babu abin da yafi wannan tashin hankali a gareta, a halin yanzu ita kanta bata san meke damunta ba, bata kishi ba domin ita kadai ta tashi gaban iyayenta abin da ta sani kawai soyayya, shiyasa abin da ya faru da ita yau bata san da mai zata kwatantashi ba.
Shigowar Mom ne ya katse tunaninta, da sauri Mom ta k'araso ganin ta a zaune, zama ta yi a kusa da ita ta kai hannu tana tatta6a goshinta zuwa wuyanta,salam! Babu zafi ajiyar zuciya ta sauke tare da godiya da abin bautarsu. Cike da kulawa tace "Princess ya jikin, yaya ki ke ji yanzu, ina ne ke yi ma ki ciwo?" "I'm fine Mom babu in da ke min ciwo, naji sauk'i." "Ok bari na kira miki Papanki ku gaisa tun dazu yake ta kira yana son yaji muryarki." Da d'unbin mamaki a fuskarta ta ce "Papa kuma?" "Yes Ur Papa." Zun6ura baki ta yi ta ce "Ya daina sona yanzu ai." Murmushi Mom ta yi ta ce "Who tell that, a duniya babu abin da Mr James yake kauna sama dake tillon y'arsa,ina tabbatar miki yafi kaunarki fiye da ni dana kawo ki duniya." Ta karashe maganar cike da d'aci a muryarta, amma sam Joy bata fahimci komai ba saboda kakanun shekaru, "Na sani Mom a da Papa yana sona amma cikin yan kwanakin nan ya canza min, abin ya dame ni amma na yi masa uzuri, nasan aiki ne ya sha kan shi." "Of course princess haka ne, jiya ya kammala duk aikin sa ya kaishi kasar Canada, yanzu hankalin sa gaba daya ya waiwayo kan little princess d'in shi, tun safe yake min waya yana neman ki,. Ta kai karshen maganar tana mika mata wayarta da ta yi dialling lambar Papa.
Cike da shauk'in so irinta tsakanin da da mahaifi ta kara wayar a kunnenta tare da cewa; He'll My Papa." "My Joy My everting." Ya amsa mata cike da soyayya, sun Dade Suna waya ta yi mai korafi akan shareta da yake yi kwana biyu hakuri ya bata da cewa shima bai san mai ya same shi ba cikin kwanakin nan, sun dad'e Suna waya kafin su yi sallama.
Mom ta amshi wayarta tana sakin wani shu'umin murmushi wanda ita kad'ai tasan ma'anarsa.......
Ko kunsan ma'anar murmushin Mom, ni da ban sani baπ’
Oum ummeetarh
09116099486
[12/29, 2:47 PM] AyshaNalado: ππ *JOY* ππ
~FARHAT~
*PAGE 37*
Mikiya Writer's Association
No editingπ
Washegari a sanyaye Fatima ta gama shirin school, gaba d'aya bata cikin walwala har sai da Ummi ta kula da yanayinta ta tambayeta ko bata da lafiya ne. Al'ameen dake wanki a tsakar gida lokacin da Ummi ke mata magana ya d'ago ya kalleta, tabbas shima ya hangi damuwa da rashin walwala a tare da ita, hakan yasa ya ce mata "Idan baza ki iya zuwa makarantar ba ki barshi kawai gobe Sai ki je" da sauri ta ce "A'a Yaya zan je." Ci gaba ya yi da wankinsa ba tare da ya sake cewa komai ba, sallama ta yi musu ta goya gakarta ta fice.
Da sauri ya dauraye hannayensa ya bi bayanta, girgiza kai Ummi ta yi ba tare da tace komai ba, tasan dama bazai iya barin ta tafi ba sai yaji damuwarta, idan ba haka kuwa a cikin damuwar zai wuni.
Kasancewar ya hada da sassarfa, ita kuma a sanyaye take tafiya yasa ya cimmata a zaure, jin k'arar taku ya sakata saurin juyowa ganin shi yasa ta shagwa6e fuska, a gabanta ya tsaya ya kafeta da ido sannan ya jeho mata tambayar "Meke damunki?" Take ruwan hawaye ya cika mata mata kaurin ido, "shiii!!!." Ya yi mata tare da daura yatsa a lips dinsa ya ce "Kar ki kuskura ki zubar da hawayen nan." Kokarin shanye hawayen ta shiga yi don cika umarnin shi, amma ina sai da su ka zubo.
Ganin haka hankalinsa, ya k'ara tashi, riko hannayenta yayi ya ce "Kin samu wanda zaki sanarwa damuwarki wanda ya fini a duniya ko?" Da sauri ta girgiza kai, ya ce "Oya tell me meke damunki." Cikin shessheka ta ce "Yaya Joy ce." Wani irin yankewa gabanshi ya yi ya fad'i, "Joyyy?" Ya maimaita sunan cikin sigar tambaya, gyada mai kai ta sake yi, cikin tashin hankalin da yake kokarin boyewa ya ce "What happend to her?" "Bata da lafiya ne." Ba karamin jarumta ya yi da bai kai hannu ya dafe heart dinsa ba saboda wani irin fad'uwa da ya yi, cikin wani irin voice da saida Fatima ta d'ago da sauri ta kalle shi ya ce "Mekedamunta." Jim! Fatima ta yi zuciyarta ne ya so shiga rudani, kasancewar ta mai azabar wayo yasa ta yi gaggawar boye yanayinta ta ce "Ji ya ne school ta dinga yin wani abu haka kamar ta sums numfashinta ya dinga sizing idanunta ya juya har saida a ka bata bed rest, kafin Mom d'in ta tazo ta dauketa su ka wuce gida, ni yanzu bansan halin da take ciki ba tun jiya." A sanyaye ya ce "Addu'a zaki ta ya ta da shi na kuka ba Fatima, ki yi mata addu'a Allah ya bata lafiya." Ta gyada kai alamar to, ya ce "Share hawayenki." Babu musu ta share, naira dari ya ciro a aljihunsa ya cika mata tare da cewa; Maza ki wuce kar ki yi latti." Amsa ta yi da hannu biyu ta ce "Nagode Yayana."
Tafiya take tana tariyo abin da ya faru yanzu cike da tarin mamaki, wani irin rauni hadi da damuwa ta hanga karara a tattare da shi, irin wanda ba kasaifai a ka fiye gani a tattare da shi na sai a kan abu mai mahimmanci a gare shi.
Bayan tafiyar Fatima k'asa komawa ya yi yaci gaba da wankinsa, gaba daya jikinsa ya yi san yi kalau, gabansa kuwa har lokacin bai dena faduwa ba, dakinsa ya shigeta ya lalubi kafifarsa ya kwanta a hankali ya lumshe idanunsa da suka canja launi sabida damuwa.
Ya dad'e a haka, ya rasa mai ke masa dad'i a lokacin ya rasa ina zai tsoma zuciyarsa ya ji san yi, tambayar da yake jehowa kansa shine "Meya sameta? Meya faru da ita? Meke damunta." Abinda ya yi ta maimaitawa a ran shi kenan, har bai san iya adadalin lokacin daya 6ata ba, kiran wayar shi ne ya dawo da shi hayyacinsa, Aliyu shine sunan daya bayyana akan fuskar wayar, a matukar sanyaye ya d'aga wayar, magana suka yi na mintuna uku zuwa hudu kafin ya sauke wayar, message ne ya shigo wayar, budewa ya yi, My Meerah ita ce ta yi masa sak'on sai da ya saki murmushi kafin ya bude sakon, kamar kullum sakon Barka da safiya ne da fatan ya ta shi lafiya hadi da zafafan kalaman soyayya, ya kan yi mamakin a ina ta koyi irin wad'an nan kalaman, Sam! Bata jin kunyar fad'a masa kalaman soyayya, ajiyar zuciya ya sauke ko babu komai suna burge shi kuma suna saka shi nishadi a duk lokacin da yake karantawa.
Kwanciya ya ci gaba da yi sai da Ummi ta gaji ta biyo shi d'akin sannan ya samu damar mikewa ya je ya karkare wankin ya yi wanka ya shirya ya tafi school inda daga nan zai zarce wajen kasuwancinsa.
**********
Da sauri Fatima ta karasa sit d'in su, dalilin hango Joy da ta yi zaune, zama ta yi ta shiga tatta6a goshinta zuwa wuyanya at d same time ta na tambayar ta na cewa; Friend ya jikin ki? Meya same ki jiya. Ina ke yi miki ciwo?" Rike hannun Fatima ta yi tana murmushi ta ce "I'm fine Teetee ki bari haka mana." Rau-rau da ido Fatima ta yi ta ce "Hankalina ya ta shi sosai jiya, ban yi zaton zaki zo school yau ba." Dan dariya ta yi ta ce "Matsoraciya naji sauki tun jiya." Daga haka bata sake bata dama sun yi magana akan abinda ya faru jiya ba sai ta canza akalar hirar da gaya mata cewa cikin Wannan month d'in Papanta zai dawo kuma sun dai-daita yanzu ya kula da ita kamar yadda yake yi da, da yake Fatima ta san komai game da tsakaninta da Papanta.
************
Da misalin karfe goma sha daya Maman Amira ta shirya ta shiga wajen Ummi, tun jiya a d'okance take da tazo ta labarta mata abin farincikin dake shirin wanzuwa a tsakanin su.
Gyara zama Maman Amira ta yi bayan sun gama gaisawa da Ummi tare da tambayar lafiyar iyalai harma da d'an ta6a hira, tace "Wai nikam Ummin Fatima ko kin hangi abin da na hango?" Cike da rashin fahimta Ummi tace "Name kenan Maman Amira?" "A game da yaran nan Al'ameen da Amira, sai nake ganin kamar a kwai wata alak'a a tsakanin su." Dariya Ummi ta yi , tace "Maman Amira na dad'e da fahimtar hakan, sai dai rashin tabbaci yasa na bar maganar a zuciyata, don su y'ay'an yau ba'ayi musu katsalandan a irin wannan lamarin, nasan dai komai dad'ewa idan zargina gaskiya ne zasu bayyana kansu, to ashe kema kin kula." Mama da fara'ar fuskarta ta kara fad'ad'a tace "Hmmm na kula Ummi lamarin yaran zamani sai a barsu." Ummi tace "In dai haka be sai muce Alhmdllh! Don wannan abin farin ciki ne." "Kwarai Ummi Fatima zan iya cewa nafi kowa farin ciki da hakan." "A'a fa Maman Aysha, na fiki farin ciki domin kuwa amira diya ce yar albarka duk wacce ta sameta matsayin rusuka ta yi dace." Mama ta amsata da shima "Aminullahi haka." Sun dad'e suna raha kamar na masu shirin zama surukai ba kafin Maman Amira ta yi sallama da Ummi ta tafi............
Oum ummeetarh
09116099486
[12/29, 2:48 PM] AyshaNalado: ππ *JOY* ππ
~FARHAT~
*PAGE 38*
Mikiya Writer's Association.
*NOTE*
Jiya na yi mistake wajen saka number, instead of 37 na sake maimaita 36, so yanzu zamu je 38 da fatan kun fahimtaπ
A kwana a tashi ba wuya, musamman a wannan zamanin da muke ciki ta karshen duniya yadda lokaci ke gudu kawai ya ishi bawa tsoron Allah. Tsakanin Al'ameen da Amira komai ya k'ara daidaita soyayya suke gudanarwa mai tsabta, kyautatawa tare da kulawa had'i da girmamawa sune manyan makaman da Amira ta yi amfani da shi wajen kafa kanta a zuciyar Al'ameen, bugu da k'ari yadda take nunawa Ummi da Fatima tsantsar soyayya da kulawa ya k'ara mata kima a idanunsa, wani babban matsayi na musamman ya ware mata a zuciyarsa, da fari ya k'arbi, soyayyar ta ne saboda Fatima sai kuma tausayinta da yake ji, sai dai da tafiya tayi fatiya rashe ya juye da mujiya, don a halin yanzu idan ya ce baya sonta to tabbas ya yi babban karya.
Ya zuwa yanzu babu wanda ya kamata yasan da maganar soyayyar su da ya rage bai sani ba, kama daga dangi, makota, yβan uwa, da abokan arziki, tuni kawunan Amira suka fara maganar cewa Al'ameen ya turo magabatansa idan da gaske yake, lamarin da ya yi masifar d'aga masa hankali, bashi da kud'in aure yanzu bai ajiye ba bai baiwa wani ajiya ba, hasalima d'akin da zai sakata kango ne bai kai ga k'ark'are ginawa ba.
Cikin kwana biyu kacal da samun wannan sak'on duk ya gigice ya shiga damuwa, tabbas yana buk'atar mace a rayuwarsa, musamman a halin yanzu da ya kai gargarar da tablet d'in da yake sha sam! ya daina yi masa aiki, ko da kuwa zai shanye sachet biyu ne a take, k'arfi da ya ji ya koyi, istimna'i, (Biyawa kai bukata) wanda a duk lokacin da hakan ya kasance yakan kwana ne yana kuka tare da neman gafarar Ubangijinsa, sarai ya san abinda yake aikatawa sa6o ne babba haramun ne , kuma cuta ne ga lafiyarsa, sai dai shi hakan ya fiye masa a kan ya aikata zina, yana kyamar zina, haka yana tsananin tsoron aikatawa domin ya dad'e da sanin bashi ne, idan kaci sai ka biya, shiyasa yakan yi taka tsantsan wajen ke6ewarsa da Amira, saboda kasancewar ta ma'abociya son gayu da kamshi, a cikin yan kwanakin nan, hirasu ta waya ya fiye masa alkahiri bisa ga ace sun ke6e, domin a duk sanda hakan ta kansance ya kan shiga wahala da garari.
Misalin karfe biyu na sulisin dare, zaune yake a bakin kafifarsa, ya rafka taguma da duka hannayensa biyu, idanunsa ya yi jajur, hankalinsa a tashe nadama da kaico kwance k'arara akan fuskarsa,ya tabbata idan mutuwa ta riskesa a wannan halin la shakka zai gamu da fishi da azabar Allah, take wani irin tsoron Allah ya dirar masa, zuciyarsa ce ta karye, take hawaye ya shiga kwaranya daga idanunsa, ya dad'e yana kuka, banda "Astagfirullah Allah na tuba Allah ka yafe mini." Babu abinda yake maimatawa a zuciyarsa, ganin zaman da yake yi da najasa a jikinsa bashi da amfani yasa ya tsagaita da kyar, ya mik'e yana layi tamkar wanda ya yi tatul, daga shi sai gajeran wando a jikinsa, sif ya bude ya dauki, wani wandon wankakke, ya kuma dauki babbar butarsa dake ajiye a gefe cike da ruwa ya fito, kamar yadda ya saba kullum cikin sand'a da taka tsantsan ya nufi toilet.
Cikin takaitaccen lokaci ya tsarkake jikinsa ya fito sanye da wankakken wandonsa yayinda ya riko daya wandon da hannu hagu cike da kyamkyami, gabansa ne ya yi wani irin yankewa ya fad'i lokacin da idanunsa ya hadu dana Ummi da ke rike da buta wanda ta gama zuba ma ruwa a ciki yanzu yanzu, da sauri ya yi kasa da kansa gabansa na ci gaba da wani irin dokawa, take ya ji wani irin sanyi na kada shi, da yana da hali a lokacin da babu abin da zai hana yace kasa ta bud'e ya shige tsabar kunya.
Kur! Ta kure shi da kallo zuciyar ta na tsinkewa, ba yaune karo na farko da ta ta6a kamashi yana wanka ba musamman ma a cikin yan kwanakin nan da abin a shi ke neman shallake tunaninta, sai dai basu ta6a yin gaba da gaba ba sai yau, ita kanta bata san yana tailet d'in ba da batta yarda ta fito alwalan ba, ta bari har sai ya gama ya shige d'aki.
Yi tayi kamar bata gane komai ba, ta ce "A' a Amintacce hala kaima zafin nan ya dame ka, da sauri ya ce "E wallahi Ummi, na kasa barci sai da na fito na watsa ruwan sanyi." Tana nufar toilet d'in tace "Hmmm! Allah dai ya saukaka mana." Daga haka ta shige toilet, da sauri ya bar tsakar gidan.
Ta dad'e a kan darduma tana kai kukanta gurin Allah tana hawaye, tun jiya da maganar cewa Al'ameen ya turo magabatansa ya risketa take cikin matsanancin tashin hankali, shin wa zai wakilci lamarin auren nan, shin wa zata nuna musu a matsayin dangin mahaifinsu, tabbas lokaci yayi da zata waiwayi wadancen azzaluman Ahlin, lamarin Al'ameen ya fara bata tsoro ita kanta zata so ya kasance da mace a kusa, domin dai ta riga ta gama fahimtar shi din mai tsananin bukata ne.
Da safiya kasa hada ido ya yi da ita, duk da yadda ta yi iya kokarinta wajen ganin ta nuna mishi bata fahimci komai, shi yasan ta fahimta d'in domin dai ita ba yarinya bace duk da babu wanda zai ganta ya ce ita ta haife shi Indai ba wanda ya sani ba, haka jiki a sanyaye ya shirya ya fice daga gidan.
School ya nufa don yana da lecture, karfe goma ya fito daga school, jikinsa duk a mace kansa ne ke masa matsanin ciwo kamar zai rabe biyu baya jin yana da kuzarin iya fita aiki yau, hakan yasa ya kira Aliyu ya ya ji ko yana gida, samun tabbacin yana gida yasa kai tsaye ya tari dan acaba ya nufi gidan su Aliyu.
Ganin shi a sanyaye yasa Aliyu tarar shi da cewa; Lafiya Ameen mekefaruwa." Zama ya yi a kan kujera 2 sita dake d'akin Aliyu ya dafe kai, yana sauke numfashi.
Ajiyar zuciya Aliyu ya sauke, ya zauna kusa da shi, sun fi minti biyar a haka, Al'ameen bai ce komai ba shima Aliyu bai matsanta mashi ba, sai da ya gaji don kan shi ya dago idanun da suka kara rinewa ya kalli Aliyu. Ya ce "Aliyu ya zan yi? Nutsuwa Ali ya kara yi ya maida dukkan hankalinsa garesa, ya ci gaba da cewa; "Iyayen Amira sunce na turo, Aliyu bani da halin aure ban ajiye ba ban ba wani ajiya, kuma ina bukatar aure Aliyu ya zan yi? Murmushi mai sauti Aliyu ya yi a zuciyarsa ya ce anzo wajen.
Wani irin kallo Al'ameen ya shiga bin Aliyu da shi ganin yana murmushin, ganin irin kallon da yake masa yasa ya dafa kafadar shi, ya ce " Abokina a kwai mafita." Tamkar wani soko ya ke bin Aliyu da kallo kafin ya ce "Akwai mafita kace Aboki?" Gyada kai Aliyu ya yi ya ce "kwarai kuwa a kwai mafita."..............
Oum ummeetarh
09116099486
[12/29, 2:48 PM] AyshaNalado: ππ *JOY* ππ
~FARHAT~
*PAGE 39*
Mikiya Writer's Association.
"Menene mafitar?" Al'ameen ya tambaya idanunsa cikin na Aliyu. Nannauyar ajiyar zuciya Aliyu ya sauke, cike da kwarin gwiwa ya ce "Dr Abdul Hafiz ." Wani irin k'ank'ance ido Al'ameen ya yi, a hankali ya maimaita sunan da sigar tambaya "Dr Abdul Hafiz S Alto?" "Kwarai shi nake nufi." Aliyu ya fad'a shima yana kafe Al'ameen da ido.
Bacin rai ne ya bayyana k'arara a fuskarsa take, a kausashe ya ce "Menene had'in ka da shi?" Dakewa Aliyu ya yi daman yasan hakan zai iya kasancewa, ba tare da shayin komai ba ya ce "Zumunci." Gyada kai Al'ameen ya yi, ya ce "Zumunci ko? Very gud." Daga haka ya mik'e bai kalli side d'in da Aliyu yake ba ya fice daga d'akin jiri na kwasarsa.
Murmushi Aliyu ya saki a yayin da ya raka bayan shi, da kallo, taurin kan Al'ameen ya wuce tunanin mai tunani, idan ya riga ya kau da kai a kan mutum da wuya ya k'ara waiwayarsa ko shi waye, sai dai ya lashi takobi zai yi iya 'kokarinsa wajen ganin komai ya daidaita.
*********
*JOY*
Tun daga ranar da Fatima ta sanar da ita batun soyayyar Yaya Ameen da Amira, bata sake yarda wani hira makamancin wannan ya sake shiga tsananinsu ba domin ta san baza ta iya jurar ji ba, zuciyar ta baza ta iya d'auka ba. Haka suka ci gaba da harkokinsu ba tare da ta bari Fatima ta fahimci komai game da abin da ke lullu6e a zuciyarta ba, ta bi ta toshe duk hanyar da Fatima zata fahimci a kwai wani abu a zuciyarta game da Ameen, tun da ta fahimci kamar Fatin na zargin hakan, sai dai duk wani walwala da kuzarinta ya ragu, sam! ta daina tambayar Fatima game da Al'ameen kamar yadda take yi ada, idan ma Fatima ta dauko hirar shi, da dabara za ta dakatar da ita ta hanyar sako wani hirar dabam ta shashantar da wancen hakan ya saka zuciyar Fatima a wa si wasi a kan zarginta, har ta samu kwanciyar hankali, don ta yi imanin cewa; Joy baza ta ta6a boye mata wani sirri na rayuwarta ba, sai ta watsar da zargin da ta ke yi suka ci gaba da sabgarsu na yau da kullum babu wani sauyi.
Joy kuwa kwantan 6auna ne kawai ta yi, don zuciyarta cike ta ke taf da kaunar Al'ameen, ita kad'ai ta san irin famar da take da zuciyarta, duk daren duniya sai ta sha kuka ta gode Allah, musamman da ta fahimci yadda ya ke kaunar Amira da kuma yadda itama Amiran ta mace a kaunar shi, ganin haka yasa ta gama sadak'arwa ta rasa Al'ameen domin dai da idanunta take ganin zallar soyayyar Amira a tattare da shi, hakan yasa take jin wani irin mahaukacin kishi da haushinta na babu gaira babu sabar, har yau ta kasa bata fuska su dinga ko da gaisuwar mutunci ne, ba yadda bata yi don ta tausasa zuciyarta a kan hakan ba abin ya gagara, Fatima da ke tsakanin su, sai ta bar hakan a kan cewa jininsu ne bai hadu ba.
A duk sanda ta zo gidan ta yi rashin sa'a da katarin ganinsu a tare, ranar takan wuni ta kwana da mugun ciwon kai, bata ta6a zaton duk wadannan abubuwan da take ji shafar mai ba ne, sai yau da suke k'ule a uwar d'akin Ummi, Fatima na sanar da ita cewa iyayen Anty Amira sun ce Yaya Ameen ya turo magabatansa a zo ayi zancen aurensu. Kamar saukar gudumar wuta haka zancen ya daki zuciyarta, da sauri ta kai hannu ta dafe saitin zuciyarta da ya yi wani irin dokawa da mugun k'arfi, a dan gigice Fatima ta kalleta tare da cewa "Ar u ok." "yes I'm ok." Ta fad'a da sauri tana ya mutsa fuska jin gefen kanta ya fara sara mata, sannu Fatima ta shiga jero mata, ta gyada kai tare da mik'ewa tsaye, Fatima ta kalleta da mamaki ta ce "Ya dai friend ina zaki je ?." "Teetee I want 2 leave now." Ta fad'a cike da wani irin rauni a muryarta, mik'ewa Fatima ta yi ta riko hannayenta tana kallon cikin idanunta, cikin k'asa-k'asa da murya ta ce "Ki gaya min dan Allah, menene?" Tsura mata idanu ta yi, na yan sakanni take hawaye ya ciko a kwaurin idanunta, can kuma kamar an tsikareta ta fisge hannayenta da sauri ta fice daga d'akin tana sharar kwallah.
Wani irin tafiya take yi tana layi kamar yar caburos, duk in da ta samu jefa kafarta kawai take yi ba tare sa kula ba, gaba daya idanunta sun kulle bata ko ganin gabanta, tuni hawaye ya gama wanke mata fuska cikin kankanin lokaci.
Babu zato babu tsammani ta ji an ca6e hannunta, yana yin sauyin bugun zuciyarta da kuma kamshin turaren shi ya tabbatar mata da cewa shi ne, hannun shi da ke rike da nata ta kalla, kafin a hankali ta d'ago kai ta sauke idanunta a fuskar shi.
Wani irin kallo yake binta da shi, mai dauke da ma'anoni daban-dabam, d'ago idanun da ta yi, ya ba shi damar sauke kwayoyin idanunsa a cikin nata, wani irin kallo suke bin juna da shi mai kama da kallon kuda, hawaye ne ke zurara a kumatunta, hawayen zallar so da kauna, yayinda shi kuma na shi idanun suka kara rinewa jajur, zakarar wuyar shi na motsawa yake alamar yana hadiyar wani abu wanda shi kad'ai yasan ko menene, dawowarsa kenan daga wajen Aliyu zai shiga gida ya ci karo da ita, ganin yana yin da take ciki yasa ya kasa bari ta wuce, domin da gani ba lafiya ba.
Kamar an wuntsilota daga sama ta bayyana a gabansu, wani irin abu ta ke hanga kwance a idanuwansu su duka biyun wanda bata fatan ace gaskiya ne, shin ina ma mafarki take yi' cike da matsanancin tashin hankali, cikin rawar murya ta ce "Yaya Ameen." Sautin muryarta ya daki kunnuwansu baki d'aya, sai dai ko da wasa Al'ameen bai dauke idanusa daga fuskar Joy ba kuma bai saki hannayenta ba.
Yayinda ita kuma ta d'ago manyan jik'akk'un idanunta ta sauke su a kan fuskar Amira dake tsaye tana binsu da kallo hankali tashe, suna had'a idanu ta ji wani irin k'ululun abu ya tokare mata makoshi, wani irin kuka ne ya taho mata daga can kasar zuciyar, da mugun k'arfi ta fisge hannunta daga rik'on da ya mata ta juya da gudu ta bar wajen.
Ba shi da kuzarin tsayar da ita domin jin damuwarta, shi kan shi cikin matsanancin damuwa yake, Sai dai ganinta cikin damuwa ya so mantar da shi ta shi damuwar.
"Yaya Ameen." Sautin muryarta a karo na biyu ya ratsa kunnuwarsa, a hankali ya dauke idanunsa daga hanyar da Joy ta bi, ya sauke a fuskarta, hawaye ya gani kwance a kwaurin idanunta, tsabar wutar kishi da tashin hankali kwance karara a idanunta.
A halin da yake
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 22