jin kansa bai san mai zaice mata ba, sai kawai ya samu kansa da cewa; Ban san menene ya saka ta kuka ba, bansan me yasa na damu da damuwarta ba abin da na sani kawai ina jinta a zuciyata misalin yadda nake jin Fatima a raina, bana son ganin hawayenta kamar yadda bana son ganin hawayen Fatima.
Kasancewarta mai tsananin wayo, yasa ta yi murmushin yak'e wanda aka ce yafi kuka ciwo, tana share hawayenta da bayan hannu a fakaice ta ce " Wata kila hakan nada nasaba da yadda suna shaku da Fatima ne, tabbas nima ina kaunarta a raina kamar yadda nake kaunar Fatima." Tsura mata idanu ya yi, shin da gaske take abin da ta fada ya ke tambayar kansa, yayinda maganganunta suka maimaita Kansu d'aya bayan d'aya a kunnuwansa.
Ganin haka yasa ta ra6a ta fice ta gefensa ba tare da ta sake kallonsa ba.
************
Ragwab! Fatima ta koma ta zauna a kan gadon Ummi, hankalinta a tashe, shin' me abinda Joy tayi yake nufi, wannan shine karo na biyu da shigen irin haka ya faru, kar dai ace zargin da ta dade da cirewa aranta ne ke shirin tabbatuwa, zumbur ta mik'e, ya zama dole ta tabbatar kafin ta zartar da wani hukunci da mugun sauri ta biyo bayanta, a zaure suka yi kicibus da Al'ameen, kallon tuhumar daya jefe mata yasa da sauri ta ce "Yayana ka had'u da Joy a waje." Girgiza mata kai kawai ya iya yi ya bude d'akinsa ya shige,yana tambayarta Ummi ta dawo? A sanyaye ta amsa mashi da "A'a Taya." Kafin ta juya jiki a sanyaye ta kima cikin gida zuciyar t ciek da tunani kala-kala.
Sai da Joy ta kwashe kwana biyar bata je gidansu Fatima ba kuma bata je school ba, tana gida tana fama da mikin zuciyarta don sai da ta kwashe kwana biyu kwance tana fama da zazza6i da ciwon kai, lamarin da sai da Mom ta kira Dr solo ya daura mata drip kafin ta ji dama dama, wannan shurun na Joy ya saka Fatima a cikin matsanacin damuwar da ya kasa 6oyuwa a tattare da ita duk kuwa yadda ta so boyewar, Al'ameen ne ya fara lura, ritsata ya yi a d'akinsa ya tambayeta meke damunta, bata 6ata lokaci ba wajen sanar da shi damuwarta ba, san da ta ambaci Joy sai da gabansa ya fad'i, tun Daga ranar da abin nan ya faru da tunanin ta yake kwana yana tashi, taurin kai da dakiya ce kawai irin ta shi yasa bai bude baki ya tambayi Fatima ba, dakewa ya yi ya shiga bata baki a kan ta cire damuwa a ranta domin dai lafiya ita ke 6uya.
Ranar Monday kamar wasa Fatima na shiga class ta tarad da ita, da gudu ta karasa ta rungumeta ya baya, ranar basu maida hankalin kan darusan da aka koyar ba, saboda yadda sukayi kewar juna, Fatima ta so ta tuhumeta a kan abin da yasa ran nan ta fice ta barta daga ta yi mata zancen Yaya Ameen da Amira sai kuma wani tunani ya fado mata ar rai wanda tilas ya sakata fasawa.
**********
Ajiyar zuciya Zainabu ta sauke bayan ta gama sauraren jawabin Amira, kallon Amira tayi da ke kuka sha6e sha6e ta ce "kin tabbatar da abinda kike fada kuwa Amira." Cikin shessheaka ta ce "Tabbas na tabbar da idanuna na hango tsantsar soyayyar Arniyar yarinyar na kwance a cikin kayan idanunsa dan Allah Zainabu ki bani shawara ya zan yi wallahi zuciyata zata tarwatse."............
Afuwan masoyaπ
Oum Ummeetarh
09116099486
[12/29, 2:49 PM] AyshaNalado: ππ *JOY* ππ
~FARHAT~
*PAGE 40*
Mikiya Writer's Association
*Masu facebook ku yi following wannan account Ιin domin samun damar cin giveaway Ιin da muke yi, da kuma tattaunawa akan yanayin rayuwa*
https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL
Kwantar mata da hankali Zainabu ta yi, tare da ba ta shawara a kan ta yi kunnen uwar shegu da abin ta cire shi daga zuciyarta ta yi kamar bata fahimci komai ba tunda dai hasashe ta ke yi bata da tabbas a kan lamarin. Cikin kuka ta ce "Wallahi Zainabu da idona na gani ya rik'e hannayenta, suna bin juna da wani irin kallo, kollon da bai ta6a yi mini irin shi ba, irin kallon da nake fatan samu daga gare shi koda a mafarki ne. Ta6e baki Zainabu ta yi ya zuwa yanzu lamarin Amira ya fara bata haushi, cike da jin haushi, ta ce " Ke dai Wallahi an yi raguwar banza, yanzu haka ma fa ba abin da ki ke tunani ba ne shegen kishinki ne yasa ki ke ganin hakan, ta yaya Ustaz kamar Al'ameen zai tsaya soyayya da wata arniya mai fistari a tsaye, ai ruwa ba sa'an kwando ba ne, ni kam ko duk jikina kunne ne ban yarda ba." Murmushin takaici Amira ta yi, ta na kallon Zainabu a zuciyarta tana cewa; Hmm! Zainabu don dai ba ki san so ba ne shiyasa ki ke cewa haka, "Kallon fa?" Zainabu ta fad'a tana dan zaro mata ido had'i da d'an hararanta, girgiza kai ta yi tare da sakin murmushin yak'e wanda ya fi kuka ciwo.
Amira ta dauk'i shawaran Zainabu don kuwa koda wasa bata yarda ta yima Al'ameen maganar Joy ba haka ma Fatima duk irin yadda abin ya tsaya mata a rai kuwa.
A haka tafiya ta mik'a a ka kwashe satittika, har zuwa lokacin kuwa Al'ameen bai tura magabatansa wurin kawunnan Amira ba kamar yadda suna buk'ata kuma bai ce musu komai ba, ganin shirun nashi ya yi yawa yasa d'aya daga cikin k'annen marigayin mahaifin nata kiran Al'ameen har gida.
Tare suka shirya da Aliyu suka tafi gidan nasa bayan sallar isha'i, d'aya daga cikin samarin gidan ya musu iso har falon kawu Basiru kamar yadda suke kiran shi, bayan gaisuwa aka gabatar musu da ruwa da abin motsa baki, sai da suka d'an ta6a hira da Aliyu kasancewar kawun mutum mai yawan magana sai dai mafad'aci ne na karshe, haka ma Alin shima magananne ne ba laifi idan ya samu waje. Al'ameen kam kansa na k'asa yana saurarensu gabansa na fad'uwa ya k'agu ya ji kiran me a ka yi masa.
Sun dan d'auki lokaci a haka kafin kawu Basiru ya yi gyaran murya ya ce "Am! Aminullahi." D'agowa Al'ameen ya yi ya kalle shi tare da sake yin k'asa da kai cike da surukuta, "Abinda yasa na kira ka, mun ji shirunkaya yi waya, yau kimanin wata 3 da aka yi maka magana ka turo magabatan ka amma har yanzu shiru, to mun gaji da gafara sa kuma har yanzu bamu ga k'aho ba, domin dai yarinya cikin y'an uwanta wani ya ganta kuma ya nuna yana so , to kaga gida bai k'oshi ba ba'a kai waje ba, sai dai kasancewar mu ba k'ananun mutane bane yasa jiya muka zauna ni da y'an uwana, a kan maganar, yanzu dai an umarceni kasancewar nine k'arami a cikinsu suka wakiltani a kan na kira ka na shaida maka, an baka nan da sati d'aya idan har da gaske ka ke muji wani motsi idan kuma ba haka ba, to gaskiya komai zai iya faruwa, wannan shine mak'asudin kiran da na yi maka da fatan ka fahimce ni."
Tun kafin kawu Basiru ya kai aya a maganarsa, tuni gumi ya tsatsafowa Al'ameen a gaban goshi, banda dukan uku-uku babu abin da zuciyarsa ke yi, sai Aliyu ne ya yi karfin halin amsawa kawu Basiru da cewa; Na'am kawu mun fahimta." Ya ce "Toh dama kiran ke nan idan kuna da abin fad'i kuma ku fad'i ina saurara." Aliyu ne ya sake amsawa da "A yi hakuri kawu, in sha Allah zaku ji mu kafin satin." Da haka suka yi sallama da kawu basiru, Aliyu ya ajiye masa naira dubu uku suka fito.
Daga Alin har Al'ameen an rasa mai karfin halin cewa wani abu, har suka yi nisa da k'ofar gidan, shi Aliyu ganin halin tashin hankalin da abokinsa ya shiga ne ya sanyayar masa da jiki hakan ya tabbatar masa da akwai wata matsala, yayinda A bangaren Al'ameen yake hasaro irin tashin hankalin da Ummi ta shiga ranar da ya fara sanar mata da cewa; Iyayen Amira sun nemi ya turo, wannan na d'aya daga cikin abin da yasa har yau bai sake tayar da maganar ba, bawai don ya rasa naira dubu goman da za'a kai a matsayin kudin gaisuwar ba, kwarai ya hangi firgici da tashin hankali a cikin kwayar idanunta, wanda har ya kai ta ga son yin su6ul da baka a gabansa ta furta wasu kalamai da suka hana shi rintsawa a daren ranar.
Aliyu ne ya katse shirun da cewa; Abokina ya kamata fa ka yi wani motsi a kan lamarin nan, ka dai ji abinda kawu ya fad'a, kar ka yi sakacin da zaka rasa Amira domin na lura kiris suke jira shi yasa suka yi maka wannan daurin talalar, duk da nasan kai ko da ta subuce makan ba damuwa zaka yi ba tun da ba wani sonta kake yi ba" Ajiyar zuciya ya sauke, da wani irin sanyin murya wanda Aliyu bai ta6a jin ya yi irinta ba ya ce "Aliyu ina son Amira, wallahi ina kaunarta ina fatan ta zame mini uwar y'ay'ana, sai dai ina jin tsoron wani abu, ina ji a jikina a kwai gagarumar matsala." "Wacce irin matsala? Aliyu ya jefa masa tambayar cikin dan tashin hankali, cike da wani irin k'unci ya ce " Dangin mahai...." Sai kuma ya yi shiru ya girgiza kai, Aliyu ya dafa kafadarsa ya ce "Dan girman Allah kar ka boye mini matsalarka abokina, idan kamin haka zaka saka zuciyata cikin zullumi." Shiru ne ya ratsa tsakaninsu na yan sakanni, kamar bazai ce komai ba, can kuma ya sauke nannauyar ajiyar zuciya, kafin ya kwashe komai ya fad'awa Aliyu, shi kan shi Aliyu abin ya so girgiza zuciyarsa, sai dai bai nuna hakan a fili ba, ya ce "Wannan ba hujja ba ce da zai ka kasa sake tunkararta da wannan maganar, Ameen ka sani anzo gabar da dole ne kusan su wanene ku." Wani irin kallo ya shiga bin Aliyu da shi kamar ranar ya soma ganin shi a duniya, domin ya sosa masa inda ya dad'e yana masa k'aik'ayi." Basu rabu ba sai da suka tsara yadda lamarin zai gudana.
Bai iso gidan ba sai wajajen k'arfe goma da rabi, kamar yadda ya zata a tsakar gidan ya tarad da su, Fatima na kwance barci ya kwasheta yayinda Ummi ke kishingid'e tana sauraran redio, ta amsa masa sallama tana mik'ewa zaune, tare da gyara rik'on carbinta da gyangyadi yasa ya kusa subucewa daga hannunta.
"Barka da gida Ummi." Ya fad'a yana zama a gefen tabarmar, dan tsira mashi ido ta yi ganin kamar yana tattare da damuwa kafin ta amsa masa da "Yawwa barka da dawowa Amintacce." Ganin irin kallon da take binsa da shi yasa ya yi saurin yin kasa da kai, gabansa na faduwa, ya ce "Fatima ta yi barci kenan." Ta amsa da "E ta yi da kyar bayan ta gama dakon jiran ka, kazo ka ji mata hadda." Murmushi ya yi idanunsa kan kanwar ta shi tare sa cewa; "Allah sarki yar uwata." Lamarin da ya saka Ummi sakin murmushi ba tare da ta sani ba.
Bayan ya ci abinci ya fusakanci Ummi gabansa na wani irin dokawa yace "Ummi kawun Amira ya kirani d'azu a kan yana son ganina." Dakatawa ta yi da kokarin canza channel din da take kokarin yi ta zubawa fuskar shi manyan fararen idanunta masu cike da kwarjini...........
Har kullum Afuwan shine abin da zan iya cewa gareku masoyaπ
*Pls a ta6a comment domin shi ke saka min karsashin yi muku typing ko da ban yi niyya ba*
Oum ummeetarh.
09116099486
[12/29, 2:49 PM] AyshaNalado: ππ *JOY* ππ
~FARHAT~
*PAGE 41*
Mikiya Writers Association
*Masu facebook ku yi following wannan account Ιin domin samun damar cin giveaway Ιin da muke yi, da kuma tattaunawa akan yanayin rayuwa*
https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL
Bayan ya ci abinci ya fuskanci Ummi gabansa na wani irin dokawa yace "Ummi kawun Amira ya kirani d'azu a kan yana son ganina." Dakatawa ta yi da kokarin canza channel din da take yi ta zubawa fuskar shi manyan fararen idanunta masu cike da kwarjini, da sauri ya yi k'asa da nasa kan, tare da ci gaba da cewa; Ya bani nan da sati d'aya in turo magabatana idan har da gaske na ke yi, idan kuma na wuce hakan to za su aurad da ita ga wani dan uwanta wanda yake son ta." Har ya dasa aya bata iya dauke idanu daga kallon shi ba, yayinda shi kuma ko da wasa ya kasa d'agowa ya kalleta, Ajiyara zuciya ta sauke mai nauyin gaske, cikin sanyin murya ta ce, "Kar ka damu yayan Fatima in sha Allah, gobe zan je na samu yan uwan mahaifinku duk da sun min kyakkyawar kashedi a kan babu ni babu su kar na sake na sake ra6arsu yanzu lokaci ya yi da dole na neme su domin su sauke hakkin nauyin daya rataya a wuyansu." Ta karashe maganar cikin karyewar harshen, tare da sauri d'auke kwallar da ta ciko mata idanu.
Hankali tashe ya d'ago ya kalleta, suna had'a ido ta yi saurin d'auke kai, don bata son ya fahimci kuka take yi, sai dai tun a yanayin sautin muryarta ya fahimci kukan ta ke yi, bata son ta ba shi damar da zai jeho mata wata tambaya hakan yasa ta mi'ke da sauri ta shige d'akinta ba tare da sake kallon gefen da yake ba.
Gaba d'aya duk wani ga6a na jikinsa ya mutu, haka ya dinga sauke wani irin nunfashi mai hade da kunci, ya yi zama ya kusa na awa d'aya a tsakar gidan nan ba tare sa ko kwakkwaran mosti ya iya yi ba, shin dole sai sune zasu nema masa aure? Tun bai mallaki hanakalin kansa ba ya san cewa; Yan uwan mahaifinsu basa kaunarsu, a she dama dalilin da yasa Ummi bata yi musu zancensu kuma ta hane su da yin zancen su kenan, me yasa zasu ce kada su ra6e su shin su d'in ba jininsu ba ne, shin ita Ummi ina nata dangin suke? Tambayoyin da ya dinga kai komo kenan a cikin kwanyarsa, sai dai bashi da mai bashi amsarsu.
Ya dade sosai a zaune kafin ya yi karfin halin mikewa ya tashi Fatima ta wuce daki shi ma ya nufi nasa dakin bayan ya nade tabarmar.
Daren ranar ya jima kafin ya iya rintsawa, yayinda a bangaren Ummi yadda taga rana haka taga dare, ta yi kuka sosai bayan shigewarta d'aki, rayuwarta ce ta baya ya dinga dawo mata filla-filla, tabas ta yi rashin masoyi na hakika Al-hussain ya kaunaceta ya tallafeta ya nuna mata hakikanin soyayya duk da irin yadda gaba d'aya kafatanin danginsa su ke kin ta, kamar mujiya a cikin taron jama'a, sun yi mata korar wulakanci tana tsaka da alhinin rabuwa da masoyinta, sai dai dole haka zata sake tunkararsu a wannan ga6ar domin bata sa wadanda suka fisu bata san kowa ba sai su.
Ta yi kuka sosai wanda rabonta da yin irin shi tun rasuwar marigayin mijinta, dakyar ta danne zuciyarta ta mike ta dauro alwala, a kan darduma ta karkare wayar gari ranar, Da safe haka ta wayi gari idanunta sun yi jajur sun kumbura, Fatima ta tsorata da ganinta, sai dai yadda ta tsare gida sai ta kasa tambayarta me ya same ta, hankalin Al'ameen ba karamin tashi ya yi da ganin ta ba, sai dai kamar yadda Fatima ta kasa tambayarta haka shima ya kasa,jiki babu kwari ya shirya ya fice daga gidan zuwa wajen harkokinsa.
Karfe goma da rabi ta gama shirinta tsab cikin riga da zani na atamfa ta sanya hijab dinta gogagge mai matsakaicin tsayi, fes ta fito a matashiyar mace kyakkyawar gaske mai cike da haiba da kamala, sallama ta yi wa Fatima bayan ta bar mata sallahun abubuwan da zata gudanar a gidan kafin ta dawo.
Tafiyar mintuna ashirin a cikin a daidata sahu ya isar da ita unguwar mak'era, a hankali ta dunfari babangidan mai dauke sa babbar k'ofa hadi da babban zaure.
Family hause ne mai dauke da dakuna masu yawan gaske, kai tsaye ta nufi cikin gidan gabanta na fad'uwa sai dai ta dake, don babu alamun hakan a fuskarta.
Kasancewar safiya ce yawancin matan gidan na tsakar gida kowacce na gudanar da sabgar gabanta, sallamar da ta yi ne ya janyo hankalin mafi aksarin jama'ar dake tsakar gidan.
Kamar wata sabuwar halittta haka wasu daga cikin matan suka Shiga kallonta fuskokinsu dauke da tarin mamaki, yayinda bakin fuskoki a gare ta ke binta da kallon rashin sani.
D'aya daga cikin matan ne ta kasa jurewa sai da ta maganta, cikin tu'ajjabi ta ce "Wa nake gani haka Lamar Balkisu? Na kusa da ita ce ta amsa da " Taya ni fada dai, ashe ba gizo bane. Tsaki d'aya daga cikin su ta ja tare sa cewa; Allah ya wadaran naka ya lalace, dai dai lokacin kuma d'aya daga cikin mazan gidan ya sawo kai jin kananun maganganu na tashi daga matayen nasu wadanda dama kullum basu rabo da hakan.
Turus ya yi da farko lokacin da ya yi arba da ita, sai dai daga bisani ya wani irin hade rai kamar hadarin gabas, a kausashe cikin zare jajayen idanunsa ya ce "Meya kawo ki gidan nan Balkisu, Ashe ba mun yi miki kashedi sake rabar inuwarmu ba, shin ke mayya ce, to wallahi wallahi billahillazi la'ilaha illah huwa idan kika kara, minti biyu a cikin gidan nan sai na yi miki mummunar lahani.
Wannan haniyar ta Yaya Al-hassan kamar yadda suke Kiran shi ita ta janyo hankalin kafatanin sauran muatane gidan dake dakunansu, suka Shiga firfitowa d'aya bayan d'aya.
Gyaran muryar da aka yi daga bayansu yasa duk suka maida hankali gurin, sabanin Hassan fuskarshi washe ta ke da wani irin shu'umar murmushi, ............
Oum ummretarh
09116099486
[12/29, 2:50 PM] AyshaNalado: ππ *JOY* ππ
~FARHAT~
*PAGE 42*
Mikiya Writers Association
*Masu facebook ku yi following wannan account Ιin domin samun damar cin giveaway Ιin da muke yi, da kuma tattaunawa akan yanayin rayuwa*
https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL
"Ka barta Hassan, ka barta mu ji da me ta ke tafe." Yaya babba ya fad'a a gadarance, cike da umarni, Al-Hassan dake huci kamar kububuwa ya juya ya kalli inda sautin muryar d'an uwan nashi ke tashi, ya ce "Yaya ka yi hakuri ka barni in ci mata mutunci, in wulakantata, kamar yadda na yi mata alkawari duk ranar da na sake ganin kafarta a cikin gidan nan zan yi mata.
" Ka bari na ce Hassan" cewar Yaya babba, bayan ya k'araso kusa da Al-hassan d'in, daga haka ya juya ya nufi falon shi ba tare da sake cewa komai ba, wani irin huci Al-hassan ya dinga furzarwa yana bin Ummi da wani irin wulakantaccen kallo mai dauke da tsantsar tsana, daga bisani ya juya ya bi bayan dan uwansa a fusace.
Jiki babu kwari Ummi ta k'arasa madaidaicin falon mai d'auke da satin kujeru da k'aramar TV, guri ta nema ta zauna daga can gefe bayan tayi musu sallamar da cikinsu babu wanda ya amsa mata.
Shiru ya ratsa falon na y'an wasu dak'ik'ai, Yaya babba ne ya katse shirun ta hanyar cewa; Ke muke saurare Balkisu me ya kawo ki garemu, bayan mun riga mun gaya miki babumu babu ke har abadan da'ima."
Dagowa ta yi ta kalle shi idanunsa kem a kan ta, yana binta da wani irin mayen kallo kamar zai cinyeta da ido, da sauri ta d'auke kanta a zuciyarta tana neman tsari daga sharrin shi, domin bata manta waye Yaya babba duk da shekaru sun ja.
Cike da fargaba da tsananin fad'uwar gaba, ta samo gabatar musu da abin da ke tafe da ita, tun kafin ta k'arasa Al-hassan dake binta da mugun harara ya daka mata tsawa, a kausashe ya ci gaba da cewa "Ban ta6a sanin ke dabba ba ce, a cikin dabbobin ma tunkiya marar hankali ba sai yau Balki! Kina nufin ni ko d'aya daga cikin ahlina ne za mujelup nemar wa shegun y'ay'anki aure? Lallai kwakwalwar kan ki iri d'aya ne sak dana jaka shiyasa ta baki wannan shawaran na ki tunkare mu da wannan maganar. To ki sani har gaban abada babu gamin mu da shegun y'ay'anki, y'ay'an zina tsintattun y'ay'an kwararo........
" Ya isa Hassan ya isashe haka!!!" Ummi ta fada da wani irin murya mai kaushin gaske, tuni idanunta sun juye sun yi jajur, ga hawaye da tuni ya gama wanke mata fuska, Mikewa tsaye ta yi ta ci gaba da cewa a tswace "Kada ka kuskura ka sake sheganta mini y'ay'a, kada ka kuskura na ce maka, y'ay'ana ba shegu ba ne ina ji a jikina y'ay'ana y'ay'an halak ne tsarkakku!!! Ta k'arashe maganar tana nuna shi da yatsa idonta kem! Cikin nasa babu alamar tsoro ko shakkarsa a ciki sai ma tsagwaron tsana a cikinsu.
Mikewa ya yi a fusace ya iso gabanta yana cewa " Ni kike nunawa yatsa, ni kike yiwa ihu Balki! To na sake fad'a cewa y'ay'anki y'ay'an zina ne shegune me zaki yi??? Saukar miyan bakinta a fuskarta ya dakatar da shi daga hargagin da yake yi, a fusace ya daga hannu zai wanke mata fuska da mari, caraf! Yaya babba ya rike hannayensa ta baya, "koma ka zauna Hassan." Yaya babba ya ba shi umarni, bai zauna d'in ba sai kawai ya fice daga d'akin yana kwafa, zuciyarsa na tafarfasa
Bayan fitar Hassan, Yaya babba ya maida kallonsa ga Ummi data durkushe a wajen tana kuka mai tsuma zuciya, shu'umar murmushi ya saki, kafin ya bita ya tsuguna shima , cikin kasa-kasa da murya kamar me rada, ya fara cewa "Duk da shekaru sun ja, kina nan a balkisunki kyakkyawar mace fara kal, d'anya sharaf mai dauke da tarin baiwarwaki, kwata kwata baki tsufa ba balki, har yanzu ina nan da kudirina a kan ki, ki amincemin koda sau d'aya ne na cimma muradina a kan ki ni kuma na miki alkawarin zan tsaya miki da ke da y'ay'anki har duniya ta nad'e muddin ina numfashi.
An yi ta babu dad'i sosai a gidan, domin sun yi musayen maganganu a tsakanin su,Ummi ta kauda ido ta wanke Yaya babba tas ta kira shi da fasiki dan akuya, kasancewar Tana cikin bakin ciki da bacin an sheganta mata y'ay'a da Hassan ya yi.
Sosai ran Yaya babba ya 6aci, Inda ya dauke mummunan kudiri akanta idea da shegun y'ay'anta, ita kuma ta kalli cikin idanunsa ta sanar masa ta Allah ba yasa ba da Allah ta dogara, da su nemarwa yayanta aure da kar su nemar musu duk daya a gareta Allah yana nan kuma bazai ta6a bari su wulakanta ba, a karshe haka Ummi ta kamo hanya gida, babu nasara sai tarin bakin ciki da ta k'unso tare da tayar mata da tsohon mikin da ta dad'e da lullu6eshi a can karkashin zuciyarta.
Su hudu ne y'an uwan marigayi mijinta Al-husssain. Mata biyu maza uku Yaya Tanimu wanda suke kira da yaya babba kasancewar shine babba a cikin su, sai Hassan sai hussain da yake mijinta, sai mata biyu wadanda ke gidajen mazajensu kowacce ta tara nata iyalin.
Kaddarace ta jeho ta cikin ahlinsu ba tare da ta san sanda ta giffa a gare ta ba, ta yi gwagwarmaya sosai a lokacin duk da karancin shekarunta, ta kowane bangare ta fuskanci kalubale rayuwa, duk don kasancewarta tsintacciya mara galihu, Mara gaba Mara baya wacce bata san inda ta dosa ba.
Tanimu mutuncinta yake nema ido rufe yake so ya keta mata haddi tun kafin su yi aure da marigayi, ta dauka aurenta da dan uwansa zai sa, ya rabu da ita , sai dai hakan babu abinda ya rage a kan irin bibiyar da yake yi wa mutuncinta saboda rashin tsoron Allah har da igiyar aurenta, igiyar aurenma na dan uwansa, sai dai har mijinta ya kwanta dama bai samu
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 18 Chapter of 22