Abba, abokinsa har ya iso, Abba kayan sanyi ya fara kawo ma abokin nasa, kafin ya nufi bangaransu Amina zuwa dakko girkin Hajiya Mansura.
Abba kitchen din ya je inda suka ci karo da Mansura da ke ta ƙoƙarin fitowa. Abba da kallo ya bita ya ce "Ina abincin fa?."
Mansura plete din taliyar ta dakko ta mika ma Abba tana addu'ar Allah ya sa ya yi masu dadi.
Abba amsa ya yi ya ce "Thanks."
Yana zuwa ya aje ma Ahmad ya ce"Bismillah." Masoyiyarka ce, Taliya.
Ahmad murmushi, kafin ya ce , "Na Kira number Amina Bata daga ba ko za ka Kira min ita." Ahmad ya fadi maganar cikin damuwa.
"Kasan ta fara koyarwa, ba a dade ba na naiman manta koyarwa a wata primary nan kusa damu. Tom yau a gida ta bar wayar nima na kirata bata daga ba sai da na shiga naga wayar tata."
Ahmad shiru ya yi bai ce komai ba. Abba Kuma Abincin ya Kara mika ma Ahmad ya ce "Ka ci abinci mana." Ahmad langabar da Kai ya yi ya ce "Zanci, Amma kafin sai na amayar maka da abin da ke cikina, inda Kai dan iska ne ka kasa fahimtata. Usman, ina son Amina ba tun yau ba, dan na jima da gabatar da kaina a wajanta, yanzu haka nai man aure na zo."
Abba da mamaki ya kalli Ahmad ya ce "Wai da gaske?Kana yawan min maganar Amina Amma Wallahi ban taba kawo haka ba, sai na ga kamar ta yi Karama." Ahmad hararsa ya yi ya ce "Tsohuwa kake so in aura kenan."
"Yanzu dai ba haka ba, ka ci abinci sai mu je makarantarsu Aminar."
Ahmad bude taliyar ya yi, ba tare da tunanin komai ba ya diba tare da yin Bismillah ya afka a bakinsa cike da saukin maganar Amina da ya zo da ita, sai dai Ahmad duk yadda ya so ya daure ya hadiye abincin kasawa ya yi, ga uban yaji ga Magi bau. take ya furzar da abincin. Abba Kuma bai kawo komai ba a tunaninsa Ahmad kwarewa ya yi, hakan ya sa ya diba shima ya Kai bakinsa, ai har gara Ahmad ma Abba da gudu ya ruga toilet dinsa ya zubar da abinci ga uban shakewa da ya yi tsabar tsananin yajin da ke cikin taliyar. Abba da kyar ya samu kansa bayan ya kwankwali ruwa.
Ahmad kallan Abba ya yi ya ce "Usman wa ya yi wannan girkin haka?." Hmmm, Wallahi wata sangartattar yarinya ce, mu je restaurant mu ci abinci."
Restaurant mai tsada Abba ya kaisu suka ci abinci. Kafin suka nufi makarantar da Amina ke koyarwa. Amina da mamaki ta bi Ahmad da kallo dan ko jiya sun yi waya da shi Amma bai fada Mata zai zo ba. Amina ba sarwa ta yi ta ce "laa, Yaya Ahmad, yaushe ka zo?." Ahmad maimakon ya Amina amsa motar Abba ya nuna Mata ya je mu je."
"Ina zuwa bari in zo."
Amina cikin makarantar ta koma ta sanar da headmastern makarantar kafin ta fito suka tafi.
"My Meena , ya hayaniyar yara." Alhamdullh ya Ahmad ya hanya." Lafiya lau."
Amina Koda suka shiga gida, hannu kawai ta daga ma Mansura ta shige bathroom ta watsa ruwa da sauri ta fito. A gaggauce Amina ta Sha fa lotion dinta, ta jira doguwar rigar lass dinta.
Mansura kallan Amina ta yi ta ce "Dear, unguwa za ki kika sha gayu haka."
Amina zama ta yi kusa da Mansura ta ce "Dear Ina Wanda kike ji muna waya da shi kullum, shi ne ya zo abokin Yaya Abba ne."
"Okay, dazu ko Yaya Abba ya sani na yi masa girki Allah ya sa ya yi masa dadi ma." Ameen, tashi mu je ku gaisa."
Mansura shiru ta yi Amma har ga ranta ba ta ji dadin zuwan ba. Amma ba ta iya musa ma Amina hakan ya sa ta tashi suka fita tare suka nufi bangaran Abba, tana sanye da brown abaya a jikinta. Da sallama suka shiga in da suka iske Abba da Ahmad zaune suna hira.
Mansura cikin girmamawa ta gaida Ahmad, sannan ta juya da sauri za ta tafi. Amina rike mata hannu ta yi ya sa ta dakata.
Abba Kuma tashi ya yi ya basu waje.
Amina kallan Ahmad ta yi ta ce "Ga sabuwar sisterna da nake baka labari." Ahmad cikin fara'arsa suka gaisa da Mansura. Mansura Kuma da ta jita duk a takure tashi ta yi zata tafi ta ce "Dear bari in shiga ciki."
Amina plate din taliyar da Mansura ta dafa ta gani, Wanda tana gani ta fahimci girkin da Mansura ta fada Mata Yaya Abba ya sa ta yi ne. Amina kallan Mansura ta yi ta ce "Dear ki tafi da kayan nan."
Mansura dawowa ta yi ta dauki plate din abincin.
Abba Kuma falon mahaifiyarshi ya dawo ya zauna wanda da itama shigowarta kenan. Kallan Abba da ta yi ta ce "Abbana, ya na ganka Kai kadai bayan na ga mota a gidan."
Murmushi Abba ya yi ya ce "Yarki ce ta yi bak'o."
Kai mahaifiyar Amina ta jinjina, ta ce "Aminar ta yi bak'o bani da labari, hala Kai ta fada maka ne?."
Abba gurin zama ya nuna ma mahaifiyarsa ya ce Mama zauna ki ji."
Mama na zama Mansura ta yi sallama ta shigo rike da plate din taliyar da ta dakko.
Mansura kallan Mama ta yi ta ce"Sannu da dawowa Mama." Tana fadin haka ta juya za ta tafi.
Mama kiranta ta yi ta ce "Mansura a binci ne a plate din nan?."Eh Mama taliya ce." Mansura ta bata amsa.
"Yauwa bani in ci."
Mansura mika ma mahaifiyar Amina taliyar za ta yi Abba ya kalli Mansura ya ce "Ke kin ci ne?."
Kai Mansura ta girgiza.
Abba waje ya nuna ma Mansura ya ce "Zauna ki ci."A'a na koshi." Mansura ta idasa maganar tana mika ma Mahaifiyarsu Abba plate din taliyar.
"Diba ki ci." Abba ya umarci Mansura. Mansura ba tare da gaddama ba ta yi 1 spoon. Tun shigar taliyar bakinta tasan an samu matsala, duk yadda ta so ta daure ta hadiye ta bakinta kasawa ta yi, hakan ya sa ta furzar da taliyar a hannunta, tana ya mutsa fuska, ga uban ya ji da har kwakwalwarta sai da ta amsa.
Mansura tagowa ta yi ta kalli Abba Wanda shima ita yake kallo✍🏻
Fadila Sani Bakori ce.
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LGosWoHsPkj3rhf9EbKjrK
⭐ABBANA⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Daga Marubuciyar 👇🏻
*Oga Habin
*Fadeela
*Meenalyn Daddy
*In da rai
*Abdurrahim
*So ne sila
*Bakin kishi
P 7-8
Abba a natse ya ce ma Mansura "Ke da kika dafa kinkasa ci Ina ga mu." Sannan ya maida kallanshi ga mahaifiyarshi ya ce, "Mama, dazufa na dawo gida dan sa Amina ta yi man girki, na iske bata nan, shi ne fa na sa yarinyar nan, shi ne ta dafa taliyar nan"
Abba kallan Mansura ya yi ya ce "Shi kenan, za ki iya tafiya, dama na sa ki ci ne dan ki ji kalar abin da kika dafa ma mutane"
Mansura da sauri ta tafi tana turo baki.
Bayan ta tafi, Mahaifiyar Abba, kallan Abba ta yi ta ce, "Haba, Abbana haka ai gwalisa ne, ina laifin Wanda kaba aiki ya tashi ya yi maka."
Abba dai bace kala ba, ya canza firar da cewa" Mama, Ahmad fa naiman aure ya zo, wai Amina yake so, so na aure."
Murmushi mahaifiyar Abba ta yi ta ce "Abba akwai son da ba na aure bane, ni dama ba tun yau ba na fahimci yaron nan yana son Amina. Amma gaskiya na ji dadin jin labarin nan, dan Ahmad yana da hankali sosai. Don haka, babu abin da zance sai dai fatan alkairi in da itama Aminar na fahimci tana sonsa, dan na dade da fahimtar suna waya."
Abba Kam mamaki ya yi dan bai taba dauka haka ba. Abba sun dade suna fira da mahaifiyarsa kafin Kiran Ahmad ya shigo wayarsa. Abba na dagawa Ahmad ya ce "Mama nake so ka zo ka yi min iso in ingaida, ka ga yanzu ta zama sirikata kunga nake ji." Malam, bana son kinibibi, Ina ita Aminar take ? Ta rakoka Mana." Abba na fadin haka ya kashe wayarsa.
Amina ita ta yi ma Ahmad iso ya zo ya gaida mahaifiyrata har falonta. Ahmad dai ya kasa sakin jikinsa kamar yadda ya saba da.
Mahaifiyar Abba kallan Amina ta yi ta ca"Tom lokacin Sallah ya yi maza ki je ki yi."
Bayan Amina ta bar falon ne, mahaifiyar Amina, ta kalli Ahmad ta ce "Ahmad, na ji wani sako wajan Abba, Kuma ya yi min dadi sosai, Ina muku fatan alkairi."
Ahmad cikin jin kunya ya amsa da "Ameen."
Kafin ya yi ma Mata sallama dan yau zai koma. 10k ya ciro a ajjihunsa ya aje ma mahaifiyar Amina. Bayan sun fita Abba ya kallai Ahmad ya ce "Yanzu sai k.d, kenan?." Bari kawai, kasan na dade ban je gida ba wannan Karan......."
Su Abba sun jima suna tattaunawa kafin Ahmad ya Kira Amina suka yi sallama. 10k itama ya faba ya tafi.
Haka rayuwar Mansura ta ci gaba da wakana a gidan har ta fara sakin jikinta, amma duk da haka dai da wuya ka yi doguwar hira da ita.
Yau ya kama weekend, mutanan gidan duk suna gida. Amina kallan Mansura ta yi ta ce "Dear ki shirya ki rakani Mama zata aike mu Mani wajan Aunty Zainab, za mu Kai Mata magani, da yake tun da kika zo ba ta zo ba, ita ke bima Yaya Abba, da yake tsohon ciki gareta Kuma tana shan wahala shi ya sa mama ta hanata zuwa sai ta haihu. Mansura shiryawa ta yi cikin daya daga cikin kayan Amina suka fito za su tafi. Inda suka iske Abba zaune a falon.
Mahaifiyar Amina kallan Amina ta yi ta ce "Har Kun shirya?." Maganin ta dauka ta mika ma Amina ta ce "ku bata ,na yi Mata bayanin yadda za ta yi amfani da shi a waya."
Amina har sun juya za su tafi, Abba ya ce "Karku Kai dare."
Misalin karfe 10 su Amina suka shiga gidan Aunty Zainab. Amira murna ta yi sosai ganin Amina. Kallan Aunty Zainab ta yi tana nuna Mansura ta ce "Mommy kinga Mommy mai kuka da nake baki labari."
Aunty Zainab da ke zaune da katoton cikinta, kallan Mansura ta yi ta na murmushi ta ce "Sanninku da zuwa Mansura, sai yau Allah ya yi za mu hadu."
Mansura murmushi ta yi ta ce"Yauwa Aunty Zainab ya karfin jikin." Alhamdulillahi."
Amina kallan Aunty Zainab ta yi tana turo baki ta ce "shi kenan, in da ni baki ganni ba."
Dariya Aunty Zainab ta yi ta ce"Na isa ince ban ga autar mama ba. Haushi kika ban, Amina tun ranar fa da za ku Kaduna rabona da gida sati na 7 muke kenan. Amma shine ko kilekoni, yanzu ma nasan da mama ba ta Aiko ki ba da ba ganinki zan yi ba. "Aunty Zainab, sai ka ce kin manta waye Yaya Abba." "Ba wani Yaya Abba, ki ce dai kin samu k'awa kin rabu dani, idan kina son zuwa bani kike sawa ba in yi ma Abban magana ba." Tom Auntyna Afuwa, ba zan sake ba." Yanzu dai bani da wani abu na ci, ke Kuma Amina na San ba son abinci mai aiki kike ba, ni Kuma lallura tasa na Bilki nake ci, idan ba za ku ci nata ba ku shiga kitchen ku girka Mana baki daya."
Su Amina sun jima suna fira da Aunty Zainab da yake mai firace, kafin Amina ta tashi ta shiga kitchen ta yi masu jallop din cous-cous.
Amina ba suka fito gidan Aunty Zainab ba sai da aka yi sallar la'asar. Suna fitowa suka ga garin ya yi bakikkirin na hadari, tsananin hadarin da Aunty Zainab ta gani ya sa ta hanasu Amina tafiya. Ruwa aka yi sosai, sai 5 ruwan ya tsaya. Aunty Zainab babu yadda ba ta yi da su Amina su tsaya su kwana ba Amma Amina taki.
Kasancewar ruwan da aka yi hakan ya sa suka samu tsaikon abin haka. Har Magriba ba suna tsaye babu mota. Da yake gidan Aunty Zainab ya na a bakin titi ne, Amina kallan get din gidan Aunty Zainab ta yi ta ce " Anya ko dear ba gidan Aunty Zainab za mu koma mu kwana b..."
Amina bata rufe baki ba wata tsaleliyar mota ta saya kusa da su. Matashin saurayin tambayarsu ya yi Ina za su. "Cikin gari zamu shiga." Ku shigo mu tafi nima can na yi."
Shiga suka yi ya ja suka tafi. Koda suka shiga cikin garin Katsina tambayar sunan layin su Amina ya yi, nesa da gidan su Amina ya yi parking ya saukesu, inda Amina ta bukata. Suna sauka yana son yi masu magana amma Amina bata bashi damar yi masu magana ba ta ja hannun Mansura da sauri suka wuce.
A baya ya bisu ya ga gidan da suka shiga kafin ya dawo.
Abba a kan idonsa aka sauke su Amina a mota zai shiga sallar isha'i kenan.
Amina Kuma bayan sun shiga gida, kallan Mansura ta yi ta ce "Dear Yaya Abba zai tambaye mu dalilin da ya sa muka Kai dare, idan muka ce mai mun fito za mu tafi kenan, aka fara ruwa zai yi fadan me ya sa muka Kai la'asar, dan haka ce mai za mu yi tun da mu je ake ruwa." Da "to". Mansura ta amsa ma Amina suka shiga gidan.
Koda suka shiga kan dadduma suka iske Mahaifiyar Amina, bisa ga alama sallar issha'i ta idar.
Mahaifiyar Amina dago kanta ta yi ta kalli Amina ba ta ce mata komai ba ta maida kanta kasa.
Amina zama ta yi tana fuskantar mahaifiyarta, cikin sanyi kamar za ta yi kuka ta ce "Mama Wallahi ki Kira Aunty Zainab ki ji muna fitowa aka tsuge da ruwa, kin ji dalilin da ya sa muka Kai dare."
"Amina, ba tun yau ba kinsani bana son kai dare, nikam babu ruwana tsakaninki da yayanki, ko kafin ku fita sai da ya jaddada miki karku Kai dar..."
Sallamar Abba ya sa Mahaifiyar Amina yin shiru.
Mansura ko da ke tsoran Abba, hakan ya sa ta tashi zata shige bangaransu, jin sallamarshi. Har ta tafi Abba ya dakatar da ita ya ce "Ke."
Mahaifiyar Abba kallan Abba ta yi ta ce "A'a Abbana, laifin Amina ne ita bata da laifi in da ba ta san dokar gidan nan ba. Mansura tafi abinki."
Mansura saida ta sauke ajiyar zuciya tsabar jin dadi.
Abba cikin fushi irin Wanda Amina ta sanshi da shi ya ce "Amina waya kawoku a mota?."
Amina kallan mahaifiyarta ta yi tana langabar da kai ta ce "Mama Wallahi tun da muke je ake ruwa, shi ya sa muka rasa mota, shine dalilin da ya sa ma Koda ya yi Mana ta yi ma muka shiga motarsa ganin dare ya yi."
Marin da Abba ya kaima Amina ne ya sa ta yi shiru ba tare da tasan ta yi shiru ba. Hannu Abba ya daga da sunan Kuma Kai Mata wani Marin mahaifiyar Amina ta rike hannunsa ta ce "Abbana inda ta ce ruwa akayi akwai uziri."
Abba Kai ya girgiza ya ce "Wallahi mama karya take acan na yi sallar ajahar sai 3::00PM Na bar garin, Kuma lokacin haɗarin ba wani sosai bane bama. Kin ga sai yamma kila ma aka fara ruwan."
Abba shako wuyan Amina ya yi ya ce"Su waye suka saukeku a mota?." Amina ihu take tana ba Abba hakuri. Wanda ko jinya baya yi, dan shi babu abin da ya tsana Kamar yaga yarinya na yawo a motar saurayi, atunaninsa haka yana taka mahimmiyar rawa wajan lalacewar tarbiya. Hakan ya sa Abba ya shake Amina Yana cewa "Ba zaki fada min ba su uban waye suka daukeku a mota?."
Amina ko zare ido kawai take ta kasa magana yadda ya shaketa.
Allah sarki uwa, mahaifiyar Amina kasa jurewa ta yi,ta kamo hannun Abba dake wuyan Amina ta yi ta ce, "Abbana, aika shaketa ba zata iya magana ba, ka saketa sai mu ji Wanda ya daukesu a motar."
Abba sakin Amina ya yi wadda yana sakinta ta samu damar fashewa da kuka. Mahaifiyar Amina Kuma, tsawa ta yi ma Amina ta ce "Dan ubanki ba za ki fada Mana uban waye ya daukeku a motar ba?."
Cikin kuka Amina ta yi masu bayani ta hada da cewa "Wallahi yana kawo mu yana tambayarmu Number waya, Amma ko sauraransa ba mu yi ba muka tafi."
Abba Kai ya jinjina ya ce "Daga nan har ki bar gidan nan Allah ya sa wani dan isa ya Kara kawoki a mota, Wallahi tallahi ranar ba za a gane kamanninki ba." Yana fadin haka ya fita ya bar falon baki daya.
Mahaifiyar Amina Kuma fada ta Kara yi ma Amina.
Amina da kuka sosai ta shiga bangaransu, inda ta iske Mansura sai zare ido take, kallo daya za ka yi Mata kafahimci a tsorace take.
Amina fadawa ta yi kan gadon tana kuka.
Mansura dai bubbuga bayan Amina taita yi tana Kuma bata hakuri. Amina ta dade tana kuka kafin ta tashi tana nuna ma Mansura wuyanta ta ce "Dear duba min wuyana ki ga bai ji min ciwo ba?."
Mansura duba mata ta yi, cikin tausaya Mata ganin yanda wajan ya yi ja na rikewar da ya yi Mata ta ce "Sorry dear."
Ranar nan dai haka suka yi barci babu wata hirar kirki, uwa uba Kuma ga sanyi damuna, ga Kuma bacin ran dukan Amina hakan ya sa da wuri suka yi barci.
Washegari, misalin karfe 7:00AM, mahaifiyar Amina ta samu Amina har dakinsu, bayan sun Kuma gaidata ta kalli Amina ta ce "Amina, Ina fatan Ahmad ya sanar da ke yau danginsa za su je wayan 'yan uwan mahaifinki naiman auranki?."
Amina zaro ido ta yi tana mamaki dan ko yau shi ya tadata sallar asuba Amma bai fada Mata ba.
Mahaifiyar Amina Kuma jin Amina bata ce komai ba, ta ce "Amina, ba da ke nake magana ba?."
Amina cikin sanyi ta ce "A'a Mama bai sanar min ba."
Shiru mahaifiyar Amina ta yi kafin ta ce "Tom Ina fatan babu wata matsala?." Eh, mama Babu." Cewar Amina.
Ajiyar zuciya mahaifiyar Amina ta sauke ta ce "Tom ma Sha Allah." Sannan ta tashi ta fita.
Mansura gaba daya jikinta sai ta ji yayi sanyi, tana tunanin yadda zata ci gaba da zama gidan idan Amina ta yi aure. Amina lura da tunanin da Mansura ta fada ne ya sa ta dafa Mansurar.
Mansura kallan Amina ta yi, ta yi murmushi ta ce "Amarya, Allah ya kaimu lokacin." Ameen, dear kema Allah ya fito miki da naki ayi tare, bana son in tafi in barki a gidan nan ke kadai, Ina nan ma kullum cikin ƙoƙarin sama kanki damuwa kike Ina ga bana nan."
Mansura sosai jin maganar Amina za ta yi aure ta daga Mata hakankali, dan tana tunanin yadda za ta rayu gidan babu Amina, Ina bata jin ma zata iya ci gaba da zama babu Amina.
Take Mansura ta fara waye wani kan wani.
Amina jin kamar shashshekar kuka da sauri ta dago tana kallan Mansura. Bata fuska Amina ta yi ta ce, "Haba, Mansura yanzu Kuma anan meye abin kuka, auran da ko sashi ma ba a yi ba, yau ne za a sashi, Kuma ke baki fatan Allah ya kawo mik naki kafin mawa a hada a yi."
Ai Amina kamar ta ziga Mansura fashe Mata da kuka ta yi.
Amina baki ta saki tana kallan Mansura, ganin abin da gaske take ya sa Amina ta fara lallashinta ta ce "Ki yi hakuri dear, nima bana son in tafi in barki ke kadai ne, in sha Allah ni Kuma na yi miki alkawari har sai kin samu miji ko zan yi aure, zanma Yaya Ahmad magana a sa lokacin da tsayi har lokacin da Allah zai fito miki da naki kema."
Amina ta dade tana baansura baki kafin ta yi shiru.
Misalin 5:00PM kanin mahaifinsu Amina ya yi sallama ya shigo falon mahaifiyar Amina. Bayan sun yi gaisuwa mai tsayi cikin mutuntawa da mahaifiyar Amina, ya dora da cewa "Tom Alhamdulillahi, baki sun iso kamar yadda suka ce. Duk wani Abu da ake bukata na sa ranar aure kudi suka bata gasu a hannuna. Mun sa ranar aure wata uku cif-cif, ya kika gani?."
"Haba baban yara, ai duk yadda kuka yi Wallahi ya yi, sai dai mu yi fatan Allah ya kaimu lokacin. Kayan aure Kuma kar kice tsaki takura ma kanki, ki bar Komai a hannuna da Abba za mu yi."
Godiya sosai mahaifiyar su Abba ta yi mashi, kafin suka yi sallama ya tafi.
Bangaran Amina da daddare suna waya Ahmad ya ke sanar da ita lokacin bikinsu da aka sa musu. Amina zaro ido ta yi jin ya ce Mata wata uku. Tom Amma Kuma tana tsoran ta yi wata magana Mansura ta ji hakan ya sa ta yi shiru ta bari ta yi ma mahaifiyarta magana, inda akwai fahimta sosai tsakaninta da mahaifiyarta.
Washegari, Amina ta samu mahaifiyarta da maganar. Amina kanta a kafadar mahaifiyar tata kamar za ta yi kuka ta ce "Mama ni dai lokacin auran nan da aka sa gaskiya ya yi kadan, dan Allah mama ki yi ma Yaya Abba magana ya yi ma Baban yara magana a Kara."
Mahaifiyar Amina dago da kan Amina ta yi tana kallanta, dan ta gasgata abin da Amina ta ce.
Shiru mahaifiyar Amina ta yi, kafin ta ce "Kamar ya wata uku ya yi kadan?."
Amina kamar za ta yi kuka, ita dai duk dan mahaifiyarta ta sausaya Mata ta yadda da kudirinta ta ce "Mama kin ga idan na tafi na bar Mansura ba za ta ji dadi ba, da ni kadai ta saba a gidan nan. Amma kin ga yanzu idan aka Mai da shekara kafin itama Allah ya bata nata sai a hada a yi."
Mahaifiyar Amina kallan baki da hankali ta yi ma Amina kafin ta ce"Amina ke ma lokacin da ta zo gidan ai ba sabawa ta yi da ke ba, sai a hankali-a hankali kuka saba, muma a hankali-a hankali za ta saba da mu daga taga baki." Ni dai gaskiya mama bana son in tafi in barta."
Amina ta fada tana share hawayanta, ita dai duk dan mahaifiyarta ta tausaya Mata ta barta ganin bata son kukanta.
Mahaifiyar Amina ido ta tsura ma Amina ganin tana share waye. Hannu tasa ta goge hawayanta ta ce "A'a abun ai Bai Kai haka ba Amina, kin ga Abba shi ne abokin Ahmad, Kuma lokacin da aka sa auran ba daga kowa ba ne daga Ahmad ne, shi ya bukaci haka, dan haka ki je ki samu Abba ki yi masa magana ya yi ma Ahmad magana a d'aga lokacin auran har zuwa lokacin da Mansura ta samu muji itama✍🏻
Fadila Sani Bakori ce.
https://chat.whatsapp.com/LGosWoHsPkj3rhf9EbKjrK
⭐ABBANA⭐
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
Daga Marubuciyar 👇🏻
*Fadeela
*Oga Habib
*Meenalyn Daddy
*In da rai
*Abdurrahim
*Daga Allah ko d'ora ma Kai
*So ne sila
*Rayuwar Haidar
*So ne sila
Domin samun littafin ABBANA daga farko 👇🏻Follow the ABBANA channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaYZGsNEFeXsr1CKQl3r
P 9-10
Amina da zummarta ta tashi ta nufi bangaran Abba, zata shiga Abba Kuma zai fito ya yi shirin aiki. Amina cikin girmama yayan nata ta gaidashi ba Kuma kamar yau ba da take naiman alfarma agunsa. Abba amsawa ya yi yana kallan Amina, wadda yanayinta ya nuna tafe take da magana.
Amina kallan Abba ta yi da shima ita yake kallo ta ce"Yaya Abba, dan Allah ka koma ciki za mu yi magana." Abba agogon hannunsa ya kalla ya ce "Amina, lokaci ya ja zan makara aiki, ki bari in nadawo sai mu yi maganar."Tom yayana Allah ya dawo da kai lafiya."
Amina na fadin haka ta juya, da Sauri-sauri itama ta yi breakfast ta tafi aiki.
Ya zamana gidan zai Mansura kadai, wadda duk lokacin da aka barta ita kadai kadaici sosai yake bankado mata rayuwartar. Ba kamar yau ba da gaba daya ta hana kanta sukuni tun da ta ji maganar auran Amina, gani take ba zata iya zama babu Amina ba, dan a iya tunaninta darajar Amina ma ya sa aka barta ta
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 15