a tsaye, kowacce da abin da yake damunta..
Gimbiya Maayah ta matso kusa da Ayat cikin sanyin jiki, tana son ba ta haƙuri..
"Aunty Ayat, dan Allah..."
Ayat ba ta bari ta ƙarasa ba, ta ɗaga mata hannu cikin dakatarwa. "Ba na son jin komai daga gare ki, Maayah. Ki tafi kawai."
Maayah ta haɗiye yawu, ranta ya ɓaci, ta juya ta fice daga fadar inda motocinta suka ja ta zuwa part ɗinta.
Yumna ta ƙaraso kusa da Ayat, ta kamo hannunta tana shafawa cikin sigar rarrashi,
"Dan Allah kiyi haƙuri Aunty Ayat, gaba ɗaya ranku ya ɓaci daga ke har Sarki..."
Ayat ta jinjina kai, muryarta ta ɗan yi sanyi ta furta
"Naji, Yumna. Ke ma ki tafi part ɗinki."
Bayan Yumna ta tafi, sai aka bar Zayana da Chingching wacce ke tsaye tana kuka a gefe.
Zayana ta taka har gaban Ayat, tana harararta da idanunta na kyanwa...
"Gimbiya sakaliya marar kunya! Kin fusata Sarki wanda hakan zai janyo miki tashin hankali. Dole kiyi respect ɗina tunda ni ce babbarku. Idan kuma rashin kunya ce kamar mahaifiyarki, to kuwa zakiyi asara duniya da lahira!"
Ayat ta juyo a slow, ranta ya ƙara ɓaci.. murmushi kawai ta sake tare da faɗin..
"Mahaifiyata kowa zai yi mata kyakkyawar shaida akan ita mutumiyar kirki ce. Ta rasa rayuwarta ne a ɗakin mijinta, tana haihuwar ƙanwata Firdos... Ke kuma fa? Mahaifiyarki tana can Australia zaman zawarci!"
Zayana ta fusata ta ce,
"To naji! Amma uwar tawa ai a gidan mulki take a can Australia ba zaman ƙasƙanci ba. Kin zo zaki zubar wa masarauta mutunci, wallahi sai an ɗau hukunci akanki!"
Ayat ta yi murmushin raini sannan ta ce,
"Zubar da mutunci wa masarauta yayi kamar yadda kika ajiye mata ƴar waje a cikinta? Ƴa fa kike da ita wacce ba ta sunnah ba! Kuma tana nan a cikin masarautar nan. Ke ba'a ɗauki hukunci akanki ba sai ni?"
Wani irin jiri ya kwashi Zayana, ta fusata ta ɗaga hannu za ta mari Ayat. Cikin zafin nama irin na jaruman tsaro ta cafke hannun ta murɗe shi kaɗan...
Wata dattijuwa, tsohuwar ma'aikaciyar fada da ta raine su, ta shigo.
"A'a, ya haka? Gimbiyoyi da faɗa kuma?"
Zayana ta daka mata tsawa.
"Ke kuma ina ruwanki tsohuwar banza!"
Ayat ta mayar mata, "Kinga irin rashin kunyar ba? Tsohuwar da tun kafin a auro uwar ki take masarautar nan, amma kike zaginta!"....
Zayana tana nuna Ayat da yatsa ta ce,
"Har yanzu baki san komai game da ni ba, da kuma ƴar da nake da ita, amma lokaci zai yi da za ki ji koma meye kuma kafin nan sai kinyi nadama domin mahaifiyata ba za ta taɓa ƙyale ki akan wannan batun ba...."
Daga nan ta daka uwar tsaki, ta fice tana huci ta shiga motarta..
Chingching ta ƙaraso tana kuka ta rungume Ayat. Ayat ta lallaɓa ƙanwarta, ta sanya ta a mota aka kai ta part ɗinta, ita ma ta shiga tata motar don komawa ɗaki, ranta cike da tunanin yadda rayuwarta ta kasance a haka...
✨
Misalin ƙarfe 8 na dare, Gimbiya Ayat tana zaune a cikin bedroom ɗinta, ranta a jagule da tunanin rigimar da suka yi da Zayana da kuma bacin ran da ta ga mahaifinta ya shiga...
Domin har cikin ranta bata son wannan zafin ran natan, tana so ta rage amma ta kasa...
Tana cikin wannan halin, sai taji ƙiran gaggawa daga babban elevator ɗin part ɗinta...
Ma'aikatan part ɗin gabaɗaya sun ruɗe, kowa na girgiza ganin Sarki Zaki da kansa ya tako har sashen Gimbiya Ayat...
Wannan lamari ne da ba a saba gani ba, domin sarki ƙiran gimbiyoyinsa yake yi zuwa fada, ba shi yake zuwa gare su ba. Ma'aikatan mata duk suka zube a ƙasa suna gaishe shi cikin girmamawa...
Sarki ya haura stairs ya nufi ɗakin Ayat. Tana jin muryar cewa Sarki ya iso, ta miƙe tsaye cikin mamaki da fargaba. Yana shigowa ɗakin da siffarsa ta Zaki mai ban tsoro, Ayat ta ɗago kai cike da firgici..
Amma yana haɗa ido da ita, sai wani abin al'ajabi ya faru.
A gaban idon ta, siffar Zakin nan ta ɓace, Sarki ya koma asalin mutumtaka. Farin dattijo kyakkyawa mai cike da kwarjini da muradi ya bayyana. Wani irin sanyayyen murmushi ya sakar mata, wanda ya nuna cewa duk fushin da aka gani a fada, ya riga ya yafe mata. Ayat ma ta kasa boye farin cikinta, murmushi ya suɓuce mata a ɓoye cikin mayafinta.
Ya tsaya na ɗan lokaci yana kallonta. Daga bisani cikin sanyin murya ya furta.
“Ayat…”
Sarki ya zauna a bakin gadonta na alfarma, ta durƙusa ta gaishe shi cikin ladabi. Bayan ta gaishe shi, Sarki ya nuna mata kusa da shi..
“Ki zauna.” ya faɗa yana kallonta..
Ta zauna, zuciyarta na bugawa kamar zata fito.
A wannan lokacin, duk wani ɓacin rai da rigimar da aka yi a fada tsakaninta da shi ya gushe. Sun zauna tamkar wasu aminan juna, inda Sarki ya zo ne domin ya sanyaya zuciyar ɗiyarsa wadda yake gani a matsayin wata bangare ta rayuwarsa.
Sarki ya numfasa, ya kalli Ayat sannan ya fara magana cikin sanyi..
“Na zo ne ba domin in hukunta ki ba.”
“Na zo ne domin in cire miki wani nauyi daga zuciyarki.”
Ayat ta ɗago kai a hankali. Idanunta suka haɗu da nasa...
Ya cigaba da faɗin
“Na san kina tunanin an fifita Maayah a kanki ko?.”
“Na san kina jin kamar an tsare rayuwarki ne, ita kuma an buɗe mata kofa.”
Ayat ta haɗiye yawu.
Hawayen da ta riƙe tun da rana suka fara taruwa...
“Abul…” ta faɗa da muryar da ke rawa,
“Me yasa ita take fita makaranta, mu kuma a’a?”
Sarki ya yi shiru na ɗan lokaci, kamar yana zaɓar kalmomi.
Sai ya ce a hankali
“Tun kafin in auri mahaifiyarta…
Muka yi yarjejeniya da ita.”
Ayat ta buɗe ido tana kallonsa a yayin da ya cigaba.
“Yarjejeniyar cewa Maayah ba za a hana ta ilimi ba. Ta dage, ta ce rayuwar ‘yarta ba za ta tsaya a bango ba.”
Ya ɗaga idonsa zuwa Ayat..
“Ba fifiko bane, Ayat.
Alƙawari ne da aka riga aka ɗauka.”
Ayat ta sauke numfashi mai nauyi.
Zuciyarta ta ɗan yi sanyi… amma ba gaba ɗaya ba.
“To ni fa?” ta tambaya a hankali.
“Ni ba ‘yarka ba ce?”
Sarki ya miƙa hannu, ya ɗora shi a kan nata..
“Ke ‘yata ce.
Kuma akwai abubuwan da na ke kare ki daga gare su.”
Ya tsaya yana nazari tare da furta...
“Ba hukunci bane.
Kariya ce.”
Daga nan ya miƙe tsaye.
“Ki yarda da ni, Ayat.
Ba duk abin da aka rufe miki, an rufe shi ne don cutar da ke ba.”
Sarki ya kamo hannun ta tare da miƙar da ita, ya matse shi a hankali yana kallon cikin idanunta waɗanda har yanzu akwai sauran jajirwar kuka..
"Ayat, ki duba fuskata. Ba zan taɓa iya jure ganin waɗannan idanun naki cikin hawaye ba. Fushin da na nuna a fada ɗazu, ba fushin tsana ba ne, fushi ne na uba da yake son kare mutuncin ƴarsa a gaban jama'a. Ki yafe wa mahaifinki idan na sa ki jin cewa ba kya da daraja a wurina."
Ayat cikin muryar kuka ta ce,
"Abul, na zata ka manta da ni ne. Na zata Maayah kawai kake so shi ya sa kake ba ta damar da kake haramta mana."
Ya juya ya nufi ƙofa, sannan ya tsaya.
“Kada ki bari shakku ya cinye zuciyarki.”
Daga nan ya fice, ƙofar ta rufe a hankali.
Ayat ta zauna ita kaɗai a ɗakin.
Zuciyarta ba ta sami cikakkiyar amsa ba…
amma ta daina jin wani ciwon yanzu, ganin mahaifinta ya tako har zuwa yanda take....
✨✨✨
Washegari, garin Alhamra ya waye da wani irin sanyi mai ratsa jiki. Ayat ta tashi ne ba don ta koshi da barci ba, sai dai don nauyin aikin da ke kanta a matsayinta na Inuwa. Idanunta sun ɗan yi lupu-lupu saboda rashin barci da tunani wanda ya hana ta runtsawa...
Ta shirya tsaf, ta sanya ɗaurin kirjinta, ta sanya kayan maza, sannan ta ɗaura rawanin ta duk ya rufe goshin. Ta sulale ta fita daga part ɗinta ta nufi sashen jami'an tsaro....
Tana isa sashen su Ibrahim, ta tarar da shi a zaune a wani fili na sirri da yake hutawa. Yana ganin ta, sai ya saki wani murmushi wanda ya nuna cewa ya daɗe yana jiran ta. Babu sauran zargi a tare da shi, sai dai wani irin sha'awa na son jin laushin hannun yaron da yake ganin tamkar mace...
"Ka zo kenan, Ɗan Ƙwaƙur?" Ibrahim ya faɗa yana miƙewa.
"Na zata ka gudu ne saboda rigimar da aka yi a fada jiya. Zo nan, yau jikina duk a mace yake, ina buƙatar wannan tausan naka."
Ibrahim ya cire babbar rigarsa, ya rage daga shi sai farar singlet wadda ta nuna ƙwanjin hannunsa da faɗin ƙirjinsa. Ya kwanta rubda-ciki a kan wata shimfiɗa ta alfarma, sannan ya yi nuni ga Inuwa..
"Fara daga kafaɗata, ina jin zafi sosai a wurin."
Ayat ta matso jiki na ɓari. Ta sanya hannayenta masu laushi a kan kafaɗun Ibrahim. Da zaran ta fara murzawa, Ibrahim ya sauƙe wani nannauyan numfashi..
"Masha Allah... Hannunka akwai albarka, Inuwa.... Wannan laushin hannun naka ko mace ba lallai ta kasance da shi ba. Sosa min gashin kaina ma yanzu."
Yayin da Inuwa yake sosa masa gashi tare da shafa masa baya a hankali, sai tunanin labarin da Sarki ya ba ta jiya ya dawo mata. Tana tunanin yadda rayuwarsu take a matsayin gimbiyoyi amma a yau gata tana tausa wa ma'aikacin mahaifinta. Wani ƙwallon kuka ya taso mata, ta kasa haɗiyewa...
Ibrahim ya ji jikin Inuwa yana ɗan rawa, kuma ya ji kamar wani abu na ɗiga a bayansa. Ya juyo da sauri ya ga Inuwa ya sunkuyar da kansa ƙasa, kuka yake yi ƙasa-ƙasa..
"Lafiya? Me ya faru Inuwa?"
Ibrahim ya tashi zaune cikin damuwa, ya kamo hannun Inuwa.
"Ko tsokanar da ma'aikata ke maka ce ta sa ka kuka? Ko kuma Gimbiya Maayah ce ta sanya ka wani aikin da ya fi ƙarfinka?"
Ayat ta kasa magana, sai kawai ta ƙara sunkuyar da kanta, tana jin dumin hannun Ibrahim a nata. A wannan lokacin, Ibrahim ya ji wani irin tausayin yaron ya kama shi, ya manta ma da cewa shi Master ne, ya fara lallashin Inuwa kamar ƙaninsa...
A lokacin da Ibrahim ya ga Inuwa yana kuka, zuciyarsa ta karye. Bai san lokacin da ya miƙa hannu ya janyo yaron zuwa kirjinsa ba, ya rungume shi sosai yana shafa bayansa don rarrashi..
Ayat ta ji wani irin shock ya ziyarci ilahirin jikinta. Tsoro da fargaba suka ziyarce ta. A ranta tana jin zafi da ɓacin ran yadda namiji ƙato, wanda ba muharraminta ba, ya rungume ta. Tana jin kamar ta keta hurumin asalin gimbiyancinta da mutuncinta, amma tana tsoron ko kaɗan ta nuna hakan don kar asirinta ya tonu a hannun Master Ibrahim...
Shi kuwa Ibrahim, rungumar da ya yi wa Inuwa ta jefa shi cikin wani yanayi na daban. Ya ji jikin yaron ya yi masa laushi da sanyi kamar na mace, wani irin kasala da feelings suka fara bin jijiyoyinsa. Ya fara sauƙe nannauyan numfashi, zuciyarsa tana bugawa da ƙarfi.
Ya rasa gane me yake faruwa da shi.
"Me yake faruwa da ni? Dan uwana namiji ne fa amma nake jin wannan yanayin? Tir da shaiɗan! Allah ya raba mu da wannan masifar," ya faɗa a ransa, yana kokarin kore tunanin cewa jikin da yake rungume da shi ba na namiji ba ne.
Jin yadda Master ya fara sauƙe ajiyar zuciya mai ƙarfi ne ya sa Ayat firgita...
Ta yi sauri ta janye jikinta ta ja da baya tana kallonsa da tsoro a idanunta. Ba tare da ta ce uffan ba, ta juya ta bar wurin da gudu tana kakkaɓe jikinta...
Inuwa ya nufi bakin gate ɗin fada cikin gaggawa, tana son barin harabar fadar baki ɗaya don ta je bakin kogi ta huta. Ta isa wurin littafin shige-da-fice ta fara signing....
Daidai lokacin, sai ga wata mota ta alfarma ta nufo gate din. Gimbiya Maayah ce a ciki, tana sanye da tsararren uniform na makarantarta mai kyan gaske. A ka'ida, Maayah tana da mugun girman kai, ba ta taɓa leƙo kai ta kalli jami'an tsaron da ke gaishe ta ba..
Amma yau, ganin Inuwa tsaye a bakin gate yana rubutu, ya sa ta zabura....Ta rage gilashin motar kaɗan, ta leƙo tana kallon sa ta cikin glas. Zuciyarta ta harba, wani irin masifar so ya sake mamaye ta...
Inuwa ya san cewa motar Maayah ce, kuma ya fahimci tana kallonsa amma ya ƙi ɗagowa. Wani irin raɗaɗi ya ji a zuciyarsa na ganin yadda Maayah ke fita cikin lumana da mota zuwa makaranta, yayin da ita kuma take cikin shigar maza tana badda kama tana fuskantar kaskanci... Duk da tasan dalilin mahaifinsu na barin Maayah ta fita, hakan bai hana ta jin kishi ba...
Maayah kuwa, har motarsu ta fice daga gate ɗin, tana nan maƙale a glas ɗin motar tana waiwayo baya tana kallon Inuwa. Ta kasa ɗauke idonta daga kansa, tana jin cewa yaron nan ya riga ya tafi da duk kan hankalinta....
Ayat tana kan dokinta, tana tafiya cikin daji kaɗan da zai kaita zuwa bakin kogi. Zuciyarta har yanzu tana bugawa saboda rungumar da Ibrahim ya yi mata da kuma kallon da Maayah ta jefa mata. Tana cikin wannan tunanin, sai idonta ya sauƙa akan wata Kuliya kyakkyawa, mai laushin gashi, kwance a ƙasa tana nishi...
Ganin yadda kuliyar take nuna ciwo a kafar hagu, Ayat ta kasa sharewa. Duk da shigar maza take yi, zuciyarta ta mace mai tausayi ta motsa. Ta yi sauri ta sauƙa daga kan dokin ta ƙarasa kusa da ita.
Ta ɗauki kuliyar ta ɗora a kan cinyarta, tana rarrashinta da murya kasa-kasa...
"Kiyi haƙuri kyakkyawa, yanzu zaki ji sauƙi..."
Ta ciro wani mai na musamman (Pain relief ointment) wanda take yawo da shi ko da yaushe a matsayinta na jami'in tsaro. Ta shashshafa wa kuliyar maganin a wurin ciwon, sannan ta ciro wani tsumma mai tsafta ta ɗaure mata ƙafar. Maganin yanada tasiri sosai, domin jininsa na ratsa jiki...
Tana ajiye kuliyar, sai ga ta ta fara takawa. Ko da yake tana ɗan dingishi, amma zafin ya mutu baki ɗaya. Ayat ta bi ta da kallo tana murmushi har ta ɓace a cikin ciyayi...
Ganin kuliyar ta tafi cikin ƙoshin lafiya ya ba ta wani irin nutsuwa. Ta sake hawa dokinta ta ƙarasa can bakin kogi, inda iska mai daɗi take busawa...
Tana isa wurin, ta sauƙa ta fuskanci kogin wanda ruwansa yake sheki kamar lu'u-lu'u. Wannan shi ne kaɗai wurin da take jin tana da yanci, wurin da tsuntsuwarta take jiran ta, kuma wurin da take iya tuna abokinta na yarinta...
Ayat ta kalli kewayen kogin, ta ga kowa shiru, babu kowa sai sautin tsuntsaye da busar iska. Tunanin ɓacin ran da take ciki da ƙuncin da ta samu wurin Ibrahim ya sa ta jin tana buƙatar wanka don ta wanke damuwar zuciyarta...
Ta ajiye dokinta a gefe, ta nufi bakin ruwan tana jin kamar duniyar tana hannunta...
Ba ta sani ba, a bayan bishiyar da tsuntsuwarta take, akwai wata halitta mai kwarjini a tsaye, cikin shigarsa ta fararen kaya masu daukar ido, dogon farin gashinsa yana kaɗawa a cikin iska...
Ransa a ɓace yake, yana tunanin meyasa wannan yaron ya ƙara ƙetare iyakar yankin da ya zaɓa don hutawa a duniyar mutane. Hannunsa ya fara miƙa wa don ƙiran takobinsa na sihiri don ya halaka shi, amma abin da ya gani ya sa shi daskarewa a wurin...
A gaban idonsa, yaga Inuwa ya cire rawanin kansa ya jefar a gefe. Sannan ya kwance ribon ɗin gashinsa, sai ga wani uban gashi, baƙi mai santsi ya zubo har gadon bayanta zuwa kunkumi...
King Diamond ya zaro ido cikin mamaki. A tunaninsa namiji ne, amma sai yaga abin ya sauya. Ya kalli yadda take fincike gashin baki da sajen da gashin girar da ta ƙara don badda kama. Sannan ta fara ɓalle rigar mazan dake jikinta ɗaya bayan ɗaya...
Idon King Diamond yana kanta, ya kasa ko kyafta idon. Ganin surar tsararriyar mace, mai fata mai sheƙi da kwarjini ya bayyana a gabansa, ya sa ya ji wani irin Shock wanda bai taɓa ji ba a duk tsawon mulkinsa na duniyar aljanu...
Ayat kuwa, tana jin daɗi ba tare da sanin cewa idon sarki aljani yana kanta ba. Ta rage saura iya short nicket da bra, gashinta a kwance a bayanta. Ta fara takawa a hankali tana shiga cikin sanyin ruwan kogin.
Tana zura kafarta, wani daɗi ya ratsa ta, ta lumshe idanunta tana murmushi.. Ta nitse a cikin ruwan tana wasa, tana iyo cikin nishaɗi kamar wata tsuntsuwar ruwa...
King Diamond yana nan a tsaye tamkar gunki, ya kasa motsawa. Kyan Ayat da irin yadda take wasa a cikin ruwan ya taɓa wani sashi na zuciyarsa da ya daɗe a bushe....
Yana tsaye a ɓoye, yana kallon ta yayin da take wasa a ruwa. Kwatsam, sai tunanin tattaunawar da suka yi a baya ya dawo masa. Ya tuna yadda ya ji wani abu game da wannan yaron amma bai ba shi muhimmanci ba..
Ya dunƙule hannunsa, ya lumshe idanuwansa, nan take siffarsa ta mutum ta ɓace, ya koma siffar aljan wadda mutum ba zai iya ganinsa ba. Ya sulale zuwa tsakiyar ruwan, ya tsaya daidai saitin inda take wasanta.
Ayat tana nishaɗi, tana nitsewa tana fitowa tana dariya ita kaɗai, ba ta san ana kallonta ba. Sautin dariyarta ya fara ratsa kwakwalwar King Diamond. Wannan dariyar ta faɗo masa da irin dariyar Ayat tana yarinya iri ɗaya ce, ba ta sauya ba...
Ya ƙura mata idanu, yana kallon kwayar idonta domin tabbatar da wacece ita. Abin da ya gani ya sanya shi tsinci kansa cikin wani sanyayyen murmushi...
"Ayat ɗina ce..."
Ya faɗa a ransa. Wannan dariyar ba za ta taba ɓace masa ba. A lokaci guda, ya ji wani irin shauƙi na son ya rungume ta..
Yanke hukunci ya yi akan ya bayyana kansa gare ta a yanzu. Ya lumshe ido, nan take ya dawo siffarsa ta mutum sanye da fararen kaya da dogon farin gashinsa yana sheƙi a saman ruwan. Ya tsaya daidai gabanta, idanunsa na kallon kyakkyawar fuskarta.
Ayat ta sa hannu ta shafe fuskarta domin ta goge ruwan da ya taru a idonta. Tana buɗewa, sai ta yi ido huɗu da wannan halitta mai ban tsoro da kwarjini a lokaci guda. Ganin dogon farin gashinsa da shekin da yake yi ya sanya ta firgita matuƙa.....kuma bata san da mutum a wurin ba kwatsam ta ganshi a ruwa tare da ita...
Ba ta san lokacin da ta saki wani irin mahaukacin ihu ba. Saboda tsananin gigita da tsoro, numfashinta ya tsaya, nan take ta sume ta faɗi cikin ruwan. Ta fara nutsewa zuwa kasan kogin, gashinta yana yawo a saman ruwan...
Ya tsaya cak a saman ruwan yana kallon inda take nitsewa, ya ji wani irin mamaki ya ziyarce shi..
Ya fara duban jikinsa yana jujjuya hannayensa da kallon fararen kayan jikinsa, a ransa yana tambayar kansa,
"Me kyakkyawar yarinyar nan ta gani a jikina da har ta kai ga yanke jiki ta suma? Shin kwarjini na ne yayi mata yawa ko kuwa muni ne dani?..."
👍 Like
🔁 Share
💬 Comment
*👑 MASARAUTAR ALHAMRA 👑*
_🪄 Gidan Mulki, Iko da Sirrin Zuciya 🪄_
✍🏽 By ASMEETAH WRITER
~Hasken Jajirtattu~
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
```JARUMAI WRITERS TEAM```
⚠️ SANARWA⚠️
Wannan littafi dukiyata ce a matsayina na marubuciya.
⚖️ Ba a yarda wani ko wata ya:
kwafa
gyara
sauya
ko amfani da wani sashe na wannan labari
ba tare da izini na kai tsaye ba.
Duk wanda ya saɓa, alhaki yana kansa..
▶️ DON BIYO DAGA FARKO 👇
🔗 WhatsApp Channel:
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
📚 ArewaPen:
https://arewapen.com/u/asmeetahwriter
📖 Wattpad:
https://www.wattpad.com/user/asmeetahwriter
📲 Contact:
09065443871
📅 FARA TURA BOOK:
🔥 01 — 01 — 2026 🔥
📘 BOOK ONE
```MATAKIN FARKO```
CHAPTER 7️⃣
*بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ*
A yayin da motocin alfarma suka tsaya a harabar makarantar Alhamra International Elite School, jami'an tsaro suka zagaye motar Maayah. Tana fitowa wani irin sanyi da shiru suka ratsa ko'ina. Daliban da ke wasa suka tsaya cak, malamai da ke tafiya suka gyara tsaiwarsu..
Maayah tana takawa ne cikin ƙasaita, fuskarta babu ko ɗigon murmushi, idanunta suna kallon sama kamar babu kowa a gabanta. Wannan shi ne ainihin halinta Izza, gadara, da nuna mulki...
Tana shiga cikin ajin, duk ɗaliban suka miƙe tsaye, kowanne ya durƙusa har ƙasa yana kwasar gaisuwa.
"Barka da isowa, Gimbiya Maayah!"
Ko kallo ba su isheta ba, ta wuce kai tsaye zuwa nata Seat ɗin. Wurin zamanta ya bambanta da na kowa, domin sarki ya bayar da umarnin a yi mata ado na musamman na sarauta, kujerar tana da laushin gaske kuma an yi mata ƙawa da zane na musamman..
Malami ya shigo aji domin koyarwa, amma yana ganin Maayah ta cire wayarta ta zamani tana danne-danne, sai ya ji wani irin fargaba. Malamin ya san cewa Maayah ba ta sauraron karatun, amma ba shi da ikon buɗe baki ya ce ta ajiye wayar..
Duk da abun yana cin ransa da na sauran malamai, sun gwammace su yi shiru da su ɓata wa Gimbiya rai, domin kuskure ɗaya zai iya sa su rasa aikinsu ko ma fiye da hakan..... Maayah tana zaune cikin Miskilanci, tana ganin hoton Inuwa daga cikin zuciyarta, tana murmushin mugunta yayin da kowa ke cikin tsoro.
Koda lokacin breakfast ya yi, babu ɗalibar da ta isa ta matsa kusa da Maayah ba tare da izini ba. Tana tafiya ne tamkar tana tattaka lu'u-lu'u. Duk wanda ya gitta ta, dole ya sunkuya...
Wannan makarantar ta zama karkashin ikon Maayah, inda kowa ke fargabar idanunta.
Ita a ranta, tana ganin kanta ta fi kowa daraja, kuma duk ilimin da ake koyarwa ba wani abu ba ne a gare ta, tunda ita Gimbiya ce kuma zuciyarta ta riga ta tafi ga wani jami'in tsaro wanda take tunanin talaka ne....
Sai a wannan lokacin Hafsat ta zo makarantar, anan motarta ta tsaya bodyguards ɗinta suka buɗe mata ƙofa ta fito sanye da ƙaton baƙin glass tana tauna chewing gum...
A duk faɗin makarantar, idan ka ga Maayah to tabbas za ka ga Hafsat a gefenta. Hafsat ba wai kawai ƙawa ba ce ita ce mutum ɗaya tilo da Maayah take sauraronsa, domin matsayinta na ƴar Shugaban ƙasa ya ba ta damar da ko malamai ba su da ita.
Duk da Hafsat tana da nata girman kan, amma a gaban Maayah ita kiyashi ce....
Hafsat ce take taya Maayah rarraba idanu ga sauran ɗalibai, kuma ita ce take ba ta labaran abubuwan da ke faruwa a wajen masarautar Alhamra...
A lokacin da malami yake tsaka da koyarwa, Hafsat za ta juyo ta raɗawa Maayah wata magana, su fara yin dariyar ƙasƙanci suna kallon malamin. Malamin zai ji ransa ya ɓaci, amma ganin ɗiyar Sarki da ɗiyar Shugaban ƙasa sun haɗe, sai kawai ya sunkuyar da kansa ya ci gaba da rubutu a board...
Hafsat ta kalli Maayah ta ce,
"Bestie, kalle shi yadda yake ta zufa, wai shi malami. Idan naso yau zan sa Daddy ya dakatar da shi daga aiki."
Maayah kawai murmushin gefen baki take yi, tana jin daɗin yadda kowa ke ƙarƙashin ikon su.
A lokacin da suke zaune wanda ko wacce ta kasance kujerar zamanta daban, Hafsat ta lura Maayah ba ta hayyacinta, sai duba waya take yi. Ta matso kusa da ita ta ce,
"Maayah, tun ɗazu kanki yana cikin waya. Ko akwai wani kyakkyawan ɗan Minister ne da kike boye min? Ko kuma wani Prince kika samo?"
Maayah ta yi ajiyar zuciya, ta kalli Hafsat cikin sanyin murya wanda ba ta saba yi wa kowa ba ta ce.
"Hafsat, akwai wani yaro a masarautarmu. Ba Prince ba ne, jami'in tsaro ne kawai... amma tunaninsa ya hana ni barci. Shi ne mafarkina."
Hafsat ta zaro ido cikin mamaki, "Jami'in tsaro? Maayah, kin san matsayinki kuwa? Yaya za ki so talaka?"
Maayah ta harari Hafsat, "Kada ki sake ƙiransa talaka. Kuma wannan sirri ne tsakanina da ke. Idan wani ya ji, zan iya yanke alaƙa da ke."
Bayan an tashi, Hafsat da Maayah suka fito kowa na takun alfarma. Motocin tsaro na fadar shugaban ƙasa da na masarautar Alhamra suka cika harabar. Hafsat ta yi wa Maayah sallama ta shiga tata motar, yayin da Maayah ta shiga tata, ranta yana ƙara kishirwar ganin Inuwa yayin da take komawa gida....
✨✨✨
A bangaren Gimbiya Firdos, wacce kowa ya sani da Chingching, ana tsaka da hargagi a cikin ɗakin wanka. Uma Altine tana ƙoƙarin yi mata wanka, amma Chingching ta sa kuka tamkar dukanta akayi..
"Wayyo Daddyyyy! Kazo ka taimake ni, Uma Altine za ta cire min nonuwanaaa!"
Ta furta tana wani
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 39