An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
[12/29, 2:19 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀
*BY*
*AYSHA NALADO*
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATIO*
*LITTAFI NA ƊAYA*
*PAGE 1*
Bismillahir-Rahmanir-Rahim
NIGER STATE
*Abayi close* fitacce ne kuma sananiyar unguwa a cikin garin na *Minna*, unguwace dake dauke da nau'ikan mutane kala kala
ƙabilu dabam dabam
musulmai,cristain, talakawa, masu matskaicin ƙarfi,da ma manya masu hannu da shuni, hakan yasa unguwar ke cakuɗe da gidaje maya da ƙanana.
Misalin karfe biyu na sulisin dare, ruwa ake tsugawa kamar da bakin kwarya, ko ina ya dau sanyi bakajin
ƙarar komai sai na yadda ruwa ke sauka a saman kwanukan gidajen mutane da mugun karfi haɗi da walkiya tare da razananiyar tsawa mai firgita mai sauraro tare da wani iska mai ƙarfi dake kadawa jefi jefi, hakan yasa gaba ɗaya garin ya ɗauki wani irin sanyi mai ratsa jiki.
A ɗaya daga cikin gidajen talakawan dake unguwar, kwance *AL AMEEN* yake cikin ɗan madaidaicin ɗakin shi dake zauren gidansu a kan yar madaidaiciyar katifar shi, kuɗundune yake cikin bargo idanun shi a lumshe, a kallo ɗaya zaka dauka barci yake, sai dai ko kaɗan ba haka bane, yadda yake sauke numfashi a wahale da yadda zufa ke karyo masa duk da matsanancin sanyi da iskar dake kaɗawa a garin ne zai tabbatar maka ba lafiya yake ba.
Cike da tsananin azabar ciwo ya buɗe rinannun idanun shi ya sauke akan wani jaka dake rataye jikin hangar dake manne a bangon ɗakin, so yake ya miƙe ya isa ga jakar domin ya dauki magungunan shi da ya musu kyakyawar buya a cikin jakar , sai dai inaa! Bazai iya ba domin Ko kwakwaran motsi baya Iya yi balle har akai ga batun miƙewa tsaye, idan kuwa yace zaiyi wani motsi mai karfi a halin da yake ciki, komai zai Iya faruwa da shi ciki harda rasa numfashin shi. Ci gaba yayi da kallon jakar, ji yake da yana da dama da ya kira jakar daga kwancen da yake, sai dai shi kanshi yasan hakan ba abune mai yuwuwa ba,
A hankali ya mayar da idanun shi ya lumshe, cike da tsananin azabar ciwon maran da ke neman hallaka shi, ya riga ya sani a duk sanda za'a wayi gari cikin irin wannan weather ko makamancin sa, to kuwa shi a ranar bashi da sauran lafiya, yau kimanin shekara hudu kenan yana fama da wannan lalurar, tun daga lokacin da yakai munzilin balaga, lokacin yana da shekaru sha takwas a duniya ya fara fuskantar wannan matsalar, tafi tafi abu ya fara ƙamari wanda har sai da ya danganta kanshi da likitaba tare da sanin kowa ba, shi ƙadai yake gwagwarmaya da faɗi tashin shi ba tare da kowa ya sani ba, ciki harda mahaifiyar shi wacce duk duniya bashi da kamar ta.
Cikin karfi hali irin nashi na jarumin namiji ya shiga, ambaton Allah a zuciyar shi domin ya kawo mishi
ɗaukin gaggawa, yayin da ya kai duka hannayenshi biyu ya dafe marar shi dake mishi wani irin matsanancin ciwo tare da daurewa kamar jijiyoyin gurin zasu tsinke.
Kimanin awa ɗaya da rabi ya dauka ba tare da bakin shi ya gaza da ambaton ALLAH ba, a hankali cikin hukucin ubangiji ya ji komai na lafa mishi.
A hankali ya miƙe hannunshi ɗaya dafe da marar shi, yana tangaɗi ya isa gaban jakan da maganin shi ke ciki, hannu ya saka can kasar jakar tare da dauko sacet din magani, guda data ya ɓalla ya maida sacet din, komawa yayi bakin katifar shi ya zauna tare da jawo jug din dake gefe cike da ruwa babu bata lokaci ya afa maganin ya kora da ruwa, ajiyar zuciya ya sauke tare da komawa ya kwanta rigingine yana sauke numfashi.
*Washe gari*
**********
6 Am dai dai Alarm ɗin agogon dake ajiye akan bed side drowan dake kusa da gadonta ya fara ƙara yana girgiza, a hankali ta buɗe kyawawan idanunta tare da miƙa hannu ta kashe alarm ɗin, kusan minti biyar ta kwashe a kwance kafin ta yaye bargon da ke lullube a jikinta ta miƙe zaune tana tattare dogon gashin kanta daya barbaje ta ɗaure shi a baya, yunkurawa tayi ta miƙe akan kafafunta, mika tayi tare da dogon hamma baki bude tana furta "in Jesus name" cikin zazzakar muryarta, kayan bacci ne riga da wando masu kauri a jikinta saboda yanayin da ake ciki yau na sanyi a garin, cike da kasala ta fara takawa a hankali Kamar wacce bata da laka a jiki ta nufi wani ɗan ƙofa ta buɗe ta shige.
Kusan minti 30 ta kwashe, sannan ta fito daure da dan ficilin tawel iyakarsa cinyoyinta, jikinta da gashin kanta na ɗigan ruwa, gaban mirron dake shake da kayan shafa na mata da turaruka ta tsaya, hand dryer ta kunna ta fara busar da gashin kanta bayan ta gaba ta shafe shi da mayukan gyaran gashin kusan kala uku masu kyau da tsada take ya dau kwalli da sheki, taje shi tayi kafin ta tattare shi tayi parking din shi a gefen kai.
Body lotion dinta mai kamshi da tsada ta shafa, tare da turarukan ta na jiki, fuskarta ta gyara batayi wani dogon kwalliya ba hoda kawai ta shafa da lip gloss sai maskara data karama Zara zaran lashes dinta.
Gaban makeken wadrob mai kofa shida dake dakin ta tsaya Wanda set ne da gadon da mirron dake dakin, kofan farko ta bude, inner wears ne shake a wurin kalakala kamar za'a bude kantin sayar da su, pant da vest da sock ta dauka ta maida kofar ta rufe, kofar dake kusa da na farko ta bude, school uniform dinta ne a goge a ninke kusan kala goma, ɗaya ta Zara tare da madai kofar ta rufe cikin Sauri ta shirya cikin farin riga mai dogon hannu tare da skirt sky blue damamme iyakarsa cinyanta, tayi stokin,farin sock ta Sanya dogo ta dauki wani farin both a cikin jerin takalmanta dake cikin abin jera takalma sunfi a kirga ta saka a kafarta, agogon ta dauka a cikin wani dirowa ta daura a hannuta, daga haka bata kara komai ba ta sunkuci gabjejen school bag dinta ta fice daga dakin.
Sauri sauri take saukowa daga kan stairs ta iso wawakeken falon dake kasa, a share yake tsab sai tashin kamshi yake babu abin da ke tashi sai sautin TV dake kunne a tsahar eagle TV wani babban pastor na wa'azi cikin karadi da tsoratarwa, da alama ma,aikatan gidan masu alhakin kula da tsabtar falon har sunyi aikin su, bata bi takan TV ba ta ajiye jakanta akan daya daga cikin kujerun dake kewaye da falo ta fice.
Hanyar dining Wanda ke kusa da makeken kitchen din gidan Wanda shine general kitchen na gidan a nan ake duk wani girki ta nufa, abin mamaki a shirye tsab ta tarad da dining din shake da warmers kala kala ga flask da kayan tea da sauran su.
Bata bata lokaci ba gurin Jan daya daga cikin kujerun dining din ta zauna tana mai duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta, motsin da taji daga stairs ne yasa tayi saurin daga kanta ta kalli hanyar gurin, kamar yadda tayi tsammani iyayen nata ne biyu mom and papa ke saukowa cikin shirin su ta tafiya aiki hannayen su sarke cikin na juna , mom sanye cikin dogon rigar less kanta babu dankwali, gashin dokin data kara a kanta a bayyane, papa kuma sanye cikin suit ash da kagansu kaga tsofafi masoya ya boko.
A tare suka sakar mata murmushi, itama babu bata lokaci kyakyawar fuskarta ta yalwatu da farin cikkin ganin iyayen nata.
Mikewa tayi tun kafin su ƙaraso tanufe su , jikin papa ta fara faɗawa ta bashi kyakkywan runguma tana cewa "gud morning my papa" shima zagayeta yayi da hannayen shi yana ɗan bubuga bayanta yake cewa "morning dear how ar U how was ur n9t." Ta amsa mai da "fyn papa." Sannan ta sake shi ta dawo jikin mom dake kallon su tana ta sakin murmushi, itama gaisawar sukayi kamar yadda sukayi da papa, kafin duk suka dunguma suka karasa kan dining.
Suna zama kuku ya futo daga kitchen da alamar dama tsaye yake yana jiran fitowar su, cike da girmamawa ya gaishesu, kafin ya shiga serving dinsu, abinci ne lafiyayyu akayi shi kusan kala bakwai kai da gani kasan a kwai almubazzaranci a lamarin.
Kusan duk a tare suka miƙe ba tare da sun ci abin kirki ba, Jakarta ta dauko a falo bayan ta shiga kitchen ta cikashi da chocolate da sauran kayan kwalama nau,i nau,i suka dunguma zuwa compound din gidan, ma,aikatan gidan ne suka Shiga kwasar gaisuwa, da sauri drivan dake kaita school ya fito da mota, duk da school din nasu ba wani nisa gare shi ba cikin anguwa ne amma kullum a mota ake kaita a dawo da ita tsabar gata.
Mom ce ta kalli driven cikin harshen nasara ta ce "Peter ka barshi kawai yau ni zan yi dropping dinta tunda ina da aikin safe, kai kuma in sun tashi sai kaje ka dauko ta." A ladabce ya amsa da "yes maa." Sallama suka kara yi da papa ya sunbace ta a kumatu bayan ya sake hugging dinta a hankali yake gaya mata ta kula mishi da kanta cikin shagwaba take amsawa a sangarce.
Daga cikin gidan zuwa school din kwata kwata tafiyar 15 minute sukayi har cikin school mom taso shigar da ita amma ta nuna bata so saboda gudun bacin ranta yasa mom ajiyeta a get, suna daga ma juna hannu har motar mom ya bace ma ganinta.
Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta sunkuci Jakarta ta goya, saida ta yi tsayuwar minti biyar a bakin get din ganin babu Wanda ya ganta yasa ta juya cikin sauri sauri gudu gudu ta bar bakin get din, dai dai zata shiga wata kwana dake bayan katangar school din taji ance " *JOY JAMES* " da ƙarfi, koda bata juya ba tasan me wannan muryar hakan yasa ta juyo ido huɗu sukayi da juna ta maka mai harara tare da kallon gargaɗi kafin ta juya ta runtuma da gudu, "Joy!! Joy!!" Haka David ya dinga kwala mata kira amma a banza dan bata juyo ba balle ta tsaya, ƙwafa David yayi kafin ya kinkimi jakar shi ya shige cikin school din.
*********
*AL AMEEN* kiran sallan Assalatun farko a kunnen shi saboda sabon da yayi da tashin asuba ko a wani iri hali yake idan har asuba tayi ko da kiran sallah ko babu zai farka, babu laifi yaji sauki sosai amma duk da hakan ciwon bawai ya gama sakin sa bane, lallaɓawa yayi ya mike yana yamutsa fuska alamar ciwo, ya dauki butar shi guda ɗaya dake ɗakin ƙofa ya nufa ya zare sakata tare da buɗe wa, wani sanyi ne ya doke shi wanda yasa yayi saurin rintse ido, danne zuciyar shi yayi ya zuro ƙafafun shi waje, a haka yana mammatse jikin shi ya nufi cikin gidan, tsakar gidan madaidaici ne mai dauke da daki babba guda daya ciki da falo, sai makewayi da madafi dake daga gefe.
Ƙofar ɗakin Ummi ya nufa kamar kullum duk asubar duniya shi yake tashin su, sai da yaji Ummi tayi gyaran murya alamar tana farke, sannan ya lallaɓa ya nufi toilet, ruwa ya kama, ya fito ya daura alwala da sauri sauri ya koma ɗaki yana rawar ɗari, ranar kasa fita sallar asuba yayi yana ji yana gani aka tada sallah a masallacin kusa da gidan su amma bazai iya fita ba domin yana tsoron abin da zaije ya dawo bugu da ƙari kuma dama ba wai ya gama wartsakewa bane, komawa yayi ya kwanta bayan ya idar da sallah, a maimakon tilawar alƙur,ani daya saba yi kullum bayan sallar asuba har gari yayi haske, dalili kuwa, saboda jiya bawai ya samu isasshen barci bane.
Ummi sai da tayi sallarta ta idar kafin ta ƙarasa kan karamin gadon dake uwar ɗakin ta, a tausahe ta kai hannu tana tsashin *FATIMA* Dake barcinta hankali kwance, ware ido fatima tayi akan Ummi, ganin ta buɗe ido yasa Ummi cewa "'ki tashi gari yayi haske, koda ba sallah zakiyi ba ki dauro alwala kizo kiyi arkar ɗinki." tashi tayi tana cewa "to Ummi" ganin ta tsahi yasa ummi komawa taci gaba da azkar ɗinta.
Alwala Fatima ta dauro ta zo ta zauna ta gabatar da azkar da addu'ointa kamar yadda ummu ta sabar mata koda kuwa tana jini ne bata yarda ta barta ta zauna haka kara zube ba .
Bayan ta idar miƙewa tayi taje gaban ummi ta tsuguna tace "ina kwana ummi." sai da ummi ta shafa adduar da take yi sannan ta juyo ta kalli fatima tace "lafiya ƙalau fatima, fatan kin tashi lafiya." ta amasa da "lafiya ƙalau ummi." "To alhamdulillah, maza ki tashi kije ki gaida yayan ki sai kizo ki amshi kuɗi ki sayo gawayi asaka ruwan wanka a dama kunu." "to ummi" fatima ta amsa tana miƙewa
Ɗakin dake zauren gidan ta nufa, tafi matukar mamakin jin yau bata jiyo sautin zazzaƙar muryar yayanata ba, haka dai ta daure tayi sallama abakin ƙofar da mamakinta shiru taji ba amsa kusan sau uku tana sallama taji shiru abinda ba kasafai ya cika faruwa ba, hannu tasa ta dan turo ƙofar dakin ta leƙa don duk atunaninta baya ciki ne, ga mamakinta ta hango shi kwance kan gadon shi ya ƙudundune waje ɗaya cike da mamaki ta juyo ta dawo cikin gidan, ganin yanayinta yasa ummi tambayarta lafiya, cikin dan damuwa tace "ummi me yasa mu yayana yau yake barcin bayan asuba ko bashi da lafiya ne." kallonta ummi tayi kafin tace ""barci kuma? cikin sigar tamaya gyada mata kai fatima tayi ta ƙara da cewa "na leƙa ɗakin shi na ganshi kwance ƙudundune cikin bargo" ɗan jim ummi tayi ita kanta ta cika da mamaki can kuma tace "eh to wata ƙila baiji daɗi bane, bari naje na duba shi ki dauki dari biyu cikin pos ki siyo gawayi ki hura wuta."
Bayan tafiyar fatima tashi ummi tayi taje ta duba Al'ameen, kamar yaddz FATIMA ta fada haka ta same shi, cike da alhini ta ja mishi kofar ta koma cikin gida.
Ko da Fatima ta dawo kitchen ta shige ta hura wuta dakyar ya kama saida ta ɓata lokaci kasancewar gawayin yayi sanyi, tana gamawa ta haɗa wanke wanke, koda ta gama ta samu ruwan baiyi wani zafi ba haka ta zauna tana fofitawa har ummi ta gama lazuminta ta fito ta same ta, ganin haka yasa ummi cewa "har yanzu baki Shiga wankan ba Bintz kinsan yayanayin makarantar Ku basu da sauki idan aka makara fa"
"Wlh ummi gawayin ne jikakke wutan baici sosai." Bude ruwan ummi tayi ganin zai isheta wanna idan ta juye duka yasa tace "je ki dauko bakitin wanka ki juye duka kije kiyi in kin tafi ni da yayanki sai musa muma muyi tunda mu babu Indi zamuje"
Bayan ta juye ruwan, ruwan kunu ummi tasa gani har bakwai ta gota, da kanta ta zauna tana fifita wutan, koda Fatima ta fito wanka ɗaki ta wuce ta ciro kayan makaranta cikin sif a goge tsab, da sauri sauri ta fara shiryawa, cikin farin Riga mai dogon hannu da skirt sky blue sai dai nata dogo ne ya sauka har kaurinta kasancewarta musulma ta daura dankwali tare da madaidaicin hijabi daya rife mata kirjinta, Jakarta ta dauko ta fito tsakar gidan bayan ta saka takalmi da safa, nan ta tarar ummi ta gama dama kunun koko, ganinta yasa ummi cewa yawaa Binta miko robar siga da ledan kulikuli in baki naki ki karya ki tafi, ajiye jakar tayi ta koma ɗaki dauko sugar da kulin ta fito tana zare ido ganin yadda lokaci yaja.
A gurguje tasha kunun bata ma shanye ba saboda da zafi ta ajiye saura ta sunkuci Jakarta, ummi tace "ki dauki nera hamsin a pos." Da Sauri ta shige dakin ta dauko tana fitowa tsakar gida *JOY* na kwada Sallama cikin gurbatacciyar hausarta, dai dai time ɗin kuma Al'ameen ya fito daga dakin shi sanye da singlet fari da dogon wando a jikinshi,turuss joy tayi gabanta na wani irin dokawa da mugun karfi take jikinta ya dau rawa lokacin da idanun Al'ameen ya sarke cikin nata.....
More comment more typing
Me buƙatar shiga group ya tuntuɓeni ta wannan lambar
09116099486
[12/29, 2:19 PM] AyshaNalado: 🌀🌀 *JOY* 🌀🌀
*BY*
*AYSHA NALADO*
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
*LITTAFI NA ƊAYA*
*PAGE 2*
Turusss Joy tayi gabata na wani irin dokawa, take jikinta ya ɗauki rawa lokacin da idanunta ya sarƙe cikin na Al'ameen, wani irin mugun kallo ya shiga jifanta da shi kallon gargaɗi da tsantsagwaron tsana wanda ita kaɗai ke ganin hakan , ta rasa dalili a duk lokacin da idanunta zai haɗu dana yayan Fatima ta kan rasa nutsuwarta, ta kan shiga firgici, da tashin hankali kwarjini yake mata kamar zaki, yanzu ma gani ta yi duk ya cika wajen, zata iya rantsuwa da yesu almasihu bata taɓa ganin murmushi a fuskarshi ba.
Cikin rawar muryar ta ce " good morning Yaya Elameen." Bata yi zaton zai amsa ba don bai cika amsa mata gaisuwa ba, sai dai ga mamakin ta dauke kai yayi daga kallonta ya ce "morning." tare da rabawa ta gefenta ya shige toilet ya turo ƙofa garam.
Daga ita har Fatima da Ummi da kallo suka bishi, bata san ta lula tunani ba sai da ta tsinkayi muryar Ummi na cewa "A'a Joy kece, baki tafi abinki ba kika tsaya biyoma Fatima salon ki ƙara makara, oya maza Ku tafi kar ku tsaya wasa Allah ya tsare." Sallama suka ma Ummi suka fice jikin Joy a sanyaye ko martanin murmushin da Fatima ke sakar mata bata iya mayar mata ba.
Da kallo Ummi ta bisu a ranta ta rasa wannan wani irin haɗuwar jini ne tsakanin Fatima da Joy, ba yadda bata yi ba don ta raba wannan alakar tun abin baiyi nisa ba, amma ina!!! abin ya ci tura tayi dukan tayi faɗan ta daure fuskar amma duk a banza karshe dole ta hakura ta fawwalawa Allah bayan ta gane tsakanin Joy da Fatima hadin Allah ne.
Motsin fitowar Al'ameen daga toilet ne ya dawo da ita hayyacinta, da kallo ta bishi har ya ajiye butar dake hannun shi, ranshi gaba ɗaya a jagule, ga ciwon daya kwana dashi yanzu kuma ga bacin ran ganin arniyar yarinyar nan mai fistari a tsaye a gidan su, tsugunawa yayi a gabanta cike da ladabi yace "Ina kwana Ummi." Amsa mishi tayi cike da kulawa tana nazartar yanayin shi, kwarai ta hango rashin nutsuwa a tattare da shi ga idanun shi ya dan fada, "Tabbas a kwai abin da ke damunshi don banza bata kai zomo kasuwa" ta fada a ranta, mikewa yayi bayan sun gama gaisawa ya nufi hanyar Zaure, murmushi tayi ta Riga ta sani dama bazai taba fada mata damuwarshi ba ita ta haife shi tafi kowa sanin zurfin cikin shi.
Har ya kai bakin Zaure ya ji tace "*AMINTACCE*." Sunan da take Kiran shi da shi kenan a wasu lokutan, zai Iya rantsuwa tunda ya mallaki hankalin kanshi bai taba ji Ummi ta kira sunanshi ba yayan Fatima tafi kiran shi sau da yawa, cak ya tsaya tare da juyowa, kallon juna sukayi cikin ido da sauri ya sauke kan shi ƙasa, a sanyaye tace "Meke damunka." Bai yi mamaki ba don yasan yadda Ummi tasan shi ciki da bai duk yadda taga sauyi a tare da shi sai ta gane.
Ba tare da ya dago kanshi ba ya ce "Ba koma Ummi jiya da zazzabin mura na kwana da ciwon kai amma Alhamdulillah zuwa yanzu ya sauka na ji sauki dan nasha maganin tun cikin daren." Cikin da nazarin yanayin shi ta ce "Ka tabbata." Ya gyada kai tare da ce wa "Eh Ummi." Ta ce "Allah ya kara sauki." Ya amsa da "Amin Ummi." "Kazo ka juye ruwa kayi wanka zaka ji karfin jikinka sai ka sha kunu ka kara shan maganin." "Toh Ummi."ya ce tare da juyawa ya nufi inda botikin wanka yake ranshi duk a ɓace.
*********
Suna fitowa Fatima riko hannunta tare da maka mata harara cikin harshen nasara Wanda shine yaren da Joy ta fi iyawa ta ce "why Bestie me yasa kike son saka kanki cikin damuwa ne sabo da ni." Kallonta Joy tayi ta sakar mata murmushi Wanda har sai da dimple dinta ya loza, cikin jin haushi Fatima ta ce "OK dariya ma na bakin ko." Fari ta mata da idanu ba tare da ta amsa ba hakan ya ƙara hassala Fatima, take ta hade rai kamar bata taɓa dariya ba sake hannun Joy tayi ta kama hanya zata wuce ta barta, ganin haka yasa Joy saurin shan gabanta rike kunnayenta tayi cikin marairaice fuska ta ce "sorry my Teetee." Jin sunan da ta kira ne yasa Fatima kwashewa da dariya tare da kai mata dundun wasa, itama dariyar ta kwashe da shi, tana kaucema dundun Fatima, sai da suka natsa, Fatima ta ce "kin san dai mun
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 1 Chapter of 22