.
“Ni kinga tafiya ta.”
Har n kai gab da ƙofa ta kira sunana.
“Nana!”
Na juyo na kalleta, ta yi min alama da hannu sannan ta ce.
“Zo.”
Dawowa na yi na zauna, itama ta zauna kusan minti biyar Yaya Rumaisa ta gyara zama, ta dubi ni, wadda idanuna suka yi jawur saboda riƙon da ta yi min kaɗai ya karyan zuciya da kuma fargabar abinda zata ce min. Ta nisa, sannan ta ƙara kama hannun na ta matse shi sosai, cikin muryar tausasawa ta fara magana.
"Nana, ki nutsu kar kice zaki yi kuka ki saurare ni da kyau. Rayuwa ba soyayya ce kawai ba, kuma zaman gidan miji ba hauka ba ne. Ina kallon yadda kika lallace akan Sardauna, kina neman mayar da shi tamkar abin bautarki. To ki buɗe kunnenki ki ji; Iyaye daban, Miji daban."
"Kar ki taɓa kuskuren nuna wa miji ya fi iyayenki a gare ki. Iyayenki sune tushenki, sune suka san ki kafin Sardauna ya san ki. Namiji, komai son da yake miki, idan lokaci ya yi zai iya juya miki baya, amma iyaye ba sa taɓa watsar da ɗiyarsu. Idan kika ɗaukaka miji sama da iyaye, to ranar da zai watsar da ke, ba za ki sami wurin komawa ba."
Ta gyara zama ta ci gaba, "Nana, musamman yanzu da za a yi miki kishiya, kada ki kuskura ki shashantar da kanki. Wannan biye-biye da lallaɓawa da kike yi masa, ki rage shi. Namiji idan ya ga kina rawar ƙafa a kansa da yawa, to wulakanta ki zai yi. Ki kame kanki, ki mutunta kanki a mace. Mace mai mutunci ita ce wadda take da sirrin kanta, ba wadda take zama tamkar tsumma a gaban miji ba."
"Kada ki bari kishi ya sa ki zama mahaukaciya, kuma kada ki bari soyayya ta sa ki zama doluwa. Ki zauna a matsayinki na Uwar Gida mai daraja. Ki yi masa hidimarsa na matsayin miji, amma ki bar wa zuciyarki sauran sararin numfashi. Idan kika bayar da komai na rayuwarki ga Sardauna, ranar da waccan matar ta shigo, za ki tarar ba ki da ragowar komai na kanki."
"Ki tashi, ki gyara kanki, ki daina wannan kukan banza. Namiji girmama shi ake yi, ba bauta masa ake yi ba. Idan kika mutunta kanki, shi ma zai mutunta ki. Amma idan kika zama tamkar tabarma a gabansa, to kowa ma takawa zai rinka yi ya hucewa."
*******
Ko da na dawo gidan Hajiya ban faɗa mata yadda muka yi da Yaya Rumaisa ba, na barwa raina da niyar in sha Allah zan ɗau matakin gyara, tsakanina da Sardauna soyayya ce da kulawa babu bautawar da kowa yake tunani, tun ina saka ran zai zo ya ɗauke ni har na kira sa, gaba ɗaya hayaniya ce a inda yake shi ya sa ban wani ji mai yake cewa sosai ba, na katse kiran na yi masa text akan ina jiranshi, amma amsar da ya dawo min da ita ta nemo ta jefani cikin ruɗani.
“Nana ba zan iya zuwa ba, Daddynsu Bilkisu ne ba lafiya tun safe ina asibiti!”
Tunawa na yi lokacin da Alhaji ba shi da lafiya, Sardauna bai ko shigi gidan nan ba sai da ya dawo. ‘Wai anya maganar da ake faɗa min ba gaskiyya ba ce? Bai ci ace na buɗe idona na yi tunani a kai ba?.’ Na tambayi zuciyata, amma da yake tafi ni mutuwa akan Sardauna sai ta ɓoye hakan, ta shiga lissafomin uzurirrika kala kala da zasu kare Sardauna, ina shirin tafiya Ra’is ya shigo yana faɗin.
“Hajiya ga Yaya Turaki nan.”
Mamaki ya kamani wai Yaya Turaki, to me yake yi anan.
“Bari na ɗan gyara wajen kafin ya shigo.”
Hajiya ta faɗa tana ɗan kwashe kayan dake wajen, sannan ta sa Yaya Radiya fa ɗauko mata dadduma ta shmfiɗa mai.
“Ke daskarewar uban me kika yi anan? Ba yanzu zai zo ba ne?.”
Yaya Radiya da zata shiga ɗaki ta tambayeni.
“Tafiya zanyi, yana wajen aiki ne.”
Daidai lokacin kuma Turaki ya shigo, shi da Ra’is kamar wasu abokai haka suka shigo suna dariya, ni abun ma mamaki ya ban, ashe akwai sauran mamaki ganin yadda Turaki ya saba da ‘yan gidanmu har da tsokanar Yaya Radiya.
“Ina yini?”
Na faɗa ganin kamar ma bai kula da ni ba.
“Amaryarmu kina nan kenan?.”
“Eyh! Ta nan tafiya ma za ta yi kuma bai zo ba.”
Hajiya ta bashi amsa, tana miƙewa zuwa kicin. Ƙila ma shi ya gyara musu gidan, dan naga Hajiya wani plast da cokali ta ɗauko masu kyau ta kawo ta ajiye a gabansa, ba tare da wata magana ba ya buɗe ya fara cin tuwon, yana ci Hajiyar tana taɓashi da hira, duk da bai da yawan magana amma su kam yana magana da su, kamar yadda yake yi da ‘yan uwansa.
“Hajiya ni zan tafi kawai.”
“Wai ba zai zo ba, to shikenan ina zuwa.”
“A’a ta jira mana mu tafi tare, ai gida ɗaya zamu.”
Ban tanka masa ba na kom ɗaki na zauna, na tarar da Yaya Radiya tana dannawa waya.
“Wai Yaya yaushe wannan mutumin ya saba zuwa gidan nan haka?”
“Tun rasuwar Alhaji, mene?”
“A’a bakomai.”
“Ai yafi mijinki hankali da nutsuwa.”
“Ku ana fara magana sai ku hau sukar mijina.”
Na faɗa ina cuna baki gaba.
“To ai mijin naki ne ba halin arziƙi.”
“Bawani nan, ni kuwa ina Hajja ne?”
“Tana nan tana tijara wai sai an siyar da gidan nan.”
“Anyi mata uban me?”
“Oho mata, sai da Ridwan ya tsinkawa yaron da ya rakota mari sannan suka bar gidan, kuma kinsan yaron da akasa a shagon Alhaji Ridwan ne ya ɗauke shi to yaja masa kunne akan bata komai, shine fa duk take rashin arziƙi.”
“Uhm, aniyar ta can ta bita, yanzu Yaya yaushe zaku gama makaranta?”
“Nan da sati biyu zamu fara jarrabawa, ke ‘yan ajinku yanzu ƙila sun shiga shekarar ƙarshe ko?”
“A’a, za dai su shiga, zango uku ya rage musu gaba ɗaya.”
“Ai gashinan kin cuci kanki, ke ba karatun anan ba ke ba tafiya turan ba, kinbiyewa jirgin ƙarya.”
“Nana fio ku tafi.”
Hajiya ta faɗa tana yayen labulen ɗakin.
“Tom Hajiya.” Na faɗa tare da miƙewa, lokacin da na fito ma baya gidan, na kalli Hajiya na ce.
“Hajiya ya zanyi da Sardauna?”
“Mene da Sardaunan?”
“Idan ya ji labarin Turaki ne ya dawo da ni, bazai ji daɗi ba.”
“To Nana a daren nan tafi a ƙafa.”
Tana faɗin haka ta shige ɗaki tabarni, ba shiri na yi waje na bishi har ya shiga mota abunsa. A hankali na buɗe motar na shiga, wayarsa yake dannawa sai kuma waƙa tana tashi ƙasa ƙasa, yadda baza ta taɓa damunka ba, kashe wayar ya yi ya ajiye ta akan cinyarsa ya ta da motar ya tana tafiya a hankali cikin nutsuwa.
“Ina zaki irga masoya na ki sanyo da ni, ki duba kanki ana kallona majunoni, ni kuma na ce indai kai naki ne ban faɗi ba, saƙo ya bayyana ne tun da ga zuciya..”
Yana tuƙi yana bin waƙarsa kamar shi ya raira abarsa, ni dai bance ko ƙala ba, sai ma tuna tuƙin Sardauna da na yi kamar za a tashi sama, ga uban waƙoƙin turanci wai na wata Ariana grande, kullum su zaka yi ta ji yana ƙurewa.
“Kin shiga raina, kin zauna dan kin sami guri, na ji kiranki na amsa kuma na zo da wuri, ke ce farko kuma kece ƙarshe, bishiyar nan tai girma wadda kikai mini dashi. Matar ƙani.”
Ya faɗa yana kallona, na juyo na kalleshi sannan na ce.
“Na’am.”
“Na ga kun fara hankali ke da mijinki, tun da ta fara barin ki ki zo gida.”
Na yi murmushi sannan na ce.
“Uhm.”
Ban san me yasa ba, amma ni wani irin nauyin shi nake ji sosai, ku sunansa bana iya faɗa.
“Yanzu saura makaranta ko?”
“Eyh in sha Allah.”
“Tom Allah Ya taimaka ya bada sa’a.”
“Amin amin.”
Daga haka bai ƙara cemin komai ba, ya mai da hankalinshi kan tuƙi ya ci gaba da bin waƙarsa.
“Ke kika ce zaki rayu da ni, so wanda bai gamuwa.”
A raina na ji dama sardauna ne yake da wannan yanayin, ina son waƙoƙin soyayya, mussaman ace ni da mijina ina yi masa yanayin min.
*********
Sai ƙarfe tara da arba’in muka shigo gidan, kusan minti talatin muna tafiya a hanya, tafiya kamar ta barin gari sabida yadda yake tuƙi, amma kwata kwata ban ji na takura ba, ko dan waƙoƙin da yake sawa suna haifar min da shauƙin da yake sani hasasomu ni da Sardauna.
Yana tsaye a bakin ƙofarmu, waya a kare a kunnensa da alama ma waya yake, gabana na ji ya tsanamta faɗuwa, na shiga maimaita Hasbunallahu wani’imal wakil, shi kam Turaki ko a kansa ya ƙarasa wajensa ya yi parking mota.
Ganin kamar bazan fita ba ya sa shi buɗewa zai fita, ba shiri na sa ƙafa na fito, gabana yana wani irin bugawa dum dum dum, kamar ana buga ganga. A hankali nake takawa kamar wacca ke tsoron taka ƙasa, idona yana a ƙasa bana son ma ɗagasu na kalli Sardauna.
“Ɗaga kai ki kalleni.”
Ya faɗa a tsawace, sannan ya juya ga Turaki dake shirin buɗe bangarensa.
“Kai uban me ya haɗaka da matata?”
“Tambayeta.”
Turaki ya faɗa yana ƙoƙarin shiga, wani irin tsalle Sardauna ya yi ya cakumo Turaki ya yi baya da shi.
“Uban me ya haɗaka da ita, na ce uban me ya haɗaka da ita?”
“Cika min riga kafin na yi ƙasa ƙasa da kai anan.”
“Ni zaka yi ƙasa ƙasa da shi, kar ka fasa Turaki uban me ya haɗaka da matata?”
“Na ce ka tambayeta mana, ko ita bata da baki ne? Idan bakasan darajarta ba ka barta ta na tafiya a titi da tsohon dare, ni nasan darajarta a matsayinta na mace, ko ba ita ba naga mace na tafiya a hanya cikin dare ni mai iya taimaka mata na kai ta gidane, bare kuma ita da nasan gida ɗaya zamu je.”
A fakaice dai Turaki ya rufa asirin cewa daga gida ga ɗaukoni, ya sauƙaƙa min sosai.
“Daga yau… ba kai… ba wani abu nawa… Turaki ba kai ba matata, ko a jeji kaganta ba kai ba ita.. na faɗa ma.”
Idanun Sardauna nake kalla yadda suka rini suka koma jawur, ga wasu jijiyon kansa da suka fito raɗau.
“To cikani, kuma matarka ce na ɗauko a mota ta, tana gaba ina gab…”
Kuɓus! Haka Sardauna ya make bakin Turaki, sannan ya saki wata ƙara kamar sabon Mahaukaci.
“Turaki akan iyalina wallahi zan iya kashe ka, ka fita sabgarta.”
Riƙe bakinshi Turaki ya yi da yake jini, a hankali ya taka ya buɗe ƙofarsa, sai da ya gama shiga sannan ya leƙo da kai.
“Kuma har ƙanshin Turarenra na ji.”
Yana faɗin haka ya tura ƙofarshi ta shige, da gudu Sardauna ya bi shi yana knocking.
“Turaki ka buɗe ƙofar nan na kakkarya ka.”
Da wani ƙarfi yake buga ƙofar yana kiran sunan Turaki.
“Wallahi Abubukar yau sai na raba hannunka da gangar jikinka, ka buɗe na faɗa maka.”
Can ta wajen window Turaki ya ƙara leƙowa.
“Ga fuskarta mai kyau, ta iya murmushi.”
Da gudu Sardauna ya dawo wajen tagar, yana faɗin.
“Abubakar zakaci kutumar ubanka wallahi, karuwa ɗan iska, me bin matan mutane.”
“Matarka dai akwai kyau ma sha Allah.”
Turaki ya faɗa daga wajen ƙofa, ni dai ina daga tsaye, na fuskanci Turaki dai haukata Sardauna yake son yi, kamar daga sama na ji yana cewa.
“Uban me kike yi anan? Sai na zo na ɓaɓɓallaki, shashasha.”
Ba shiri na shige ciki, ya yo kaina yana faɗin.
“Wato Nana ke baki da hankali ko? Da zaki shiga motar wani namiji da ba mijinki ba, Nana ko yayanki uwa ɗaya uba ɗaya ai bazaki shiga mota tare da shi ba, shine zaki shiga da wancan ƙasurgumin ɗan iskan ko? Wallahi Nana yau sai kinji a jikinki.”
Legendspen
08129553971
*SARTSE*
-Amanar-Janafty-
*Sayyid Legendspen*
MAH/2026/001
Sadaukarwa.
RAMLAT ABDULRAHMAN MANGA
(Mai Dambu)
Shafi na ashirin da bakwai.
(27)
Ina shiga ciki na yi cikin ɗakina na kulle ƙofa nasa Sakata, yadda yake wannan saman ai tsaf ya
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 16