girgiza kanta...
“A kawo min sabon lemun tsami mai sanyi. A tsabtace wannan falon kamar ba'a taɓa taka shi ba. Party ɗin nan zai ci gaba!”
Ta juya zuwa ɗakin gyaranta...
A bayanta Bodyguards suka ɗauki mutumin, suka nufi Ɗakin Huɗu....
Can Gimbiya Maayah ta sake mamaye falon da kasaitarta...
kamar babu abin da ya taɓa faruwa..
Kudi, iko, da gata sun gama lalata zuciyarta…
A tsakiyar falon, inda aka gyara shi da labulen alharini, wasu Masu Rawa daga Indiya da aka ɗauko na musamman sun fito...
Mata guda uku da maza biyu, sanye da kayan rawa na gargajiya..
Sun fara rawa mai ban sha’awa (Indian Dance) cike da tsari da fasaha, inda suke juyawa da yin motsin kai da ido na musamman....Anan Maayah take zaune a kan Kujerar alfarma mai ƙasaita, tana kallo ba tare da ta nuna ko ɗan sha'awa ba...
Waƙar Indiya mai daɗi ta cika wurin, kuma Masu Rawa na ƙoƙarin nishaɗantar da Gimbiya ta kowace hanya. Sauran baƙin Party ɗin sun yi shiru, suna kallon rawar da kuma Gimbiya, wadda ta fi kowa muhimmanci a wurin...
Ana cikin wannan nishaɗi na ƙasaita sai aka ji wata ɗan hayaniya a babban ƙofar fadar... Hayaniyar ta kasance muryar mutum ɗaya wanda ke masifa da ƙarfi..
Nan take, wani Bodyguard ya shigo da girmamawa ya durƙusa a gaban Maayah...
“Gimbiya, Babban Minista Alhaji Bello yana waje. Ya zo da zafi yana masifa. Yana neman ganin ki a kan dalilin da ya sa kika wulaƙanta ɗansa, Zaid... Muna ƙoƙarin hana shi shiga saboda yanayin zafin ransa.”..
Maayah ta yi murmushi wanda ya nuna cewa ta shirya domin faɗa... Ta ɗaga hannu, ta yi nuni ga Masu Rawar Indiya da su tsaya...
“Ku barshi ya shigo. Idan har Babban Ministan ƙasa zai zo ya yi min faɗa a gidana, to zan nuna masa matakin sarauta da ikon Gimbiya Maayah! Ku barshi ya shigo. Kuma ku kawo Zaid tare da shi.”
Bodyguards suka buɗe ƙofar. Minista Bello ya shigo, fuskar sa cike da ɓacin rai... A bayansa kuma Zaid ne wanda yake duƙar da kansa saboda kunya...
“Gimbiya! Me kika yi haka?! Wa ya ba ki izinin kore min ɗa daga Party?! Na san cewa Sarki baya nan ne, amma wannan bai ba ki ikon wulaƙanta Babban Minista ba! Ni ba talaka ba ne! Ina da kuɗi! Ina da gata!”
Ministan ya fara masifa, muryarsa cike da zafi.
Nan da nan, Bodyguards guda biyu suka matso kusa da Ministan...
“Mai Girma Minista, don Allah ka sassauta muryarka. Kana cikin Fadar Sarauta ne!”
Amma Maayah ta ɗaga hannu....
“Ku kyale shi. Ina son in ji duk abinda yake da shi. Bari Minista ya yi speech.”
Minista Bello ya ci gaba da masifa, har ya kai ga zagin rashin ladabin Gimbiya... Ya rufe da cewa...
“A tunani na, za ki yi hankali. Amma a’a! Kuɗi da gata sun lalata ki!”
Bayan ya kammala, Maayah ta gyara zamanta a kan kujera. Ta lumshe idanunta tana kallon Minista da ɗansa, kamar tana kallon kashi. Ta fara magana da murya mai sanyi mai shiga jiki!...
“Minista, ka kammala? Zan fara da kai, Zaid.... Ka san dalilin da ya sa na kore ka, ko ba haka ba? Bari in tuna maka!”....
Maayah ta kalli Ministan...
“Minista Bello, ɗanka bai san matsayinsa ba! Yana da fitsara! Yana abu irin na ƙazaman mutane!”
Ta sake juyawa ga Zaid...
“Ka zo Party na, sannan ka aiko min da letter na soyayya a cikin makaranta! Letter! Wai kai har kasan soyayya? Ni Gimbiya ce! Ni ba ƴar makaranta ba ce da za a aiko mata letter na soyayya! Wannan wulaƙanci ne!”
Ta kalli Minista Bello, idonta cike da ƙasaita...
“Minista, ka ce kana da kuɗi da gata? To, ikon sarautata ya fi kuɗin da gatanka! Kuma a cikin wannan fadar, ni ce Sarauniya! Kana gani? Ka raina ni ne saboda mahaifina baya nan? To, ka sani, babu wanda Gimbiya Maayah take jin tsoro a duniya! Ko Shugaban Ƙasa ne! Idan har ɗanka ya sake min kallo na soyayya, ko kuma ya sake zuwa kusa da ni, to zan kore ka Minista! Zan cire maka mukaminka har abada!”
Ta ɗaga hannu...
“Bodyguards! Ku fitar da waɗannan mutanen marasa aji daga nan! Kuma ku tabbatar ban sake ganinsu ba a cikin Fadar masarautar Alhamra har abada!”...
Minista Bello da ɗansa Zaid sun ji matukar kunya da kuma tsoro! An ja su da ƙarfin tsiya daga cikin taron...
Maayah ta jingina a kujerar ta, fuskar ta cike da nasara...
★★★
Bayan korar Minista Bello, Fadar Maayah ta koma shiru, amma tashin hankali ya mamaye zukatan baƙin da ke wurin, sam babu wanda ya ji daɗin wukaƙancin da Maayah tayi wa minista....
A kan kujerar ta, ta jingina, fuskarta cike da baƙin ciki da gajiya....
“Mama Liyatu, raina fa ya sosu,”
Maayah ta yi magana da murya mai sanyi...
“Wannan Party ya zama cikin kasala! Ba ni da farin ciki! Komai a gidan nan yana da tsari, amma babu nishaɗi.”
Mama Liyatu ta durƙusa, hannunta a ƙirji...
“Allah ya taimaki Gimbiya, ya huci zuciyarki mai jiran gado. Komai zai daidaita.”
Maayah ta juya kai...
“Ba wannan nake so ba! Ina so a nemo mun wasu mutane masu barkwanci! Waɗanda za su iya sanya raina nishaɗi! Ina so in manta da wannan ƙazantar mutanen da suka fita..!”
Mama Liyatu ta yi saurin miƙewa...
“An gama, Gimbiya! Za a nemo miki ƙwararru! Allah ya taimaki Gimbiya mai jiran gado!”
“Duk wanda ya sanya ni farin ciki,”
Maayah ta ƙara,
“yana da kyauta mai tsoka! Har da mota da gida! Amma idan ka ƙara ɓata min rai… za ka ga tashin hankali!”
Nan take, aka sanar a birnin cewa Gimbiya Maayah tana neman masu barkwanci don sanya ta farin ciki, kuma kyauta mai tsoka na jiransu....
Cikin ɗan gajeren lokaci, mutane kusan talatin masu neman kyauta suka cika ƙofar Fadar..
Maayah ta kalle su ta faifan bidiyo (CCTV)...
“Mama Liyatu, ina buƙatar nishaɗi, ba tattara datti ba! Ba na buƙatar yawan wannan ƙazanta! A zaɓi mutum biyar kawai masu ɗan tsabta a ciki. A korar sauran da bulala don su san cewa Fadata ba gidan wasan kwaikwayo ba ce!”
Hakan kuwa aka yi. Bayan minti talatin, an kawo masu barkwanci guda biyar a gaban Gimbiya Maayah, dukansu sanye da sabbin tufafi kuma suna cikin tsoro...
Maayah ta zuba musu ido ɗaya bayan ɗaya...
“Shin zaku iya sanya ni farin ciki? Ni ba kamar sauran bane, ni Gimbiya Maayah ce. Ku san cewa ina da wuya wajen dariya.”
Ta sake ɓata rai...
“Duk wanda bai sanya ni nishaɗi ba, zai sha bulala 50 a gaban kowa! Kowa zai fito, cikin minti ɗaya ya yi barkwancinsa. Idan kuma duk ku ka sanya ni farin ciki, zan baku kyauta mai tsoka gaba ɗaya!”
Dukansu mutum biyar ɗin suka hadɗiye yawu cikin tsoro...
Na Ɗaya:
Wani saurayi mai ɗan lukuti ya fito.... Ya fara rawa ta barkwanci yana lanƙwasa jiki, ya fara wata baƙon sauti kamar kukan akuya...
Maayah ta sauƙe kai, ta toshe kunnenta da hannu...
“Mama Liyatu! Wane ne wannan? Meye wannan sautin na dabba? Ya ɓata min rai! Ku janye shi! Kuma ku tabbatar ya sha bulala 50 kafin ya fita daga gate ɗin mu!”
Nan take, Bodyguards suka ja shi da ƙarfi, ya fara neman gafarar su...
Na Biyu:
Wani dattijo ya shigo, ya fara salon sa na tsohuwar barkwanci ta hanyar ƙoƙarin yin yabon Maayah ta ƙarya...
Maayah ta zuba masa ido. Hawaye suka fara zuba mata, na baƙin ciki da bacin rai...
“Ku! Meye wannan? Kuna nufin baƙin ciki yake so ya sanya ni? Wannan ya fi mai yunkurin kisa ɗin nan ɓata min rai! Ku koreshi! Bulala 50!”
Na Uku:
Wani mai tumbi ya shigo, ya sanya wani abu a baya da ya ƙara masa girman ɗuwawu. Ya fara lanƙwasa jiki yana motsa tumbin sa da duwawun sa a salon wasa...
Maayah ta fara ƙoƙarin amai! Ta rufe bakinta da hannu....
“Wai ku! Meye wannan ƙazantar banza! Wannan datti ne! Wannan cin zarafin Sarauta ne! Ku cire min shi daga nan! Bulala 60 saboda ya sanya ni amai...!”
Na Huɗu:
Wani saurayi mai ƙarfi ya shigo. Ya fara ƙirari da yabon Sarauta da gata...
“ƴar Sarki jikar Sarki! Taka lafiyarki, ƴar gata! Hasken birnin Alhamra!” Haka ya ci gaba da yi da girmamawa mai yawa...
Maayah ta kawar da kai cikin gajiya...
“Wannan kirari a kowace rana ana min! Idan ma ba a yi min ba, sai an ga tashin hankali! Don haka, kaima ka ban wuri! Ka tafi! Babu wani abu na musamman a cikin kirari! Bulala 50!”
Na Biyar:
Shi ne mafi tsoro a cikin su. Ya ga yadda Gimbiya Maayah take ba da hukunci. Ya shigo, duk jikinsa na rawa, ya durƙusa a gaban Gimbiya. Yana kuka cike da tsoro!
“Dan Allah ki yi haƙuri! Na san ba zan iya sanya ki farin ciki ba! Wallahi inada Basir! Zai iya motsa wa saboda wannan tsoron! Ga tamowar da ke damuna! Wayyo Gimbiya! A gafurce ni...bulala hamsin zan iya rasa rayuwata ga iyalai..."
Nan take, Gimbiya Maayah ta fara dariya! Dariya ta gaske, ba tare da shautin da yake fita ba kamar na marasa aji, sai dai murmushin nishaɗi..
“Basir kuma? Subhanallah! Hahahaha!” Ta riƙe fuskarta, tana murmushi da nishaɗi!
“Tamowa! Hahaha!”
Mutumin ya yi mamaki, shi ma bai san cewa wannan roƙo na tausayi zai zama barkwanci ba...
Maayah ta tsaya, tana dariya cikin class. Ta nuna shi da yatsa...
“Kai ne! Mama Liyatu, wannan mutumin ya yi nasara! An sanya ni farin ciki da tamowa da Basir! Wannan shine nishaɗi na gaskiya!”
Ta umarta cikin nishaɗi..
“A ba shi kyauta mai tsoka! Motar alfarma, gida mai kyau, da kuma Kuɗi masu yawa! Sannan a ba shi likitan basir da ya dace! Amma sauran, duk su sha bulala 50 kowa!”
Gimbiya Maayah ta samu dariyarta a kan mugunta da kuma tausayi..
Mama Liyatu ta matso kusa da ita ta furta..
"Gimbiyata, sauran a musu sassauci mana, bulala hamsin yayi yawa kuma basu san da wannan hukuncin ba..na san ki da tausayi, a musu adalci..."
Gimbiya Maayah ta sassauta murya ta ce,
"Sauran ma, a basu dubu ɗari-ɗari saboda son taimaka mun nayi dariya..."
Mama Liyatu tayi murmushi domin wani sa'in gimbiya Maayah nada sauƙin kai...
Hakan kuwa akayi..
Bayan nan
Gimbiya Maayah ta zauna, amma nishaɗin ya mutu kamar wutar da iska ta hura.... Ba ta wuce minti biyu ba, sai ta miƙe, fuskarta ta koma taurinta na dā...
“Mama Liyatu, na gaji! Wannan Party ya ishe ni. Ina buƙatar hutawa!”
Mama Liyatu ta durƙusa da sauri. “An gama, Gimbiya. Za a yi yadda kika ce.”
Maayah ta kalli falon taron, wanda har yanzu akwai baƙi masu gata da kayan ciye-ciye masu tsada...
“Mama Liyatu! Ina nufin kowa ya watse yanzu! Ba na buƙatar ganin kowa a cikin Fada na! Wannan taro ya ƙare! Ku watsar da komai, ko da kuwa nawa ne kuɗin da aka kashe a kan wannan abincin marasa amfani!”
Mama Liyatu ta yi sauri ta tura Bodyguards da masu aiki don su fitar da kowa...
Cikin lokaci ƙanƙani, an watse taron! An kashe fitilu, an rufe ƙofa, kuma duk abincin Ƙasaita da aka kawo ya zama datti!..
Gimbiya Maayah ta shiga ɗakinta, baƙin ciki da gajiya sun koma mata.....
✨✨✨
Ayat ta shigo ɗakin baccinta cike da fara'a, ɗauke da manyan kulolin abinci na alfarma waɗanda aka girka na musamman..
"Lokacin cin abinci!"
ta faɗa cikin sanyin murya tana kallon Reems...
Yau ta ƙuduri aniyar cin abincin dare tare da abokinta kuliya. Ta ajiye tiren abincin, sannan ta juya zuwa sashen sutura don ta cire manyan kayan gimbiyancinta ta sanya lallausan kayan bacci domin ta saki jikinta...
Yayin da Ayat ta ba da baya, King Diamond a siffar kuliya ya daki hancinsa da wani irin kamshin kifi mai daɗi... Tun da yake a duniyar mutane, bai taba jin yunwa irin ta yau ba. Cikin hanzari, ya yi amfani da kafafunsa ya dinga bubbuɗe kulolin abincin. Ganin irin daɗin kifin da aka sarrafa, ya kasa jurewa...
Ya fara ci, sai da ya cinye kula na ɗaya tass.... Ya koma kan kula ta biyu, nan ma ya cinye tass, bai rage ko loma daya ba!..
Ayat ta nufo wurin abincin tana gyara gashinta, amma tana isa, ta tarar da kulolin wayam! Ta zaro ido, numfashinta ya kusa tsayawa...
"Wayyo! Duk ka cinye abincin? So kake na kwana da yunwa?"
Ta faɗa cikin murya mai cike da shagwaɓa...
"To ni yanzu me zan ci? Idan na sake komawa neman wani abincin, za su fara zargin me nake yi da abinci mai yawa haka, ni da ko rabi kula bana iya cinyewa!"...
Ganin Reems yana kokarin nufar wata karamar kula dake dauke da ferfesun kifi mai yaji, Ayat ta yi sauri ta janye kular...
"Wannan ma ba za a bar min ba?" ta faɗa tana turo baki...
Reems ya lallaɓa ya koma gefe ya kwanta kamar wanda aka zalunta...
Ganin haka, zuciyar Ayat ta karaya...
"Laaa... kar ka yi fushi My Reems... ga madara bari na baka."
Ta zuba masa madara mai ɗumi a kwanon azurfa, nan ma tass ya shanye gaba daya...
"Allah, ka cika ci da yawa! Zamanka sai a lambu!"
ta furta tana dariya da kuma mita...
Ta ɗauki ferfesun kifin ta kai loma ɗaya a baki, amma sai ta ga Reems ya zuba mata idanunsa na zinare, yana kallon lomar da take kaiwa...
"Na shiga uku! Wannan ma ba za ka bar min ba?"
Ta numfasa, sannan ta ce,
"To shikenan, bari na gani ko kana sona, za ka bar min wannan?" Ta ajiye masa kular...
Ai kuwa, King Diamond bai ko yi wata-wata ba, ya lankwame ragowar kifin nan tass!...
Ayat ta saki baki tana kallonsa, sannan ta fara kukan shagwaɓa tana shure-shure...
"Mugun kuliya!"
Ta miƙe ta nufi firij ɗinta, ta ɗauko fruits ta zauna can nesa da shi, ta fara cin apple ɗinta cikin ɓacin rai, tana kau da kai don kada ta kalle shi ta ji tausayinsa har ta ba shi ragowar...
King Diamond ya zauna yana lashe bakinsa, yana kallon yadda take cin apple ɗinta cikin fushi... A ransa ya ce,
"Ayat, da kinsan irin daɗi da nake ji na cewa yau kin zama uwar gida dake ciyar da ni, da tabbas ba zaki yi fushi ba."...
Ayat tana zaune a kan kujera can nesa da gadon, tana cin apple ɗinta cikin fushi, tana tauna shi da ƙarfi kamar tana tauna Reems ne....
Tana jujjuya ƙwayar idanunta, tana kau da kai duk sanda ta ji motsin kuliyar. Ta ƙuduri aniyar ba za ta kula shi ba har sai gari ya waye, domin kuwa ya kwashe mata duk abincin da take takama da shi...
King Diamond, dake cikin siffar kuliya, ya lura cewa wannan karon fushin na gaske ne. Ya san cewa idan bai yi dabara ba, Ayat ba za ta ba shi damar kwanciya kusa da ita ba yau....Ya miƙe a hankali, yana takunsa na kuliya mai sanyi, ya fara lallabawa har zuwa ƙafafunta...
Ya fara goga kansa a jikin lallausar fatar ƙafarta, yana fito da wani siririn sauti na kuliya mai ban tausayi...
Ayat ta ji sanyin gashin Reems a fatarta, ta yi ƙoƙarin janye ƙafarta tana mita...
"Ka tafi can! Mugun mai ci da yawa kawai. Ka cinye min shinkafa, ka cinye min tuwon shinkafa, ka cinye min kifi, ka cinye min ferfesun kifi, sannan ka shanye.. madara, yanzu kuma me kake nema? Apple ɗin ma so kake ka cinye?"
Duk da maganganun da take yi, ta kasa jure yadda Reems ya ɗaga kansa yana kallonta da idanunsa masu sheƙi, kamar yana roƙon gafara. Ya yi tsalle ya dawo kan cinyarta, ya fara goga hancinsa a hannunta dake riƙe da apple.
Ganin yadda ya dage wajen ba ta haƙuri, sai Ayat ta fara murmushi, har dariya ta fara subuce mata....
"Allah ya shirye ka Reems, ba ka da dama! To shi ke nan, tunda ka zama mai neman afuwa, bari na raba maka wannan."
Ta gutsuri ɗan ƙaramin guntun apple ta sanya masa a baki...
King Diamond ya karɓa ya fara taunawa, duk da cewa ba shi ne abin da yake so ba, amma taɓa shi da take yi da kuma murmushinta ya fi masa kowane irin abinci daɗi. Ayat ta rungume shi, tana shafa bayansa..
"Ka ga yadda kake da kyan gani? Idan ka daina wannan kwaɗayin, zan fi kowa daɗin zama da kai."
Ta koma kan gado tare da shi, tana jin wani irin natsuwa. Ta manta da duk wani damuwa. A wannan daren, ita da Reems ne kawai a duniyarsu ta daban. Ta kwanta tare da shi, tana raɗa masa a kunne..
"Wani lokacin ina jin kamar kana fahimtar kowace magana da nake yi, Reems.... Shin kai wanene ne a asali?"
King Diamond ya lumshe ido, yana jin ɗumin jikinta. A ransa ya ce,
"Ina fatan ranar da zan amsa miki wannan tambayar, Ayat, ba za ta zama ranar da za ki guje ni ba."....
*Likes ɗinku shine albashin marubuci*
👍 Like
🔁 Share
💬 Comment
*👑 MASARAUTAR ALHAMRA 👑*
_🪄 Gidan Mulki, Iko da Sirrin Zuciya 🪄_
✍🏽 By ASMEETAH WRITER
~Hasken Jajirtattu~
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
```JARUMAI WRITERS TEAM```
▶️ DON BIYO DAGA FARKO 👇
🔗 WhatsApp Channel:
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
📚 ArewaPen:
https://arewapen.com/u/asmeetahwriter
📖 Wattpad:
https://www.wattpad.com/user/asmeetahwriter
📲 Contact:
09065443871
📅 FARA TURA BOOK:
🔥 01 — 01 — 2026 🔥
📘 BOOK ONE
```MATAKIN FARKO```
CHAPTER 2️⃣4️⃣
*بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ*
Yayin da Ayat ta lula duniyar bacci, King Diamond ya fito daga siffar kuliya ya koma asalin sa. Ya zauna kusa da ita, yana shafa lallausan gashinta cikin wata irin kulawa mai ratsa jiki. Wani irin ƙauna yake ji yana ratsa kowace jijiyar jikinsa, ƙaunar da ba shi da mizanin aunata. Ya kalli kyakkyawar fuskarta, ya kasa jurewa, ya kwanta a gefenta a matsayinsa na mutum, baccin natsuwa ya kwashe shi shima...
Ayat mace ce mai yawan juyi a bacci. Cikin daren, ta fara neman inda take jin ɗumi. Ba tare da ta sani ba, ta haye saman King Diamond...
Can ta ɗora ƙafafunta a kan ƙirjinsa, bayan awanni ta yi pillow da cikin sa.... In the last night ta hau kansa gaba ɗaya ta ƙanƙame shi sosai kamar tana tsoron kar ya gudu, tana jin wani irin ɗumi dake sanya mata natsuwa. Shi ma Diamond, saboda gajiyar kwanakin nan, bai ji daddaɗan nauyin da ta ɗora masa ba, suka ci gaba da sharar baccinsu...
Yau ƙaddara ta so hakan, domin dukkaninsu sun makara har aka idar da sallar asuba a masarautar. Hasken gari ya fara ratsa ɗakin... King Diamond ya fara buɗe idanunsa, ya ji jikinsa ya yi nauyi. Yana kallon ƙasansa, sai ya tarar da Ayat ta mayar shi dokinta, ta rungume shi sosai....
Wani murmushin gefen baki ya yi, yana magana a ransa..
"Ta riƙe ni sosai, ta yaya zan janye ta ba tare da ta farka ba?" Ya san muddin ta buɗe ido ta ganshi a haka, babu abin da zai cece shi daga takobinta...
Cikin dabara da takatsantsan, King Diamond ya sa hannayensa ya ɗaga hannunta da ƙafafunta a hankali, ya juyar da ita zuwa gefe...
Sai Yaraffff! ta faɗa a kan gadon. Sakamakon hakan, Ayat ta fara motsawa, tana shirin buɗe idanunta domin ta tsinci kanta a wani sabon yanayi...
Cikin kifawar ido, ya yi amfani da ikonsa, ya ɓace a matsayin mutum ya koma siffar kuliya a gefenta, daidai lokacin da ta buɗe idanunta tana miƙa...
Ayat ta buɗe idanunta, ta ga gari ya waye sosai. Ta ji jikinta yana mata wani irin ɗumi daban, kuma tana jin tamkar ta yi matashi da wani abu faffaɗa.. Ta kalli Reems dake kwance a gefenta yana kallonta kamar yanzu ya tashi...
"Ya salam! Reems, mun makara!" ta furta tare da miƙe wa. Ta fara tunanin juyin da ta yi a daren, tana mamakin me ya sa take jin tamkar akwai mutum a kusa da ita...
"Wannan juyin nawa kam, ko gado ne ya ruguje ba zan sani ba," ta faɗa tana dariyar ciki..
Ta miƙe tsaye tana murza idanunta, tana jin wani irin ɗumi na musamman dake yawo a jikinta. Ta kalli gadon ta ga yadda ya hargitse, alamar ta yi juyi sosai....
Lokacin da ta kalli madubi tana shirin gyara gashinta, sai idonta ya sarƙe da wani abu dake kwance a kan kafaɗar rigarta ta bacci..
Ta sa hannu ta ɗauko shi. Dogon gashi ne guda ɗaya, fari sol kamar hasken wata, kuma yana sheƙi mai ban mamaki...
Ta zaro ido, ta matso da gashin kusa da idonta..
"Wannan kuma daga ina yake?" ta tambayi kanta..
Ta kalli kanta a madubi, gashin kanta baƙi ne wulk, ba shi da ko saƙar fari. Ta juyo ta kalli kuliyar...
"Reems, wannan gashin naka ne?" Ta matsa kusa da kuliyar ta duba gashin jikinsa. Duk da cewa kuliyar fara ce, amma gashin jikinta ɗan gajere ne kuma mai laushi, ba shi da tsayin da zai kai wannan gashin da take riƙe da shi a hannu..
"Wannan gashin na mutum ne, kuma mutum mai farin gashi!.."
Nan take zuciyarta ta harba. Hoton mutumin nan da ta gani a bakin kogi ya dawo mata...
"Mai Farin Gashi!" ta furta a hankali. Wani irin fargaba da tsoro suka baibaye ta...
"Shin ina nufin mutumin nan yana shigo min ɗaki ne yayin da nake bacci? Amma ta yaya? Masarautar nan fa tana da kariya!"
Ta fara duba ko'ina a ɗakin, tana bincike ƙarƙashin gado da bayan labule, tana jin kamar ana kallonta...
King Diamond, wanda ke cikin siffar kuliya, ya daskare a wurin da yake kwance. Zuciyarsa ta buga ganin ta tsinci wannan gashin nasa. Ya san cewa yau ya tafka babban kuskure. Yana kallon yadda Ayat take bincike cikin fargaba, yana jin tausayinta kuma yana jin tsoron abin da zai faru idan ta gano gaskiyar...
Ta sake dawowa kan gadon, ta zauna kusa da Reems...
"Reems, akwai abin da ka sani wanda ni ban sani ba? Me ya sa nake jin tamkar ba ni kaɗai nake a ɗakin nan ba?"..
Ta matse gashin a hannunta, sannan ta miƙe ta nufi wurin tufafinta...
"Yau dole na je na ga babban malamin tsafi na masarauta... Dole na san ko akwai wata inuwa dake biye da ni, domin wannan gashin ba na duniyar nan ba ne."..
Ta shige banɗaki da gaggawa, yayin da King Diamond ya sauƙe wani nannauyan numfashi. Ya san muddin ta kai wannan gashin wurin malamin tsafi, asirinsa na matsayin kuliya zai iya bayyana..
Ayat ta kammala shiryawa cikin kayan gimbiyanci, jikinta na fitar da daddaɗan ƙamshin mayukan alfarma. Ta nufo gadon da niyyar ɗaukar Reems, amma sai ta tarar da gurbinsa wayam. Ta ɗaga blanket, ta duba ƙarƙashin gado, ta bincika kowane lungu amma kuliya ba ta nan...
Cikin matsananciyar fargaba, ta juya kan madubin don ɗaukar gashin nan dake hannunta, nan ma ta iske ba komai!
Hankalinta ya tashi fiye da kowane lokaci...
"Reems! Reems ina ka shiga ne? Don Allah ka fito!"
Ta fara hawaye lokaci guda, zuciyarta na gaya mata cewa ɓacewar Reems babban rashi ne da ba za ta iya jurewa ba.
Tsabar ruɗani ya sa Ayat ta manta da sanya mayafin da take rufe fuskarta da shi. Ta buɗe ƙofa ta fito, gashinta baƙi wul ya bazu a bayanta, fuskarta tana sheƙi tamkar hasken farin wata...
Tana sauƙa falon ƙasa, ma'aikata da bayin da suka saba ganinta a rufe suka daskare...
Saratu da take ganinta kullum ma ta kasa motsi. Kyawun Ayat ya wuce misali, fara ce sol, idanunta masu kalar zinare suna fitar da hawaye... Kyawunta ya zama tamkar nurul-ayn, wani kwarjini ne dake sanya kowa sunkuyar da kai da daskarewa tsabar kallo. Ba su ma iya tambayarta ina za ta ba, sai kawai suka ba ta hanya tana gudu tana ƙiran sunan kuliyarta...
Tana fita harabar sashenta, jami'an dake tsaron wurin duka sumar tsaye suka yi. Ba su taɓa sanin cewa Gimbiya Ayat tana da wannan irin siffar ba. Suka bi ta da kallo, wasu ma har makaman hannunsu ya faɗi ƙasa ba tare da sun sani ba. Sun ɗauka wata halitta ce daga aljanna ta sauƙo cikin masarautar Alhamra...
Cikin kuka da ƙiran sunan Reems, Ayat ta nufi babban lambun dake cikin sashenta. Wuri ne mai cike da furanni jajaye da farare, masu ƙanshi da kyan gaske... Ta shiga duba bayan kowane fure da ƙarƙashin bishiyoyi, amma babu Reems babu alamunsa...
Wannan lambun dake sashenta ya kasance mafaka a gare ta, domin babu wanda yake da ikon shigowa ya takura mata a ciki. Ta duba ko'ina amma shiru, kukan da take yi ya ƙara tsananta...
Ganin ba ta ga Reems ba, ta durƙusa a tsakiyar lambun, ta haɗa kanta da gwiwa ta fashe da kuka mai ban tausayi...
"In har baka nan, to na sani na
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 21 Chapter of 39