balle nata, se bin mutane nake da kallo kamar yadda ake kallona, mafi yawancin mutanen basu lura Dani ba.
Tattausan hannu naji cikin nawa, hakan yasa nayi saurin dago idanuna, fes cikin na Yaya Suleiman, idanunshi Sunyi jawur, ga jijiyoyin kanshi sun firfito waje, baice min komai ba haka zalika Nima Bance komai ba, se cikin gida, da Adda Salma na Fara Karo, Tana zaune a kofar parlor Tana waya, ba kuka take ba amma kallonta kawai zai saka mutum yaji ya karaya, inda take na nufa da sauri, tamkar duk wani kuzarina ya dawo nace
STORY CONTINUES BELOW
“Adda waye ya rasu? “
Hannuna ta rike tace cikin lallashi
“Kiyi hakuri…..”
Hannuna na kwace bansan me ya fusata ni ba, amma a lokacin gani nake idan banyi ihu ba, Adda Salma bazata jini ba, tamkar we’re miles apart Haka nake gani, nace
“Ki sakeni! Ki fada min waye ya rasu? “
A hankali naji abu me dumi Wanda babu ko tantama hawaye ne, ya fara zarya akan kumatunshi. Banyi Ko kokarin gogewa ba, se naji an dafa kafadata hakan yasa na juya da sauri, Ummaah ce, Idanunta Sunyi ja, sun cicciko da kwalla tace
“Mukhtar ya rasu! “
Tamkar saukar aradu, haka naji saukar Maganar nan cikin dodon kunnuwana, lokaci daya ganina, jina baki daya suka dauke bansan iya adadin lokacin Dana shafe ba, all I know bayan na nutsu na ganni a dakin Inna Ade, tana zaune da carbi hannunta tana ja, hawaye na diga mata.
“Inna Wai da gaske Yaya Mukhtar ya rasu? Ya tafi gaba daya? “
Bata amsa ni ba, se rungumoni da tayi hakan yasa na saki kuka me ciwo, babu abinda nake maimaitawa Se conversation dinmu da ko awanni uku bamui da rabuwa ba. To me ya sameshi? Ashe rabuwar kenan? Ashe shi kenan mun rabu? Ashe bazan kara ganinshi ba? Kukan da nake se naji is insufficient, wani kululun abu ya tokare min makoshina, sakin Inna nayi na kwanta a dandanyar tiles, may be hakan zaisa na rage jin abinda nake ji amma tamkar ana babbaka wuta cikin zuciyata Haka nake ji, duk yadda Inna taso na daina kuka abin ya gagara.
Bayan mun rabu nida Yaya Mukhtar, kuma bayan sun gama magana da Rayhana se ya tafi, tunda dama yace mata tafiya Zaiyi, yana fita daga cikin campus dinmu Ko kofar famfo bai je ba ya bugi wata Mota dake fitowa daga cikin wani layi. Da yake a karar kwana abin yazo, kafin azo rescuing dinshi Har ya rasu shi kuma Wanda sukai Karon kafarshi ta karye. Shi ne aka kira Abba saboda shi ne last call dinshi kuma akai saa Umma Falmata da Abba Imam sunzo gida, so tare sukaje asibiti aka dakko gawarshi, aka Kira mutanen Kwalam da yan uwan kusa!
Hawaye kam bai Ko tsaya ba, zuciyata ta kasa sukuni, ni nasan baa wasa da mutuwa amma da tabbas zan karyata rasuwar Yaya Mukhtar. Da kyar da sudin goshi aka samu nayi shiri, ko kanneshi da sukeuba daya bazasu nuna min jin rasuwar Mukhtar ba, I can’t believe cewar komai ya zama tarihi, his smile, his laughter, his caring. So komai na karshe ne.
Zuciyata bata karye ba seda naga Umma Falmata, se naji wani reason nake dashi na yin kukan rashinshi, abinda ta mallaka kwaya daya tak, ya tafi ya rasu lokacin da ake tsananin bukatarshi, haka rayuwar take.1
🎶Show me the meaning of been lonely, is this the feeling I need to walk with? Tell me why I can’t be there where you are? There’s something happening in my heart 💖
Washegari se lokacin na hadu da Rayhana, tun safe nayi wanka saboda Inada test din 1301, babu Wanda ya sani ma, amma ni nayiwa Kaina fadan na tafi, dan idan banyi test din ba, nasan nida medicine sede na Tara wata Shekarar. Dakin Ummaah naje na samu Umma Falmata da kishiyarta, tayi kuka marar har ta gaji, Har kasa na tsuggunna na gaisheta sannan na musu gaisuwa saboda a jiya babu wannan halin, Numa tausar nake so, kuma na samu Dan su Adda kusan a Kaina suka kwana Har nayi bacci, Dan kowa har ita Umma Falmata Sunyi tunanin soyayya muke basu San one sided feelings bane.
A kitchen na tarar da Ummaah nayi mata sallama tayi mamakin ganina a Haka amma fuskarta ta nuna jin dadi. Yaya Halifa ne ya kaini nida Rayhana bisa umarnin Abba. Duk wata nutsuwa da nasan Inada ita tattara ta nayi guri daya saboda nasan my future relies on each thing I wrote on that paper, Hakanan nayi sannan muka gama, naje hostel na kwaso abinda ya kamata, ban Tarar da kowa ba kasancewar sun tafi class. Se a bakin hostel ne naga Anty Zubaida, Tana kallona tace
“Asma’u me ya samu fuskarki? “
Tamkar an bude famfo na fashe da kuka, rikeni tayi tace
“Kiyi Shiru Kinji? “
Kaina na gyada sannan na fada mata abinda ya faru, ta jajanta min dukda bata sanshi ba, kuma ni ban sake dasu ba balle suji cikina. Kuma tunaninta muna tareda Rayhana shiyasa bata kirani ba.
A Napep Rayhana ke cemin
“Fara ‘yar shehu, kin yafewa Yaya Mukhtar? “
Kallonta nayi sannan nace
“Me Yayi min? “
Hawayenta ta share tace
“Ki yafe masa ko zai samu gafarar Allah saboda niyyarshi akanki Bamai kyau bace. Naji mutuwarshi kasancewata mutum ta karshe da tayi magana dashi. Ina fata zaki lura da darsain da Allah Yayi a rasuwarshi”
Nidai Bance da ita komai ba amma maganarta Se echo take min, niyyarshi bamai kyau bace? How comes? Nidai abinda na sani har zuciyata na yafe masa!
Ayshatuuu_Astagfirullah Wa’atubu ilayka_
🎶 Walking down the street of Nothing ville, where our love is young and free, can’t believe what an empty place it has to come to be, I’ll give my life away, if it only be the same! Cuz I can hear a voice inside of me, that’s calling out your name….. 🎶
Wannan wakar mistakenly naji ta a wayar Yaya Halifa, shikenan na tura ta, se naji tamkar danni da Mukhtar Westlife sukai wannan wakar. Kullum naji ta Se nayi kuka, kuma naki na daina jinta, harseda Lubna ta fadawa Rayhana sannan tayi deleting dinta daga wayata, amma a banza it already stuck in my upstairs!
A Haka na cigaba da rayuwata, dukda tabon rasuwar Mukhtar yana cikin zuciyata, ban kuma ga abinda zaiyi nasarar goge shi ba. Amma Allah yafi kowa sanin me zai faru, me kuma zai kasance, kuma shi daya ya tsara mana yadda rayuwar mu zata kasance.
Watan shi daya da rasuwa na Fara semester exams, na maida hankalina sosae wajen Karatu, ga kuma nasihar Ummaah da Abba da suke min akan it’s now or never, Haka Yaya Halifa kullum mukai waya se yace min, idan na Bari damuwa ta saka na fadi exams na sani na gama da rayuwata, ga Adda Sa’ada sun dawo Kano baki daya, kullum se ta aiko min da Abinci, dukdan nayi Karatu. To idan na tuna hakan se naji Kamar ya tafi karatun kawai nake son nayi.
Sati biyu muka dauka muna Exams, Dama nafi gane Karatu cikin dare hakan yasa ranar da aka gama exams, kamar zan fadi saboda baccin da nakeji, hakan yasa nayi deciding tafiya gidan Adda Sa’ada nasan anan zanyi bacci son raina, Dan Ummaah tace min jikokin duka suna gida, Nikam I can’t be that reckless.+
Wajen Karfe biyar na yamma na isa gidan, kofar a bude take hakan yasa na tura na shiga, a parking lot na tadda Mijinta Yaya Bilyaminu da wani abokinshi, dukkansu Juyawa sukai suna kallona, gurin na isa na gaishe da bakon sannan na gaida Yaya Bilyaminu.
“Young Doctor, Ya exams”
Hamma nayi, cikin sauri na rufe bakina ina A’uziyya tareda yin murmushin nace
“It’s over Alhamdulillah! “
Kanshi Ya gyada, hakan yasa na dan saci kallon abokin nashi, kwatakwata hankalinshi baya kanmu, se naji Banji dadi ba, at least I deserve a second glance, tunda ni mace ce, Fara ce nasan kuma abinda maza suke rubibi kenan, amma ni me yasa bana samun hakan. Se na fita fin a kirga amma ko kallo ban ishi maza ba, na rasa Wanne irin jini gareni. Kuma most mutanen da basu kaini ba, a kyau din, nutsuwa da komai zakusha mamakin yadda ake rubibinsu amma ni ko Oho!
Wucewa nayi ciki saboda idan na kara dadewa akwai matsala. Allah Sarki Addata ta kaina, Ina tunanin na manta ban fada muku Adda Sa’ada ita ce favorite sister dita ba, she’s the best I can ever ask for. Tana zaune akan cushion, Idanunta sanye cikin farin medical glasses dinta, ko ban Kalli karamin glass table din dake gabanta ba nasan aiki take, Architecture ce.1
Tana jin sallama ta, ta aje HB pencil din dake hannun ta, ta taho inda nake a tsaye, tasan me nake nufi I need a hug. Rungumeni tayi nima Haka tace
“Oyoyo Lil Sis, Ya Exams din? Oh kinga yadda kika kode kuwa? “
Dariya nayi na saketa Ina tattaba kumatuna, nace
“Kai Adda, ina wuni “
“Lafiya “
Ta amsa ni sannan muka wuce dakinta spare din, gado na fada Ina fadin
“Its been a while gaskiya”
Dariya tayi ta shige toilet nasan ruwan wanka take hada min, hakan yasa na tashi na cire kayana, Tana fitowa na shiga, na jima ina wanka kafin na fito, Har Kaina seda na wanke, dukda bawai opinion dina bane, Adda tace na wanke Dan akwai barbushin kazantar in store.
STORY CONTINUES BELOW
Bankai 30 minutes ba na gama shiryawa, wata carbon color gown na saka, irinta na Bubu ne, so babu inda ya kamani, bakin veil na yafa akai har ya sakko kirjina sannan na tsaya gaban dressing mirror ina kallon fuskata wadda ta zama pale tsabar yadda nash wahala kwana biyunnan. Chappette din dake aje kan Vanity Table na goga a tattausan siraran labbana, numfashi naja me karfi inajin wani sanyi a raina saboda kamshin vanilla da ya bugeni.
A parlor na zauna, Har lokacin mijinta bai dawo ba, Abinci naci muna Dan hira jefijefi, Har muka gangaro kan hirar Mukhtar, tace
“Amma Yanzun you’re over that ko? “
Dan Murmushi nayi nace
“Adda, Mukhtar bai taba cewa yana sona ba da. Kawai yana nuna min alamar Yana sona”
Glasses dinta ta cire, tamkar cirewar zaisa ta gaskata abinda nace. Kaina na gyada mata irin na tabbatarwa dinnan. Kai ta girgiza tace
“Tab, ban taba tunanin hakan ba, amma ke kina sonshi Ko? “
Dan dariya nayi, se naji ruwa ya Fara tarar min a idona, Kaina na girgiza nace
“Babu amfani Yanzun, tunda ko ina sonshi babu abinda zai canza cewar shi din ya rasu”
Kaina ta shafa tace
“Abinda nake son naji kenan. Ina son kisan, ke din me daraja ce, ke mace ce a priceless and uncut diamond, Wanda ya aureki shi daya yasan worth dinki. Kiyi hakuri da hukuncin Allah, rabonki yana nan zuwa. Dama Mukhtar is just a passerby. Kin gane? “
Kaina na gyada, ina share hawayen da ya Fara zubamin saman fuskata, Bance komai ba amma zuciyata ta nutsu, idan da ace victims Irina Zaa dinga tuna musu Allah yana sane dasu kuma yanada plan ga rayuwarsu, tabbas da basu zama abinda suke Yau ba.
🎶…..When you worry the most, there’s no easy way out, when you ready to go and your heart left in doubt, don’t give up on your faith. Love comes to those who believe it! And that’s the way it’s! 🎶1
Karfe takwas tuntuni bacci yayi gaba dani, bani na farka ba seda akai assalatu, nayi sallah Ko azkhar Se a gado na karasa, shima ban tabbatar ba Ko na kai karshe, bacci ya daukeni. Ban tashi ba se goma da rabi, wanka na farayi inajin tamkar wata sabuwar halitta ce Ni din, duk wannan gajiyar ta tafi, se wani karfi da nake ji, fuskata normal wannan paleness din da nake hangowa babu shi. Haka na kara kwana daya sannan na tafi gidan Ummaah . Ashe rabon zanyi tsintuwa ne, tsintuwa Babba kuwa sede a lokacin is insignificant a gurina.
A kofar gate Naga Abba shida wani mutum da ban taba manta fuskarshi ba, suna tsaye se hira suke, kuma alamun sun nuna cewar sun jima basu hadu ba. Da sallama na karasa Inda suke na gaishesu, Abba farin ciki sosae a fuskarshi, Mutumin yace
“Badai Asma’u bace ta girma haka ba? “
Dariya Abba yayi, yayinda na rufe fuskata da hijab din jikina ina Murmushi, naji Abba yace
“Ita ce fa, Yanzun level 2 zata shiga tana Medicine “
“Mashaaa Allah, amma naji dadi sosae. Kasan Abdujjabbar shima medicine Yayi, Yanzun Haka residency yake. “
Kai Abba ya gyada yana ta san barka, wucewa nayi inajin hirar ta koma ta Abdujjabbar da yawa, amma a raina tunani nake cikin su ukun waye Abdujjabbar???
Tunda na tashi Kaina ke ciwo, da kyar na fito zuwa kitchen, na bude emergency kit dinmu na balla Pcm guda biu na kora da ruwan dana taro daga sink din kitchen. Zama nayi kan stool tareda daura kaina kan kitchen island din dan naga Inada Sauran time daya rage na daura abinci. Ina nan kwance naji shigowar Ummaah, ban masan ta shigo ba seda naji hannunta a wuyana, hakan yasa na dubeta da sauri, tace
“Zazzabi kike ai Asma’u, tashi kije daki, kamar dole? “
Dukda azabar da gabban jikina sukeyi, kuma nasan zazzabi ne tun ina daki, but to me rashin lafiya is the worst enemy, na tsani na ganni ina jinya.
“Ummaah ki bari zan iya, kinga idan na kwanta dada rufeni zaiyi”
Kanta ta gyada, kamar ta amince se ta dawo tace
“Kin tabbatar? Nifa hankalina bai kwanta ba “
Faint smile nayi mata nace
“Ummaah ni ce fa”
Kaina ta shafa sannan ta fita, a hankali na Fara aiki amma mainmakon ya ragu se karuwa da yake, hakan yasa na bar abincin halfway, nasa Amal din Adda ta fadawa Ummaah Bazan iya karasawa ba.
Ina zuwa na kudunduna cikin bargo, hakorana Har karkarwa suke saboda sanyin da nake ji. Ummaah data zo seda ta tsorata, can se gata ta dawo da Yaya Suleiman Wanda da alamun zuwanshi kenan, naji dai last week ana cewa zai fara Internship a Nassarawa kuma anan gida zai zauna. Ban wani ji dadi ba.
Ummaah fita tayi ta barmu, se Aleeya yarinyar Adda Sa’ada, bude bargon yayi yace
“I’ll feel the temperature? “
Kamar tambaya amma kafin na bashi amsa se hannunsa me taushi naji a dokin wuyana, banida karfi amma dukda haka seda nayi kokarin ture hannunshi. Ficewa Yayi a raina Ina mitar wannan abu. Har bacci ya Fara daukata naji sallamar Adda Sa’ada data Yaya Suleiman. Se naji dadin zuwanta. Bude Kaina nayi Ina mata Sannu da zuwa, hannuna ta kama tana ta yimin Sannu, se lokacin naga syringe hannunshi yana hada allura gaba daya se naji raina Ya baci, kada dai ace allura zaimin? Ban gama tunanin hakan ba naji yace
“Sa’adatu gyara ta nayi mata allura”
“Sule bazaka daina cemin Sa’adatu ba right? “
Dariya yayi yace
“Tit for Tat! Gyarata Dan Allah “
Mutsu mutsu na Fara amma hakan bai hana Adda Sa’ada yaye min doguwar rigar dake jikina ba, Allah yasa akwai under skirt a ciki da naji kunya, da kanshi ya saukar da skirt din da pant dina ya caka. A take naji wata muguwar kunya ta lullubeni, ga haushinshi, ai yana cire Allurar na Fara kuka. A’a Se ya Fara lallashina Har da cewa1
“Sa’ada duk kun bata yarinyar nan, Har kukan allura take. “
Ayshatuuu*Anty Asma’u Madugu…… Thank you so much for always having my back, for been there for me…. Thank you. This page Issa token of appreciation from me.*
Naji haushin furucinshi sosae, se na bata fuska ina share hawayen fuskata. Dariya yayi sannan yace
“Kawo asaka canula”
Wanne musu zanyi, Dan hannu ai bazai hada fada ba, haka na mika yasa canular, Yayi allurai sannan yasa min infusion. Wani dadi naji a jikina, Tun Ina jin hirarsu Ko ince musunshi shida Adda Sa’ada Har nannauyen bacci yayi gaba dani. Bansan iyakar time din dana dauka Ina bacci ba. Amma nasan se da aka idar da Maghrib sannan na tashi. God so kind ba sallah zanyi ba. Koda na tashi, babu inda yake min ciwo se jikina da babu karfi. Amma haka na daure na sakko daga gadon, Amal na zaune da wayata a hannu Tana game. Kallonta nayi nace
“Amaly!”
Dagowa tayi, tana ganin yanayina ta saki Murmushi, se kuma ta aje wayar tayi waje. Kaina na girgiza na wuce bandaki Dan nayi wanka. Koda na fito yan dubiya sun cika dakin, kowanne na fadin Anty Sannu, ya jiki? Lafiya nayi ta fada sannan nace suje waje na saka kaya, dukkansu suka fice a hakan na samu na shirya Sannnan ya fito. Dakin Ummaah naje suna tareda Adda Sa’ada, dukkansu Sunyi farin cikin ganin na warware. Zama nayi ina cin Abinci munata hira.+
Ban jima ba, Ikhram Tazo akan naje Yaya Suleiman yana kirana. Bansan na zunbura Baki ba seda naji dariyar Adda Sa’ada tace
“Meye hakan ke kuwa? Ki wuce kije mana”
Mikewa nayi ina gunguni, Inaji tana bawa Ummaah labarin allura Yayi min shiyasa. Banji abinda Ummaah tace ba nayi gaba abina. A parlor na tadda shi Yara sun baibayeshi. Zama nayi fuskata a murtuke nace
“Gani Yaya Suleiman”
“To ku daga ni, Se da safe Zamui wasan”
Basu Musa ba suka daga shi, daya bayan daya suka wuce dining Dan tun fiwota naji ana fama dasu akan Anyi serving dinner, amma da yake wasa ne a ransu basu lura ba. Bana takura musu saboda duk ranar da suka tafi se naji na zama so empty tamkar Anyi min mutuwa. They’re company gaskiya.
“Na zata idan patient ya tashi, Doctor dinsa yake fada nema? See you “
Dauke kaina nayi bance komai ba, saboda bansan abinda zan ce dinba. Kafadarshi yayi shrugging yace
“Ya kikeji Yanzun? “
“Alhamdulillah “
Kanshi Ya gyada sannan ya mukamin Leda yace magunguna ne, godiya nayi mishi na koma dakina.
Bayan sati biyu ko barbushin zazzabi babu kuma na warke tas, babu wani abu dake damuna. Shima kuma baifi sau daya muke Haduwa a rana ba, kullum he’s busy a asibiti. Da sassafe ina kitchen Ina daka barkono zan zuba cikin Naman kai, inason Adan saka kadan saboda yadda yake fito da flavor din. Banji sallamar shi ba se ji nayi yace
“Haba early morning kinzo kina daka, bakuda grinder ne? “
Dagowa nayi na kalleshi from head to toe, babu karya jinin Inna Ade ne, zancen bazaiyi kyau ba wannan wasa ne.
“Bamuda ita amma tunda Kaima gidanku ne, idan ka siyo Bakayi shishigi ba”
Na zata zaiji haushi, Se naji yayi dariya sannan yace
“I’ll try, zansha coffee “
Yadda ya fadi coffee dinma daban ne, tamkar mace Haka yake da kakale kakale, kallonshi nayi sannan na juya Naman nace
“Bamu shan coffee, amma Munada Tea.”
Ban jira abinda zaice ba, na shige store saboda turarenshi gaba daya Ya dameni, bansan zama kusa dashi. Ina fitowa na samu ya zubar min da gyadar Dana Dama baki daya ta malale a Kasan kitchen, kawai tsayawa nayi ina kallonshi raina a jagule.
STORY CONTINUES BELOW
“Biyani Sweetheart, naxo janyo cup ya bare”
Bance komai ba na kashe Gas sannan na dakko cup cikin wani rack dake a rufe, ba lalle ka gani ba in ba kasan gurin ajiyarsu kenan ba. Mika mishi nayi sannan na bashi Tea bag nace
“Komai yana kan dining, don’t stress yourself”
Hannunsa Ya hade guri daya yace
“Kumaya”
Se nayi Murmushi hakan ya tabbatar masa na fahimci abinda yace. Da yamma na samu bakuncin Nadia, friend dita ce da mukai New Horizon tare, muna jimawa bamu hadu ba, dukda unguwarmu daya amma dake ita Tana Karatu a wannan Private University dake Yola yasa haduwarmu Se lokaci zuwa lokaci.
Lokacinda ta shigo Ina daki, Yaya Suleiman kuma yana parlour shida Yara, so seda suka gaisa sannan ya nuna mata dakina Wanda ta rigada ta sanshi tuntuni. Ina ninke kaya naji sallamar ta, rigarda ke hannuna na wullar Inata Murmushi na nufi inda take tsaye Tana kare min kallo.
“Oh Nadia, Oyoyo….. Is this a surprise? “
Hararata tayi tace
“Kinfi kowa dadin baki idan aka zo gurinki, amma Kira a waya ya gagara, and you always brag of I been your friend ko? “
Rufe bakina nayi ina Dan dariya kasakasa, idan da Sabo na saba da korafin Nadia, tanada zumunci Ina tunanin ba dan ita ba inaga da tuni we’re separated tuntuni amma ta rike abin.
Janyota ciki nayi na ture himilin kayan dake gefen gado nace
“Zauna mana, se magana kike”
Kanta ta gyada tace
“Bari na gaida Ummaah se na dawo”
Hannunta na kama nace
“Ummaah sunje Abuja zasuyi visa zuwa Hungary”
Kanta ta gyada tace
“Dan Allah su sani a jaka”
Dariya nayi sannan na fice na dakko mata juice da cake da fish pie. Na kawo mata, tanaci munata hira, Dan banida kamar ta, ko islamiyya ma class dinmu daya. A mutanen dana zauna dasu Wanda bamu hada komai dasu ba, tafi kowa tolerating halayena.
“Ya ake ciki, kuma karkice min babu wani motsi “
Langwabar da kaina nayi irin abin tausayi dinnan nace
“Nads karya kike so nayi miki? wallahi har Yanzun Ina nan as single as me zance miki? “
Dariya tayi sosae sannan tace
“Kiga yadda kike kwabe fuska Kamar wata marainiya”
Daidaita fuskata nayi nace
“To Ya zanyi, I’m lonely I need a partner”
Numfashi taja me karfi tace
“Dama loneliness dole ne, tunda shekaru sun kai, amma Kinsan me? Lokaci ne fa, kuma har kyayi karatunki a nutse babu takura. “
Kaina na gyada nace
“An Kai kudin Rayhana da Abdul “
Wani ihu Nadia ta buga tace
“Shegu ce Rayhana, Kice an kusa? “
Dariya nayi nace
“Ke Kina ganin idan Baa saka ranar nan bazasu samu matsala ba. Ya jira da yawa ai, tun muna Js2 fa”
Daga nan muka wuce kitchen Dan ta tayani mu hada dinner, a parlor har lokacin Yaya Suleiman na zaune, kallo yake cikin system dinshi, yana jin fitowar mu ya dago muka hada ido, dauke kaina nayi inajin Nadia suna Kara gaisawa, ni kuwa ko ta kanshi banbi ba na wuce kitchen, seda ta shigo sannan tace
“Ke wannan handsome din fa? “
Tabe Baki nayi nace
“Handsome kam, Dan Anty Shamsiyya ne kanwar Abba. Internship yake a Nasarawa. “
Kanta ta gyada tace
“Yayi miki laifi ne? Naga Kamar kuna fada “
Kaina na girgiza Ina kokarin kuna gas nace
“Ko daya wallahi, in fact he’s nice. Kawai dai bana son mu saba dashi yazo Ya mutu”
“Mutu kuma? Haba ke kuwa, kowa ai se lokacin shi Yayi, Mukhtar da ya rasu lokacin shi ne. To ya zaayi? “
Na amince da abinda tace amma haka kurum nake jin bana son sabawa dashi, a rayuwata na tsani rabuwa da mutane, I’m selfish nafi son idan na samu Abu to ya zama nawa, kada abinnan ya tafi, to a wannan rayuwar ta Yaya, ai bazai yiwu ba.
Nadia bata bar gidanmu ba se wajen Karfe Tara na dare akaxo aka dauke ta tafi, Se naji inama ta zauna dan naji dadin yinin ranar. Ban bar parlon ba se wajen twelve, muna ta kallo nida Yaya Halifa, can kuma Yaya Suleiman yayi joining dinmu, anan na sake dashi for the first time Tun zuwanshi gidanmu.
AyshatuuuHutuna Ya Kare na koma school, big lady na zama yar level 200, tunda naje registering courses dina Naga babu su basics dinnan da nayi a level 1 na Fara jin wani shaukin dadi. Community based medical education, physiology, Anatomy, pharmacology and many da zaisa naji yeah I’m a medical student. Koda muka koma, first week ne kadai nayi day amma second week na tattara kayana na koma hostel, Dan na lura the higher we go, the hotter it becomes.
Ranar Friday na fito daga lecture din Biochemistry, wayata a hannu na, sauri nake Zanje hostel na dakko jakata saboda na wuce gida kafin a shiga sallah. wayata ringing tayi, na dakko na duba, Yaya Suleiman ne,
“Ajhumma! “
Ya fada Ina picking, dariya nayi nace
“Ajhussi! “
Se muka kara kwashewa dariya, sannan yace
“Nazo wucewa ta school dinku nace bari na dakko Sweetheart”
Cikin jin dadi nace
“Kai Yaya Suleiman, naji dadi, ka jirani kofar hostel dinmu, jakata kawai Zan dakko”
“At your service Ma’am “
Ko bana kusa nasan saluting dina Yayi, nayi Murmushi na katse wayar. Na tuna ranar da ya Fara cemin Ajhumma, naji haushi sosae, saboda ni nasan I’m not Ajhumma. Ina school ranar ya kirani da daddare lokacin mundan Fara sakewa da juna, yace min Ajhumma, I was like Kasan me kake fada kuwa, se yayi ta dariya, so ni kuma se nace mishi Ajhussi. Shikenan mukai naming kanmu, dake gaba dayanmu die hard fans din Korean dramas ne. Munada abubuwa sosae that are related ni dashi. I can even say, hakan ya karawa relationship dinmu karfi.+
Wani sanyi naji cikin raina, I’m sure kowacce mace ta samu
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 4 Chapter of 18