abinci na yake."
Ameera tai dariya tace "irin cin abincin Yaya kenan, hmm kunyi anko."
Idanunta ta dago kadan ta kalli Sagir wanda yake ta juya abincin.
Shiru ne ya biyo bayan falon sai dan karar cokula da suke tashi, Ummy ta rasa me yasa gabanta ke ta faduwa.
Mikewa tai dan abincin da kyar take danci, ta kalli Ameera tace "ki dauko mata magungunanta tasha." Ta karasa maganar tana wucewa d'aki.
Ameera ta mike tai daki, ya rage daga shi sai ita agun, Sagir ya kalleta yace "Ya jikin naki?"
Bata kalleshi ba tace "na warke."
Shiru suka karayi yace "Jalilah....."
Ajiye cokalin tai da sauri sannan ta mike, dan batasan jin kalma daya daga gareshi, ina zata?
Nufar dakin Ameera kawai tai, Ameera na fitowa ta kalleta tace "ina zaki?"
Tace " hmm bandaki zan shiga."
Ameera ta mika mata maganin, amsa tai ta shiga ciki.
Tunda ta mike yake kallanta harta shiga, idanunsa ya rufe yana neman tsari daga sharrin zuciya, shikam ya san ya hakura sai dai yana san ya warware misunderstanding dake tsakaninsu.
*********
Acan Abuja kuwa Abba ne ya kalli abokin nasa yace "wai kai da mukazo yin signing contract me ya kawomu nan?"
Ya fada yana kallan wani gidan da abokin nasa yai parking.
Abokin nasa mai suna Hafiz ya kalleshi yace " abu zan amsa gun wani, yanzun nan zan fito.
Fitowa yai daga motar yabar Taura a ciki, tsaki taura yai shi ya kosa su gama ya koma masaukinsa dan ya manta da wayarsa garin sauri.
Sam bai kula ba sai jiyai ana kwankwasa glass din motarsa.
Zuge glass din yai tare da kallan windown, wani irin kamshi ne ya shiga ratsa cikin motar, kallanta yai yarinyace wacce batafi shekara 28 ba, fara ce wanda har farin nata ma yasa zakasan ba cikakiyar bahaushiya bace, kana ganinta zaka san irin matan nan ne shuwa.
Tasha kwalliya irin na zamani, kamshin da takeyi kuwa ba'a magana.
Ya rasa dalilin dayasa ya kasa dauke idanunsa daga kanta.
Murmushi tamai sannan tace "Yaya yace ka shigo kaci abinci."
Yace "Yaya?"
Tace "Eh ai mijin yayatane."
Yace "oh gidanshi ne kenan?"
Tace "eh."
Gani yai tasa hannu ta bude lock din cikin motar sannan ta bude kofar.
Kallanta yai, kayan da ke jikinta irin material ne mai kyalkyali, mace ce mai suna mace dan shape din ta ma abin kallo ne.
Kai ya girgiza da sauri dan shikam mace baiga kyan da zaisa ta rinjaye shi ba.
Kauda kansa yai daga kanta, matsowa tai saitin kunnensa tace "Please."
Baisan sanda ya mike ba yace "muje."
Gaba tai tana wani murmushi, dan dama wannan shirin sunfi wata biyar sunayinshi, tundaga sanda taganshi a Abuja yazo shida matarsa wani taro, kayan jikin matar kadai ta kalla tasan kudi ya zauna musu, data tambayi mijin yayarta shine ta karajin irin kudin da yake dashi.
Tun daga lokacin suka fara shirin jawoshi inda suke.
Haryasa kafa zai shiga sai ya tsaya, juyowa yai ya kalleta yace "kicemai yai hakuri inada abinyi."
Ya fada tare da juyowa tana mai magana bai tanka mata ba.
Motarsa ya shiga ya jata da sauri.
Ita kuwa Zaliha tana shiga cikin gida ta hade fuska, yayarta ta kalleta tace "ya ya?"
Kai ta girgiza mata kawai sannan ta wuce daki cikin takaici.
Yayarta ce ta kalli mijinta tace "Hafiz ya haka?"
Yace " Taura namiji ne da bai kallan matan waje kuna tunanin daga haduwa daya zai amince?"
Harararsa tai sannan tai gun kanwarta.
***********
Abba na koma wa dakinsa ya dau wayarsa, kiran Ummy ya sau goma, sannan yaga kiran Sagir sau biya, sai sauran wanda abune na aikinsa.
Yana shirin kiran Ummy wayar Hafiz ta shigo, dagawa yai cikin takaici yace "Hafiz bakada hankali ne?"
Hafiz yace "kayi hakuri dan Allah wlh dana shigo ciki ne matata ta dage akan sai na kiraka kaci abinci shiyasa nace Zaliha ta kiraka."
Yace "meyasa to baka fadamin gidanka bane?"
Yace "banasan ne kaji ba dadi, haba Taura dan Allah kayi hakuri."
Kashe wayar yai sannan yai cilli da ita kan gado, ya rasa me yasa yarinyar ta tsayamai a ransa......
***********
A can gidansu Hassan Kuwa jalila tana zaune a dakinsu Ameera, har wajen karfe 10, Ameera ta kalleta tace "ki tashi kije ki kwanta kafin Ummy tai magana."
Jalila tai ajiyar zuciya sannan tace "bazan iya kwana anan ba ko?"
Ameera da sauri tace "a ina? Ba ruwana wlh."
Jalila ta kara yin ajiyar zuciya sannan ta mike, ta fito.
Haka ta haura sama jiki a sanyaye, hannu tasa a hankali ta murda kofar dakin, yana kwance akan gado yana karatu.
Kamar munafuka haka ta shiga cikin dakin, ko kallanta baiyi ba ya cigaba da karatunsa.
Jalila tana tsaye har kusan minti ashirin, jitai kafafunta sun gaji nan ta matso kusa da gadon kadan, ta karasa kan kujerar dake dakin ta zauna tana dan matsar da littatafan dake jere agun.
Jitai ance "karki kuskura ki hargitsamin abu, komai da kika gani agun a jere yake."
Baki tadan tabe sannan ta daina taba litattafan, dama haushi yakeji dalilinta duk an canzamai tsarin dakinsa.
Shiru ne ya kara ratsa dakin sai sanyin Ac dake kara sanyaya dakin.
Bacci ne ya fara kamata dan har 11 ta wuce, tana zaune tana tunanin Goggonta.
Ganin bashida niyyar fadamata inda zata kwanta yasa ta mike ta dau pillow din dake gefensa sannan tazo tana san daukan bargon dake kan gadon.
Kafafunsa ne akai ta kalleshi tace "zan dan dauka."
Kallanta yai yace "banaji naki ne."
Tace "a ina zan kwanta?"
Alama ya mata da kasa da hannunsa ba tare da ya dauke kafarsa ba.
Jalila haushi ya kamata, harararsa tai cikin takaici, sannan ta sa pillow ta kwanta a kasa, ai bayau ta saba kwanan kasa ba, dama saboda sanyi takesan luluba.
Shikuwa bai kalleta ba sai dai ya tabbatar ta harareshi dan ya kula idanunta sun kware da harara sannan bakinta ya kware da murguda a bayan fage.
Kwanciya tai ta lulube kafarta da zani, bacci ne yai gaba da ita.......
Kallanta yai sannan shima ya juya ya kwanta, abinda zai baka haushi bafa luluba zaiyi da bargon ba haka kawai.........
Wajen asuba ya farka, yai hamdaka da samun bacci mai kyau dayai, dan dama ba kullum abin tashi ba.
Dome light din dakin ya kunna sannan ya mike.
Alwala yai sannan ya dauko sallaya zai shimfida, kallan Jalila yai tana kwance a inda yake shimfida sallayarsa, bacci take sosai kafa yasa ya zunguri kafarta.
Kara gyara kwanciya tai, ya kara sa kafa ya dan kara zungurar kafar tata, a hankali ta bude idanunta.
Ganin namiji tai a kanta da doguwar riga fara, tsorata tai, da sauri tai baya tare da yin ihu, tace wayyo Allah......
Da sauri ya rufota ya rufe mata baki, yace meye hakan?
Sai alokacin ta tuna ashe fa wai a wani gidan take, sannan daki daya da namiji.
Shiru tai sannan ta kalleshi, shima kallanta yai sannan ya mike yace " bakiji kiran sallah ba?"
Tai shiru, dan batasan me zatace ba.
Mikewa tai ta nufi ban toilet.
********
Inna ce ta kalli Dady tace "bazaka iya ba?"
Yace "ba wai bazan iya bane sai dai banga dalilin dazaisa a dauketa daga asibitin da take ba zuwa wani ba."
Ranta a bace tace "kayi abinda na saka kawai, ko kana tunanin zan cuceta ne?"
Kallanta yai yace "ba haka nake nufi ba."
Tace " kamaida ita Premier m, sannan kasa a gyara mata bangarenta, asa mata duk wani abu da ya kamata."
Mamaki ya kamashi, a canza mata asibiti sannan a gyara mata bangarenta? Ya tabbatar wani abun take shiryawa na cigabanta ko na cigaban yarta.
Bai musa ba yace to sannan ya mike ya fita.
Shiru tai tana tunani........
#OneLuv💕
**********
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*27*
Dady na fita daga dakin ta dau waya ta kira Mumy.
Mumy na shigowa ta kalleta tace “ki shirya muje ganin daki.”
Mumy tace “ganin daki kamar ya?”
Inna tace “ au a aurar da yarki guda? Sannan babbar jika a gareni ina tunanin ya zama dole muje bayan an kaita muga muhallinta.”
Mumy tai yar dariya tace “Lalai Inna, jikarki? Ni dai a kara za’a iya cewa ‘yatace amma Inna ke ai......”
Kallanta tai fuska a d’aure tace “ me kike nufi?”
Mumy tace “Inna ai kece bangane me kike nufi ba.”
Inna ta ajiye wayarta sannan ta mike tace “ na rasa sai yaushe ne kwakwalwarki zata fara aiki yanda ya kamata.”
Mumy ta mata kallan rashin fahimta, Inna tace “nikam wacece babbar ‘yarki?”
Tace “Safeena mana.”
Inna ta kalleta cikin takaici tace “wacece babbar yarki?”
Mumy tace “ni Inna rudani kikeyi.”
Inna ta harareta sannan ta girgiza kai cikin takaici tace “ni wuce muje ki shirya mu tafi, ni in munje gidan na miki bayani.”
Mumy ta mike ta fita tana tunanin kalaman Inna, batagane wacece babbar ‘yarta ba, yo ai kowa yasan Safeena Qta fara haifa.
Hart takai matattakala uku sai ta tsaya cak tace “ba dai......?
Komawa tai da gudu saman ta bude dakin Inna, tace “Inna badai so kike ki cema mutane nice mahaifiyar Jalila ba?”
Inna bata kalleta ba sai shafa man zafin da takeyi a kafarta da takeyi, Mumy cikin mamaki ta karaso kusa da ita tace “Inna?”
Inna ta kalleta tace “ me? Kina tunanin is in possible?”
Mumy cikin tsoro tace “Inna me kike tunani? Taya zaki canzama yarinya mahaifiyarta? Bayan mahaifiyarta nanan da rai?”
Inna ta kalleta tace “ kina tunanin in Taura yasan gaskiyar al’amari akan ba yarinyarki bace zai yarda? Bakya tunanin zai ga yaudararsa mukai? In ya kwace kudin dayai investing a company dinmu fa saboda munyi betraying dinsa?”
Mumy tace “to ai bai fito filli yace ‘yata yakeso ba, shidai babbar yarinyar gidan nan yace, sannan in ta sanar dasu fa kafin kije? Ni Inna wannan karan ban amince da abinda kika tsara ba.”
Inna ta kalleta tace “shiyasa akoda yaushe nake ganin hankalinki da wayan ki na banza ne, ke wai haryanzu kina tunanin Abakar sanki yake?”
Tace “Inna zaki fara ko?”
Tufe maganin zafin tai tace “ kiyi gaggawar tashi daga baccin da kikeyi, kada ki kuskura kiyi relying akan kowa inba ni ba, sannan kada kiyi trusting din kowa inba ni ba.”
Mumy ta kalleta sannan ta mike kawai batace komai ba ta mike ta fito, itakam duk abinda Inna tace mata tana bi sai dai wannan karan hankalinta bai kwanta da hakan ba.
**********
Jalila kam da sutai sallar asuba falonsu na sama ta fito ta kwanta dan taga alamar baida niyyar mikewa daga gun.
Wajen karfe tara ta farka, jitai jikinta ya ware, saukowa tai daga kan kujerar data ke kwance sannan ta karaso jikin kofar, hannu tasa a hankali ta murda kofar, kanta ta zuro a hankali tana lekawa, bata ganshi akan gadon ba hakan yasa tai tunanin baya dakin, tura kofar tai shiga, tana shiga ta hangoshi a kwance akan sallaya inda yai sallah, baki tadan tabe tace “kamar gaske.”
Wucewa tai zata shiga toilet, gani tai ya fara wani abu harta je bakin toilet din, juyowa tai da sauri ta kalleshi, gani tai yana zufa sannan sai wani murkusus yake, idanunsa a rufe gam.
Kallansa ta sakeyi tace “mafarki yake?”
Kusa dashi taje tadan sa hannu tadan tabashi, hannunta ya rike da karfe yana wani irin numfashi, sankamewa taga yanayi, tsoro ne ya fara kamata, ga hannunta ya kankame da karfi wanda zafinshi ya isheta.
Cikin tsananin tsoro ta fara cewa “Yaya!” Dan abinda taji suna cemai kenan, Yaya! Yaya! A tsorace take kiran sunan nasa.
Ganin zufa tana keto mai ta ko ina ga sai kara kamewa yakeyi, yanzu kam hannunta ya saki yasa hannunsa a wuyansa yana kokarin jawo numfashinsa da yake mai wahalar shaka.
Jikinta ne ya fara rawa, ganin yanda yake sa hannu a wuyansa yasa tai saurin sa hannu ta rike nasa da karfi, a tsorace take cewa “Yaya! Yaya! Menene?”
Ganin abin karuwa yake yasa ta fara tofamai kulhuwallahu, falaqi da nasi, dan bata iya addo’oi ba.
Hannunta data rike nashi ya jawo hakan yasa ta fada jikinsa, da sauri ta mike, sannan ta shiga kiransa tana tabashi.
Ahankali yai wani dogon numfashi, sannan ya bude idanunsa wanda sukai jaa.
Idanunsa ne suka sauka a kanta tayi tsuru tsuru kamar kace mata kyaa ta ruga a guje....
Kallanta yai cikin rashin jin dadi, dan shikam yasan abinda yake tsoro kenan, bayasan wani ya ganshi cikin wannan halin.
Jalila kam tana nan a zaune kamar abu mara motsi har ya mike zaune, ganin yanda ta kame yasa ya mike tsaye ya zaune a bakin gado sannan yasa hannu ya shafi fuskarsa cikin takaici.
Jalila a hankali ta juyo ta kalleshi bakinta na rawa tace “ hmm ka ka......”
Kallanta yai fuskarsa a hade ga idanunsa sunyi jaa, wani irin tsoronsa ne ya kamata, gabanta ya shiga faduwa.
Idanunsa na kanta yace “ ka me?”
Kai ta girgiza da sauri tace “hm ba komai.”
Ta juya da sauri gaban wardrobe taje ta bude ta rasama me zatayi a kai sannan ta matso gaban madubi shima ta tsaya, sannan ta bude bandaki da sauri ta shiga ciki.
Duk abinda takeyi idanunsa na kanta, idanunsa ya sake runstewa cikin takaici, gani nai ya bude idanunsa ya mike da sauri ya dau waya da key din motarsa.
Yana kokarin fita itakuma tana fitowa, kallan juna sukai da sauri ya dauke kansa sannan yai waje.
Kallan kofar daya rufo tai sannan ta zauna a bakin gado tana maida numfashi kai kace gudu tai, me ke nan? Me ya faru dazu? Aljanu ne dashi? Kansa kalau kuwa? Badai wannan bace matsalar da Ummy tai magana?
Ta dade a zaune sannan ta mike tai wanka, haka ta sa kaya jiki a sanyeye sam hankalinta ya kasa kwanciya.
Ameera ce ta kwankwasa kofa, Jalila ta bude mata.
Tiren abinci ta miko mata tace “ga abincin yaya, ke kuma ki sako muje kasa.”
Jalila ta kalleta cikin sanyin jiki tace “Bayanan, sannan ni banajin yunwa.”
Ameera ta kalleta tace “yaza’ai kice bakyajin yunwa?”
Jalila ta kalleta sannan ta koma ciki, gaba daya itakam abin duniya ya dameta, Ameera ta ajiye tiren sannan ta kalleta tace “ga na yaya nan sai kici anan, shi nasan ba yanzu zai dawo ba.”
Ajiye abincin tai ta fita.
Jalila kam a zaune kawai take akan gado tama rasa ta ina zata fara tunanin abinda ke faruwa.
Ganin ta rasa amsa kawai ta dauko hijab dinta ta sauko, su Ummy na cin abinci ta sauko kasa, kusa da Ummy taje ta gaisheta sannan ta gaida Sagir, Ummy tace “zauna muci abinci.”
Jalila wacce ta fito dan sanar da ita tana san zuwa gun Goggo tai shiru tana wasa a hannunta.
Ummy ta kalleta tace “Ya akai Jalila? Wani abin kikesan fadamin?”
Dagowa tai ta kalli Uncle sannan ta kalli Ummy.
Sagir ya kalli Ummy yace “ko jikin ne?
Ummy ta kalleta tace “Jikin ne?”
Jalila da sauri tace “bashi bane.”
Ummy tace “to menene?”
Jalila ta kalleta sannan ta sake yin shiru, Sagir ya yace “ asibitin zaki koma?”
Kallansa tai sannan ta kalli Ummy, Ummy tace “wai haka?”
Jalila ta daga kai, Ummy tai murmushi tace “menene to da kika kasa fada? Ki zauna kici abinci sai kuje da Sagir.”
Kallan Sagir tai da sauri, sai dai batace komai ba.
Ummy tace “in bakya san ci anan ki hau sama kici kafin ya gama.”
Jalila tace “nagode Ummy.” Sannan tajuya tai ta hau sama.
Zama tai a falon tai shiru Hassan take hangowa abinda yai dazu.
Kanta ta kwantar akan kujera, Muryar Ameera taji tana kiranta, nan ta mike ta sauko ko dakin bata koma ba.
Da zata fita Ummy ta kirata, Jalila ta juya taje gunta, Ummy ta miko mata leda sannan tace ki gaisheta, dan gwarama da kika tuna min yau kije, dan Abban Ameera inya dawo ba lalai ya barki ki fita ba, bayasan fita.”
Jalila ta amshi ledar tana godiya.
A bakin mota ta hangoshi a tsaye, nan ta karasa kusa dashi, gani tai ya bude mata bayan motar sannan ya juya ya shiga gun zaman driver tare da kunna motar.
Rufe kofar motar tai yaja suka fara tafiya, Motar tayi shiru sai karar redio dake tashi a cikin motar.
Sunyi tafiya mai dan tsayi kafin can yace “Jalila.”
Idanunta na jikin window tace “naam.”
Yace “Jalila nasan na miki laifi sai dai nan gaba zaki fahimci dalili na nayin hakka sannan na tabbatar a lokacin zaki san abinda nake nufi da kalamai na.”
Kallansa tai sannan ta daure tace “ magana ta wuce, sai dai meke damun Yayan naka?”
Shiru yai kafin yace “Ni kaina ban sani ba, dukanmu yan gidan ba wanda yasan meke damunshi, shikadai yasan abinda ya faru a lokacin.”
Lokacin?
Yace “ eh lokacin da su Husain da Nazir dan kanin Abba.”
Jalila tai shiru batace komai ba, Sagir ya kalleta ta madubin gaban motar, yana tsananin san yarinyar nan haka kuma yana tsananin tausayinta sai dai duk yanda yaso da so da kaunar ta bai isa ba.....bai isa ba.”
Dagowa tai ta kalli madubin suka hada ido, kanta ta kawar sannan a hankali tace “Uncle!”
Yace “naam.”
Har zata cemai Goggo mahaifiyarta ce sai ta fasa, tace “shikenan ma.”
Yace “menene? Dan Allah ki fadamin.”
Shiru tai kafin can tace “Goggo nace a asibitin.”
Yace “nayi tunanin Goggon da kike maganar ta ne amma ya kuke?ni da nadauka ai Goggon mahaifiyarki ce.”
Zatai magana ya taka burki da karfi, juyowa yai ya kalleta yace “Jalila are u okay?”
Tace “eh menene?”
Yaran da suka tsallaka titin ya kalla yace “ yara ne wlh saura kiris su ja mana.”
Shiru tai batace komai ba, gangarawa asibitin yai, parking yai sannan yace “Jalila ki yi hakuri dan Allah.”
Kallansa tai tace “zancen hakuri da rashinsa ai ya kare, kafin ai abu ne ake neman canzashi ba bayan anyi ba.”
Ta bude motar sannan tace “nagode.”
So yake ya shiga amma bayasan ya kara bata mata rai.
Bata dade da shiga ba sai gatanan hankali a tashe tace “Uncle na rasa Goggo na.”
Sagir yace “ban gane ba?”
Kuka ta saka hankalinta a tashe take cewa sunce an mata transfer zuwa wani asibitin kuma basusan sunan asibitin.”
Yace “ban gane ba?”
Tana kuka tace “wai basu sani ba......”
********
Abba kam dakyar ya samu bacci jiya, ya rasa meyasa gaba daya tunanin yarinyar da bata fi sa’an dansa ba ya dameshi.
Ai kuwa da sassafe ya fada mota da driver dinsa suka nufo kano, ko kara bi ta contracts din baiyi ba.
Me ya sameshi? Me ke faruwa dashi?
*£**********
Mumy ce ta kalli Sultan tace “Sultan bari muje gidan Jalila, ko zakaje?”
Inna ce tai kakari wanda yake nuna mata ta daina, Mumy ta kalleshi tace “bari muje.”
Nan suka fito daga gidan suka shiga mota.
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*28*
Kasa tsayuwa tai kawai ta tsugunna agun tasa kuka, Sagir ya koma cikin asibitin ya tambayesu, yanda suka fadamai haka suka fada mai, fitowa yai gunta yace ta shiga mota tunda ai sunce wanda ya kawota shine ya dauketa.
Tanaji tace "Dady ne."
Nan suka shiga yaja motar da gudu suka nufi gidansu, basuyi nisa da fara tafiya ba wayar Sagir ta shiga kara, Sagir ya daga tare da cewa "Ummy!"
Ummy tace "Sagir kuyi sauri ku dawo iyayen Jalila da kakarta sunzo."
Yace "gamunan."
Ya juya kan motar yana cewa "jalila iyayenki suna gida."
Hawayenta ta share tace "an fadama wa nene yazo?"
Yace "kawai dai cemin tai iyayenki da ko kakarki ne?"
Jalila tai shiru sai fatan Allah yasa ba wani abin bane ya faru, suna isa gidan ta fita da sauri ko motar bata rufe ba ta nufi cikin gidan.
Da gudu ta shiga, a falo ta taradda Ameera rike da waya tana latsawa.
Jalila ta matso tace "Ameera ina Mumy?"
Kallan ta tai tace "suna sama."
Jalila tai sama da gudu, a falon sana ta taradda Inna, tsayawa tai sannan ta karaso a hankali, tsugunnawa tai ta gaida Inna kafin ta gaida Mumy.
An ajiye musu kayan ciye ciye a gaban su.
Ameera ce ta hawo saman sannan ta mika mata makullin dakinta, Jalila ta mike ta bude dakin sannan tace ku shigo.
Mumy ce ta fara mikewa, Inna kuwa sai data karema falon kallo sannan ta shiga dakin, zama tai tana kallan dakin kafin tace "ina mijin naki?"
Jalila tace "ya fita."
Inna ta kalleta tace "rufe kofar."
Jalila ta mike jiki a sanyaye ta rufe kofar, Inna ta kalleta ta mata alama data matso kusa da ita.
Jalila gabanta sai faduwa yake ta matsa a hankali, ta tsugunna.
Mumy ta kalleta tace "Jalila gun Goggo kika je?"
Ta kalleta sannan tace "eh amma bata asibitin, ance Dady ya dauketa."
Mumy ta kalli inna, Inma ta kalli Jalila tace "ni nasa ya dauketa daga asibitin."
Jalila ta kalleta tace "Inna kikace in na amince da auran nan zaki kula da Goggo?"
Inna ta kalleta tace "hakane."
Jalila tace "kuma....."
Inna tai murmushi tace " ba dai kina tunanin wani abin muka mata ba?"
Jalila a tsorace ta kalleta, Inna tace " kinsanar ma wani a gidan nan Goggo ce ta haifeki?"
Jalila jiki a sanyeye tace "a'a amma......."
Inna tace "Jalila wacece ta haifeki?"
Kallan mamaki ta mata tace "ban gane ba Inna?"
Har yaje zai shiga dakinsa yaji kamar ana magana a dakin Jalila bayan yasan Ummy ta rufe dakin, kuma yaga Ummy da Ameera a kasa.
Hannu yasa kamar zai bude kofar yaji ance "tambayarki nake sannan amsarki nake so naji."
Jalila tace "to ai Inna tambayarki gaba daya na kasa fahimtarta, bangane wanene ya haifeni ba?"
Har ya juya zai tafi dan shi mutum ne da bai damuwa da abinda bai dameshi ba.
Jiyai ance " abinda zamsanar dake inaso ya zama amsarki a duk lokacin da aka tambayeki, daga yau ko waye ya tambayeki mahaifiyarki ki tabbatar kince Mumy ce ta haifeki."
Da sauri Jalila ta kalli kofar, shima da sauri ya kalli kofar, meke faruwa? Shidai a iya saninsa bai taba ji inda ake sanar da d'a mahaifiyarsa ba.
Jalila tace "Bangane Mumy ce ta haifeni ba? Goggon tawa rasuwa tai ko me? Ina kuka boyeta? Ta fada cikin wani yanayi mai ban tausayi wanda yasa Hassan din jingina da bangon jikin kofar.
Inna tace "ko daya, ina dai sanar dake ne hakan shine kadai zaisa mu taimaki mahaifiyarki mu kuma bata rayuwa na gari."
Jalila jitai ta sa wata dariya mai tattare da bakin ciki da kuka, tana hawaye tace " A lokacin da za'amin auran nan kunce in na amince zaku kula da Goggona, sannan bayan na amince yanzu kunce kuma gaba daya ma in canza mahaifiyar datai wahala akai........"
Marin da aka kifa mata ne yasa tai shiru, Inna tace " dan kinyi aure a gidan nan ne yasa kika fara tunanin yin jayayya dani? Ina magana kina magana?"
Haryasa hannu zai bude kofar saboda ransa ya baci sai kuma naga ya tsaya, hannunsa naga ya dunkule sannan a ja baya daga jikin kofar, cikin takaici.
Saboda nine kenan? Saboda iyayena sun nemi auranta yasa har ake neman sata yin haka.
Labansa ya ciza sannan ya bude dakinsa ya shiga, ya rufo kofar da karfinsa na gaske.
Wanda yasa sukaji kara, Inna ta kalli Jalila tace "mijin naki ne?"
Jalila tana hawaye ta daga kai, Inna ta tabe baki a ranta tace hauka yake muraran irin wannan buga kofa haka? Ai kanaji kasan na marasa hankaline.
Maida kallanta tai kan Jalila tace "shawara ya rage naki, inhar kinasan kiga mahaifiyarki kiyi abinda na saki, in kuma bakyaso ki hakura da ganinta ne wannan ya rage naki."
Ta kalli Mumy tace "tashi mu tafi dan ba'a dadewa gidan surukai."
Jalila tana kallansu suka mike gaba daya inbanda hawaye ba abinda takeyi, Inna ta fita daga dakin ta juyo tace "bazaki rakamu ba?"
Jalila ta kallesu, yanda Inna take kallanta ne yasa ta mike ta fito falon.
Tana fitowa shima yana fitowa daga dakin, rufo kofa, fuskarnan tasa a daure kallo
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 38