na karasa jiki a sanyaye na dauki wayar tareda karawa a kunnena nace
“Barka da dare Sir”
“Barka dai Asmau. Ya saukin jikin?”
Se dana kalla kaina kafin na amsa masa da sauki se kuma mukai shiru dan nidai bansan me zance msa ba kuma baya son godiya. Hakan yasa nayi shiru. Se can yace
“Kiyi bacci and ki tabbatar kinci abinci”
Kamar wata doluwa haka na shiga gyada kaina in agreement amma sede bama gani na yake ba balle, seda yace
“Huh! Asmau?”
Sannan nace
“Inshaaa Allah Sir”
STORY CONTINUES BELOW
Daga haka mukai hanging, wani irin raruma nayiwa wayar taredq rungume ta a kirjina inajin wani farin ciki marar misaltuwa. Murmushi kuwan from ear to ear kamar bakina zai yage. Can kuma na kashe wutar tareda yin addua na kara lula duniyar tunani a haka daddan bacci ya daukeni, it was peaceful dan ko mafarkan da nayi where of love. Dan haka da asuba dana tashi komai lafiya lau jikina ba wannan rashin kuzarin se ma wani karfi da nake ji. Hakan ya bani mamaki amma a kasan zuciyata nasan menene nasan dalili. Ina idar da sallah na janyo babban quran dina na fara tilawa a kalla nayi izu daya kafin nayi azkhar lokacin tuni gari ya waye hakan yasa na gyara dakina na shiga wanka. Ina fitowa na zura wata morning gown ta wani silk purple yadi. Kaina na zura hula sannan na tafi kitchen.
Na jima tsaye a jikin working surface ina karewa kitchen din kallo wanda a zahiri kenan amma a badini ina tuannin bidirin da aka sha a kitchen din, tun daga Yaya mukhtar down to Yaya Suleiman. Kowannensu it started at this very place. Ajiyar zuciya me nauyi na sauke ina kara kallon guraren tareda saka hannuna ina tattabawa wasu nayi murmushi a haka na kashe time din da bansan iya adadinshi ba. Se can dana fara jin motsin yan gidan sun tashi sannan na dukufa fara aiki. Na kusa gamawa Mama da Asiya suka zo muka karasa na wuce na gaida Inna sannan Abba da Ummaah. Muna kammalla breakfast na koma daki na dudduba wasu soft copy pages da aka turon akan Breast cancer da Cervical cancer. Ban wani dauki time ba na gama na janyo system dita na fara aikin da na saba wato kallon korean movies, wani Love In The Moonlight.
Gaba daya na sakankance ina kallona naji an turo kofar dakin, normally mun saba indai zaka shiga dakin koma waye seka yi knocking da sallama kafin ka shiga. Hakan yasa na dago da sauri tareda pausing film din, mamaki sosae ya kamani ganin Nadia, its been long da naga kafafunta a cikin gidanmu kuma dakina. Mikewa nayi ina sakin murmushi nace
“Nads manyan mata, sannu da zuwa”
“Yawwa!”
Kawai tace min se ban wani damu ba tazo ta zauna nace
“Bari a kawo ruwa, yau akwai hirar yaushe gamo kenan”
Na fada ina kokarin tashi daga gefenta, hannunta tasa ta rike nawa, hakan yasa nayi saurin kallonta kafin nayi magana tayi beating dina to it tace
“Bashi ya kawo ni ba. Kina kallon yanayi na kinsan ba ruwa nazo sha ba. Gargadi nazo nayi miki, mijina Suleiman nawa ne ni daya kinganshi yafi karfin wadda tayi kwantai ta gama aiki cikin kartin maza irinki. Saboda kin kasa auruwa you decided kizo kimin snatching miji? Kul dinki!”2
I was dazed, confused and amazed! Tunda ta fara magana nake kallonta da tsananin mamaki wanda ya kasa boyuwa ya fit baro baro akan fuskata. Tana gama fada ta hankadar da hannuna ta mike da niyyar fita, nasa hannuna na riketa ina kallon idanunta wanda na rasa meye a cikinsu amma nawa firgici ne a cikinsu
“Ta yaya zaki fita baki fahimtar dani abunda maganar ki take nufi ba, Nadia ni ce fa”
Hannunta ta kwace kamar wata damisa, cikin daga murya tace
“Se me dan kece? Ai nasan ke dince shiyasa na sassauta miki, tunda bakiji kunyar kawancenmu kin kai idanunki kan mijina ba bazanji kunyar na miki gargadi ba. Me mijina zaiyi dake tsofe tsofe dake…..”
Ban barta ta karasa ba na wanka mata mari ina wani irin huci, i was boiling in,
“Kada ki kuskura Nadia…..”
Se na dunkule hannuna na kasa karasawa, zuciyata na fada min Nadia ce fa, wannan dinnan, kin manta ta? She doesn’t deserve this. Bana tunanin akwai circumstance da zai zo na manta matsayin rayhana da Nadia a rayuwata, sudai zasu iya mantua amma ni nasan alheri bana mantawa dashi. Ai tana ganin nayi shiru ta fara zage zage wanda ya janyo hankalin Inna da Ummaah dasu Mama, su basu san ta shigo bama dan kowanne na dakinsu. Ummaah tazo tana fadin
STORY CONTINUES BELOW
“Nadia me ya faru? Me ya hadaku?”
Wani mugun kallo tayiwa Ummaah tace
“Ki fada mata ta fita harkar mijina, mijina yafi karfin ta shi ba tsaranta bane, idan ba haka ba……”
Gaba daya har Inna muka tsaya muna kallonta da tsananin mamaki, kuma shirun da mukai mata baisa tayi shiru ba sema kara daga mirya da takeyi a haka Abba ya fito ya samemu a tsatsaye, Nadia tana ta wulakanci ita me miji. Kallonta yayi yace
“Kiyi hakuri ki koma dakinki, ni na miki alkawarin Asmau bazata taba auren mijinki ba, itama nata yana nan tafe da izinin Allah”
Kawai tana bude bakinta se cewa tayi
“Better!”
Ta juya ta fice, tana fita naji wani irin yanayi me wiyar na fada ya lullubeni, kaina kamar zai tsage gida biyu, idanuna da suke neman lumshewa na bude da karfin gaske nace
“Abba me ya faru”
Ashe yaya Suleiman ya samu Ummaah akan yana sona zai aureni tace masa aa kar ya manta abinda ke tsakanina da matar shi, bai jiba ya samu Inna ita kuwa kowa yasan yana daya daga cikin favorite jikokinta hakan yasa tayi naam da maganar. Kallon Inna nayi kamar zan daketa idanuna se hawaye ke zubowa, gaba daya na manta Inna bata jin turanci nace
“For goodness sake, Inna why will you do this? Danme? Kinsa yarinya yar cikinku tazo tayi muku fitsara. Saboda banyi aure ba, kun taba ganin macen da takai age dina bata damu tayi aure ba, in bai zo ba zan fita titi nayi shelar wa yake sona? Waye zai aureni…!”
Wani abu naji ya tokaren makoshi hakan yasa na juya dan tafiya daki amma wani mugun jiri ya kwashe ni se gani a kasa, dukkansu suka yo kaina dan tashina amma na mike seda Abba ya rikeni aka kaini har daki daidai shigowar yaya Suleiman a birkice, Abba yace baya son yaji komai kawai yazo ya dubani. Yana dubani ya daura min drip se na lumshe idona kamar me bacci hakan yasa suka fita dan na samu na dan huta amma maimakon na mutsu se kawai na tashi na hada kaina da gwiwa na dinga kuka, a raina ina ayyana yadda rayuwa ta juya, ni Nadia tazo har guda ta ciwa mutunci akan mijinta? Su Ummaah basu tsira ba. Asiya ce ta shigo ta sameni a hakan ta zauna tana ta lallashina har nayi shiru sannan ta dauki wayata dan nace duk wanda ya kira tace banda lafiya.
Misalin karfe bakwai na dare nayi sallar maghrib, na dan nutsu ba kamar da safen ba shima Abba da Ummaah suka zo sukai ta lallashina tareda nuna min haka rayuwar take, we must expect worst from life, it’s a trial which are never meant to be easy. Wannan ya karfafa min gwiwa har nasha tea sannan nayi wanka amma idanuna kadai zaka kalla kasan kodai ina cikin damuwa ko banda lafiya.
“Yar fara tashi maza maza ki canja kaya kizo parlor kinyi baki”
“Baki?”
Na maimaita ina kallon Ummaah data bude wardrobe dina da alamun kaya take nemo min kaya, mikewa nayi jin bata bani amsa ba nace
“Ummaah su waye?”
Juyowa tayi tana kallona kafin tace
“MD dinku ne”
Idanu na zaro cikeda mamakin abinda ya kawoshi, taba ni Ummaah tayi tace
“Tun dazun sukazo so kiyi sauri kisa wani abin kizo”
Idanuna Na lumshe ina jin wani mintsini da ale min a cikin zuciyata na farin ciki, kallon kayana nayi ba tareda daukar ko daya ba na rufe na nufi inda Abayas dina suke na samo wata simple royal blue abaya wadda egde dinta aka mata ado da wani silk blue material yayi kyau. Mayafin na yafa bayan na wanke fuskata na fito parlor Amma maimakon na ganshi se wata yar karamar yarinya wadda shekarunta bazasu wuce shekara biyar ba, sanye take da jeans se top an saka mata hula kalar top din. Wasa take da throw pillow din kan cushion din da take kai, gefenta wata middle aged mata ce tana zaune da waya a hannunta amma kamar da suke da wannan yarinyar ta baci. Hakan yasa naji hankalina ya kwanta daga tantamar da zuciyata take. A hankali na karasa inda matar take Na tsugunna a gefenta nace
“Barka da zuwa, ina yini?”
Da sauri ta dagani Na zauna gefenta tana ta murmushi kamar bakinta zai yage tace
“Mashaaa Allah, Alhamdulillah! Barka dai Asmau ya jikin naki?”
A kunyace nace
“Alhamdulillah!”
Dan yadda idanunta ke sparkling daga gani na kamar irin abinda kake jira dinnan shekara da shelaru ne yazo.”
“Yayi kyau, Raudha bakiga Anty ba, zo ki gaisheta”
Yarinyar tazo tayi hugging dina ta gaisheni , ina murmushi na zaunar da ita kaina naace
“Raudha”
Kallon Maman ta tayi tace
“Amiey, wannan ce Matar uncle Abbas din?”
Da sauri na kalli yarinyar dake shafa fuskata sannan na kalli uwar dake kallona with love a idanunta tace
“Inshaaa Allah”
Kunya ta kamani sosae, zuciyata wani irin bugawa take na kasa tantance a wanne yanayi nake ciki farin ciki ne ko mamaki. Kafin ta kara magana Ummaah da mama suka zo dauke da abinci akan tray, sannan ta zauna suka gaisa inajin tana fada mata su asalinsu iyayensu yan sokoto ne amma dukkansu a hadejia aka haifesu ta jigawa hakan yasa suke indigene tunda sun samu by birth. Nidai hankalina yana kan Raudha da nake feeding tana ta bani labarin Uncle Abbas. Can sega Abba ya shigo, har kasa Maman Raudha ta tsugunna ta gaisheshi ya kirani parlonshi. Tunda nasa kaina nasan Dr Kwaccido na ciki saboda kamshin turaraenshi daya baibaye ko ina Na parlon. Abba fita yayi so daga ni se shi se Raudha data biyoni tana ta tsalle tsallenta.
Cikeda damuwa yace
“Me yake damunki ne kin kalle ki kuwa? Nasa ki taho gida ki huta amma you are still falling sick. Y kike so nayi ne?”
Da sauri na dago kaina ina kallonshi, ya dage girarshi yace
“I care of course! My heart flutters whenever I see you or i remember you. Can you do me the favor of marrying a bachelor like me?”
9
Rate the page on a scale of ten
3
Ayshatuuuu ❣️Tantama na shiga yi akan abinda naji ya fito daga bakinshi, favor yace nayi mishi na aureshi ko kuma auditory hallucination ne ya sameni lokaci guda. Idanuna na dago na sauke cikin nashi wanda ya tsareni dasu, zaku rantse da Allah kuce amsar tambayar tashi cikin idanuwan shi take.
“Can you do me a favor of marrying a bachelor like me?”
Ya kara maimaitawa, haka kowa yake ji idan akai masa proposing. Yanayi ne sabo da ban taba jin makamancin irinshi ba, to ta ina zanji tunda babu mahalukin daya taba cewa zai aureni? Kowa sede yazo ya gama wasa da zuciyata sannan ya wullar da ita inda yaga dama.
“Asmau, ba se kin amsa ni yanzun ba, sede kin ganni bana da hakurin jira, waiting really sucks kingane?”1
A hankali na gyada kaina kamar wata sokuwa shi kuma ya cigaba da fadin+
“Ni ba yaro bane, kema you don’t look like a teenager, gaba dayanmu adult ne mu. To ya kamata dukkan approach dinmu ya zama very matured. Dan Allah Asmau don’t make me wait!”
Kasa nayi da kaina inajin wani sashe na zuciyata na fadin kice kin yadda, kice kin amince amma bazan iya ba shima ba lokaci daya yaji yana sona zai aureni ba, it took him time kafin ya fahimci me yake bukata. Shirun da mukai yafi na mintina biyar kafin yayi breaking silence din da fadin
“Ashe dubiya nazo fa, ya jikin naki?”
Dan murmushi nayi a raina ina fadin jinya kam ai ta tafi sede wata amma ka rigada ka wanke duk wani dafi da tsatsa dake kanta. A zahiri nace
“Jiki yayi sauki Alhmdllh. Nagode…….”
Mikewa yayi yana hararata yace
“Ki cigaba da godiyar nan dana hana”
Mikewa nima nayi ina murmushi nace
“Idan akai maka abin arxiki, is not bad when you show your gratitude right?”
Bansan ya expression din fuskata yake ba da nayi maganar, abu daya na sani nadan daga girata. To yadda ya tsaya yana kallona da bakinshi da hancinshi ya shagala sosae har seda na rufe fuskata da gefen veil dina kafin ya girgiza kanshi yana wani irin murmushi wanda idan zai kwana yanayi bana tunanin zan gaji da kallonshi, he looked so charming and loving.
“Hakane kam, why not ki adana mana hakan se right time yayi”
Dan murmushi nayi bance komai ba Shima se yace zai tafi yana son sallama da Abba, kallon snacks din da aka kawo mishi dadu lemu nayi amma bai taba komai ba hakan yasa nace
“Ummaah zatayi magana baka ci komai ba”
Kallon gurin yayi sannan ya kalleni yace
“Bake bace kinzo kinata kallona ta yaya zanci abu na kware”
His funny side na ayyana a raina ina dariya, karshe se packaging akai musu, su su Raudha sunci nasu. Seda yaje ya gaida Inna tana ce masa
“Kai yanzun Abbas ka rasa wa kake so se wannan kodaddadiyar, ina laifin ni?”
Yayi dariya yace
“Ai karki damu kece uwargida kuma mowa, ita zata shigo a yar aiki ne.”
Gaba daya mukai dariya inata kallon shi ban taba tunanin he has this side ba, farkon ganina dashi kawai naga serious mutum da bai san bata lokaci ko wasa ba, shidai foremost thing shi ne kayi aikinka kada ya kama ka da laifi. Na yadda da mutane sukace never judge a book by its own cover!
“Ko kada Na tafi ne, naga se kallona ake?”
Hararshi nayi ina mita cikin raina akan dalilin da yasa nake ta kallonshi. Nan yaje gurin Ummaah nan babu wasa se girmamawa da darajawa kafin su Raudha suka tashi bayan Abba da Ummaah sunyi mata kyauta nima na duba dakina na samo chocolate da sweet na bata, suka aje min kayan dubiya inata mitar hakan na rakasu har bakin mota. Ina saitin Maman Raudha tace min
STORY CONTINUES BELOW
“Se munji magana me dadi”
Dan murmushi nayi cikeda kunya ina shafa fusakar Raudha, kallona yayi daga dayan gefen yace
“Kiyi bacci da wuri very early zamu wuce”
Kaina na gyada masa suka tafi ni kuma na koma gida, tamkar bani nake kukan nan da nayi dazun ba, i was so so happy har dana shiga daki kawai kan gado na fada tareda rungumo pillow a kirjina ina jin kamar zan maida shi cikin jikina, farin cikin da nake ciki kasa misaltuwa yayi, mikewa nayi na dauro alwala nazo nayi raka’o’i biyu na godiya ga Allah inajin a jikina komai yazo karshe. Jin Ummaah na kirani yasa na cire hijabin tareda wullar dashi na daidaita kaina na fito sede fuskata betrayed me dan wani kyakyawan murmushi ne yaki barinta, dukkan dimples dina a lotse suke.
Kallona Ummaah tayi sannan tace
“Yar fara wannan murmushi haka?”
Rufe fuskata nayi nace
“Kai Ummaah”
Jikinta na kwanto ta shafa bayana tace
“Allah ya zaba mafi alkhairi, kiyi istikhara ki nutsu sosae. Duk wanda yasa Allah a lamarinshi bazai taba dana sani zabin shi ba. Ok?”
Kaina na gyada na tafi gurin Abba shikam tambayoyi yayi tayi min akan Dr Abbas wanda na sani na fada idan ban sani ba kuma nayi shiru. Nasiha sosae yayimin se naji kamar auren gobe ne, harda kwalla ta.
Washegari sunday muka tashi da mummunan labarin sakin da yaya Suleiman yayiwa Nadia, ni gaba daya na manta da abinda ya faru kwatkwata. Inna ta dinga murna tace gwara taje ta koyo tarbiyya Ummaah ta korashi akan indai ya dauketa kamar ta haifeshi to ya mayar da Nadia, saki ba koda yaushe yake gyara ba kuma Nadia tayi rashin hankali amma se ya barta da kunyar haduwa damu ma nan gaba. Abba daya ji kamar zai daki yaya Suleiman yace ya wuce ya dawo da ita. Wajen laasar ina zaune a parlor da system dina ina kara harhada presentation din da zanyi akan Spinal Bifida, dake duk monday akeyi kuma wannan turn dinmu ne.
Kamar daga sama naji sallamar Yaya Suleiman ko dagowa banyi ba amma na amsa sallamar, zama yayi se lokacin na dago naga shida Nadia ne, tayi zuru zuru idanunta sunyi jawur, dan murmushi na kirkiro na musu sannu da zuwa tareda kwalla kiran Asiya akan ta kira Ummaah nikuwa na cigaba da aikina. Ummaah na zuwa na tattara kayana na koma daki dan nasan hakuri aka zo bayarwa ni kam meye nawa a ciki. Ta rigada ta nuna min matsayina gurinta so ko komai ya koma normal alwai abinda har abada an wuce gurin.
Ina karasa kallon love in the moonlight se naji ta turo kofar ta shigo, pausing episode din nayi har ta zauna ta kasa magana haka nima tunda ni banida abin ce mata. Hannuna ta kama tace
“Kiyi hakuri”
Kaina na gyada nace
“Ya wuce”
Se mukai shiru nikam na cigaba da kallona har ta gaji da kanta tayi min sallama. Kamar jira ake ta fita sega kira ya shigo, seda nayi murmushi kafin na daga kiran
“Sir barka da yamma”
“Barka dai Asmau, kin gama compiling presentation din?”
Kaina na gyada nace
“Eh na gama”
“Nice of you, turo min na gani”
Kaina na sake gyadawa nace
“Sure Sir”
Daga haka mukai hanging na tura masa ta mail sannan na tafi nayi sallah se wajen tara na dare ya turon na duba naga corrections din da yayi.
Washegari karfe shida da rabi na gama shiryawa, tea kadai nasha yazo muka tafi. Tunda muka gaisa bai kara cemin komai ba seda muka wuce mariri sannan yace
“Asmau ya maganar mu?”
Da sauri na kalleshi bama kallona yake ba idanunshi yana kan titi hakan yasa na janye idanuna slowly ina tuna maganar Adda Sa’ada data cemin yanzun babu jira, babu sanya kawai i should let things flow naturally kawai.
“Can i blow the winds up for you? Can i treat you like the most precious lady that ever existed in this world? Can you do me the favor of marrying me?”
Ya fada yana kallona bayan yayi parking gefen titi, bazan iya daurewa ba, ba zan iya ja ba kuma words din are so sincere yadda suke fitowa daga bakinshi. Kawai ce mishi nayi
“You most welcome!”1
Kallona ya dinga yi da wani kwantaccen murmushi daya kara kayatar da fuskarshi yayi kyau, ga rana data ratso ta window ta sauka kan fuskokin mu. Dauke idona nayi ina murmushi tateda jin wata nutsuwa ta mamaye ni kamar wani puzzle ya kamata na jera kuma na jera din.
“Naso ace ke din halaliya tace , i would have hug you kiji yadda zuciyata take bugawa. Babu damuwa soon, very soon zan cika mana burinmu. Inshaaa Allah bazkiyi dana sanin amincewa da aurena ba”1
I was emotionless ban ma dago ba ganin bazanyi magana ba yasa ya fara driving muka koma hanya har lokacin kaina yana kasa ina wasa da zoben dake hannuna. Cikin wannan yanayin na tsinkayi muryar shi yana fadin
“Sunana Abbas Aliyu Kwaccido, mu asalinmu fulanin sokoto ne. Kwaccido family name dinmu ne. Mahaifina shi ne dan sokoto, mahaifyata yar kebbi ce a arugungu. So kinga dukkan su dai kusa da kusa suke. Mahaifina dan kasuwa ne wasu dalilai yasa ya koma hadejia gaba daya da zama. Babban yayana Umar shi kadai aka haifa a sokoto suna zuwa hadejia babu jimawa ya rasu. Ni ne dansu na biyu a yanzun ni ne babba a gidan daga ni se Maman Raudha wadda mukazo dubaki da ita. Se autar mu hajara ita ce kamar zakuyi sa’anni da ita kuma tana sokoto tana aure. Bayan barin Alhaji sokoto se ya samu wasu yan uwanshi suka biyo shi shi ne muka tada wani familyn anan. Se ya zaman mu mun tashi a matsayin yan jigawa tunda mun samu indigene by birth. A hadejia nayi primary school dina, seda na gama sannan aka kaini unity school a kwara anan nayi secondary dina baki daya har na kammalla. Allah ya taimakeni sciences nayi, kuma WAEC dina tayi kyau so da aka tashi bada scholarship harda ni anan naje russia nayi medicine and surgery, duk shekara ina dawowa hutu haka dana gama nazo nayi internship dina na koma nayi Family medicine se suka rikeni nayi musu aiki na shekara biyu a haka ina kara fadada karatu na har na samu na dawo. A Aminu kano na fara aiki kafin na koma murtala muhd daga nan na tafi germany nayi wani course akan dialysis. Ina dawowa aka bani MD a hadejia bayan na koma Kazaure se kuma na dawo nan only to meet the love of my life”2
Murmushi mukai dukka a tare sede na gamsu da bayanan sa amma akwai abinda nake bukatar ji daga bakinshi kamar yasan me nake tunani yace
“Izzatu, cousin dita ce. Mahaifinta shi ne babban yayan su Hajiya. Itada Maman Raudha sa’anni suke dukda Maman Raudha ta gurmeta da akalla shekara daya amma duka same boat suke. A lokacin suna Abuja da sauran yan uwanta daga baya mahaifinta aka bashi Ambassador a Russia so kusan duk karatun da nayi a embassy dinsu na zauna. Dukkansu maza ne a gidan ita daya ce mace kuma basu jituwa da ita saboda been the only female child se ta zama over pampered child. Kusan ko da yaushe muna tare da ita ni nake kaita makaranta kuma na dakko ta. Bazan iya cewa ga lokacin dana fara sonta ba na dai san wannan shakuwar ita ta rikeda mana ta zama zazzafar soyayya. Ban taba son wani abu kamar yadda na so Izzy ba, she was everything I ever wanted Asmau amma Allah is the best planner. Muna haka na gama karatuna, lokacinda zan taho tayi kuka a ganinta mun rabu kenan shi ne dalilin da yasa na dawo na karba aikin da aka bani a lokacin tana year 2 a nursing son sena jira ta gama muyi aure amma Abban Abuja yace da zarar zan koma nigeria da matata zan tafi. Hakan ba karamin dadi yayi mana ba, aka shiga shiru mudai kullum a shiriritar soyayya muke. Haka lokaci yazo muka dawo nigeria dan ayi aure. Sede tunda aka fara bikin Izzy ke wasu irin weird maganganu kamar Allah sarki naso na zama matarka da maganganu iri iri wanda sede nayi dariya har aka daura aure….”
Se yayi shiru tareda parking motarshi a gefe, dagowa nayi na kalleshi he looked disturbed, idanunshi har sun canja, se naji jikina yayi sanyi hakan yasa na bude baki zanyi magana amma yace
“I’m sorry it’s still hurting zan karasa miki wani time din”
Kaina na gyada muka cigaba da tafiya cikin wani yanayi me zafi, atmosphere was tensed shi yana tunanin Izzatunshi yayinda nake tunain me ya faru suka rabu da izzatu?
1
AyshatuuuuCikin nutsuwa na maida hankalina wajen presenting spinal bifida, condition ne dayake affecting yara, mukan kirashi “congenital defect” tun lokacin yaro yana ciki spine dinsa “laka” bata rufu ba, hakan is a very rare cases da yafi affecting whites amma anan dinma ana samu. Cause dinshi dai takamaimai baa sani ba sede hankali yafi karkata a rashin sinadarin folic acid a jikin uwa lokacinda tana dauke da ciki.
Ina kamallawa hannun daya fara clapping na MD ne, se kuma sauran suka dauka aka cigaba. Nayi murmushi ina jin dadi sannan na fara amsa questions da kuma consultants da suke kara min wasu points din. Se wajen tara kowa ya nufi office dinshi ready to start the work of the day. Dakina na koma dan na canja kaya saboda ba wears din aiki bane a jikina, seda Na kammalla shirina tsaf na nemo powder cikin wani kit na shafa, na murza kohl nasa lip balm sannan na kalli kaina, nayi tsaf dani se wani murmushi da yake kwance kan fuskata da yaki ya bar kanta, ni kaina na manta lokacin da na fito cikin nutsuwa ta haka, wanka dai bana fasa shi amma fuskata kullum maiko take tun Dr fadima na mita hakan har ta tattara ta kyaleni.+
Kulle dakin nayi na nufi lounge dan nasan house officers din da zamui rounds dasu suna can kamar yadda na umarcesu su jirani. Ina shiga dukkansu suka mike tareda gaisheni. Da murmushi nace
“Are we ready?”
Dukkansu suka amsa sannan muka fito, tamkar wata sabuwar halitta haka nake jin kaina yadda nake jin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 18