An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
Sunana Asma’u Shahada, Mahaifina Dan sanda ne Wanda ya taka Har matsayin CP that’s commissioner of police, sede yayi retire a halin Yanzun. Amma dukda haka baya zama saboda shi mutum ne me kazar kazar, he’s a patriotic citizen, never believe in zaman banza. yana da gonaki inda shi ne invest dinsa, to kusan kullum se yaje, hakan yasa koda yayi yayi retire amma bai huta ba
.
Asalinmu Yan Taura ne ta Jigawa, cikin garin Kwalam, kakanni na a Kwalam suke. Malam Aminu shi ne kakana da ya haifi Mahaifina, manomi ne sosae, if I can say Abba anan yayi gadon noma, Don idan kaje kofar kudu kace gidan Sarkin Noma, don’t be amaze amma kowa ya sanshi. Inna Ade ita ce mahaifiyar Abba, sunanta Sa’adatu, so se aka cire karshen Sa’ade ake kiranta Ade. Nasha ayyanawa da kuma tunanin yadda akai har zaman Alhaji da Inna Ade Yayi wannan doruwar. Alhaji mutum ne me hakuri da kauda kai, bazaka taba fahimtar fadanshi Ko Maganar shi ba cuz the tone is always same. Inna Ade kam! Jarabar duniya, matar tana da fada na bugawa a Jarida, so far, zan iya cewa akwai possibility din Tasha ruwan Atafi da ake fada saboda sunyi zaman hadejia. Lol. Amma duk wannan hayaniyar tata, bana gani saboda muna mugun good time da ita, Tana sona kuma tana fito na fito da duk Wanda ya nemi takurawa rayuwata, koda Abba ne ko Ummaah, Yanzu Yanzu zata wanke su tas tas, su da suka haifeni kenan balle kuma yan uwana da ba ganinsu take da gashin Kai ba, wannan ai sede dan kansu su bar mata gurin. I knew her Best side so far.+
‘Ya’yansu takwas, Hajiya Uwani ita ce babbar yayarsu Abba, Tana aure a Majia ta Taura garinsu Nanaye. Tana da Yara wajen goma, kuma baki daya matar photocopy din Inna Ade ce plus Wasu mugayen halayenta Wanda basuda asali bare kuma tushe. Daga ita se Abba shi ne Shahada, kuma Mahaifina, na yadda partially da mutane su kace ana inheriting Uwar miji a gurin haihuwa, yeah akanmu Hakane. Abba shi daya Shi ne namiji, surrounded by sisters, haka nan Ummaah, kuma haka muke a gurinta.
Daga Abba se Umma Falmata, Tana can Adamawa anan take aure, dake Inna Ade asalinta daga can take. Asalin bafullatana ce, bansan yadda akai ta aura Alhaji ba, har ya dakko ta tun daga Uwa duniya Har Kwalam. Mabiyar ta Anty Hauwa ce, boss kenan, se Anty Shamsiyya , Anty Mero sai Anty Rakiya da Adda Ummiey wadda ita ce autarsu, kuma a gidanmu ta tashi, Dan Saar Adda Habiba ce, Tare akai musu aure abinsu.
Sauda Ummaah bakanuwa ce ‘yar koki, mahaifanta dukkansu yan nan cikin kanon ne. Ummaah ita kadai ce mace a gidansu, dukkan Yan uwanta maza ne, amma Dayake Allah shi yake tsarinsa bakwai daga cikinmu Duka mata ne se namiji daya tal. Babbar yayarmu Adda, Tana aure anan Kano, wani yaron Abba ta aura, me bi mata Yaya Halifa, sunan Alhajin Kwalam ne dashi shiyasa sunanshi yake a boye. Shidai baiyi aure ba se Karatu kamar zai cinye Boko, Yayi degree, Yayi Msc, banda PgD da yayi, da courses kanana kanana. Yanzun Haka PhD yakeyi. Duk gidanmu ni ce nafi shiri dashi saboda Ina son Karatu, I find joy and happiness in studying. Wannan yasa na zama Kamar kawarshi, I enjoyed been with him. Adda Sa’ada ita ce takwarar Inna Ade, as we all know a gida idan kana da takwara you seems to be in the most goodest relationship da ita, wannan karya ne when it comes to Inna Ade and Adda Sa’ada basu shiri Ko na mintina daya, hardly ka gansu tare. Tana aure a Niger state, Adda Habiba Saar Adda Ummiey ita ce a dutse, se Adda Meeyna, Adda Salma da Adda Maryam se ni kuma auta Kare nono as they always call me.
1995 aka haifeni, Ummaah da Inna Ade, sun bani labarin ranar da zaa haifeni, ranar kawar Inna Ade wadda ita ce Asma’u. Kawarta ce sosae, tun suna Yanmata Har seda akai musu aure. Kunsan aikin police federal aiki ne, so transfer Ko da yaushe ana cikinta. Amma lokacinda Ummaah ta samu cikina, shi ne lokacin da Abba yake ASP a kano, I was lucky baayi tafiye tafiya da cikina ba.
Ranar Alhamis ce, dake Inna Ade, in har Ummaah Nada ciki to duk sati se Tazo, Har Se Ummaah ta haihu kafin zata tattara ta tafi, wannan zaman an dinga balai da ita, musamman itada Adda Sa’ada, wani lokacin Abba ke raba fadan. Ile kuwa ranar sun gama yinta, Adda Sa’ada tayi girki Inna Ade tace Allah ya kasheta, ita tuwo zataci, Adda tace ita kuwa kitchen ta gama shigarshi a wannan ranar sede Inna tayi da kanta.
“Saude Saude! Ki fito Ki raba Dani da wannan shedaniyar yar taki”
Ummaah na daki, ita kadai tasan halinda take ciki, ta jiyo kiran da Inna Ade ke yi mata, Ta sani Ko Baa fada ba, Adda Sa’ada ce kawai Inna zata dinga ihu akanta. Gaba daya ta jike da gumi sharkaf, ta fito da kyar, daidai karasowar Inna Ade, Tana mitar rashin amsata da Ummaah tayi, kicibis sukai, abinka da Manya tana kallon fuskar Ummaah, tasan nakuda take, babu bata lokaci ta saka wani cousin din Abba, kawu balarabe wanda ke zaune gidanmu Ya dakko Mota suka wuce asibiti.
Ana karbar ta, Inna ta saka a sanar da Abba, Allah Ya taimaka ya tashi a aiki, hakan yasa ya nufo asibitin, Babu jimawa aka fito Dani cikin zani an haifeni, Inna Ade tace min kwatakwata da karbata baifi mintina uku ba, sakon rasuwar kawarta Asma’u ya iske ta. Ta shiga Tashin hankali marar misaltuwa, Inna Ade tayi ta kuka Abba yana lallashinta. Duk yadda akai ta hakura amma taki, se fadin
“Shahada, idan zaka saka a kaini Jimeta ka saka, idan baka sawa ka barni na tafi! “
Babu yadda ya iya haka yasa a ranar aka tafi da ita Jimeta. Seda akai kwana uku sannan ta dawo. Tana dawowa kuwa tace lallai sunan aminiyarta Zaa maida min. Ranar da na cika kwanaki bakwai aka rada min sunan Asma’u, Inna Ade tana cemin FARA ‘YAR SHEHU!
Na tabbatar once a rayuwar Abba da Ummaah, Sunyi regretting saka min wannan sunan, ba Dan komai ba se Dan Inna Ade. Duk weekend din duniya tana kano Tare dani, as I heard, bakina da sunanta Ya Fara budewa, sunanta na Fara kira.
Nayi shekaru biyu aka bawa Abba commissioner of police, sannan aka masa transfer zuwa Taraba state, inda anan ne Zaiyi commissioner din. Aka kammalla dukkan shirin tafiya, amma Inna Ade tayi tsalle tace babu me tafiya Dani, a gurinta zan zauna. Inna Ade yar daru ce ta gaske, waye Zaiyi musu Abba ko Ummaah? Babu. Haka aka tattara ta tafi Dani Kwalam su kuma suka wuce Taraba abinsu.
Da wannan rayuwar na tashi, babu Wanda na sani se Innata, a Haka Har na Fara Wayo nakai shekara hudu, duk lokacinda Abba yazo da niyyar tafiya Dani Dan Ya sani a makaranta, Se Inna ta Fara kuka,
“Shahada akan yarka zaka nuna min iyakata? “
Ummaah ta lallabashi Badan ransu yaso ba, suka kyaleni a gurinta, amma seda aka kaini central primary school dinsu. Ni mutum ce me wasa da kiriniya, I pay attention to nothing, so ko da mukai exams, it was beyond comment, ni na dakko ajin. Abba Kamar Zaiyi kuka Dan takaici, Yaya Halifa kam Kirirkiri Ya fito sukai ba dadi shida Inna Ade, bata kulashi ba saboda Tana yawan cewa, ita tasan darajar miji, so shi yana cin darajar sunanshi Aminu.
A Haka rayuwa ta cigaba da gungurawa, kullum hankalin iyayena yana kaina, as for me duk tunanina Inna ta haifeni, su ina daukarsu kawai yan uwanmu, Kamar yadda naga Sauran na zuwa. Seda nayi shekara bakwai sannan nayi wata rashin lafiya wadda seda muka kwanta a Aminu Kano. Munfi wata sannan na samu sauki, wannan shi ne asalin dawowata gidanmu, Inna ta hakura a cewarta kada mayu su lashe mata kurwata. God so kind!
Surprised? Ooooo
Ayshatuuu
Bayan dawowata abinda aka Fara kokarin yimin, shi ne makaranta. Dayake lokacin Ummaah ta gaji da binshi, se sukai settling baki daya a kano, shi kuma Yana zuwa ya koma. Adda Maryam kadai ke primary lokacin, itama kuma Tana Basic 5, a excel college. Spring aka kaini duk dan na dan farfado daga asarar da akai, Basic 1 aka kaini, amma matsalar ko two letter words ban iya ba. Bazan taba manta wannan abin ba.1
Ranar da aka Fara kaini school din, Inata murna abuna, saboda uniform din kawai birgeni yake, ga lunch box dina, Ummaah ta shake shi da chips, ga Caprisonne. Oolala! Yaya Halifa ne ya Fara kaini, seda ya rakani Har class sannan Yayi min kashedi, tareda fadawa uncle din ya saka min ido sosae, Aikuwa Ya saka, dan na amshi wuya hannun bawan Allah nan.
Abinda ya Fara sakawa na karaya nafi kowa girma a ajin, saboda Inada Girman jiki, ga yawanci duk sun iya turanci ni kuwa daga come and go babu abinda na sani, gashi Baa vernacular a school din. Se ya zamana idan na shiga har a tashi bana magana, saboda na taba gwada surutu da Hausa, aka fadawa uncle Ya zaneni. Tun daga lokacin na daddara bana taba gigin yin surutu.+
Idan na dawo gida bayan an tashi lesson, islamiyya ce zamu tafi nida su Adda, bazamu dawo ba se 5:30. Da anyi Sallar Maghrib, Yaya Halifa zaizo da Belt in dakko books dina, ina kuka Haka Zamui homework dina sannan ya koya min sabon abu, wannan belt din na gefe, bawai dukana Zaiyi ba amma ita ta barazana ce. Karshen dukan shi ne rankwashi. Duk yadda nake son kallo musamman cartoon banayi, ana gamawa zanyi Sallar ishai na kwanta. Cikin sati biyu gaba daya na fita a hayyacina saboda ban saba irin wannan rayuwar ba. Rayuwar Kwalam babu sawa bare takurawa, kullum se nayi kukan zan koma gurin Inna amma babu me kulani, se idan Boss din gidan tana nan Adda Salma ta bubbuge ni, so shirina da ita kadan ne.
Ana haka aka kawo wani new student, Emma a class dinmu, Shi duk yafi mu, gashi azzalumi babu hasken musulinci tattare da yaron nan, tunda yazo shikenan Sauran walwalar da nake da ita ta tafi. Ya rigada ya gane ban iya turanci ba kuma ko yayi min abu I can’t express myself hakan yasa yake cin zalina shida gang dinsa. Ranar duka gida aka makara, so ko breakfast bamuyi ba haka muka taho se daga baya Ummaah ta aiko driver ya kawo min Abinci, Inata murna saboda azabar yunwar da nake ji, amma ina karbowa Emma da mutanenshi suka karbe abincin, Ina kallo suka cinye, Aikuwa Na dinga kuka na tafi gurin uncle, it was embarrassing. Ina zuwa yace min
“Asma’u what happened? “
Gaba daya na diririce saboda bazan iya cewa “He ate my food” ba haka na gaji da tsayuwa na koma na zauna. Shikenan suka gane lagona Har dukana suke, gashi ni kuma a gida haushin kowa nakeji, ina ganin duk su suka jawo min, da ace Ina Kwalam waye zaimin haka? Ai babu shi idanba so yake yaga kaddamarwar Inna Ade ba.
Da sassafe Adda Meeyna na shirya ni, Inata kuka, kallona tayi tace
“Menene Wai? Yau kwana uku kenan kullum se Kinyi kuka. Makarantar ce baki so? “
Kaina na gyada, Wasu hawayen na sakko min nace
“Ni bazanje ba Adda zazzabi nake”
Wuyana ta taba sannan tayi dariya tace
“Yar gidan Inna, babu wani zazzabi fa, kede kawai kin zama yar baci”
Muna haka Adda Sa’ada, service take anan Kano, kuma mijinta ya tafi wani official assignment a Urk, ta shigo tana fadin
“To! Autar Ummaah me ya faru? “
Nan Adda Meeyna ta fada mata yadda mukai da ita. At this stage, iyaye ya kamata ku lura da wani abu, bullying yafi karkata a primary school, sosae Wanda suka fi karfinsu suke zaluntar su. Shiyasa yaro zai dinga kukan makaranta, saboda Wasu lokutan Yaran Zaa iya threatening dinsu su kasa fada, ya kamata kowacce Uwa ta zama alert.2
Shiru Adda Sa’ada tayi sannan ta kama hannuna muka fito, Ummaah ta fito dauke da bag pack dita, ganin fuskata kacekace da hawaye yasa taja ta tsaya, fuskarta da damuwa tace
STORY CONTINUES BELOW
“Uwata” Kamar yadda take kiran Adda Sa’ada, da yake Baa boye mata sunanta, “Me Ya sameta? “
Inajin tayi wannan tambayar na kara kwabe fuska, Inata kuka, Inaji Adda Sa’ada nayi mata bayani, dake Ummaah classroom teacher ce, take ta fahimci abinda yake faruwa. A ranar tare dukka mukaje school akai complain, haka a gaban class aka Zane Emma, shikenan na samu sauki, kuma na dage na Fara turanci, idan nayi ai tayumin dariya amma a hankali da taimakon family na, na samu nake iya hada sentence.
Har term din ya kare babu Inna Ade babu dalilinta, haka muma bamu samu Munje Kwalam ba, in banda Ummaah da Abba, nayi mitar nayi kukan har na hakura abuna. Ranar da akai Hutu na dawo Inata murna Dan zan dan huta at least, Tundaga tsakar gida nake jiyo muryar Inna Ade, matar is very lousy, inhar tana guri some miles away zaka dinga jiyo muryarta, bansan lokacinda na sake lunch box dina da school bag ba nayi parlor a guje ina fadin
“Inna Ade! “
Kanta na fada nayi mata wata runguma me karfi, itama rungumeni tayi tana shafa jikina tareda fadin
“Fara ‘yar shehu, Asma’u Sannu “
Sakinta nayi na dawo gefenta na zauna nace
“Inna Ina yini? “
“Lafiya lau, “
Tana magana Tana assessing jikina, se naga ta bata fuska ta kalla sashen da Ummaah take, zuwa lokacin na fahimci har Abba dasu Adda suna zazzaune Kamar Wanda ake wani karamin meeting.
“Saude amma Kinsan ba haka na kawo ‘yar shehu ba Ko? Ta Yaya na baku yarinya da kibarta Yanzun Nazo Naga kashi da rai? “
Ni Kaina seda nayi dariya, balle kuma su Adda, amma Ummaah tsakani da Allah Ta Fara kokarin kare kanta. Nanfa Inna ta hau sababi, ita kafata kafarta bazata barni anan ana cuta ta ba, Abba da Ummaah se hakuri suke bata. Se ka rantse da Allah ita ta haifeni, basu suka haifeni ba. Inajin wannan Maganar na Fara murna Dan tabbas a lokacin babu abinda nake adawa dashi kamar zaman gidanmu.1
Halayena Wanda na aje a kofar gida lokacinda zan dawo daga Kwalam su na bude, sabon shafin rashin mutunci, saboda I’m sure babu Wanda ya isa Ya taba ni tunda Inna Ade na nan, islamiyya na tattara na aje, Da daddare nayi ta rigima se nayi kallo, sannan da safe se eleven nake tashi. Babu Wanda ya cemin ci Kanki, se ana gobe Inna zata tafi, mun kammalla breakfast tace da Abba Wanda ke kokarin fita
“Shahada, gobe zan tafi Maganar Asma’u Fara da ita zan tafi.”
Abba ya bude baki Zaiyi magana yaga har ta tashi ta tafi, Nima gudun abinda zai biyo baya na take mata baya zuwa dakin da yake nata, Dan tun zuwanta na tare a can.
Adda Sa’ada ce ta mike ranta a mugun bace ta nufi dakin Yaya Halifa bansan abinda tace mishi ba, all I know ina kwance naji sallamar Adda Maryam, amsawa nayi sannan ta shigo, tareda tambayata inda Inna Ade take, bandaki na nuna ba tareda na furta komai ba, kanta ta gyada sannan tace min Yaya Halifa na nemana. Wata muguwar faduwar gaba naji, saboda babu Wanda nake Tsoro, har cikin raina kamar shi da Adda Salma. Mikewa nayi jikina a matukar sanyaye na nufi dakinshi.
Da sallama bakina na isa, yana zaune gabanshi Wasu manyan text books ne, se wata dorina me Baki biyu a gefe. Jikina Se ya Fara rawa, naji tamkar na ruga gurin Innata amma who born me? Da kuwa Yayi min dukan mutuwa. Tsugunnawa nayi a gabanshi bakina na rawa nace
“Yaya gani”
“Na ganki” ya furta ko kallona baiyi ba, nafi mintina goma a Haka kafin ya daura kafafunshi akan table din yana kallona yace
“Idan Inna zata tafi gobe zaki bita? “
Shiru nayi saboda bansan right reply ba, zuciyata kowa yasan Inna Ade take son bi, amma wannan Zakin dake gabana, I don’t think zan iya fadar son raina. Ina tunani Ashe har ya dauki dorinar, sede jinta nayi a kafafuna dana mikar, wani tsalle na buga saboda azabar radadin da naji tareda bude baki zanyi ihu,
“Idan kika bari naji Kinyi Ko tari ne, se na karkarya ki na zubar anan. Dawo ki zauna”2
Its funny gaskiya, jiki na rawa na dawo na zauna inajin yadda kafafuna ke zugi, yaye skirt dina nayi, abinka da fara tuni gurin ya tashi Yayi jawur, hawaye tamkar an bude famfo haka ya dinga zubowa, kafin wani lokaci fuskata tayi jawur. Sakkowa yayi ya zauna gefena yace
“Kinsan idan na kara jin kince zaki koma Kwalam, wannan bulalar se ta karye a jikinki, kuma Yanzunnan kije Kicewa Inna bazaki bita ba”
Kaina na gyada cikin sauri sannan na mike, kamar haske har na isa kofa Ya dawo Dani akan na wanke fuskata. Ina Naga ta musu, toilet dinshi naje na wanke amma kana kallona zaka San nayi kuka, nasan idan Inna Ade ta ganni a Haka, kilan kashe Yaya Halifa zatayi hakan yasa na wuce dakin Ummaah na kwanta, ranar anan na kwana.
So you guys where truly waiting for me! I got it. Thank you so much for the comments and prayers! I got you
AyshatuuuA ka’ida tafiyar Inna da sassafe take yinta, duk inda goma take to ta kama hanya, Haka idan zuwa zatayi da sassafe take zuwa. Tunda mukai Sallar asuba, Ummaah ke harhada min kayana, ranta a mugun bace, I can swear cewar ban taba ganin fuskar ta a Haka ba, saboda ta kasance mutum ce me faraa, hardly kaga ranta a bace.
Ina kwance ni kuwa Bance mata komai ba, seda ta gama sannan ta dubeni tace
“Tashi kiyi wanka”
Ban Musa ba, na tafi bandaki nayi jika jika Kamar yadda na saba na fito. Da kanta ta shafa min Mai ta shirya ni sannan muka fita zuwa parlor, Har an hada breakfast, Yana aje an baza katuwar dining mat anan parlor, komai an kawo se ci Ya rage. Zama nayi gefen Inna da ta gama amsa gaisuwar Ummaah dukda an rigada an gaisa Tun asuba. Tana ta bani labarin kawayena na Kwalam, da yadda suke dokin dawowata amma ni jinta kawai nake, muna nan Sega su Adda sun fito kusan lokaci daya gaba dayansu, se Yaya Halifa fuskarshi a murtuke ya samu guri ya zauna yana wurga min harara, cikin rashin saa Inna ta lura da hararar, kawai gani nayi ta dada mishi Duka a bayanshi tareda fadin
“Dan banza kawai, uban me tayi maka da safiyar nan zaka kafa hararar ta? Dole yarinya tabi ta lalace, kun saka ta a gaba kamar mayu”+
Idaanuna sukai raurau alamar kuka, su kuwa banda dariya babu abinda suke, a Haka Abba da Ummaah suka iske mu, abincin duka babu wani armashi haka mukaci, ana gamawa Inna ta dubeni tace
“Maza Kawata tashi dakko kayanki kizo mu tafi”
Kowa a parlon zuba min idanu yayi, suna jiran ganin abinda zanyi. To everyone utmost amazement kallonta nayi nace
“A’a Inna Ade, kije ni bazanje ba”
Wani mugun kallo Tayi min zatayi magana se kuma ta juyar da kanta zuwa inda Adda Sa’ada ke zaune hannunta da tea mug tana kurba,
“Ahaf! Ni nasan zaayi Haka, wannan yayan suna gidannan ai na daina ganin daidai. Sa’adatu da Aminu ba. Nagode sosae Kunyi kokari. Amma ku sani Fara ‘yar shehu Ko kunso Ko kun ki tawa ce, barazanar ku babu abinda zatayi mata! “
Tana gamawa ta Mike tareda kallon Abba tace
“Zan wuce Shahada”
Abba da Ummaah Wanda suka rasa bakin magana suka mike tareda bin bayanta, Nikam dakin Ummaah na koma Inata kuka, wayaga samu da rashi.
A hankali rayuwa ta cigaba da tafiya na hakura da zancen zuwa Kwalam na rungumi sabuwar rayuwar dake gabana. A wannan hutun sosae nayi Karatu, Yaya Halifa ba karamin kokari Yayi a Kaina ba. Babu Wanda yake min magana da Hausa seda turanci. Kafin Hutun ya kare har na Fara mayarwa. A bangaren islamiyya shima sosae nake abin kirki, hakan ba karamin dadawa su Abba yayi ba, shikenan aka daina takura min, tunda na riga nayi blending da yadda suke son na zama.
Duk Hutu idan akai Zaa kaini Kwalam nayi sati daya sannan na dawo. A Haka shekaru sukai ta ja har nakai shekaru goma sha biyu, lokacin ake ta cukwukun kaini secondary school. Matsalata daya ce wadda kusan kullum se anjini da Ummaah da Sauran sisters dina, bana Aikuwa, I’m very lazy, laziness dina Har ya saka jikina kanshi na gyara se ya zama abu, wanka se Ummaah tace min naje nayi, balle gashina, se nayi sati biu ban taje shi ba, idan aka samu nayi kitso zan iya 3 months ban tsefe ba. Kuma nafi kowa Baki idan akace Ni kazama ce, kuma deep down inside me nasan ni kazama ce, kuma san jiki shi ne ummul aba’isin kazantar.
Wani yammaci mun dawo daga islamiyya nida Adda Salma da Adda Maryam, tunda muka taho bakina yake a cunne Kamar Karin kunama, saboda Adda Salma tace kaina yana wari, Bance komai ba Har muka isa gida. Ina shiga dakinmu na tarar da kayana duka na cikin wardrobe an fito dasu an watsar a tsakiyar dakin.
Takaici kamar zanyi me, ciki na karasa Ina bin kayan da kallo, gaba daya an cakuda wankakku, gogaggu da masu datti. Idanuna taf da kwalla nayi kofa zan Kai Kara naji an bude kofar toilet an bude, komawa nayi, Adda Meeyna ce hannunta rikeda face towel tana goge wet face dinta.
“Yawwa kwashe
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 1 Chapter of 18