An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
⭐ABBANA⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Daga Marubuciyar👇🏻
*Meenalyn Daddy
*Oga Habib
*Fadeela
*Abdurrahim
*In da rai
*Daga Allah ko dora ma Kai
*So ne sila
*Rayuwar Haidar
*Bakin kishi.
By FADILA SANI Bakori
GARGADI
Ban yadda ba, ban kuma laminta ba, wani ko wata ya canza min labari, ko ya yi min amfani da shi ba tare da amince wata ba. Yin hakan kuskure ne babba dan haka a kiyaye.
P 1-2
Bismillahir rahmanir rahim.
Garin Kaduna, safiya ce, 8:00AM wanda ya yi daidai da 9/7/2025. Amma sakamakon tsananin hadarin da yake garin ya sa garin ya yi hudu.
Gudu take Wanda babu waiwaye acikinsa bare kuma alamar gajiyawa, sai uban haki da take yi. A yanayin yadda take gudin kadai zaka kalla ka san ba cikin hayyacinta take gudin ba. Ga garin ya yi duhun hadari Wanda har an fara sakin ruwa kadan-kadan. Bisa ga alama, hakan ya sa mutane su ka yi Karan ciki a hanyar, duk an yi gudun ruwa. Zan iya cewa ita kadaice a hanyar wadda baka jin komai sai shashshekar hakin da take yi. Ja ta yi ta tsaya dan tsananin ruwan da ake yi ya sa har ba ta ganin hanya. layi ta fara kamar wadda ta sha ta bugu. Daga karshe dai jirine ya dibeta ta yanke jiki ta fadi a wajan. Ya zamana ruwan saman nan gaba daya kanta yake sauka. Bisa ga alama Kuma kamar ba a suma ta yi taba, dan tana jijjuya hannunta wanda da alama ta bugu da shi ne.
"Yaya kalli can ka gani kamar mutum?" Cewar wata matashiyar budurwa da suke cikin mota wanda da alama tsananin ruwan da ake yi ne ya sa suka yi parking. Da kallo ya bi in da Amina ta nuna mai. Shiru ya yi yana kallan matashiyar budurwar da ke kwance a wajan, ga ruwa na sauka kanta babu alamar za ta tashi.
Motarsa ya fara ƙoƙarin ja ya bar wajan, Amina da suke tare ta ce "Yayana, mutum fa na ce maka a kwance, Kuma kana ƙoƙarin jan mota."
"Amina, me za mu yi mata ana ruwan nan? Wana irin taimako za mu iya yi mata mu da ba yan garin nan ba?." "Ko Asibitin garin nan Yaya sai mu biya mu mikata Mana, daga can sai mu wuce."
Kallan baki da hankali ya yi Mata ya ce "Amina kin san Allah babu inda zani, zai yi wahala ma ba mahaukaciya ba ce, in da dai babu yadda za ai mai hankali ya kwanta a kasa a titi ruwa na bugunsa."
Yana gama fadar haka ya ja motarsa ya bar wajan sakamakon ruwan saman ya fara tsagaitawa.
"Laaa, Yaya kalli tana daga hannunta, Wallahi daga gani taimako take naima dan Allah mu tsaya mu yi magana da ita ko damuwarta mu ji Mana."Cewar Amina.
Tsaida motar Abba ya yi, yana kallan Amina, ya ce "Ki je ki dubata ki yi maganar da za ki yi da ita babu inda zani."
Amina sauka ta yi tana tafiya dari-dari kamar mai jin tsoran za a kamata, a haka har ta karasa in da matashiyar budurwan nan take kwance. Amina cikin tsoro ta ce "Baiwar Allah Lafiya kika zo nan kika kwanta?."
Da sauri matashiyar nan ta tashi kamar zautatta ta rirrike Amina tana cewa "Ki taimaka min dan Allah, ki taimaka min." Amina tsayawa ta yi tana kare Mata kallo, a iya fahimtarta kamar ba babu alamun hauka a tare da ita, tsabar razana ne da tashin hankali ta hanga tare da ita. Ajiyar zuciya Amina ta sauke, ta ce na ji zan taimaka Miki, fada min da me kike so in taimaka Miki?." Matashiyar budurwan nan, babu abin da take cewa ma Amina sai "ki taimaka min." abin da take ce Mata kenan.
Amina hannunta taja suka nufi motar yayanta da ita. Tun kafin su karasa ta fisge hannunta daga na Amina ta ruga ta shige cikin motar da yake a bude Amina ta barta ta dauke umbrella da za ta fita sakamakon ruwan da ake yi.
Daga Amina har yayanta da mamaki su ka bi matashiyar budurwan nan da kallo, wadda kallo daya za ka yi Mata ka fahimci ba cikin hayyacinta take ba.
Abba kallan matashiyar budurwan nan ya yi ya ce, "Lafiya wacece ke?"
Maimakon taba Abba amsar tambayarsa, kallansa ta fara yi, can Kuma ta Fashe da kuka tana huna masu hannunta tana cewa "Na kasheshi! Na kasheshi!! Na kasheshi!!! Kun ga hannuna." Ta idasa maganar tana nuna masu fararan hannunta.
Abba kallan Amina ya yi yana cewa "Amina, kin ga abin da kika jawo Mana ko?." Yanzu sai ki san yadda zaki yi ki fitar min da ita daga mota."
Ajiyar zuciya Amina ta sauke tana mai Kuma kallan matashiyar budurwan nan da har yanzu abin da take furta wa kenan na kashe shi, Kunga hannuna.
Amina handbag dinta ta bude ta ciro kudi tana mika ma matashiyar budurwan nan ta ce "Kawata amshi wannan ki je ki sai wani abu ki ci kin ji ko."
Maimakon ta amshi kudin da Amina ke miko Mata, Kai ta fara girgiza ma Amina tana Kara tsananta kukanta tana cewa "Na kasheshi." Tana mai Kuma nuna masu hannunta da basu fahimci kamai ba a hannun da take nuna masu.
Amina cikin karfin hali ta ce "Wa kika kashe?." Kuka ta Kuma fashewa da shi Maimakon taba Amina amsa, ta Kuma maimaita mata
"Na kasheshi."
Amina Kai ta girgiza tana kallan Yayanta ta ce "Yaya Abba, ya za mu yi da ita? bisa ga alama ma kamar ba cikin hayyacinta take ba."
"Babu yadda za mu yi da ita, Kuma kinsan dai ba zai yuwu mu tafi Katsina da ita ba, kin ji dai furucin da ke fita a bakinta."
"A'a, Yayana Ina ganin kamar furgici ne ya sa ta fadin haka, wannan daga ganinta ko kiyashi ba za ta iya kashewa ba, ka ga har yanzu ruwan bai tsaya ba, Ina ganin mu yi hakuri mu tafi da ita kafin ta dawo hayyacinta, na san ko mama ba za ta yi fada ba, inda ita ke horarmu da yin taimakon."
Shiru Abba ya yi bisa ga alama nazarin maganarta yake yi.
Amina hannun yayanta ta kama ta ce "Dan Allah yayana."
Motar Abba ya ja suka tafi ba tare da ya ce komai ba.
Suna tafiya matashiyar budurwan nan ta kwanta ta kama barci. Amina da yayanta da kallo suka bi ta.
Ba ita ta farka ba sai suna gaf da shiga garin Katsina, ta tashi a gigice tana ƙoƙarin balle murfin motar ta fita. Amina ganin abin da take ƙoƙarin yi ya sa ta ce "Yaya Abba, tsaidar da motar nan tana ƙoƙarin budewa ta fita."
Gefan titi Abbab ya koma ya yi parkin. Matashiyar budurwan nan Kuma bugun glass din motar ta take tun karfinta. Bisa ga alama dai kamar a gigice take.
Wata uwar tsawa Abba ya yi Mata Yana Mai bude mata murfin motar ya ce "Fita! Idan tafiya kike son yi fita na ce." Cikin gigi ta fita tana mai rike Amina da itama ta fito daga cikin motar.
"Wayyo Allah na kashe shi! Na kashe shi!!." Ta fada da karfi tana mai Kuma rirrike Amina tana nuna mata hannunta."
Amina kafin ta yi magana sai ganinta su ka yi ta yanke jiki ta fadi sumammiya.
Abba kuma cikin takaicin wahalar da suka dakko ma kansu da kansu ya kalli Amina ya ce "Kin ga wahalar da kika sa muka dakko ma kanmu ko?, Kiri-kiri Kinga tana naiman tara Mana mutane, yanzu sai ki fada min yadda za mu yi da ita?."
Amina cikin sanyi ta ce "Yaya dan Allah ka kamata mu kaita asibitinku Mana a dubata."
Abba cikin takaici ya ce "Kina da kudin da za a dubata a asibitin mu din ko?."Yaya Abba Ina da su, ka kamamin ita mu maidata mota dan Allah."
Abba kafafunta ya kama a kyamace kamar ya taba kashi suka shimfidar da ita cikin motar. Sannan ya ja motar suka tafi.
Tafiya kadan su ka yi ya danna hancin motarshi cikin wata private Asibiti da ke bakin hanya.
Amina cikin sanyi ta ce "Yaya dan Allah mu kaita asibitinku Mana, ka ga can komai zai zo da sauki, nan fa asibitin kudi ce ni dai dan Allah ka kaita asibitinku."
Abba ko saurarar Amina be yi ba ya danna hancin motarsa cikin Asibitin. Suna zuwa ya kalli Amina ya ce "Na gama iya nawa, saura na ki, fitar min da ita daga motata."
Yadda Abba ya yi magana bai ba Amina damar sake neman wata alfarmarsa ba.
Hakan ya sa itama bata Kuma cewa komai ba ta fita daga cikin motar ta nufi cikin asibitin, babu jimawa suka taho da gadon da aka tana da dan taukar marasa lafiya. Da taimakon malaman Asibitin aka sa baiwar Alllah nan gadon da suka ta nada dan daukar marasa lafiya.
Amina kallan Yayanta ta yi ta ce "Yaya daga an dubata zan taho nima."
Shi dai ko tankama Amina bai yi ba ya ja motarsa ya tafi.
Tafiya kadan ta Kai Abba gida, kasancewar babu nisa sosai tsakaninsu da Asibitin da ya Kai 'yar tsuntuwar tasu.
Ana ta sallar la'asar hakan ya sa Abba bai shiga gida ba sai da ya yi Sallah sannan.
Yaran kanwar Abba na jin parking din motarshi suka ruga da gudu suna mai oyoyooo. Take Kuma suka fara waige-waigen Amina ganinsa shi kadai.
Amira ta ce "Yaya Abba Ina mommy Amina fa?." Abba murmushi ya yi masu ya shafa kan Sadik ya wuce ba tare da ya basu amsa ba.
Mahaifiyarsu Amina da kallo ta bi Abba ganin ransa kamar a bace yake Kuma ba ta ga Amina ba, bacin ko lokacin da za suka taho sun yi waya da Aminar. Bayan ya zauna ta kallai ta ce "Abbana, ya na ganka Kai ka dai, Ina Aminar fa?."
"Mama, ina tsoran Kar tausayin Amina ya jefata a wani halin."
Nan Abba ya kwashe duk abin da ya faru ya sanar da mahaifiyar tasu.
"Ikon Allah, ni ban san kalar zuciyar Amina ba, Kuma Abbana har da laifinka, taya zaka biye mata ku dakko yarinya tun daga garin Kaduna har nan Katsina, haba Abbana, sai ka ce baka san wacece Amina ba. Ni Kam na yarda da hausar nan da ake cewa wai d'an gado ya fi magaji. Haka mahaifinku yake da tsantsar tausayin nan amma Amina har ta fisa. Yanzu Abbana hakuri za ka yi in ka ci abinci ka koma kar yarinyar nan ta jawo Mana wata masifar.
Abba ya San idan ya ce ba za shi ba mahaifiyarsa za ta yi ta yi masa magiya, har sai ya yadda ya tafi, hakan ya sa ya barta a zai je. Yana gama cin abincinsa ya kama hanya ya fita.
Har dare mahaifiyar Amina ta ji shiru-shiru basu dawo ba, ba Abba ba Amina, Kuma ta Kira wayar Abba bai dauka ba, Amina ma haka ta Kira wayarta bata shiga.
Mahaifiyar Amina tana zaune tana zagaye madaidaicin falonsu ganin har 8:30 babu ko mutum daya a cikinsu. Tana a haka Allah ya shigo da Abba. Tun kafin ya karaso ta ce mai, "Ina Amina?." Gaban Abba faɗuwa ya yi dan bai dauka ba har lokacin Amina bata dawo ba.
" Ka je ka zo min da ita yanz..." Shiru mahaifiyarsu Amina ta yi sakamakon sallamar Amina da ta ji. Amina da sallamarta ta shigo falon tare da matashiyar budurwar da suka tsinto ita da yayanta.
Mahaifiyar Amina da kallo ta bi Amina da matashiyar da suke tafe da Amina. Wadda sai zare ido take tana kallan mahaifiyar Amina.
Amina cikin sanyi ta ce "Mama, kin jini shiru, ki yi hakuri tafe muke da bakuwa matsala ta fada Kuma sai da muka biya asibiti aka dubata."
Mahaifiyar Amina dai bata ce komai ba, kallan yarinyar da ke tafe da Amina ta yi, tana mamakin yadda take kallanta ba tare da ta gaidata ba. Mahaifiyar Amina cire mamakinta ta yi ta kalli matashiyar nan ta ce " 'Yan Mata ya sunanki?." Shiru babu amsa, Kuma babu wata alamar da ta nuna bata ji ba, dan kallan Mahaifiyarsu Amina take yi. Amina ganin haka tashi ta yi ta dafa kafadarta ta ce "Kawata bi ki ji ba, Mamana na tambayarki sunanki ba? Ya sunanki?." Ido ta daga tana kallan Amina, sannan a hankali ta ce "Mansura." Amina kallan mahaifiyarta ta yi ta ce "Mama, kin ji wai sunanta Mansura."
Mahaifiyar Amina shiru ta yi, sannan ta ce "Amina ku shiga ciki ta yi wanka ta ci abinci sai mu ji daga Ina take."
Amina hannun Mansura ta kamo ta ce "Kawata, zo mu je ki watsa ruwa ki ci abinci ki Sha magungunanki." Amina ta fadi maganar tana kamo hannun Mansura, Mansura Kai ta girgiza ma Amina alamun ba za ta ba. Babu yadda Amina bata yi da ita ba, Amma taki yadda ta tashi ta bi Amina, daga karshe ma sai ta yi kwanciyarta kan caution din da take. Daga Amina har Mahaifiyarta da Abba da ke tsaye duk mamaki ya cika su.
Mahaifiyar Amina kallan Mansura ta yi, ta ce a'a, ki tashi ki je ki ci abinci ki Sha maganinki tukun sai ki kwanta din."
Mansura shiru ta yi kanta sama daga gani ma ta yi nisa a duniyar tunani ba jin abin da Mahaifiyar Amina ta ce ta yi ba.
Abba da ransa ya fara baci ganin yarinyar kamar tana naiman raina masu wayau, ya ce "Ke! ba da ke ake magana bane, ba zaki tashi ba ana miki magana dan samun waje kin yi banza da mutane." Ya yi maganar cikin tsawa sosai wanda ba Mansura ba har Amina sai da ta firgita.
Mansura ko da ba jin abin da ya ce ta yi, ita dai ta ji ya yi Mata tsawa, hakan ya sa ta tashi ta rirrike Amina jikinta na rawa. Yadda take rawar jiki kawai zai nuna maka ba Karamar furgita ta yi ba. Tana Kuma zare manyan idanunta.
Amina ganin haka janta tayi suka nufi bedroom dinta da ita. Suna zuwa Amina da kanta ta hada Mata ruwan wanka, Amma babu dabarar da wayan da ba ta yi Mata ba taki yi, dole ta rabu da ita, ta kawo Mata abinci shima ko kallansa ba ta yi ba bare Amina ta sa ran zata ci. Amina ganin taki cin Abincin, Kuma taki shan maganin hakan ya sa ta kalleta ta ce " Ki dauki maganin ki Sha ko in je kin Kira miki yayana in ce kin ki shan magani." Mansura Kai ta girgiza ma Amina tana daukar maganinta ta Sha.
Abincin ko babu wayan da Amina ba ta yi Mata ba Amma taki ci, har cewa ta Kuma yi zata Kira Mata yayanta, sannan ta samu dakyar ta yi 1 spoon. Tana gamawa ta kwanta a wajan Amina dai kasa ce Mata komai ta yi ganin ko Sallah ba ta yi ba. Tana kwanciya Kuma kamar an tsakureta ta tashi ta shiga bathroom din dakin bata jima ba ta fito, ta koma inda ta tashi ta kwanta. Amina na nuna Mata bed dinta amma ko kallanshi ba ta yi ba ta kwanta kasa.
Amina Kuma wanka ta fara yi, kafin ta ci abinci dama kuma Sallah take yi ba.
Amina na gamawa ta fita falon sakamakon kiranta da Mahaifiyarta ta yi. Amina zaune ta iske Mahaifiyarta da yayanta da alama dai suna tattaunawa ne game da bakuwar da su ka yi.
Mahaifiyar Amina kallan Amina ta yi ta ce "Amina me kika fahimta game da yarinyar nan ?."
Ajiyar zuciya Amina ta sauke ta ce "Mama, Wallahi har yanzu ban yi magana da ita ba, ban da sunanta da ta fada mana har yanzu ban San komai game da ita ba. Amma gaskiya kamar yadda likitan da ya dubaya ya yi min bayani har yanzu bata cikin hayyacinta, dan ina da karancin kudi ne ma amma sansamu tana da bukatar kulawar likita a halin da kwakwalwarta take ciki yanzu, kamar yadda likitan ya ce, Amma likitan ya ce mu ci gaba da janta a jiki har a samu ta warware ta dawo Normal Sense dinta."
"A Wana gidan za a ci gaba da lallabata har ta dawo normal sense din nata?." Cewar Abba.
Amina shiru ta yi, kafin ta ce "Yaya Abba dan Allah ka yi hakuri ko kwana uku mu bata mu gani. "Hmmmm, Amina kenan, kina Sara baki duba bakin gatari, yanzu dunuyar ce ta canza mutun mugu ne, Amma koma meye inda kin jajibota ya za mu yi dole mu yi hakuri mu bata nan da kwana biyu mu gani." Shi dai Abba bai ce kamai ba, inda yasan mahaifiyarsa ma halinta daya da Aminar, ba iya korarta za ta yi ba. Sai yanzu ma yake ganin laifinsa da ya biye ma Aminar suka dakkota.
Amina ma sanadiyar gajiya da ta yi hakan ya sa tafiya ta yi ta je ta kwanta.
Cancikin dare ihun da Mansura ke yi ya tada ilahirin mutanan gidan daga dogon barcin da suke yi.
Ihu take tana Kiran "Abbana!, wayyo Abbana!!."
Amina da sauri ta rirriketa tana tambayarta lafiya. Ita ko tun karfinta ta dage ta ture Amina tana Mai Kuma Kiran Abbanta da karfinta. Wanda mahaifiyar Mansura shigowarta kenan ta ci karo da ingizar da Mansura ta kaima Amina da ke ƙoƙarin riketa, ana cikin haka ne Abba m ya shigo dakin a rude yana tambayar lafiya.
Amma ganin wadda ke ihun take ransa ya bace. Bai San sanda ya kamo Mansura ba yana girgizata ya ce "Ke! wacece ke da za ki zo cikin daran nan ki hana mutane barci kina Mana ihu cikin dare haka! Ko so kike ki tara Mana mutane ne?."
Mansura ko bata fasa kukan Kiran Abbanta da take yi ba, sai dai yanzu ta rage sautin Kiran bakamar dazun ba. Abba hannu ya daga zai mareta, mahaifiyarsa ta yi sauri ta rike hannunsa ta ce "Kul, karka mareta, baka ga ba cikin hayyacinta take ba, ina jin ma kamar mafarki ta yi."
Abba zafin mahaifiyarsa ta hanasa Marin Mansura ya sauke hannunsa akan fuskar Amina dake tsaye ba zato ta ji mari. Ya ce "Duk ke kika jawo Mana, Kuma Wallahi kin ji na rantse gobe karki yadda in dawo aiki in iske yarinyar nan a gidan nan, idan ba haka ba Wallahi! Wallahi!! Wallahi!!!, Kin ji na rantse Wallahi sai ranki ya yi munmunan ba ci na dawo na isketa a cikin gidan nan ✍🏻
Fadila Sani Bakori ce 🤗
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LGosWoHsPkj3rhf9EbKjrK
⭐ ABBANA⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Daga Marubuciyar 👇🏻
*Meenalyn Daddy
*Oga Habib
*Fadeela
*In da rai
*Abdurrahim
*Daga Allah ko d'ora ma Kai
*So ne sila
*Rayuwar Haidar
*Bakin kishi
Follow the ABBANA channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaYZGsNEFeXsr1CKQl3r
P 3-4
Amina kwana ta yi tunanin yadda za ta kuri Mansura.
Washegari, Amina bayan ta idar da sallar asuba kallan Mansura ta yi dake kwance babu alamar zata tashi. Amina bubbuga kafar Mansura ta yi ta ce "Kawata, ki tashi ki yi Sallah mana, ko kina hutu ne?."
Mansura shiru ta yi bata tanka ma Amina ba, karshe dai Amina gajiya ta yi ta rabu da ita ta nufi bedroom din mahaifiyarta.
Zaune ta isketa kan abin Sallaya tana lazimi, Amina zama ta yi har mahaifiyarta ta kammala laziminta. Amina cikin sanyi ta ce "Ina kwana mama." Lafiya lau Amina, ya bakuwarki ta tashi kuwa?." Cewar mahaifiyar Amina.
Amina cikin damuwa da lamarin bakuwar tata ta ce, "Wallahi mama, nama rasa yadda zan yi bata tashi ba, jiya ma fa ko Sallah ba ta yi ba ta kwanta, yau ma na ga ba ta yi Sallah ba."
Murmushi mahaifiyar Amina ta yi ta ce "A'a rashin sallarta ba damuwa ba ce kila tana hutu ne, ni dai yanzu Amina ya kike ganin za a yi da yarinyar nan? Kin ji dai abin da yayanki ya ce Kuma kin san halinsa."
Amina shiru ta yi dan sosai ta rude da gargadin yayan nata tasan halinsa sosai. Kallan mahaifiyarta ta yi ta ce "Wallahi mama gaba daya tun jiya barci ya kaurace min, Ina tunanin yadda zan yi da ita, dama ban rabota da garinsu ba dada sauki."
"Amina, ni yarinyarce sai inga kamar bata da hankali, anya ba ciwan hauka take ba? Yanayin yarinyar ni dai ya fi min kama da ciwan hauka." Cewar Mahaifiyar Amina.
"Tom kila, Amma dai a asibitin da Yaya Abba ya kaimu sun fi danganta abin da razana, da tsananin damuwa, Kuma nima nafi yadda da haka kamar damuwa ce ta yi Mata yawa. Ni dai mama duk ba wannan ba, ya zan yi da ita kin ji dai abin da Yaya Abba ya ce min?."
Mahaifiyar Amina Kai ta jinjina kafin ta ce, "Amina kin San dai halin yayanki, ba ƙaramin aikin shi bane ya kamaki ya buga akan yarinyar nan, dan haka idan za ki ji tawa ga kudi ina da su ki amsa daga gari ya Kara haske ki je ki sata a motar Kaduna ki dawo."
Amina kamar za ta yi kuka ta ce "Wallahi Mama likitan da ya dubata ya tabbatar min ba cikin hankalinta take ba, ya ce mu bata nan da kwana biyu mu gani kila ta dawo cikin hankalinta. Dan Allah Mama ki yi ma Yaya Abba magana, Allah bashi daga ta dawo hankalinta sai ta tafi garinsu, dan Allah Mama mu tausaya Mata ba mu San halin da take ciki ba, daga ka ganta ka ga wadda razani da tashin hankali ya bayyanar Mata,Wanda daga gani shi ne silar damuwar nan tata."
Mahaifiyar Amina shiru ta yi, sannan ta ce "Amina ba Wai naki bane, rayuwarce me wuya, kina ganin abin da ya faru da gwaggonki kwanakin baya daga taimako yarinyar nan ta
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 1 Chapter of 15