π¬
[12/29, 2:46 PM] AyshaNalado: ππ *JOY* ππ
~FARHAT~
*PAGE 34*
Har ya k'arasa shigowa d'akin jikakkun idanunta na kafe a kan fuskar shi, ta kasa koda keftawa, gani take yi idan ta rintse ido ta bud'e zai 6acewa ganinta. Aysha ce ta bashi wajen zama kafin ta fice daga d'akin ta basu guri. Sai lokacin ya samu damar sauke idanunsa a kan ta, wani irin kwance-kwance gabansa ya yi ya fad'i, Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun! ya ambata a zuciya. hankalinsa ya yi k'ololuwar ganin gaba d'aya yadda ta rame ta lalace, ta fice daga hayyacinta kamar na Amiran daya sani ba, take tausayinta ya yi wa zuciyarsa kawanya.
Sassanyar Muryarta daya ratsa dodon kunnesa ya jawo hankalinsa, cikin maganarta 'kasa-k'asa irin ta majinyata take cewa; Yaya Ameen kaine da gaske! Ba gizo idanuna ke min ba, A she zan sake saka ka a idanuna kafin na amsa kiran mahaliccina, nagode sosai da ka zo gareni na yi farin ciki, nagode sosai." Ta karashe maganar tana sakin murmushi, hawayen soyayyarsa na kwaranyo mata ba tare da tasan da kwaranyarsu ba.
Jikinsa ne ya yi sanyi kalau! Gefe guda kuma wani irin kunyarta ya ji ya lullu6e shi, sai ya samu kansa da kasa ci gaba da kallon idanunta. Lallai zuciyar so makauniya ce, duk irin abin da ya aika ta mata Sam! bata ga laifinsa ba, bata yi fushi ba, wata d'aya da kwanaki ta kwashe cur! Tana jinya saboda soyayyarsa, bai ta6a koda aikowa bane yace ace mata sannu, amma take mashi godiya don yau ya shigo dubiyar da bata kai zuci ba.
Dakyar ya d'ago idanunsa da ke kyallin hawayen tausayinta ya sake kallota, da wani irin sassanyar murya ya ce " *Meerah* ya jikin ki."
Kusan suman wucin gadi ta yi, don lokacin da tattausar murya shi ya ratsa kunnenta, cak bugun zuciyarta ya tsaya, kamar sabuwar makauniya haka ta kure fuskar shi da kallo ba tare da ta amsa mishi ba.
Ganin haka yasa ya yi karfin halin sakar mata tattausar murmushi, abin da ya yi sanidiyar lumshewar idanunta a hankali ta sake budewa a kan shi, still murmushin na nan bai 6ace a fuskar ba, cikin k'asa k'asa da murya ya sake kira sunanta da cewa "My Meerah."
Gudun wahayenta ne ya ninku, la66anta ne su ka kama rawa alamar tana son furta wani abu amma ta kasa, gyada mata kai ya yi ya ce "Yess My Meerah, do u lik d name? Bata iya amsa tambayar ba, sai kawai ta tsinci kanta da rintse idanu tare da furta "Ya Allah na roke ka, kar ka farkar dani daga wannan daddadar barcin da nake yi, Ya Allah ka dauwamar dani a cinkasa." Ta karashe maganar da fashewa da kukan da ita kanta bata san na mai zata kira shi ba.
Bai san sanda ya isa gabanta ba, cike da tausayi ya shiga share mata hawaye, cikin rad'a ya ke cewa; It's reality Meerah ba mafarki bane, nine Ameen d'in ki a gabanki, bud'e idanunki ki kalleni." Samun kanta tayi da budewar kamar yadda ya umarta, suna hada idanu ta mika hannu ta kama nashi ta rike gam! Cikin kuka da fitar hayyaci ta ke cewa; Dan Allah Yaya Ameen kar ka barni, ka tsaya a tare dani ka dauwama a tare dani, kar ka gusa kusa dani na roke ka, yin hakan daidai yake da yankewar numfashi na, bazan iya rayuwa ba tare da kai ba, Ina son ka Ameen, ina son ka ina son ka, kaine rayuwata farin ciki na, idan babu kai a duniyar Amira zan zamo kamar mutum mutumi." Ta karashe da fashewa da wani irin kuka mai narka zuciyar mai sauraro.
"Shiii! ya isa Meerah, ga Ameen a gabanki, na yi miki alkawarin zan rayu dake zan zamo maji6ancin rayuwarki insha Allah." Ya fad'a cikin wani irin amo wanda yake fitowa tun daga kasan zuciyarsa.
Sun dad'e a haka hannun shi, cikin nata, dakyar ya lalla6a ya zare hannunsa tare da komawa mazauninsa ya zauna, yana ci gaba da gaya mata kamalai masu kwantar da hankali, sai ga Amira tana dariya kamar wayiya, kallonta yake cike da tausayi tare da kara tabbatar da cewa lallai shine farin cikinta.
kiran isha'i ne ya tayar da shi, kafin nan sai da ya yi mata alkawarin shigowa da safe ya dubata kuma ya jaddada mata ta tabbatar ta ci abinci da yawa.
Cikin kwana uku da faruwar haka sai ga Amira ta gyagije ta mike tsaye kan kafafunta, kamar ba itace a kwance rai a hannun Allah ba, lamarin da ya baiwa kowa matukar mamaki banda Aysha Fatima da Zainabu da su ka san abin da ke ciki.
Al'ameen yana iya kokarinsa wajen ganin ya wanzar da farin ciki a gareta, kullum yakan shiga ya dubata suyi hiran hakan ya jefawa Mama zargin wani abu a zuciyar ta, Fatima kam kusan tafi kowa farin ciki don tsakanin ta da Allah har zuciyar ta take kaunar Anty Amira, ba don warning din da Al'ameen ya mata akan kar fa fadawa Ummi ba, da tuni ta fada, duk da haka takan yi su6utar baki wani bin.
Yanzu damuwar Al'ameen bai wuce Aliyu ba, tun daga ranar da wannan abin ya faru basu sake haduwa ba ranar da damuwa yadda su ka rabu ya kwana, a zuciyar sa yaji bai kyauta ma shi ba, ya je gidan su sau biyu baya samun shi, kiran waya kam ya mishi ya fi sau shurin masaki amma baya d'agawa.
*********
Tun da Joy taje gida take ta tunanin albishirin da Fatima ta ce , zata mata a kan Yaya Ameen, kasa juriya tayi don akan duk abin da ya shafe shi zuciyar ta azalzala take, babu yadda bata so ba ta samu hanyar fita ran Sunday zuwa gidan sai dai babu dama, don Mom tasata tayi a gaba tunda sassafe suke wuce church ranar acen suna kusa wuni, haka ta kwana da daukin wayewar garin Monday, sai dai cikin rashin sa'a ranar karatu ta yi musu zafi, kuma da aka yi closing Mom ce da kanta ta zo daukarta, ba don ta so ba ta bita suka wuce gida da kudirin koma menene gobe baza ta rabu da Teetee ba sai ta gaya mata......
[12/29, 2:46 PM] AyshaNalado: ππ *JOY* ππ
~FARHAT~
*PAGE 35*
Washegari tun six thirty ta gama shirin school saboda gand'oki, a gaggauce ta sauko dining, a shirye ta same shi tsab! Kamar yadda ta tsammata, sai dai tea da cake kadai ta iya sha shima kad'an, sake kallon agogon dake daure a tsintsiyar hannunta ta yi, ganin bakwai saura yasa ta naima waje a parlour ta zauna tana kallon cartoon a tv duk da kallon kawai take amma hankalinta baya gurin, karfe bakwai dai-dai ta nufi upstairs, direct d'akin Mom ta nufa, tura kofar ta yi ta shiga ba tare da knocking ko excuse ba. Mom bata falo dama bata yi zaton ganinta a nan ba, kai tsaye ta nufi bedroom, muryar Mom da ya daki dodo kunnenta ne, ya dakatar da ita daga karasawa cikin d'akin.
Cike da tabbatarwa ta ke cewa "Kar ki damu Esther bani da kowa a duniyar nan bayan ke, ke kad'ai ne iyayenmu suna haifemu tare mu biyu kuma a yanzu basa raye, ki sani ita d'in ba komai bace a gareni fa ce tsanin cikar burina, lokacin dana dibar mana na daf da k'aratowa, sai na tabbatar da ya mallaka mata komai nasa daidai da tsinke bai bari ba, zan kashe shi, sannan daga baya ita......" Sauran zancen ne ya mak'ale lokacin da idanunta suka sauka a kan Joy rik'e da k'ofa, da alamar ta ji me take cewa' Jikinta ne yaso daukar rawa, amma tuna wacece Joy yasa ta dake rainonta ce, ta fi kowa sanin halinta bata da shiga sabgar da bai shafeta ba. "Excuse me." Ta fad'a tare da sauke wayar daga kunnenta, sakar mata murmushi ta yi, cike da wayancewa ta ware mata hannayenta tare da cewa; "Come to me my dearest princess." Martanin murmushi ta mayar mata ta k'arasa ta fad'a jikinta suka jungume juna, "Morning my lovely Mom." Joy ta fad'a tana zare jikinta daga na Mom, rike hanayenta Mom ta yi ta na kallon ta cikin ido don son karantar yanayinta ta ce "Morning my Happiness, har kin shirya? "Yes Mom har ma na yi breakfast." "Auh! Shine babu jira ko gud." Dariya ta kyalkyale da shi, "I'm sorry Mom na tashi da yunwa ne." "Ok no prblm." Mikewa ta yi tana cewa; "Bye bye! Mom till I came back." "Ok princess nima yanzu zan shirya na tafi gidan antynki Esther, tana can tana rigima da Mr Moses wai sai ya sake ta, yanzu ma da ita nake waya kika shigo Esther bata jin magana lamarinta ya fara isa na." Ta karashe maganar tare da dafe kai cike da takaici, "Ki yi hakuri Mom ki ci gaba da abin da kike yi na alkhairi zaki samu lada." Tana gama fad'in haka ta fice, a parlour n k'asa ta dauk'i jakarta ta fito compound, already Peter na jiranta basu 6ata lokaci ba, ta shiga ya tukata zuwa school.
Da biyu Mom ta fad'i wannan magana, don ta kauda hankalin joy daga zargi ne, hakan kuwa ya yi tasiri, da farko kalmar kisan da ta ji a cikin maganganun Mom sun saka ta a shakku, sai dai jin zancen Esther yasa ta yi watsi da lamarin don bata kaunar abin da zai had,a ta da tilon kanwar uwartata, tun a bedroom d'in Mom ta watsar da batun, ko kafin su isa school ta shafe babin batun a ranta.
Shiganta aji da mintuna kad'an Fatima ta iso, kasancewar babu teacher a ajin yasa ta tashi da gudu ta tare ta suka rungume juna, dakyar suka saki juna suka k'arasa sit suka zauna, sauran student na masu dariya masu jin haushin kawancensu kuma na ta6e baki da zund'en su.
"Teetee tell me about him, ki gaya min mana sai ja min rai kike yi." Dariya Fatima ta saka ta ce "Sai during break." Fushi Joy ta yi ta juya mata baya, magana Fatima ta dinga mata amma ta share da gaske fushi ta yi sosai don harda guntun kwallah ta share ba tare da sanin Fatin ba.
Abin da ya ba Fatima mamaki da kuma dariya ana ringing bell, Joy ta kalleta tare da cewa; "Oya tell me." Dariya Fatima ke son yi, amma sanin halin Joy na saurin fushi yasa ta danne, ta yi abinta a ciki, narai-narai Fatima ta yi da ido ta koma kalar tausayi kafin ta ce "Zan gaya miki amma sai kin saki fuskarki, kinji my beautiful friend." Murmushi ta saki, Fatima na dariya ta ce "Ba irin wannan ba gaskiya, idan ba haka ba kuma bazan fad'a ba." Ga mamakinta sai ji ta yi Joy ta kyalkyale da dariya. Gimtse nata dariyar ta yi tana binta da kallon mamaki, gira Joy ta d'age ta ce "A kan Yaya Ameen komai zan iya yi domin nima a yanzu shine komai nawa." Rass gaban Fatima ya fad'i da sauri ta kauda tunanin da yazo mata zuciya, jin Joy din ta ci gaba da cewa; "Shine ya bani matsayin kanwa, ya zame mina Yaya dan uwa abin da na nake tsananin kewa shekara da shekaru, ina jinsa har cikin bangon zuciyata." Murmushi Fatima ta yi ta ce "Umm! Kaji masu yayyi muma Allah ya bamu." "Amin!" Joy ta amsa mata a gatsile. Fatima ta ce tana murmushi, "To albishirinki." "Goro fari kal!" Ta amsa mata, "kawo kunnenki kiji." Matso da kunnenta ta yi fuskarta a washe yau dai finally zata ji abin da Teetee ke ja mata rai a kai kwana da kwanaki, Fatima ta kama kunnen ta matsa da bakinta cikin rad'a ta ce "Yaya Ameen ya yi budurwa very soon zai yi Aure, zai auriAnty Amira....." 6at tattausar murmushin dake kwance a kan fuskarta ya ba ce within second, kamar saukar gudumar wuta haka kalaman Fatima suka daki zuciyarta take idanunta suka fara juyawa, wani irin dunkulallen abu ya tokare mata kirji, take numfashinta ya shiga sama da kasa kamar mai cutar Asthma.
Jin shiru yasa Fatima kallon ta, a tsorace ta zaro idanu tare da furta "Na shiga uku." A bayyane "Joyyy!"ta kira sunanta da karfi tana jijjigata, suuu! Ta ta tafi zata fad'i, da sauri Fatima ta rikota cikin tashin hankali take kiran sunanta da karfi tana jijjigata, lamarin daya jawo hankalin yan tsirarun student d'in dake ajin, da gudu wasu suka yo kansu suna tambayar menene, ya yin da wasu suka tafi kiran class teacher d'in su. Wata cikin yan ajin ne tayi dabarar fasa pure water mai sanyi da ke hannunta ta shiga antaya mata daga kai zuwa fuskarta, wani irin ajiyar zuciya mai karfi ta shiga saukewa tana kokawa da numfashinta tare da kokarin hadiye kululun daya tokare mata wuya amma ina! Abin ya ci tura. Tuni Fatima ta dad'e da fara kuka, hannayenta bisa kai, ta ke cewa; "Na shigo uku! Joy dan Allah kar ki mutu ki barni, wasa nake yi miki." Ana cikin haka class teacher ya shigo bayan shi nurs na school d'in ne cikin uniform d'in su, d'auke da first aid box.....
Kishin balbalπ±
***********
A karo na babu adadi ya sake trying lambar, yana kallo har kiran ya katse kamar koda yaushe ba'a d'aga ba, text ya shiga rubuta ma shi na ban hakuri, tare da tabbatar mashi a kan lallai yana so su had'u a kwai story.
Ajiyar zuciya Aliyu ya sauke lokacin da ya gama duba sak'on, ya tabbatar ya zuwa yanzu abokin nasa ya yi laushi, zai jaraba sa'ar shi wata kila ya dace. Replay ya yi ma shi cewa; Zai shigo after magrib.
Karfe bakwai da yan mintuna a k'ofar gidansu Ameen ta yi Aliyu, zama ya yi a kan dakalin wajen ya zaro waya da niyyar kiran shi, sai ga shi, babu yabo babu fallasa Aliyu ya ba shi hannu suka yi musabaha, zama ya yi kusa da shi yana murmushi, ya dafa kafad'ar shi ya ce "Timekeeper nawa, har yanzu kana nan da dabi'arka ta r'iko ko?" Ba tare da ya kalleta shi ba ya amsa da "E kamar yadda kaima dabi'arka ta kafiya bata canza ba haka nima." Murmushi ya sake yi ya ce "Baka ce min ya jikina ba." Dage kafad'a Aliyu ya yi ya ce "Naga ai ba ka damu da lafiyar taka ba bare aje yi maka ya jiki." Dariya ya yi ya ce "To naji baka tambayeni ya jikin My Meerah ba." "Wacece haka?" Aliyu ya tambaya, amsa mashi ya yi da cewa; Masoyiyata mana Amira wacce kake fushi da ni saboda ita." Sai lokacin Aliyu ya d'ago ya kalle shi. Ajiyar zuciya Ameen ya sauke a nan ya kwashe duk abin da ya faru bayan wucewar shi ran nan har zuwa yanzu. Ya daura da "Aliyu ina matukar tausayinta, na amince zan zama maji6ancinta zan rayu da ita koda a zuciyata babu d'igon soyayyarta." "Bare ma baza a rasa ba." Aliyu ya fad'a yana hararanshi, murmushi kawai ya yi ba tare da ya tanka ba, sun dad'e suna hira, sosai Aliyu ya nuna mishi jin dadinsa game da amicewarsa da Amira ya k'ara da nusar da shi alfanun hakan ga shi karankanshi, sai dai koda wasa bai sako zancen Dr Abdul ba, don so yake ya bi komai daki-daki.
Tare suka yi isha'i bayan sun dawo daga masallaci ne, Aliyu ya shiga gida suka gaisa da Ummi, ya ce "Ummi ya mai jikin nan na kwanaki." Fara'ar fuskarta ce ta fadada ta ce "Hmmm! Aliyu mai jiki ta ji sauk'i sai hamdala, kar kaso ka ganta yanzu kamar ba ita ba." "Masha Allah, Ubangiji ya k'ara mata lafiya." "Amin Amin Aliyu nagode sosai." "To Ummi ni zan tafi a gayar da Fatima idan ta tashi." "To zata ji Aliyu a gaida mutan gida."
Tare suka fito da Al'ameen don yi masa rakiya, "Aboki ya kamata ka kira Amira mu gaisa, ka gabatar dani a matsayin babban aboki tun yanzu." Harara Ameen ya watsa masa, ya ce "Dalla Mallam muje na raka ka, matata mai tsada ce ba'a ganinta haka a arha." Rik'e ha6a Aliyu ya yi ya ce Ya ce "Da bamu san asalin balbela ba da sai tace mana daga saudiya take." Had'e rai Ameen ya yi ya ce "Me kake nufi."dariya Aliyu ya yi ya ce "Naga dai bada wani yare na yi magana ba ko?" "Kai dai ka sani ja'iri." Haka suka yi ta raha suna wasa da dariya har ya rako shi bakin Babar titi a nan suka yi sallama kamar kar su rabu.
Direct gidan su Amira Al'ameen ya nufa, ta sheka wanka da kwalliya tana jiran shi, jin sallamar shi yasa ka yin wuf ta mike, kallon da Mama ta watsa mata yasa ta yi saurin k'asa da kai, Aysha dake kallon abinda ke faruwa sai dariya take mata, hararar ta ta yi ta gefen ido tare da yin kwafa.
Shiga falon ya yi ya zauna bayan ya risina ya gaisar da Mama, Aysha da sauran kannenta suka gaishe shi, da gefen ido ya saki kallon side d'in da take, jin idanunta na yawa a kan shi, gaba d'aya ta shagala da kallon shi, Mama jin kowa ya gaishe shi banda ita yasa ta kallonta, ganin yadda ta shagala yasa ta cewa "Amira." Ina sam bata ji ba, don ta yi nisa Sam bata jin kira, ganin haka yasa Mama sake kiran sunanta a karo na biyu a tsawace "Amira!!!!" Firgigit ta yi ta kalli Mama, wani irin kunya ce ta lullu6eta sai kawai ta tashi da gudu ta bar falon, tafa hannaye Mama ta shiga yi tana sallallami.
Juyowa ta yi da zumar yiwa Al'ameen magana, sai dai wayam! babu shi babu mai kama da shi a falon sam babu wanda ya kula da sanda ya sudad'e ya fice, ai sai ta sake rafka salati tana rik'e haba take cewa; Aysha kin ga abin da na gani kuwa, dariya Aysha ta kyalkyale da shi, cike da nishad'i, "Ikon Allah, yaran zamani ka haifesu baka haifi halinsu ba ai kuwa banga ta zama ba ni hafsatu, wannan abin farin ciki har ina." ta fada tana mikewa tsaye............
Comment and share masoya
Oum Ummeetarh
09116099486
[12/29, 2:47 PM] AyshaNalado: ππ *JOY* ππ
~FARHAT~
*PAGE 36*
A firgice Mom ta shigo cikin makaranta, tana gurin aiki kirata same ta daga principal na school d'in Joy babu lafiya, office d'in principal ta nufa bayan gaisuwa principal da kanta ta yi mata jagora zuwa d'an karamin clinic d'in makarantar in da Joy ke kwance tana hutawa, don koda nurses suka tambayeta cewa ta yi kanta ke ciwo maganin ciwon kai kawai suka bata na kwaya ta sha, daga nan kuma suka bata bed rest kafin a iyayenta su zo.
Tun da ta kwanta idanunta ke lumshe, da gaske kanta ke yi mata ciwo, bayan ciwon da zuciyarta ke yi mata, har zuwa lokacin babu abin da ya ragu dangane da abin da take ji a zuciyarta,wannan kululun na nan tokare a kirjinta, babu abinda ke amsa kuwwa a kunnenta sai maganganun Fatima, babu yadda bata yi ba, don hawaye su zubo daga idanunta ko zata samu sassauci a zuciyarta amma abin ya faskara sai kukan zuciya take wanda irin wanda ke kara ma mutum kunci.
Cikin wannan yanayin Mom da principal suka iso d'akin, sarai ta ji su amma ta kasa bude ido ta kallesu, tana ji d'aya daga cikin nurses d'in wajen na yima Mom bayanin cewa kanta ta ke ciwo kuma sun yi mata abin da ya kamata sun bata magunguna, godiya Mom ta yi musu, ta matsa gaban gadon tare da dafa kanta, kan da d'umi, ga jijiya nan a goshinta sun tashi alamar dai ciwon kan mai yawa ne, kallon principal Mom ta yi ta ce "Dama tana da larurar ciwon kai tun tana k'arama, ina ga shine ya tasar mata, amma kuma gaskiya ya dad'e bai tashi ba don tun tana da shekara bakwai muka fitar da ita kasar Mexico ta ga wani babban likitan kwakwalwa shikenan bai k'ara tashi ba sai yau." Cike da Alhini principal ta jajanta lamarin. "Zan tagi da ita gida sai na kira Dr ya sake dubata." Cewar Mom, "Ok ba damuwa hakan dama shine daidai." Matso da mota Mom ta yi har bakin clinic d'in, da taimakon nurses ta samu ta isa motar don da ta mike jiri ne ya ringa dibanta dole a ka suka rirrik'eta suka taimaka mata.
Har a ka tashi Fatima kuka take yi, ta firgita sosai da yadda Joy ta yi, tunda suke tare bata ta6a ganin ta cikin yana yin makamancin wannan ba,ta yi nadamar fad'i mata wannan maganar yafi sau shurin masaki, sai dai taki baiwa zuciyarta damar gaskata zarginta na cewa Joy tana son Yaya Ameen ne, duk wani kofa da zai bata damar gasgata hakan ta toshe, har suka yi closing bata fahimci wani teacher da wani teacher bane suka shigo class d'in bare tasan me suka koyar, itama da nata kamashon ciwon kan ta koma gida, sa'arta d'aya Ummi bata nan, dama Yaya Ameen ta san baza ta same shi a gida ba daidai wannan lokacin sai da wani kwakkwaran dalili. Sallar azahar ta gabatar ko abinci bata iya ci ba, ta sha paracetamol ta hau gadon Ummi ta kwanta, babbar damuwarta rashin sanin halin da Joy ke ciki, gashi ko giyar wake tasha baza ta iya taka 'kafarta zuwa gidansu ba, haka ta yi kwanta cikin damuwa tana tunane tunane cikin sa'a barci ya yi awon gaba da ita mai cike da mafarkai barkatai.
**********
Dr Solo ya kalli Mom bayan ya gama duba Joy ya yi mata duk abin da ya makata ciki harda alluran barci don ta samu hutun zuciya da kwakwalwa, ya ce "Ciwon kan ta ne ya yi kokarin ta shi dalilin wani yanayin tashin hankali da ta shiga, amma zuwa yanzu da sauk'i, sai dai a kiyaye shigarta cikin irin wannan yanayin, gudun samun matsala." Cike da damuwa Mom ta ce "ok Dr mungode kwarai." A ranta tana mamakin wani irin tashin hankali ne Joy ta shiga haka. Sallama Dr ya yi ma Mom ya tafi tare da alkwarin sake kira zuwa dare yaji halin da ake ciki. Tare suka five da Mom daga d'akin don yi mashi rakiya.
Duk abin da Dr yake fada tana ji domin kuwa idanunta biyu, sai dai fitar su daga d'akin bai fi da minti biyar ba wani nannauyar barci ya yi a won gaba da ita.
Awa bakwai cur! Ta kwashe tana barci, kafin ta farka lokacin karfe shidda daidai na yamma, a hankali ta bud'e idanunta da suka mata nauyi, ta ji sauk'i sosai don wasai take jin kanta babu d'igon ciwo, haka ma nauyin zuciyarta ya ragu kaso hamsin cikin d'ari, a hankali ta lalla6a ta mik'e zaune, tankwashe kafa a tsakiyar gadon tare da rafka tagumi da hannayenta bibbbiyu.
Maganganun Fatima ne suka shiga dawo mata filla-filla, "Yaya Ameen ya yi budurwa very soon zai yi aure, zai auri Anty Amira." Kalmomin da su ka yi ta amsa kuwwa kenan a kunnenta suna neman rikitar mata da kwakwalwa, da sauri ta saka hannu ta toshe kunnenta da hannayenta tare da fashewa da kuka, take hawayen da take muradin fitarsu tuntuni suka samu hanya, a guje suka shiga wanke mata fuska.
Kuka tayi sosai don a kalla ta kwashe kusan awa guda tana yi, a hankali ta ji kuncin dake zuciyarta na yayewa, ajiyar zuciya ta shiga saukewa akai akai hadi da shessheka, ita kanta baza ta ce ga dalilin kukan nata ba abin da ta sani kawai umarnin zuciyarta take bi, sam! Zuciyarta baza ta iya jurar jin Kalmar Yaya Ameen yana son wata mace ba, balle har a kai ga batun aure, tabbas a duniya tana ganin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 22