gidan ba, sannan bamu siyo generator ba."
Goggo da sauri tace "hakan ma ya isa, ba sai anja wutar ba dan acan gidan ma bamu samu wannan darajar ba ni har na rasa ta inda zan soma yi muku godiya."
Ummy tace "dan Allah ki bari, yanzu bari mu barku anan, sai nasa yanzu Sageer ya samo katuwar fitila kafin a gyara wutar gidan, kayanki kuma gobe in Jalila zata zo sai na bada a kawo miki."
Goggo ta kamo hannun Ummy cikin wani irin yanayi na farinciki tace " nagode nagode, sai dai dan Allah ina da alfarma daya dazan nema."
Ummu tace "menene?"
Goggo tace "Jalila tana bala'in san makarantar addini ta islamiyya, bansani ba ko da yanda zakuyi ku taimaka mata."
Ummy tace "basu sata a makaranta ba?"
Tace "basu sata ba, karatun da nake dashi kadan shi na koya mata."
Ummy tai shiru tana tunanin wannan muguntar kafin tace "shikenan zan sanar ma mijinta, hafizi ne na karatu dan da wuri ya sauke alqur'ani zan ji shawarar da zai yanke."
Goggo tace "nagode sosai."
Haka suka fito sukabar Goggo da Lantana a gidan, sai da suka sai katuwar fitila suka kai musu sannan suka fito.
Ummy a hanya ta kalli Sageer tace "Sageer akwai iyayenda in basuyi wasa ba alhakin 'ya'yansu shine dalilin da zaisa su shiga wuta."
Sageer yace "Ummy nikam haryanzu kwakwalwata na mamakin irin wannan mahaifin, wanda san kansa yamai yawa da har baya damuwa da halin da 'ya'yansa suke ciki."
Ameera ta kalli Ummy tace "Ummy nikam dan Allah kumin bayani, wai ya akai Goggo ta zama mahaifiyar Jalila, Mumy fa? Nifa gaba daya na rasa meke faruwa tun jiya nakesan yin tambaya."
Ummy tasa yatsa ta ta tura goshita tace "gulmar me kike sanji? Magana daya dai wannan ce mahaifiyarta me kike nemanji bayan wannan?"
Sageer ya sa dariya yace "Ummy in Ameera batai gulma ba ai ba Ameeran bace."Cikin shagwaba tace "Yaya Sageer haka zakace? Harda wani in banyi gulma ba?"
Ya kara sa dariya yace "To yahkuri ba gulma ba."
Ummy ta kalleta tace "ba wani tayi hakuri, ai dama uwar gulma ce da san jin komai."
Ameera ta kara shagwabewa tace "Ummy Allah ni abubuwan da nakeso in tambaya dayawa fa amma tun yanzu kunsa na kasa."
Ummy tace "sai ki hadiye gulmarki inkin samu Abbanki sai ki tambayeshi."
Tace "shikenan ai nasan Abbana bazai min haka ba..."
Haka sukai ta zolayarta suna dariya cikin farinciki har suka isa gida.
********
A can gida kuwa Hassan tunda ya shiga daki ya zauna a bakin gado yai shiru yana tunani, tabbas gaba daya rayuwarsa ta canza a 'yan kwanakin nan, gaba daya yarinyar nan taki barin zuciyarsa.
Abu daya ne ya fara zuwa mai badai santa kake ba?
Da sauri ya girgiza kai yace "so? Ni? Yarinyar nan?"
Kai ya sake girgizawa alamar ba haka ba yace "tausayine."
Tausayi akan me? Ka tabbatar shi kadai ne? Damuwar da kakeyi fa in abu ya sameta?
Tambayar dake tamai yawo a zuciya kenan, shiyasa ma gaba daya daga ta shigo sai yai gamar yana bacci, ko ya dau littafi wai a dole karatu hakeyi ko ya dau wayarsa....
Ita kuwa daga baya ta sauka falon kasa ta zauna.
Bayan tayi sallar isha'i ne Abba ya dawo, ta gaisheshi ya amsa fuska a sake bai dade da dawowa ba su Ummy suka dawo.
Tanajin dawowarsu ta tashi da sauri tazo taryarsu.
Ummy ta kalleta cikin kulawa tace "Jalila jikin ne?"
Tace "na warke Ummy gashi banyi abinci ba."
Tace "nina hana kiyi, bakida lafiya wake ta abinci?"
Sunkuyar da kanta tai, Ummy ta amshi ledar hannun Sageer tace "ga shi kije kuci da Hassan muma munyo namu tsarabar."
Jalila ta amsa tace "angode."
Ta fada sannan ta leka bayan Ummy, Ummy tace "tana can."
Jalila ta sunkuyar da kai tace "tam."
Ameera ta matso tace "ya jikin?"
Jalila tace da sauki.
Ummu tai gaba Ameera ma tabita, ta kalli Sageer tace "Sannu da zuwa."
Kallanta yai yace "ya jiki?"
Tace "na ware ba wani serious bane dama."
Ya kalleta cikin kulawa yace "Sannu Allah ya kara sauki."
Tace Ameen ta juya, da kallo ya bita.
Kowa daki ya shiga da ledarsa dan duk sun gaji.
Jalila ta wuce sama.
Tana shiga ta sameshi a zaune, yana ganinta ya dau littafi wai karatu yake.
A ranta tace ko gajiya bayayi.
Ta matso dan dama ta dauko plate daga kasa, ta bude tace "yaya sauko Ummy ta kawo mana abin dadi."
Kallanta yai yace "menene abin dadin?"
Ta bude kedar ta ciro ledar juice sannan ta ciro foil paper ta bude, kaza ce da kuma daurin kundu wanda yasha hadi na musamman.
Juyowa tai ta kalleshi, kallanta yai sannan ya sauko fuska ya zauna, dandai yunwa yakeji amma da cewa zaiyi bazaici ba.
Kallansa tai batasan yanda zata raba musu ba gashi plate daya ta dauko, kallansa tai shima kallanta yai tace bari na dauko wani plate din.
Ta fada tana kokarin mikewa, hannu yasa akan hannunta data dafa kasa zata tashi, kallansa tai, yace "muci tare."
Tace "naam?"
Yace "me? Dama ba haka kikeso ba?"
Tace "nakeso kamar ya kenan?"
Yace "duba ki gani, kinsan mu biyu ne a dakin nan kika dauko plate daya, yimin bayani meyasa kikai hakan to?"Jalila ta kalleshi kamar zatai magana kawai sai tasa dariya tace "lalai Yaya, yanzu nace zan dauko plate ka hanani sannan kace nice nakeso."
Yace "to ba hakan bane?"
Tace "wlh ba haka bane, ni na....."
Yanda ya mata da fuskarsa ne yasata ta kasa magana alamar bayarda zaiyi da duk abinda ta ce ba.
Bismilla tai tasa hannu tana cewa "shikenan tunda an dakeni an hanani kuka."
Bai tanka mata ba yasa hannunsa, a tare suka fara ci, itadai kunya take, shikam wani irin sanyi yakeji a ransa, yana kallanta yasa hannu cikin plate din, a kann hannunta yasa hannunsa.
Dagowa tai ta kalleshi, kallanta yai sannan ya kalli hannunsa, yace "yanzu nine nasa hannuna ko kece?"
Tai dariya sannan ta kalli hannun nashi tace "to hannun waye a sama?"
Ya kalla yace "nawa ne sai dai me yasa nakeji a jikina kamar dauramin akai?"
Tace "me? Daurama?"
Dariya ta fara yi tana kallansa, samun kansa yak da shagala gun kallanta, wanda har bai san ganin yanda take dariya yasashi sakar murmushi ba.
Tsayawa tai da dariya tace "Yaya! Kasan kayi murmushi yanzu?"
Fuska ya hade tare da zare hannunsa da sauri yace " a ina nai murmushin?"
Tace "wallahi kayi yanzu, baka san kayi ba?"
Juya kansa gefe yai yace "u are mistaken."
Tai shiru tana kallansa kafin tace " mistake nai? Amma na tabbatar naga kayi murmushi."
Yace "are u sure ba hakan kike san gani ba?"
Tace"wannan karan bazan musa ba, dan ina san inga ka yi murmushi kullum fuskarka a daure take."
Ya kalleta tare da daukan cup din juice yasha.
Haka sukaci abinci tare sannan ta mike ta wanke hannu ta sauka kasa dan kai plate.
Tana fita ya saki ajiyar zuciya yace "Hassan?"
Gaban madubi ya koma ya kalli kansa, a hankali naga yanayin fuskarsa ya canza zuwa tashin hankali, yasa hannu ya bude drawer karshe ta jikin madubi.
Wani littafi ya dauko ya bude tsakiyar hoto be ya bayyana, kallan hoton yai cikin wani yanayi sannan yamaida hoton ya rufe ya runtse idanunsa, bancancanci farinciki ba, ban kuma cancanci inso ko a so ni ba.
Mikewa yai ya dafa kansa dake sarawa........
Gaba daya ranar bai sake magana ba har ta gaji ta kwanta dan ba alamar fuska.
Washegari ma da Ummy tace ya kaita gidan Goggo bai musa ba ya jira ta suka fita tare, yana kaita kofar gidan baijira me zatace ba yai gaba.
Da kallo tabi motar tana mamakin abinda ya faru, ko a mota duk yanda taso suyi magana kin yarda yai.
Shikuwa yana ajiyeta yaja mota yana tunani.
Jalila kam tana shiga gidan Goggo ta saki baki tana kallan iko Allah, ta shigar da kayan data taho dashi, nan suka zauna suka hau hira cikin farin ciki.
Lantana ma ta zauna sukaita hira.
Goggo cikin hira ne take tambayarta wanda ya kawota.
Jalila tace driver dinsu ne ya kawoni, Yaya ya fita ne.
Goggo tace "Allah sarki, na dauka shine ince bai shigo mun gaisa ba na mai godiya."
Jalila tace "zaizo shima."
Haka sukai ta hira suna tuno rayuwar baya da yanda sukasha wahala, Goggo tanata kara nuna mata ta kula da mutanen nan dan tabbas sun musu hallacin da basu taba tunani ba.
Jalila jefi jefi tana tuno abinda yaya ya mata yanzu da zata sauko, ta fito ta kalleshi tace "Yaya baza......"
Gano tai ya dauke kai yana neman wucewa.
Tsayawa tai dagalo tana kallan ikon Allah kafin ta shigo.
Meya sameshi?
Sai bayan magrib yaro ya turo ta fito, tana fitowa taga Mamman, jikinta ne yai sanyi ta bude bayan mota ta shiga tayima Lantana da Goggo sallama akan sai ta dawo.
Haka suka hau hanya, ta kasa daurewa tace "Mamman ina Yayan?"
Yace "wlh Hajiya bansani ba, waya yamin yace in daukoki."
Tace "okay."
Haka suka isa gida taitama Ummy godiya da Abba.
Kafin ta hau sama.
A daki ta sameshi yana karatu, sallamarta kawai ya amsa shima baiko kalleta ba, Jalila ta daure tace "Yaya na dawo."
Yace "naganki."
Shiru tai a tsaye kafin ta nufi toilet, tai wanka ta sa kayan bacci sannan ta fito ta dau bargo ta shimfida tana cewa "Yaya bacci nakeji, yau da alama na zama kasa, ko dan banyi baccin safe bane? Ina ta zumudi?"
Bai tanka mata ba, tai dariya tace "hmm basa banba, ni fa da agida bansan ma wani baccin safe ba amma yanzu jin dadi yasa har in banyi ba sai naji wani iri."
Bai tanka mata ba hakan yasata yin shiru, ta sa bargo ta kwanta, bata dade ba bacci ya dauketa.
Juyowa yai ya ajiye littafin ya kura mata ido, idanunsa ne suka canza kala a fili yace " Jalilah! Jalilah!"
Sannan yai shiru, mikewa yai ya shiga toilet ya watsa ruwan zafi sannan ya zura riga, harzai wuceta ya tsaya, sai kuma ya koma ya zauna kusa da ita.
Hannu yasa a gefen fuskarta yana kallanta cikin wani yanayi.
Cikin wata raunaniyar murya yace " nasan i am hurting u, sai dai kafin kiji zafin abinda nake miki ni na ji zafi, duk sanda na wulakantaki inaji a jikina sai dai bansan ya zanyi ba, Jalilah bansan ya zanyi ba banasan naga na dawwama a koda yaushe a cikin kuntata miki."
Shiru yai yanajin wani abu a kirjinsa kafin yace "Jalila Husain......."
Ya runtse ido a hankali wasu hawaye naga sun zubomai masu zafi, hannunsa yakai kan labanta.
Idanunsa ya sake rufewa a hankali ya shiga matso da kansa ya sumbashi bakinta, bakinsa ya bari a kan labanta.
Idanunta ta bude, me zata gani?
Shima idanu ya bude suka kalli juna, da sauri tasa hannu ta tureshi, ya mike tsaye da sauri.
Tace "Yaya!"
Yace "bargona nakesan dauka sanyi nakeji."
Tace "bargo?"
Bargo a.......
Ta kasa karasawa, yace "bargo a me?"
Tace "bakomai, nagane tun jiya kaki kulani, yanzu kuma gashi kanamin magana."
Yace "yanzun ma bakiji me nace miki ba? Bargona zaki bani."
Tace "to in na baka in shimfida me?"
Ya kalleta taya zaiyi yace mata shi kwanan kasan ne bayaso?
Ya hade fuska yace "sai ki kwanta akan gado ni sam laushin katifa samin ciwon baya take."
Da sauri tace "haba? Da gaske na kwanta?"
Ya kalleta sannan ya dau bargonsa ya kwanta akasa.
Murmushi tai sannan ta hau kan gado tana dariya jin dadi.
Can kuma tace "yaya badai barmin kai ba?"
Yace "barmiki? Bakiji me nace ba?"
Tace "oh naji."
Ta kwanta tare da juya baya.
Shiru tai kamar mai bacci tana tunanin abinda ya faru yanzu, hannunta takai kan labanta ta shafasu, shima kwanciya yai yana tuno abinda ya faru, me yakai shi? Baisan ya akai yaji a lokacin sumbatarta yakesan yi ba.
Ahhh kansa ya shafa yace "Hassan!"
#OneLuv💕
[12/7, 9:54 PM] El-hajj: *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔️ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*50*
Yana cikin barci wajen karfe uku taji ana wani irin numfashi sama sama, yanzu kam ta riga tasan shine da sauri ta sa hannu ta danna waayarta sannan ta kunna fitilar dakin, yau a rufda ciki ta gashi ya tukunkune daga can gefe hannunsa nakan wuyansa gaba daya zufa ce take keto masa, mikewa tai da sauri tazo kusa dashi.
Hannuntasa ta janye hannunsa daga kan wuyansa, idanunta sun ciciko tana kiran sunansa.
Amma ina, hannunsa ya fizge daga gunta ya rike kansa dake wani irin sarawa, Jalila ta ga yau abin nasa dayawa dan har pillow ya dauka ya danne kansa dashi.
Cikin tsoro da tausayinsa yasa ta janyowshi ta rungumeshi ta baya tare da sa kuka tana cewa "Yaya! Yaya dan Allah kandaina......."
Jitai jikinshi duk yanata ketowa da zufa, sakeshi tai da sauri ta kure karfin AC din dakin sannan ta dawo a rikice ta kara janyoshi tana kuka.
Yau abin ya dade dan ita kawai data rungumeshi ta kifa kanta a jikinsa bata sake dagowa ba.
A hankali numfashinsa ya dawo, ya bude idanunsa, ganinshi yai a jikin Jalila tanata kuka.
Shiru yai cikin takaici abinda ke faruwa wanda gashi duk sanda abin ya tashi sai yasa Jalila kuka haka.
Mikewa ya fara kukarinyi, idanunta ta bude ta daukeshi a kansa, da sauri tace Yaya?
Zama yai sannan ya jawota kusa dashi, jiki a sanyaye take kallanshi.
Bata an kara ba taji ya rungumeta tsam, ya kwantar da kansa kan kafadarta.
Bakinta na rawa tace "Yaya!"
"Let's stay like this for a moment......" cikin wata murya mai sanyi ya fadi hakan, shiru tai ta kasa motsi.
Can yasa hannu a bayanta kamar me lallashi yace " sai yaushene zaki canza hobby dinki?"
A hankali tace " to ya zanyi duk ka canza lokaci daya, ga....."
Yace "are u worried about me or are u scared?"
Tace "zaka fara ko Yaya?"
Shiru yai kafin ya saketa ya kalleta yace "irin wannan kure mana AC haka fa?"
Ta tashi ta dau remote tana cewa, zufa kaketayi shiyasa na kunna.
Ya kafeta da ido yace "kin tabbatar dan ni kika kunna?"
Tace " ban gane ba???"
Yace "a'a to haka kawai dan ina zufa sai a kure AC haka?"
Ta kalleshi tace "nikam ko dan ka kwanta a kasa ne? Naga ka dade lafiya."
Kallanta yai sannan ya girgiza mata kai yace "ko daya."
Ta kalleshi bayan ya mike daga gun tace "Yaya nikam dan Allah meke damunka? Mafarki kakeyi? Ko.......?"
Sai kuma tai shiru, yace "ko aljanu gareni?"
Da sauri tace "ba haka nake nufi na...."
Ruwa ya dauko yasa sannan ya dawo ya kwanta, kallanta yai da take dukushe a gun yace "Hajiya zan kwanta."
Tace "Hajiya? Lalai Yaya matar da bata taba zuwa hajj ba, batama iya karatu sosai ba itace Hajiya."
Juyowa yai ya kalleta sosai yace "daki shiga islamiyya ku dinga zuwa da Ameera da kuma ki zauna a gida wanne yafi?"
Tace "in zauna a gida kamar ya?"
Tai tambayar tana kallansa, juyawa yai baice komai ba.
Da sauri ta kalleshi tace "da ka koyamin a gida?"
Idanunsa ya rufe da sauri tare da harde hannayensa, ta sako kanta tace "Yaya dagaske?"
Bude idanunsa yai, sam baiyi tunanin ganinta daf dashi haka ba, idanunsa ne ya sauka a nata, da sauri ta mike tsaye ta hau kan gado ta kwanta tare da saurin kashe fitilar dake jikin gadon.Kwanciya tai tana dan ajiyar zuciya a hankali.
Dakin ne ya baibaye da duhu.
Tana kwance sai dan juye takeyi, can tace "yaya kayi bacci?"
Shiru yai baice komai ba sai dai yana jinta, tadan sake ajiyar zuciya kadan.
Muryarsa taji yace "baki taba tambayata dan uwana ba, bayan duk wanda yaji sunana Hassan ya tabbatar inada Husain."
Juyowa tai ta kwanta akan tafukan hannayenta ta jiyo ta saitinshi, duk da duhu ya sa bata ganinshi tace "taya zan tambayeka abinda ka kasa fadama kowa?"
Shiru yai dan harta dauka bazaice komai ba sai taji yace " shekararsa 10 kenan da rasuwa."
Zatai magana taji yace "tare suka rasu da dan kanin Abba, Sudais wanda yazo gidannan karatu."
Jalila yanzuma hartace "sh........"
Ya kara katseta yace "karkice komai kijini kawai."
Shiru tai tana kallangun da yake.
Yace " karki kunna fitila."
Tai shiru, tare da kallansa, Hassan yana kwance yace "they died because of me......"
Ya fada tare da runtse idanunsa da karfi yana jin wani abu na tokare mai zuciya.
Wasu zafaffan hawaye ne suka zubomai, yace "He is a bright person, mutum ne mai tsananin hakuri, a koda yaushe cikin fara'a yake Jalila..........."
Nauyin da zuciyarsa taci gaba dayi, ga numfashinsa na seizing ne yasa yai shiru, saukowa tai da sauri har tana buge kafa ta matso kusa dashi.
Tace "yaya!"
Ta dauka abin ne ya tashi.
Jinta a kusa dashi ne yasa yasa hannunsa dan jin a inda take, a durkushe a kusa dashi ya jita.
Hannunta ya riko sannan ya kwantar da kansa akan kafafunta dake a durkushe.
Da sauri ta kalleshi.
Hannunta ya riko.
Kallansa tai zuciyarta na bugawa da sauri, a hankali tace "karka cigaba yaya inhar zuciyarka bazata iya dauka ba, sannan bansan menene yafaru tsakaninku ba amma na tabbatar ba............"
Yanzu ma katseta ya sakeyi, yace "don't comfort me."
Shiru tai, yace " nikaina bansan meyasa nakesan fadamiki abinda ban fadama kowa a duniya ba, sai dai ina alakanta hakan da zaman da nai dake sannan da yanda nasan komai naki."
A hankali ya lumshe ido zuciyarsa na kunna, yace "later....."
Kai ta daga tace " later Yaya.... sanda kaji zaka iya."
Kansa ya kara gyarawa, shiru tai sai jikinta dayai sanyi, zuciyarta na bugawa da sauri.
Ya dade a haka kusan minti ashirin kafin yaji an fara kiraye kirayen sallah, ita ta dauka ma bacci ne ya daukeshi, ga kafarta ta fara zafi.
A hankali ya dagata sannan ya mike ya kunna wutar dakin.
Haske ne ya baibaiye dakin, kallan juna sukai, ya dauke kai ya shiga toilet.
Yana shiga ya kalli kansa a madubi, yanzu kam ya tabbatar ya fara san yarinyar nan, garin yaya? How can i??? Ya furzar da wata iska.
A inda ya barta anan ya ganta, ya kalleta yace "me kike anan?"
Da sauri ta mike ta fara ninke bargo tace "bakomai."
Kallan fuskarsa tai, tanaso taga canji a tattare dashi, kallanta yai yace "kallan fa namenene?"
Ta mike rike da bargo tace "bakomai, ba kai na kalla ba."
Yace "then?"
"Uhmm yauwa toilet na kalla."
Sallaya ya shimfida batare da ya kalleta ba, ta mike da sauri ta shiga toilet.
Tana rufe kofar tai ajiyar zuciya tace "meke damun yaya? Ya tone din maganarsa ta koma ta da?"
Shima tana shiga toilet ya kalli kofar toilet din sannan yai ajiyar zuciya shima, ya tadda sallah.
[12/7, 9:54 PM] El-hajj: *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔️ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*51*
Kallanta yai yace "bazaki shiga ba?"
Juyawa tai ta shiga dakin, ta ajiye tiren sannan ta kalleshi tace "Yaya abinci."
Bai kalleta ba yace "sai nayi wanka."
Ya fada tare da nufa ciki,, da kallo ta bishi tana mamakin halayensa.
Harta bude zata zuba sai kuma ta maida murfin kular ta rufe.
Hannu tasa ta janyo littafin da yake karantawa ta dauko, ta bude cikin littafin.
Ajiye littafintai sannan ta kalli hanyar toilet, ta mike ta fito falo.
Tv ta kunna tai shiru tana tunanin abinda ya faru tsakaninsu a daren jiya.
Kalamansa na kara dawo mata, meya faru a can baya? Wanda yake hanashi bacci? Yake hanashi shiga mutane? Yake hanashi murmushi? Yake hanashi zama cikin yan uwansa?
Shiru tai tana tunani, da alama shima yanada painful past wanda yafi nata.
Yana fitowa daga wanka ya shirya, ganin bata dakin ga motsin karar TV a falon yasa yasan tana can, sai dai bazai iya kiranta ba.
Zama yai akan kujera yana kallan kofa yana jiran shigowarta, dan yunwa yakeji.
Jalila kuwa ta shiga tunani sai can ta dawo daga tunanin nata, ta mike ta bude kofar, a zaune taganshi tana shiga suna hada ido, yana kallanta yai saurin dauke kai.
Ta shigo ciki tace "Yaya ka fito shine ba magana?"
Bai kalleta ba yace "inyi magana ince me?"
Ta kalleshi tace "kacemin ka fito in taso."
Ya kalleta yace "gashinan ai ban kiraki ba kin taso."
Tace "lalai yaya, to bari nakoma sai ka kirani." Tai maganar cikin zolaya.
Yace "nidai kafin ki koma bani abinci naci inyaso sai ki koma."
Ta kalleshi tadan canza fuska tace "ba kara ma kenan? Bari na fadama Ummy to nace kace ba sai naci abinci ba."
Baisan sanda ya dan murmusa ba yace "yaushe kika koma haka?"
Matsowa tai tace "yaya wlh yanzu bakinka ya motsa, wallahi yau na gani sosai."
Tsuke fuska yai yace "yau menene ruwanku da dariyata?"
Tace "ni kuwa nake da ruwa yaya, bakasan yanda abin ke damuna ba, kome fa zakace fuskarnan a tsuke kake fada."
Kallanta yai yace "bakyaso?"
Ta daga kai da sauri tace "sosai ma, wani sa'in in tone din maganarka ya koma cold sai jikina yai sanyi."
Kalaman Ummy ya tuno data fadamai dazu, kallanta yai yace "magana zaki tsaya yi bazakiban abinci ba?"
Ta dan turo baki ta nufi inda ta ajiye abincin, a ranta tana cewa what am I expecting?
Zubamai tai tace "ka sauko."
Yace "yanzun ma kin manta da plate din ne? Dan muci tare?"
Cikin shagwaba tace "yaya Allah fa ba haka bane."
Yace "shagwaba kika koma?"
Ta kalleshi tace "yaya wai meyasa kakemin haka?"
"Menai?"
Ta kalleshi kamar zatai magana sai kuma tai shiru, a ranta tace "rannan kamin kiss bance komai ba, jiya ka kwanta a cinyata bance komai ba amma kai komai nai sai ka fassara."
Mikewa taga yayi ya wuceta ya zauna a inda ta zubamai abincin.
Kallanta yai tana tsaye hannu yasa ya jawota, ta zauna a kusa dashi.
Kallansa tai tana mamaki tace "Yaya!"
Yace "wai ni yaushe nake yayanki ne? Kin kama suna kin rike kamar ke kika samin?"
Baki tadan turo sannan ta zuba abinci a nata plate din, gani tai yasa spoon dinshi cikin plate dinta.
Da sauri ta kalleshi yace "ba haka kikeso ba?"
Tace " bangane ba....?
Bai kara mata magana ba yacigaba da ci, kallansa ta tsaya yi tama kasa ci, sai can ya kalleta yace "kin koshi ne?"
Spoon din ta maida ciki ta cigaba daci ta mamakin wannan abu.
Yana gamawa ya dau key ya bar dakin baice mata komai ba, baki ta saki tana kallan ikon Allah.
Saukowa yai kasa ba kowa a falon, yai hanyar waje.
Mota ya shiga kawai ya fita, Jalila ta dade a zaune kafin ta kwaso kwanuka ta fito.
Ganin bakowa a falon ta wuce kitchen ta wanke kwanukan, tasan Ameera na skul, da alama Ummy na daki.
Sageer fa? Bude kofar daki taji da sauri ta kalli gun.
Sageer ne ya fito sanye da kaya da hula da alama fita zaiyi.
Kallanshi tai shima ya kalleta, da sauri ta dauke kai ta juya zata koma kitchen.
Yace "Jalila?"
Tsayawa tai a inda take sannan ta juyo ta kalleshi.
Ya matso inda take kadan ya kalleta yace "ina making dinki uncomfortable ko?"
Kallansa tai ta girgiza kai alamar a'a sannan tace "a'a
Yai murmushi yace "kiyi hakuri Jalila."
Tace "Uncle sai yaushe ne zaka daina bani hakuri? Bazance ban taba jin zafin abinda ya faru ba, dan da naji zafinka sosai sai dai a yanzu ko kadan banajin zafin ka, na fahimceka, nasan dalilinka."
Kallanta yai yace "nagode Jalila, nagode da fahimtar da kikamin."
Ta kalleshi tace "Ummy tace duk ka canza, ni kaina nasan ba haka kake ba, Allah yasa banice sillar canzawarka ba."
Ido ya kura mata kafin yace "ko kadan Jalila, inma akwai dalili to bazai wuce zuciyata ba wanda kuma basai kin damu da ita ba, zata daina da kanta."
Kallansa tai tace "Uncle!"
Yace "kidinga cemin Sageer kawai, hakan shine daidai a matsayinki na matar yayana."
Shiru tai kafin tace "saidai na kiraka da Yaya sageer yanda Ameera ke cewa."
Yace "hakan yayi, nagode Jalila sannan Please let us take it to our grave, kar kowa yasan abinda ya faru."
Zatai magana sukaji muryar Ummy tana cewa "Sageer fita zakai?"
Da sauri ya juya dan baiji karar kofa ba, Jalila ma ta kalleta.
Ummy ta kalleshi tace "menene?"
Yace ba komai, na fito ne banganki ba nake tambayar matar Yaya.
Tace "ina ciki ina addu'oi.
Yace "Ummy zanje gun Abban."
Tace "to Allah ya bada sa'a."
Yace "Ameen ya fita."
Ummy ta kalli Jalila tace "Jalila!"
Jalila ta matso tana cewa " Ummy nikam banga Ameera ba."
Ummy tace "sun koma skul yau dama hutu ya kare."
Tace "oh shiyasa, naji gidan shiru."
Ummy tai dariya tace "wlh kuwa, Jalila gidan namu is so boring."
Jalila tai dariya itama tace "muma haka gidan yake, Sultan kullum yana daki yana game ko jin kida, Safeena kuma tana gun Mumy ko suna kallo ita da Yasmeen, Inna na sama, Mumy kuma itama ko tana falo ko daki, dama gun Goggo nane muke zama muyi ta hirarmu."
Ummy tace "sanda kowa yake zama, bacci da kallo ke me kikeyi?"
Tace "aiki, girki, ko wanki."
Ummy tace "hmm da alama ya kamata ki kara samun hutu a gidan nan, yanda kikai aiki acan ba hutu yanzu duk sai ki fanshe hutunki gun mijinki."
Jalila tai dariya tace "ai nan gidan ba aiki Ummy."
Tace "ba wani nan, ina mijin naki?"
Cikin kunya ta girgiza kai.
Ummy tai ajiyar zuciya tace "Haryanzu baice miki zai fita?"
Tace "eh, yanzu ma fa....."
Sai kuma tai shiru tare da sa dariya.
Ummy ma tai dariya tace "Jalila bansan ke ba amma i am sure Hassan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 38