Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ita bata taba kawo kawa ba, bata taba zuwa gidan kawa ba, nasan bawai dan batada shi bane sai dan tana gudun wulakancin dazai biyo baya, dan Allah Hassan ga amanar yarinya ta nan, ka taimakeni kamar yanda Allah ya taimakeka ya baka iyaye na gari ya baka duk wani abu da ya dace ka kularminn da ita, ba marainiya bace sai dai tafi wasu marayun rashin gata, dan garasu a kalla sun san mahaifinsu ba rai gareshi ba akanta, wacce tana ganinsa sai dai yafi karfinta." Tai shiru kafin ta daura da cewa "nagode sosai da kaunar da kuka nuna mata, da kuma kaunar da kuka nunamin sai dai kuyi hakuri bazan iya zama a gidan 'yata ba." Cikin mamaki Hassan ya kalleta yace "meyasa?" Tace " taya zan iya zama a gidan ku? Bayan kudin sirikainane? Wani irin zama zamuyi?" Hassan yace "wlh bakomai." Tace "nafi kowa sanin ba komai, dan kaunar da kuka nunamin a kwana dayan nan yasa na fahimci hakan, sai dai kuyi hakuri bazan iya zama a gida daya da sirikaina da yata ba, abinda yasa ban fadama kowa ba sai kai bakomai bane sai dan kaidin kaine ka kawoni gidan sannan inaso inbaka girmanka na mijin 'yata tilo." Hassan yai shiru dan baisan me zai kuma cewa ba Goggo tai murmushi tace " ka sanar dasu ra'ayina, zan koma inda na fito." Yace "ina kenan?Goggo?" Tace "karka damu kauye nake nufi bawai gidan Babanta ba." Hassan yai shiru yana nazari, jiyai tace "jeka dama abinda zan fadama kenan kar na tsayar dakai, zuwa anjima ko gobe zan tafi in Allah ya kaimu." Hassan yai shiru kafin ya mike ya fito, mota ya shiga yana nazarin kalamanta, bazai takura akan ta zauna ba dan hakan ita kuma zai iya zama takura ne a gareta sai dai ya kula ganin mahaifiyarta shine zaifi sata farinciki........ Kofar da aka bude ne yasa ya kalli kofar, shigowa tai ta zauna. Yauce rana ta farko data taba saka doguwar rigar abaya, shima a cikin kayan lefenta yake ta dade tanasan ta saka amma kunya ta hanata, yau ma daurewa tai ta saka, dankwali baki ta daura a ciki ta yafa dankwalin abayar. Tana shigowa idanunsa suka kalli kirjinta, da sauri ya dauke ido daga kanta, meye hakan? Abinda zuciyarsa ta tambayeshi kenan. Tada mota yai baice komai ba, itama tai shiru ranta a bace wai ita a dole ya bata mata rai, bazanci ba, kalmar nan ta bata haushi. Ina zaije? Bayan Goggon tace bazata zauna ba? Sai dai ya rasa meyasa ya kasa fada mata, da alama san fitar yakeyi da ita. Bayan sun hau titi ne yadan gangara bakin wani shago yai parking. Fita yai bai dade ba ya dawo, yana shiga ya bude leda ya dauko robar yoghurt ya mika mata bayan yaja motar. Jalila ta kalleshi tace "nima banasha." Yace "ce miki nai naki ne?" Tace "nawaye to?" Yace "budemin zakiyi yunwa nakeji." Wani kallo tamai tace "yunwa?" Yace "bazaki budemin ba?" Ta kara hade fuska ta fizgi robar yoghurt din da karfi daga hannunsa ta budemai sannan ta mikamai. Amsa yai sannan ya kurba. Takaici yasa tace "yunwa kakeji amma kaki cin abinci?" Yace "dama dan mutun najin yunwa sai ya zama dole sai yaci abinci?" Tace "ba dole tunda cikin mutum ne." Yai shiru tare da cigaba da tukinsa, meyasa nace haka? Ahh meke damuna? Abinda zuciyarsa ke fadamai kenan. Jalila kuwa ta kara kumbura, kallanta yadanyi kadan sannan ya mika mata yoghurt din, tace "me zanyi kuma?" Yace "sha?" Tace "nace banasha." Yace "ke da kikejin yunwa meyasa bakici abincin ba?" Ta kalleshi sannan tace "Yaya wai dan Allah me yasa kakemin haka?" Yace "me?" Tace "yau sai ka min magana cikin sanyi, anjima sai kamin cikin zafi, wata anjimar kuma amsa ma ban isa samuba." Yace "haka kike gani?" Cikin wata irin murya da ita kanta bata sani ba tace "hakan ne mana." Da sauri yai gefen titi dan jiyai wani abu ya tsirgamai, kallanta yai sannan ya kalli kirjinta, da sauri yamaida kansa titi ya hade rai, kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa, fizgar motar yai da karfi. Haushi ne ya kara kamata, ta juya tana kallan titi. Can dai ta daure tace " ina zamu siyo kayan?" Yai shiru kafin yace " me kike tunani akan nemawa Goggo wani gidan? Ko a cikin gidajen Abba ne dan yanada na haya." Jalila tace "Goggo tace wani abun ne?" Yai shiru, ta dan yi ajiyar zuciya tace " dama tunda naje gaisheta da safe naji tana cewa ina ita ina zama gida daya da sirikai? To ni ban gane me take nufiba, dana tambayeta kuma sai tace bakomai." Hassan ya kalleta yace "me kike tunani?" Ta kalleshi tace "Yaya nikam tsoro nake, kar Goggo ta zauna inda mutanen nan zasu sani, dan wlh Inna bazata barni ba tunda na bata mata plan." Hassan ya kalleta yace " karki damu dasu, ba abinda zasu iya." Jalila tace "Yaya bakasan Inna bako?" Yace "me zai sa na santa bayan banida hadi da ita?" Jalila tai murmushi tace "ya kake gani?" Yace "yanzu muje ki siyo mata kaya, da abinda zata bukata sannan sai ki mata magana akan gidan da zata zauna kiji." Jalila tai shiru tana kallansa, juyowa yai ya kalleta yace "kallanfa?" Tace "wani sa'in rasa abin cewa nakeyi." Yace "kin huce kenan?" Tace "ai ba fishi nai ba, kaine fa kacemin wai bazakaci ba." Yace "bazanci ba so kike nace zanci?" Tace "ba haka nake nufi ba. "To me kike san ji?" Shiru tai tare da tambayar kanta, me nake sanji? Hassan bai kalleta ba ya cigaba da tukinsa. Can Jalila tace "Yaya nagode sosai harma bansan ta ya zan yi godiya ba, yaushe Ameera zata dawo ne?" Yace "Ameera batanan?" Kallan mamaki tamai tace "bangane ba?" Bai tanka mata ba, ta cigaba "dan Allah bakasan bata gida ba? Ta dade fa batanan." Nan ma baice komai ba. Haka suka isa ya zauna a mota yace ta shiga ta siyo kayan, ya mika mata Atm dinsa. Kallan mamaki tai tace "wai ni kadai zani?" Yace " badai kina tunanin dani zaki shiga ciki ba?" Jalila cikin mamaki ta kalleshi tace "Yaya ni wlh tunda nake bantaba zuwa irin wannan gurin ba, sannan bantaba siyo abu ma da Atm ba bare nasan ya akeyi." Kallanta yai kamar zaiyi magana sai ya fasa. Kallansa itama tai tadan shagwabe fuska tace "Yaya Please!" Shiru yai yana kallanta kafin ya bude kofar ya fito, yana fitowa itama ta fito da sauri ta matso inda yake. Can gefe yaje ya tsaya yana kallanta wai ta gama zaba, tsayawa tai a gun atamfofi tana tunanin wanda zata dauka tare da duba kudin da aka rubuta a jiki. "Bakya tunanin wannan yafi kyau?" Abinda taji an fada kenan, muryar daga bayanta ta fito. Da sauri ta juyo, baya tadanyi kadan ganin mutum a bayanta. Murmushi ya sakar mata yace "Sunana Al-Ameen Abbah." Dan baya ta sakeyi tace "Malam......." Ganin Hassan tai a bayanshi, hannu yasa ya dan bugi kafadarsa, mutumin ya juyo rai a bace yace "Malam meye hakan?" Hassan yace "zaka tafi abinda ya kawoka ne ko kuwa?" Yace "mene? Kai." Wani kallo daya bugama Jalila ne yasa tai saurin matsowa kusa dashi, kallanta yai yace "wuce muje." Gani tai ya nufi kofar fita tace "bamusai kayan ba." Yace "banasan shagon." Jalila ta bishi fa kallo, tare da binshi mota. Waya ya dauko ya kira Ameerah. Yauce rana ta farko data fara ganin kiran yayanta a wayarta, cikin mamaki ta daga tace "Hello." "Kina ina?" Tace "Yaya? Ina gidan Aunty Nana." Yace ki shirya zanzo in daukeki." Mamaki ya kamata bayan ya kashe wayar tabi wayar da kallon mamaki. Da sauri ta mike ta hau shirya kayanta. Aina'u tace "Ameera tafiya?" Tace "eh yaya ne zaizo ya daukeni yanzu." Aina'u tace "Kice yau akwai zolaya gun Yaya Sageer?" Tace "Yaya fa ba yaya Sageer ba." Mamaki ne ya kama Aina'u bata dade da shiryawa ba ya kira wayarta yace ta fito yana waje." Aina'u tace "Ameera tafiya zakiyi ga Mamana batanan?" Tace "inta dawo kya fada mata." Cikin hanzari tai waje. Mamaki ne ya kama Aina'u ta biyota waje dan tabbatar ma idanta, aikuwa shine a zaune matarsa na gefensa. Aina'u kishi da takaici ya kamata ko fita daga gate din batai ba ta koma ciki ta fada gado tana hawaye, itafa ya kamata ta zauna a kusa da Hassan ba wannan yarinyar ba. Ameera ta shiga baya bakinta yaki rufuwa, yauce rana ta farko da yayanta zai fita da ita guri a motarsa. Jalila sai murna take taga Ameera tana ta neman jan ta da hira, Hassan yai gyaran murya sannan yace "maganar ta isa, inkunje gida kwayi." Jalila tai gum da bakinta. A kofar wani store ya ajiye su ya kalli Ameera yace "Ameera kuje tare kaya za'a siyoma mahaifiyarta, sannan ya mika mata Atm dinsa." Tace to yaya, ta fita. Jalila na neman fita ya riko hannunta, juyowa tai ta kalleshi yace "yanzun ma inkin je ki kara bari wani katan ya miki magana." Tace "wancan din ma ni na bari? Sannan bafa komai yace min ba cemin kawai yai wannan yafi......." Wani kallo ya maka mata, ya rufe bakinta tace "to." Ya saketa ta fita. Da kallo ya bita har ta shiga cikin shagon na Jifatu. Meke damunshi? Meke damunshi???? Abinda yaketa tambayar kansa kenan..... #OneLuv💕 [12/7, 9:44 PM] El-hajj: 🗯 *JALILAH* 🗯 Written By : *AYUSHER MUHD* ✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd* *HASKE WRITER'S ASSOCIATION* (_D home of expert and perfect writer's_💡) *46* Hassan na saukowa kasa ya nufi hanyar fita da sauri "Hassan!" Juyowa yai da sauri kamar mara gaskiya ya kalleta. Karasowa yai inda take sannan ya gaisheta, fuskarta dauke da murmushi tace "fita zakai?" Yace "eh ni da...." sai kuma yai shiru, murmushi ta sakeyi tace "ya zaka fita baka gaida sirikarka ba?" Yace "sirika?" Nunamai dakin Ameera tai da hannu, Hassan ya kalleta alamar rashin fahimta, tace "badai bazaka ba?" Kallan dakin ya kuma yi sannan taga ya nufi dakin, da kallo ta bishi cikin jin dadi. Hassan ya kwankwasa kofar dakin, daga ciki Lantana ta mike ta bude. Tsayawa yai yana tunanin me ma zaice inya shiga? Goggo dake zaune a kasan carpet tana ganin shine ta mike tace "Hassan? Shigo mana." Shigowa yai ya zauna daga gefe yace "Ina kwana?" Kansa na kasa. Goggo tace "ka tashi lafiya? Ya dawainiya da mu?" Hassan yai shiru dan bai san me zaice ba, Goggo tadanyi shiru haryana shirin mikewa. Tace "Hassan." Komawa yai ya zauna tare da kallanta, Goggo tace "in ba damuwa magana nakeso muyi." Yace " ba komai, menene?" Tadanyi shiru kafin tace "da farko dai nasan kafi karfin Jalila, saboda ita ba gata gareta ba, ba kudi gareta ba sannan ba 'yan uwa dake santa take dashi ba, yarinyar tasha wahala agidan mahaifinta wanda har bata iya cewa ko kawo kawarta da sunan gidansu, tunda nake da ita bata taba kawo kawa ba, bata taba zuwa gidan kawa ba, nasan bawai dan batada shi bane sai dan tana gudun wulakancin dazai biyo baya, dan Allah Hassan ga amanar yarinya ta nan, ka taimakeni kamar yanda Allah ya taimakeka ya baka iyaye na gari ya baka duk wani abu da ya dace ka kularminn da ita, ba marainiya bace sai dai tafi wasu marayun rashin gata, dan garasu a kalla sun san mahaifinsu ba rai gareshi ba akanta, wacce tana ganinsa sai dai yafi karfinta." Tai shiru kafin ta daura da cewa "nagode sosai da kaunar da kuka nuna mata, da kuma kaunar da kuka nunamin sai dai kuyi hakuri bazan iya zama a gidan 'yata ba." Cikin mamaki Hassan ya kalleta yace "meyasa?" Tace " taya zan iya zama a gidan ku? Bayan kudin sirikainane? Wani irin zama zamuyi?" Hassan yace "wlh bakomai." Tace "nafi kowa sanin ba komai, dan kaunar da kuka nunamin a kwana dayan nan yasa na fahimci hakan, sai dai kuyi hakuri bazan iya zama a gida daya da sirikaina da yata ba, abinda yasa ban fadama kowa ba sai kai bakomai bane sai dan kaidin kaine ka kawoni gidan sannan inaso inbaka girmanka na mijin 'yata tilo." Hassan yai shiru dan baisan me zai kuma cewa ba Goggo tai murmushi tace " ka sanar dasu ra'ayina, zan koma inda na fito." Yace "ina kenan?Goggo?" Tace "karka damu kauye nake nufi bawai gidan Babanta ba." Hassan yai shiru yana nazari, jiyai tace "jeka dama abinda zan fadama kenan kar na tsayar dakai, zuwa anjima ko gobe zan tafi in Allah ya kaimu." Hassan yai shiru kafin ya mike ya fito, mota ya shiga yana nazarin kalamanta, bazai takura akan ta zauna ba dan hakan ita kuma zai iya zama takura ne a gareta sai dai ya kula ganin mahaifiyarta shine zaifi sata farinciki........ Kofar da aka bude ne yasa ya kalli kofar, shigowa tai ta zauna. Yauce rana ta farko data taba saka doguwar rigar abaya, shima a cikin kayan lefenta yake ta dade tanasan ta saka amma kunya ta hanata, yau ma daurewa tai ta saka, dankwali baki ta daura a ciki ta yafa dankwalin abayar. Tana shigowa idanunsa suka kalli kirjinta, da sauri ya dauke ido daga kanta, meye hakan? Abinda zuciyarsa ta tambayeshi kenan. Tada mota yai baice komai ba, itama tai shiru ranta a bace wai ita a dole ya bata mata rai, bazanci ba, kalmar nan ta bata haushi. Ina zaije? Bayan Goggon tace bazata zauna ba? Sai dai ya rasa meyasa ya kasa fada mata, da alama san fitar yakeyi da ita. Bayan sun hau titi ne yadan gangara bakin wani shago yai parking. Fita yai bai dade ba ya dawo, yana shiga ya bude leda ya dauko robar yoghurt ya mika mata bayan yaja motar. Jalila ta kalleshi tace "nima banasha." Yace "ce miki nai naki ne?" Tace "nawaye to?" Yace "budemin zakiyi yunwa nakeji." Wani kallo tamai tace "yunwa?" Yace "bazaki budemin ba?" Ta kara hade fuska ta fizgi robar yoghurt din da karfi daga hannunsa ta budemai sannan ta mikamai. Amsa yai sannan ya kurba. Takaici yasa tace "yunwa kakeji amma kaki cin abinci?" Yace "dama dan mutun najin yunwa sai ya zama dole sai yaci abinci?" Tace "ba dole tunda cikin mutum ne." Yai shiru tare da cigaba da tukinsa, meyasa nace haka? Ahh meke damuna? Abinda zuciyarsa ke fadamai kenan. Jalila kuwa ta kara kumbura, kallanta yadanyi kadan sannan ya mika mata yoghurt din, tace "me zanyi kuma?" Yace "sha?" Tace "nace banasha." Yace "ke da kikejin yunwa meyasa bakici abincin ba?" Ta kalleshi sannan tace "Yaya wai dan Allah me yasa kakemin haka?" Yace "me?" Tace "yau sai ka min magana cikin sanyi, anjima sai kamin cikin zafi, wata anjimar kuma amsa ma ban isa samuba." Yace "haka kike gani?" Cikin wata irin murya da ita kanta bata sani ba tace "hakan ne mana." Da sauri yai gefen titi dan jiyai wani abu ya tsirgamai, kallanta yai sannan ya kalli kirjinta, da sauri yamaida kansa titi ya hade rai, kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa, fizgar motar yai da karfi. Haushi ne ya kara kamata, ta juya tana kallan titi. Can dai ta daure tace " ina zamu siyo kayan?" Yai shiru kafin yace " me kike tunani akan nemawa Goggo wani gidan? Ko a cikin gidajen Abba ne dan yanada na haya." Jalila tace "Goggo tace wani abun ne?" Yai shiru, ta dan yi ajiyar zuciya tace " dama tunda naje gaisheta da safe naji tana cewa ina ita ina zama gida daya da sirikai? To ni ban gane me take nufiba, dana tambayeta kuma sai tace bakomai." Hassan ya kalleta yace "me kike tunani?" Ta kalleshi tace "Yaya nikam tsoro nake, kar Goggo ta zauna inda mutanen nan zasu sani, dan wlh Inna bazata barni ba tunda na bata mata plan." Hassan ya kalleta yace " karki damu dasu, ba abinda zasu iya." Jalila tace "Yaya bakasan Inna bako?" Yace "me zai sa na santa bayan banida hadi da ita?" Jalila tai murmushi tace "ya kake gani?" Yace "yanzu muje ki siyo mata kaya, da abinda zata bukata sannan sai ki mata magana akan gidan da zata zauna kiji." Jalila tai shiru tana kallansa, juyowa yai ya kalleta yace "kallanfa?" Tace "wani sa'in rasa abin cewa nakeyi." Yace "kin huce kenan?" Tace "ai ba fishi nai ba, kaine fa kacemin wai bazakaci ba." Yace "bazanci ba so kike nace zanci?" Tace "ba haka nake nufi ba. "To me kike san ji?" Shiru tai tare da tambayar kanta, me nake sanji? Hassan bai kalleta ba ya cigaba da tukinsa. Can Jalila tace "Yaya nagode sosai harma bansan ta ya zan yi godiya ba, yaushe Ameera zata dawo ne?" Yace "Ameera batanan?" Kallan mamaki tamai tace "bangane ba?" Bai tanka mata ba, ta cigaba "dan Allah bakasan bata gida ba? Ta dade fa batanan." Nan ma baice komai ba. Haka suka isa ya zauna a mota yace ta shiga ta siyo kayan, ya mika mata Atm dinsa. Kallan mamaki tai tace "wai ni kadai zani?" Yace " badai kina tunanin dani zaki shiga ciki ba?" Jalila cikin mamaki ta kalleshi tace "Yaya ni wlh tunda nake bantaba zuwa irin wannan gurin ba, sannan bantaba siyo abu ma da Atm ba bare nasan ya akeyi." Kallanta yai kamar zaiyi magana sai ya fasa. Kallansa itama tai tadan shagwabe fuska tace "Yaya Please!" Shiru yai yana kallanta kafin ya bude kofar ya fito, yana fitowa itama ta fito da sauri ta matso inda yake. Can gefe yaje ya tsaya yana kallanta wai ta gama zaba, tsayawa tai a gun atamfofi tana tunanin wanda zata dauka tare da duba kudin da aka rubuta a jiki. "Bakya tunanin wannan yafi kyau?" Abinda taji an fada kenan, muryar daga bayanta ta fito. Da sauri ta juyo, baya tadanyi kadan ganin mutum a bayanta. Murmushi ya sakar mata yace "Sunana Al-Ameen Abbah." Dan baya ta sakeyi tace "Malam......." Ganin Hassan tai a bayanshi, hannu yasa ya dan bugi kafadarsa, mutumin ya juyo rai a bace yace "Malam meye hakan?" Hassan yace "zaka tafi abinda ya kawoka ne ko kuwa?" Yace "mene? Kai." Wani kallo daya bugama Jalila ne yasa tai saurin matsowa kusa dashi, kallanta yai yace "wuce muje." Gani tai ya nufi kofar fita tace "bamusai kayan ba." Yace "banasan shagon." Jalila ta bishi fa kallo, tare da binshi mota. Waya ya dauko ya kira Ameerah. Yauce rana ta farko data fara ganin kiran yayanta a wayarta, cikin mamaki ta daga tace "Hello." "Kina ina?" Tace "Yaya? Ina gidan Aunty Nana." Yace ki shirya zanzo in daukeki." Mamaki ya kamata bayan ya kashe wayar tabi wayar da kallon mamaki. Da sauri ta mike ta hau shirya kayanta. Aina'u tace "Ameera tafiya?" Tace "eh yaya ne zaizo ya daukeni yanzu." Aina'u tace "Kice yau akwai zolaya gun Yaya Sageer?" Tace "Yaya fa ba yaya Sageer ba." Mamaki ne ya kama Aina'u bata dade da shiryawa ba ya kira wayarta yace ta fito yana waje." Aina'u tace "Ameera tafiya zakiyi ga Mamana batanan?" Tace "inta dawo kya fada mata." Cikin hanzari tai waje. Mamaki ne ya kama Aina'u ta biyota waje dan tabbatar ma idanta, aikuwa shine a zaune matarsa na gefensa. Aina'u kishi da takaici ya kamata ko fita daga gate din batai ba ta koma ciki ta fada gado tana hawaye, itafa ya kamata ta zauna a kusa da Hassan ba wannan yarinyar ba. Ameera ta shiga baya bakinta yaki rufuwa, yauce rana ta farko da yayanta zai fita da ita guri a motarsa. Jalila sai murna take taga Ameera tana ta neman jan ta da hira, Hassan yai gyaran murya sannan yace "maganar ta isa, inkunje gida kwayi." Jalila tai gum da bakinta. A kofar wani store ya ajiye su ya kalli Ameera yace "Ameera kuje tare kaya za'a siyoma mahaifiyarta, sannan ya mika mata Atm dinsa." Tace to yaya, ta fita. Jalila na neman fita ya riko hannunta, juyowa tai ta kalleshi yace "yanzun ma inkin je ki kara bari wani katan ya miki magana." Tace "wancan din ma ni na bari? Sannan bafa komai yace min ba cemin kawai yai wannan yafi......." Wani kallo ya maka mata, ya rufe bakinta tace "to." Ya saketa ta fita. Da kallo ya bita har ta shiga cikin shagon na Jifatu. Meke damunshi? Meke damunshi???? Abinda yaketa tambayar kansa kenan..... #OneLuv💕 [12/7, 9:51 PM] El-hajj: 🗯 *JALILAH* 🗯 Written By : *AYUSHER MUHD* ✔️ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd* *HASKE WRITER'S ASSOCIATION* (_D home of expert and perfect writer's_💡) *47* Hankalinsa ya kasa kwanciya, fitowa yai daga motar tare da dan matsowa kadan da kofar shiga yadan leka ciki kadan. Security din dake gun ne ya kalleshi yace "Yallabai shiga zakai?" Hade rai yai ya juya jikin motarsa, hannayensa ya hada yana dan hadasu da waresu, kafin ya koma cikin mota ya dauko wayarsa. Mintinsu sha biyar kenan da shiga, me sukeyi haryanzu? Ko alert bai gani ba bare yasa ran sun biya. Wayarsa ya dauko ya danna number Ameera. Sukuwa suna ciki Jalila kome Ameera ta dauko indai taga kudi sai ta maidashi, Ameera ta tsaya tace "to nidai bansan me kikeso mu siya ba, duk abinda na dauko sai ki maida." Ta karasa maganar tana kallan kwandon nasu da bakomai a ciki sai atamfa kwaya daya. Kiran Hassan ne yasa ta kalli Jalila tace "Yaya!" Jalila ta kalleta bayan ta amsa kiran, Ameera tace "Yaya...." Yace "me kukeyi haryanzu? Badai shirme kuka tsaya yi ba?" Tace "a'a Yaya, ni narasa me zamu siya ne, duk abinda na dauko sai Yaya Jalila tace wai yayi tsada sai ta maida." Hassan ya kashe wayarsa baijira ya gama jin abinda zatace ba. Tahowa yai ya shiga ciki, security din ya bishi da kallo yana yan kunkuni, inkasan shigowa zakai gulmar ta menene? Tun dazu ka tsaya kamar mai jira. Hassan na shiga ya sake kiran Ameera ya tambayeta inda suke, ta sanar dashi. Yana isowa ya bugama Jalila kallan harara sannan ya kalli Ameera yace "ina kayan da kika zaba?" Nan ta shiga daukowa tana sawa a cart din, mamaki na kara ratsata, bata dade a gidansu Aina'u ba yaushe har yayanta ya koma haka? Jalila na tsaye tana kallansu sai zuba kaya sukeyi a cart din har sai da ya cika sannan suka nufi gun biyan kudi. Tana can gefe suka biya kudin sannan ya kalleta ya nuna mata ledoji, matsowa tai ta dau leda biyu manya itama Ameera tadau biyu suka nufi kofar fita. Yana kallanta da yanda ledojin suka mata nauyi dan kamar ma janta sukeyi, kallanta ya sakeyi sannan ya kalli ledar ji yake kamar yaje ya amsa sai dai inaaa bayaji zai iya yin hakan, balle agaban Ameera. Taje kusa da motar bata kula da saman interlocks din daya dago ba, jitai tayi tintibe da sauri yasa hannu ya riko cikinta. Ajiyar zuciya tai dan ta tsorata ga kayan da suka kara rinjayarta. Juyowa tai ta kalleshi kawai sai tai dariya tace "yaya wlh na tsorata, har na hango kaina ya bugu da jikin motar." Jawota yai ta mike daidai sannan ya kalli gun datai tuntube, lalai mutanen nan basuda hankali tayaya bazasu gyara gun ba? Fuska a daure ya kalleta yace "meyasa bakya kallan kasa in kina tafiya? Da bana kusa ko da banyi hanzarin kamoki ba me kike tunanin zai faru?" Ta kalleshi jikinta yai sanyi tace "wlh ban......" Gani tai ya wuceta rai a bace, ledar hannunta ya amsa ya sa a boot din motar sannan ya bude ciki ya shiga. Ameera ta ajiye nata itama ta shiga baya sum sum. Jalila ma jiki a sanyaye ta shiga, to laifinta ne? Itama ai da saninta bazata bari ta fadi haka ba. Harya tada motar ya fito daga ciki ya nufi gun secuydin. Kallansa yai fuskar nan a daure, security din ya kalleshi yace "Yallabai da wani abun ne?" Shiru yai yana tunani, menene damuwarka da har kazo nan zakai fada akan su gyara gun da yarinyarcan zata fadi? Menene damuwarka Hassan. Bai tanka mai ba ya juya, security din ya bishi da kallo yace "yau ni kuma ina na samo wannan?"Hassan ya bude motar ya shiga dya rufota da karfi yaja motar da gudu suka bar gun. Shiru motar tai ba wanda yake magana, sai sanyin Ac dake ratsa cikin motar. Jalila ta kalleshi taga ba alamar wargi, tai gum. Can ta sake kallansa nan ma taga ba alama tai gum. Sunyi nisa sosai sai tace "Yaya kashanye yoghurt dinka?" Bai tanka mata ba sai dai yasa hannu ya miko mata ledar, ba haka taso ba, ta daure ta sake cewa "kasan

Chapter 21 of 38