wacce ta zo bakina, Baaba Hajo na amsawa da Amin.
A haka likita ta shigo ta same mu, dama already tun farkawata Baaba Hajo ta sanar mata, bayan ta gama duba ni, ta tabbatar komai normal, sai ta ja kujera ta zauna a gabana, cikin tsananin tausayi da kulawa ta shiga yi mini nasiha, tana yi tana kara ba ni hakuri da kwarin gwiwar tunkarar gobena, ta karkare da sanar mini cewa cikin jikina ya fita sakamakon tashin hankalin da na shiga da kuma faɗuwar da na yi akan cikin.
Kwatanta ma ku yanayin da na shiga da jin wannan furuci ɓata lokaci ne, domin Cak numfashina ya tsaya na hucin gadi, na dinga jin kaina kamar ina yawo a cikin gajimare, "Ki ambaci Allah Balkisa, ki ce Inna lillahi wa Inna alaihi raji'un." Kalaman Baaba Hajo suka doki kunnena, take na bi umarninta, na fara maimaitawa kamar yadda ta ce, hakan ya ɗan samar mini da nutsuwa.
Kwana biyu na kara a asibitin aka sallame, saboda matsawar da na yi, domin zuwa lokacin kwanan Yaya Hussain bakwai a bayan ƙasa.
Har na gama zamana a asibiti, ko karen gidan Mamman kura bai zo duba ni ba bare mutum, abin ya yi mini ciwo duk da nasan basa kaunata amma a tunanina ahalin da nake ciki ni abar tausayi ce ga mai cikakken imani.
karfe biyar na yamma dai-dai mai adaidaita sahu ya dire mu a kofar gidan Maman kura.
Kallon gidan ƙadai ya karyar mini da zuciya, sai lokacin na ji wani maraici ya lulluɓe ni "Shikenan Yaya Hussain ya tafi ya barni a wannan gidan ba tare da sanin ina na dosa ba, wacece ni? daga wacce duniyar na ke? Ya Allah me yasa ka fara daukar rayuwar Yaya Hussain kafin nawa, Allah ka sani shine komai nawa, Allah shine Uwata shine Ubana, Yayana, Ɗanuwana, Mijina, kuma Uban ƴaƴana na zahiri, Allah ina roƙon ka ka yi gaggawar daukar raina na bishi ya Allahhh!!!."
Na karashe zancen zucin da na ke yi hawaye na gudu a dakalin fuskata. Muryar Baaba Hajo ne ya katse mini tunani da sauri ka ɗauke hawayen da hijabina don bana bukatar ta gan su faɗa za ta yi mini.
"Ku shiga Balkisa zan shiga gidana
idan na yi sallar magriba zan shigo." Na amsa mata da to tare da kama hannu Amintacce ga goyan Fatima a bayana muka durfafi shiga gidan gabana na dakan uku uku.
Gaba ɗaya idanu suka zubo min tamkar sunga sabuwar halitta, hakan ya sa muryata rawa yayinda na ke sake rangaɗa sallama a tsakar gidan.
Ba wasu ba ne a tsakar gidan Illa Daada da iyalanta ba ki ɗaya, idanuna ya sauka cikin na shi, take daren rasuwar Yaya Hussain ya faɗo mini a rai, tabbas shine wannan mutumin da na ji yana waya cikin dare.
Tunanina ya katse lokacin da Daada ta ce "Ke kuma daga ina? gayyar arna a idi, me ya kawo ki, me ki ka zo yi, ko kina da alaƙa da Gidan Maman kura ne?."
Na yi saurin girgiza kai hawaye na bin fuskata.
A wannan yammaci Daada da iyalanta su ka yi mini korar wulaƙanci tare da kora mini kyakkyawar warning akan babu ni babu su har abada, shegiyar ƴar Hussain Fatima sun yafe mini ita halak malak dama bata da ko gadon Allura a cikin dukiyarsa, shi kuma tayin cikin suna farin ciki da zubewarsa domin basa buƙatar bara gurɓi a cikin zuri'arsu.
Ina kuka ina rokonsu su taimake su rufa mani asiri ko takaba ne na yi a ɗakin mijina amma suka ƙi, dakyar suka yi mini Alfarmar daukar wasu daga cikin kayan sakawarmu, a sannan ne na samu damar daukar makulli da takardun gidan da Al-Hussain ya mallaka mini a jajibarin ranar dazai rasu ba tare da sanin su ba.
Ummi ta sauke numfashi ta kalli Fatima Al-ameen da Aliyu da kowannen su ke sharar kwalla, itama kwallar ta dauke a idanunta, ta ce "wannan shine rabuwata da ahalin Mamman kura, yau shekara goma sha biyar cif! Basu taɓa nema na ba haka nima ban taɓa neman su ba, sai da maganar Auren nan ya tashi, na je ne da ƙoƙon barata ina neman su tsayawa Amintacce akan maganar aurensa, domin idan ba su ɗin ba, ba ni da wasu ban san kowa ba sai su, wannan shine abin da na sani game da rayuwata, bacin wannan ban san komai a kaina ba, sai dai ina fatan wata rana ta zo da zan tuna ko ni wacece daga wacce duniyar na ke, ina fata wata rana na tuna wacece Balkisu.........
Masha Allah wannan shine karshen littafi na ɗaya gobe za ci gaba da labarin joy Al-ameen da kuma Amira ina fatan baku manta ba
*Shin Al-ameen zai auri Amira❓
Menene asalin Ummi❓
Wacece Joy❓
Me Mom ɗin Joy ke ƙullawa❓
Yaya batun soyayyar da Joy ke yiwa Al-ameen❓
Mene alakar Dr Abdul Hafiz da Al-ameen da yasa ya damu da shi ya ke son shiga rayuwarsa.❓
Ya batun ciwon Al-ameen zai samu lafiya ko A'a❓
Ya labarin dattijon da ke kwance a asibiti❓*
Shin wanene wannan mutumin da Ummi ta ji yana waya cikin dare❓
Amsoshin waɗan nan tambayoyin na cikin littafin Joy kashi na biyu wanda zamu fara posting a gobe idan Allah ya ara mana rai da lafiya.
Alhamdulillah🙏
09116099486
WhatsApp Only
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 22 Chapter of 22