fuska yana kallansu yace " wato dai kune masu kula dani ko? Sai a fadamin wanene ma ya samar daku?"
Hassan ya kalli Sageer, da sauri Sageer ya juya kai yace "Abba na manta inada appointment" dariya suka saka a tare hardashi Abban, Abba yace "amma yanzu ai bazata sake dawowa ba ko? Sageer yace "inta dawoma tana da mai maganinta....
Suka kara yin dariya.....
Abba yace kuyi alwala muje masallaci sallar la'asar tare.
Hassan ya kalleshi, Abba yace "let us try kaji?"
Ya daga kai alamar to.
Haka suka yi alwala suka zauna a office din Abba macema Sageer ya daure ya fara aiki anan, Hassan na taya Abba har la'asar ta karasa, Abba ya kalli Hassan yace "muje?"
Atare suka fito su uku abin sha'awa, basuga motar Zaliha ba agun da alama ta bar gun.
Masallacin suka nufa, tsayawa yai yana kallan yanda mutane ke ta shiga ciki, ya kalli Abba.
Abba yasa hannu ya riko hannunsa sannan ya riko hannun Sageer yace "gamunan mu uku, ka cire komai a ranka kawai kasa a ranka gun bautawa Allah zaka, sannan gamu a kusa dakai."
Hassan yai murmushi suka nufi masallacin, daurewa kawai yake dan zuciyarsa sai bugawa take da sauri da sauri.
A bakin kofar suka tsaya sukai addu'a sannan suka shiga.
Haka suka shiga, suna shiga ciki suka hau jam'i a tsakiya suka sakashi, liman yaja sallah.
Suna idarwa Abba ya kalleshi, wasu zafaffan kwalla ne suka shiga neman zubomai a lokacin daya daga hannu yana rokon Allah, yaushe rabo? Addu'a ya shiga yi har bai san sanda hawaye ya zubo mai ba.
Sageer ma sai daya zubo da kwalla saboda tsananin tausayi.
Ya dade yanata addu'oi kafin su fito, dan sukan shi suka tsaya jira, dukansu sai tausayinsa yakeyi.
^**********
Dady ne ya kalli kofar gidan, kwanansa biyu kenan yana zuwa yana komawa dan shifa gaskiya ya kasa sa kafa cikin gidan, ko dai wayau zaiyi ya fara zuwa gidan da Goggo take? Ita yasan mai sauki ce inyaso sai tazo nan da kanta ta basu hakuri.....
Juyawa yai da motar kamar zai koma sai ga motarsu Abba.
Kallansu yai sun shiga ciki, sun hada ido da Hassan amma sai ya dauke kai, da kallan takaici ya bishi yace "wannan dan iskan yaran....."
Suna shiga shima ya shiga da motarsa.
Su Abba na fitowa shima ya fito da sauri yace "Ranka ya dade!"
Abba ya juyo ya kalleshi, murmushi yai yace "Ah Alhaji kai ne?"
Dady ya matso yana kallan Sageer da Hassan da sukai kamar basu ganshi ba.
Hassan ya kalleshi bayan ya karaso yace "Ina wuni?"
Dady ya washe baki yace "Hassan an wuni lafiya?"
Hassan yace "lafiya."
Ya wuce ciki, Sageer ma yace "Ina Wuni?"
Nan ma yace "malam Sageer ko?"
Sageer yace "eh."
Ciki yai Abba yace "bismillah!"
Nan suka shiga ciki...........
Falonsa ya kaishi ya zauna sai wani washe baki yakeyi, yana cewa "wlh na dade inasan nazo."
Abba ya kalleshi baice komai ba.....
Shiru sukai dan Abba kam shikanshi haushinshi yakeji, ai koda laifin su Inna da Mumy to tabbas laifinsa yafi yawa, dan a matsayin sa na uba, miji abinda ya aikata shi kansa yayi alawadar dashi, tun ma daga auran mahaifiyar Jalila zuwa zaman da sukai......
Dady ya kalli Abba jiki a sanyaye yace "Ranka ya dade nace........"
Abba ya kalleshi, Dady yanda yaga ya kalleshi ya daure yadanyi shiru......
**********
Hassan na shiga ya kalli kitchen, Ameera ce ta fito rike da kofi tana shan abu, tana ganinshi ta matso tace "Yaya."
Kallanta yai yace "baki tafi islamiya ba?"
Tace "ai yau alhamis."
Yace "okay."
Ya wuce sama, da sauri ta koma kitchen ta taba Jalila tace "Aunty mai sanyin ya dawo...."
Jalila ta juyo ta taka kafarta, Ameera ta saki yar kara Jalila tace "bari na fadamai wai mai sanyi."
Ameera tace "wayyo Allah na ki rufamun asiri."
Jalila tana dariya ta fito, da sauri ta hau sama tana murmushi, ina yaje dazu?
Tana shiga ta taraddashi yana cire kaya, da sauri ta juya baya tana cewa "yaya ashe ka dawo."
Yana cire kayan amma kallanta yakeyi, yace "nemana kike?"
Juyowa tai ta manta sam da abinda yakeyi tace " naga......."
Ganin ya cire rigar tasa gaba daya tai sauri sake juyawa, murmushi yai yana kallanta, Jalila menene tsakaninki da Sageer? Me ya faru a baya? Anya ya dace nama Sageer haka?
Tambayoyin da yakeji kamar ya yimata kenan, ta juyo ita kuka da sauri tace "Yaya kasan me?"
Kallanta yai, ta kara kallan jikinsa da sauri ta sa hannu ta rufe fuskarta.
Murmushi yai sannan yace "ki hadiye maganarku tunda kunyata kikeyi, in kuma so kike in matso to."
Tace "ka matso ina?"
Takowa yai yazo inda take, idanu ta bude da sauri, ya sa hannu ya lankayo cikinta yace " haka kikeso?"
Idanu ta zaro tana kallansa tace "yaya wlh ni......."
Shiru yai yanayin fuskarsa ne ya dan canza, murmushi yai sannan ya saketa yace "Mahaifinki fa yazo."
Tace "yaushe?"
Yace " yanzu ya shigo, da alama yazo ganin yar sa ne."
Tace "hmm yadai zo abinda yazo yi, ko an turoshi."
Hassan ya kalleta kamar zaiyi magana sai ya fasa, cikin toilet ya shiga ya rifo kofar.
Da kallo ta bishi tare da yin ajiyar zuciya.....
Itakam batasan ya akai take tsananin san ganinta da Hassan haka ba, lalai yanzu ta fahimci kaunarshi ta fara yin nisa a ranta.
Dolene ta je gun Goggo ta fada mata dan itakam yanzu tanajin Hassan har ranta...........
#OneLuvđź’•
[12/7, 10:12 PM] El-hajj: *_đź—ŻJALILAH!!đź—Ż_*
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_đź’ˇ)
_Wannan shafin sadaukarwa ce gareku yan Sparkling Son Soriansđź’– ina godiya da kaunar da kukema min da littafin nanđź’•Luv u all....._
*60*
Juyowa tai ta fito daga dakin fuskarta dauke da murmushi.
Shikuwa Hassan a toilet ruwa mai dumi ya sakar ma kansa yana ta zuba a jikinsa, Jalilah! Sageer! Wani irin so Sageer yakema JalilahA? Wani irin so Jalila takema Sageer? Abinda yaketamai yawo kenan a kwakwalwar kansa, duk yanda ruwan ke zuba a jikinshi baiyi tunanin lafiyarsa Wba.
I jm. J
Ya dade a haka kafin ya saba jikinsa ya fito, ya zura doguwar riga jallabiya ya zauna akan kujera yana tunane tunane.
Jalia kam tana sauka Ummy ta fito daga falon cxAbban nc, kallanta tai tace “kun gaisa Wn
Tace “da wa?”
Ummy tace “mahaifin.......”
Yanayin fuskarta ne ya canza wanda yasa Ummy kallanta tace “ki shiga yana ciki.” Jalila tace to sannan ta nufi ciki.
Abba kuwa a falo ya hade fuska yana sauraren Dady dakemai zancen banza, ya cika yayi fam.
Dady kuwa tsabar hauka baima kula ba ya dauka fahimtarsa Abba yakeyi.
Ya kara kallan Abba yace “ gaba daya haka rayuwata take a cikin wannan gidan nasu, komai sai abinda suka tsara, basu dauke da girma ba duk kuwa da nine mahaifin yaran.”
Ya kara neman marairaicewa zai kara wani rainin hankalin Ummy ta shigo falon dauke da ruwa da juice.
Wannan dalilin ne yasa ta yin shiru, tana kallan yanayin Abba ta fahimci baya jin dadin hirar, sai tai sa’a kuwa tana fitowa sai ga Jalila.
Dady ya kalleshi ya sake marairaicewa yace “a koda yaushe sai sun yanke hukunci nake sani, sannan ban isa na kawo nawa uzurin........”
Sallamar Jalila ce ta katseshi, haushi ya kara kamashi.
Abba kam yana ganin Jalila ya mike tsaye yace “bari na barku ku tattauna.
Dady ya mike da sauri yana cewa “Danka ya dade......”
Ai Abba bai jira cigabansa ba yai waje, yana fita yaja wani dogon tsaki ya kalli Ummy yace “wlh dabadan mahaifin Jalila bane da wlh mutumun nan...” sai kuma yai kwafa.
Ummy tai daria tace “ni ina kallanka nasan ha labari.”
Ya kalli kofar yace “mutum na kara banzatar da kansa da wulakanta kansa saboda abin duniya?
Dady kallan Jalila yai bayan ta shigo ta tsugunnadaga can bakin kofa.
Yace “Jalila! Ya da zama daga nan? Nine fa mahaifinki, yanzu in wani ya shigo ya ganmu ai dauka zaiyi wani abin nake miki, taso dan Allah.”
Kallan mamaki tamai, sannan ta mike ta taso, zaka tai daga gefensa kadan matso da jikinsa inda take, yace “Jalilah!”
Dagowa tai ta kalleshi sannan ta gaisheshi, ya amsa fuska a sake kamar wanda akayima wani gagarumin albishir, Dady ya kara sakin fuska yace “ya jikin Goggon taki?”
Kallansa ta sakeyi tace “da sauki.”
Yace “Jalilah!”
Ta kalleshi sai dai fuskarta ba a sake ba, tace “naam”
Yace “Jalila ni mahaifinki ne wanda nine na haifeki, nafi kowa sanin zafinki da darajarki, koda duk mutanen duniya zasu kike wallahi ni bazan taba gudarki ba.”
Jalila batasan sanda ta juyo ta kalleshi ba cikin mamaki take kallansa.
Dady yace “ki dainamin kallan tantama sai dai nidin da gaske nine na haifeki, jinin jikinki daga jikina yake, amma nikam Jalilah kinji wani abu na harkar company dinmu a nan gidan?”
Yanzu kam zargin da take ta gama tabbatarma kanta, ta daure tace “kamar name kenan?”
Dady ko kunya yace “ dama inata tunani ne ko da yanda za’ai tunda dai yanzu kudin sirikanki ne gaba daya yanzu yake tafiya da company din me zai hana ki taimaka ki sanar dasu a bani company din, ni nafi kowa sanin darajarsa, lokacin kankani zan maida musu kudin su, na tabbatar bazan taba basu kunya ba.”
Jalila kallan mamaki kawai takemai, baijira tama kaiwa kwakwalwarta amsar da zata fadamai ba taji yace “Jalila har zuciyata banasan rabuwa da mahaifiyarki, in har suka takura sai na bar musu gidan kawai, muzo muyi rayuwarmu daga ni sai mahaifiyarki, sai ke inkinzo.”
Jalila yanzu kam ta kai matuka gun tunzura wato itace kuka mai dadin hawa kenan itada mahaifiyarta, shiyasa yazo mata da wannan zancen?
Ta kalleshi ta tuno kalaman Hassan tace “Dama ko da wasa nasan wallahi Dady bazaka taba zuwa saboda ni ba, ko goggo.”
Ya kalleta yace “bangane ba?”
Tace “yanzu Dady wani mahaifine zaiyiwa matarsa haka? Wani mahaifine zai nemi saida yar sa amma daga baya ya dawo ya nemi kara saida nasa mutunci?”
Cikin tsananin bacin rai yace “Jalilah? Bakida hankali? Ni kike..........” sai kuma ya canza tone din maganarsa yace “Nine na haifeki ba wani ba, nine jininki.”
Hawaye ne ya zubo mata tace “jini? Dady sai yanzu kasan jini? Sanda ni da mahaifiyata muke kuntata muke neman tallafinka, Dady kana ina? Kana ina lokacin da.........”
Hawayene yacikarfinta, ta kasa karasawa, Dady ya turzuko yace “bakin ciki kikemin? Bakin ciki kikeyi zaki taimakeni?”
Jalila ta kalleshi cikin takaici tace “bakin ciki kamar ya?”
Yace “inba bakin ciki ki...........”
Bakin ciki take maka, ko dole ne dan ka haifeta sai ya zama dolene duk wani abu daka zarta mata sai ta bishi?”
Juyowa yai da sauri, saboda muryar dayaji, a tsorace ya mike tsaye ya kalleshi.
Hassan wanda har ya zauna yai tunanin kamar ya dace yazo ya gaida shi, yana tsaye Dady ya fara mata zancen karshe da amsar data bashi, dan dama yana fitowa daga wanka riga ya zura kawai ya sauko.
Dady ya kalleshi yace “Hassan ba.......”
Hassan yai saurin cewa “bansan me ka ke nema a gunta ba, na dauka bayan neman saida ita dakai bakada idan neman wani abu daga gunta, amma yanzu na gane duk ba haka bane, tun farko zuciyarka dama ba komai a ciki sai tsantsar san kai, in ba kanka ba banaji akwai abinda kakeso a ciki.”
Dady ya fara kokarin yin magana, Hassan ya matso ya kama hannun Jalila yabar falon da ita.
Dady ya tsaya sakato, cikin kunar rai.
Hassan kam janta kawau yakeyi, ya matse mata hannu har sai da suka shiga daki, ransa ya gama baci ya kalleta yace “sau nawa zance ki zama mai confidence?”
Kanta ta karkatar tana kallansa, a hankali ta saki murmushi tare dacewa “ Kasan dazu harda hawaye na? Amma kana zuwa falon naji sun dauke.”
Kallanta ya sakeyi fuskarsa a hade yace “ ina tambayarki abu daban kina ban wata amsar.”
Tace “Yaya, me yasa inkaga ana wulakantani baka iyayin shirun? Ko wanene kuwa?”
Kallanta yai kamar zaiyi magana sai ya saketa, juyawa yai zai fita ma daga dakin.
Da sauri ta riko hannunsa daya saketa dashi, tsayawa yai sai dai bai juyoba tace “Yaya.”
Juyowa yai yanzu ya kalleta idanunsa sunyi jaa, Jalila ya zanyi da kaunarki? Menene tsakaninki da Sageer?
Kallansa tai tace “me kake tunani?”
Kallanta yai sannan ya girgiza kansa alamar a’a, zame hannunsa yai ya juya ciki me makon ya fita, jitai yace “yau munje masallaci da Abba.”
Cikin tsananin zumudi ta matso kusa dashi, shi kuma baisani ba ya juyo tare da takowa, bugar kirjinsa tai tsayawa sukai a haka, a hankali ta dago ta kalleshi, idanunta sun canza.
Shima kallanta yai cikin wani yanayi, murmushi ta sakar mai sannan tace “dan Allah? Tayaya?”
Idanu kawai ya kura mata kafin yace “tare da Abba da Sageer.”
Cikin jin dadi batasan sanda tasa hannu ta zagayo dashi ta cikinsa ba ta rungumeshi, tace “naji dadi yaya Alhamdulila.”
Wani abu ne ya shiga ratsashi kafin yace “Jalilah?”
Yanda ya kira sunan nata ne yasa gabanta faduwa.
yace “menene ya faru tsakaninki da Sageer a baya?”
Gabanta ne ya fadi da sauri ta sakeshi tare da kallansa, zuciyarta na bugawa da sauri da sauri.
Tace “naam?”
Kallanta yai yana shirin yin magana...........
Www—
#OneLuvđź’•
[12/7, 10:12 PM] El-hajj: *_đź—ŻJALILAH!!đź—Ż_*
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_đź’ˇ)
_Ga taku na musamman 'yan JALILAH NOVEL, D QUEEN BEE & AYUSHER FANS CLUB._
_Wannan shafin sadaukarwace gareku gaba daya, ina godiya sosai da kaunađź’•OneLuv_
*61*
Kallansa tai cikin tsananin tsoro idanunta suka firfito cikin tsananin mamaki, daurewa tai tace "Yaya......."
Kallanta yai bakinsa na san magana amma ya kasa, idanu kawai ya kura mata, sai dai shikam a gunsa yaga rashin gaskiya karara a bayanne a fuskarta, murmushi yai wanda gaba daya inka shakeshi bazai ce ya iya irinshi ba, sannan bazaice ma yasan manufarsa ba.
Juyawa yai kawai ya koma hanyar waje, Jalila kam gaba daya ta kasa furta komai, saboda tambayar tazo mata a ba zata, sannan bata taba tunanin zai mata irinta ba.
Kallan kofar tai wacce ya rufota, saukowa kasa yai Ummy na kokarin yimai magana taga ya fita da sauri, ina zaije da magrib din nan?
Jalila kam tafi minti goma sha biyar a tsaye ta kasa motsawa daga gun, kafin haushin kanta ya kamata. Me yasa batace mai komai ba? To me zatace? Da munyi soyayya amma aka kwaceni daga gunshi akamin auran dole?
To me zata ce? Hanyar kofa ta nufa da sauri ta fito daga dakin, saukowa kasa tai da sauri, sai dai baya kasa.
Fitowa waje tai nan ma bataga motarsa ba, jiki a sanyaye ta kalli inda yake ajiye mota, sannan ta juyo ciki.
Ameera ce wace ke rike da cup da spoon tana juya cornflakes din data hado ta kalleta tace "Matar Yaya daga ina?"
Jalila ta kalleta tare da yimata yake kawai ta nemi hanyar sama, Ummy ce tace "Jalila?"
Juyowa tai ta kalli Ummy wace itama take fitowa daga kitchen tace "ashe Mahaifinki ya tafi?ai bansani ba."
Jalila tace "nima bansan ya tafiba Ummy."
Kallan mamaki ta mata "wani abun ya faru ne? Naga Hassan ma ya fita."
Jalila tace "bakomai Ummy."
Ummy ta kalli Ameera tace "in zakici abu ki zauna banasan cin abincin nan naki a tsaye."
Ameera ta koma ta zauna, Jalila kuwa tahau sama.
Ummy ta bita da kallo tare da fatan Allah yasa ba wani abun bane.
Jalila kuwa tana komawa ta zauna a falo tana jiransa, ganin ta kasa zaman yasa ta dauko wayarta ta sauko da sauri, dakin Ameera ta shiga.
Ameera wacce shigowarta kenan tana kokarin yin alwala ta kalleta tace "Yaya Jalila lafiya?"
Jalila ta matso ta dau wayar Ameera ta mika mata, Ameera cikin mamaki take kallanta, Jalila tace dan kira Yayanki.
Cikin mamaki Ameera tace "ni? In kirashi ince mai me?"
Jalila tace "ki dai ki kirashi."
Ameera ta amsa tana cewa "yaji yayi ne?"
Jalila tace "abinda yafi yaji ne. Tunda kin taba gani namiji da gidansa yayi yaji."
Ameera tai dariya tana dialing tace "kece dai baki taba gani ba amma yanzu maza ma yi suke."
Jalila ta harareta tace "wallahi Ameera nikam kina ban mamaki, bansan a ina kika san komai haka ba, yarinya kafin ki tafasa kina neman konewa."
Ameera tai dariya tace "nasan komai wlh, pratical ne......."
Jin alamun kamar an dauka yasa tai gum tare da cewa "hello!" Ta fada tana kallan Jalila.
Jin ba magana yasa ta kalleta, sannan ta kalli wayar.
Cikin mamaki tace "banaji."
Jalila tai shiru kafin ta amshi wayar tasa a kunnenta, tace "Hello!"
Tana magana aka kashe wayar, kallan Ameera tai ta amshi wayar ta sa number ta juya ta fita.
Ameera na san magana amma ba dama, saboda ta fahimci sabani suka dan samu.
Jalila na fitowa ta koma sama ta zauna a bakin gado rike da waya a hannu.
Ta zarfafa cikin tunani taji wayarta na kara, da sauri ta dauka ko kallan mai number batai ba tai sallama.
Goggo tace "Jalila!"
Cikin mamaki ta kalli number sannan tace "Goggo? Number wanene?"
Goggo tace "tawa ce, yanzun nan aka aikon da ita."
Tace "wane?"
Tace "ai ke zan tambaya,tunda haka akacemin gashi daga Jalilah, na dauka ma number ce baki sani ba."
Jalila tace "bansani ba wlh,amma nasan bai wuce inji Ummy."
Tace "kila to, ya gidan naku?"
Tace "lafiya kalau inatasan nima nazo."
Goggo tace "a'a banasan yawon zuwan nan ba dadi, ke dai ki zauna a gidanki cikin iyalanki, ni muna zaune da Lantana lafiya anan, komai muna dashi, a koda yaushe sai dai in muku addu'a dake da mutanen nan na arziki."
Jalila tai murmushi sanda ta tuno Hassan a ranta tace Goggo ina cikin wani hali.
Amma a fili tace "to Goggona."
Nan sukai yar fira kadan kafin suyi sallama, Kara kallan wayar tai tana tunani, idanunta ta rufe sannan ta mike tai alwalar magrib tai sallah ta kara dauko wayarta, yanzu kam kiranshi tai sai dai bai dauka ba harta katse.
Shi kuwa Hassan tunda ya fita yake tafiya a mota, yayi tafiya mai tsawo kafin ya ja gefen titi yai parking? Kansa ya kwantar akan kujera ya rufe idanunsa, da wani irin zama zasuyi? Ya tabbatar akan wata alaka a tsakaninsu mai karfi, yanda ta razana, idanunta ta ya tuno da yanayin da ta shiga a lokacin, kenan har yanzu tanasan Sageer?
Idanunsa ya runtse cikin wani irin hali, yana ganin kiranta bai dauka ba har ta gaji ta daina.
Ummy daga kasa taga ba Jalila gashi har lokacin cin abincin dare yayi, Ameera ta aiko akan ta kirata, lokacin tana kwance akan sallaya, Ameera ta turo kofa tana lekowa tare dayin sallama a hankali, Jalila ta kalleta tana ganin ita kadaice ta shigo.
Ameera tace "ki sauko muci abinci, yaya fa?"
Jalila tace "nakoshi, sai dai bari sauko na daukomai nashi."
Ameera tace "kinsan sai dana bude kofar na shiga tunanin in yaya na nan fa?"
Hmm kawai Jalilah tace batace komai ba, ta mike suka sauko w AUmmy tace "bai dawo ba?"
Tace "eh Ummy inaji ya tsaya a wani gun ne bari na daukar mai."
Ummy ta dauka su biyun take nufi, shiyasa batace komai ba.
Kitchen ta shiga ta zuba mai sannan ta dau tiren ta fito, tana shigowa falon Sageer da Ameera na fitowa daga daki, da alama kiransa taje yi.
Gaisheshi kawai tai ta wuce sama tareda yima Ummy sai da safe.
Ta hau sama, abincin kawai ta ajiye tai sallar isha'i sannan ta dauko qur'ani inda ya koya mata jiya ta biya sannan ta dawo farko, ta dade tanayi kafin ta rufe qur'anin tadan kishingida tai akan sallaya, bacci ne ya dauketa.
Sai can wajen karfe 11 ya dawo, yana shiga ya shiga toilet ya fito ya kwanta.
Juyi ya shiga yi, hankalinsa bai kwanta da kwanciyar datai a kasa ba, gashi ba bargo, duk yanda yaso yai bacci ya kasa.
Mikewa kawai yai yadau bargo ya rufa mata ya koma ya kwanta.
Da asuba yana sallah yau ko karatun bai koya mata ba taga ya juya ya kwanta.
Dama tashin ma sai data farka taganshi kawai yana sallah.
Tace "Yaya ba....."
Yanda ya kwanta yasata yin shiru dan bashida alamar sauraranta.
Tama rasa me zatace, haka ta gaji ta kwanta.
Tana tashi taga baya dakin.
Gaba daya hankalinta ya kara tashi, ta fito falo ta zauna idanunta suka ciciko, batasan ta damu da Hassan ba kamar yanzu, gaba daya kin kulatan dayai na kwana dayan nan jitake kamar tayi hauka, me yasa Yaya bazai bari tayi magana ba?
Shikam gaba daya bayasan yaji wani abu daga gunta, tsoro yake kar tacemai Sageer takeso ba shiba, dan bayaji zuciyarsa zata dauki wannan hukuncin, a yanzu bayaji zai iya rayuwa ba Jalilah, to in itama bazata iya rayuwa ba Sageer bafa? Ko shi yace bazai iya rayuwa ba ita fa? Wannan dalili yasa yake tsoron jin abinda zai fito daga bakinta.
Wajen karfe 8 ta farka, da sauri ta bude dakin sai dai ba shi ba alamarsa, abincin daren ta kalla, ta bude kulolin, gaba daya ba alamar ma ya bude shi.
Kawai zama tai a kasa tasa kanta a cikin cinyoyinta, samun kanta kawai da sa kuka, yanzu inyace yabarma Sageer ita fa? Dan ta kula gaba daya ba wanda yake damuwa da ra'ayinta dukansu tunanin junansu kawai sukeyi.
Haka ta sauko da abincin, tai sa'a Ummy ma sun fita da Abba, tana fitowa Sageer ya sanar da ita, Ummy ta riga hartayi abincin safe, komawa tai sama kawai ta kwanta dan bazata ma iya cin abincin ba, tai wanka tasa atamfa riga da skirt kawai ta murza mai da turare ta kwanta.
Wayarta na hannunta jefi jefi tana kokarin kiran Hassan.
Sai wajen rana ta sauko tai abinci kawai tasa a kula ta koma sama.
Yauma bai dawo ba sai data kwanta barci, ya dade a tsaye yana kallanta, sannan ya kalli abincinsa data ajiye masa, zuciyarsa na tsoron jin labarin nan, jiyake bazata iya daukan abinda zata ji ba.
Bargo ya dauka kamar jiya ya luluba mata, sannan ya kashe wutar dakin ya taho kamar zai wuceta sai kuma ya dauko pillow yazo yadagata ya sa mata sannan ya mike zai tashi.
Hannu tasa da sauri dan taji alamunsa ta rikoshi, idanu ta bude da sauri.
Kallanta yai sannan yace "ba bacci kike ba?"
Tace "bacci nake yanzu na farka."
Hannunta ya dan zare zai mike, da sauri ta kara rikoshi, bai kalleta ba sai dai ba damar tashi.
Cikin sanyin murya tace " Yaya haka zamu zauna? Kafin na farka ka fita sannan kafin ka dawo nayi bacci?"
Kallanta yai kamar zaiyi magana sai ya fasa, tace "Yaya ka tambayeni dan Allah duk wani abu da kake sanji, ni kuma na baka amsa, wannan abin ba shine mafita ba."
Hannunsa ya zare yamike tsaye, Jalila ta mike tsaye da sauri tare da rungumeshi ta baya.
Tsayawa yai sai dai zuciyarsa na harbawa da sauri da sauri, tace "yaya dan Allah."
Kasa daurewa yai kawai ya juyo ya rungumeta tsam ajikinsa, can yace "Jalila zuciyata ta kasa daukar abinda take zargi, na kasa samun nutsuwa, ina tunanin kamar na tauyekine da abinda kikeso....."
Kai ta shiga girgizawa da sauri da sauri, kafin tace " ko kadan Yaya, bazan musa ma akan da ba amma banda yanzu."
Dagowa yai ya kalleta, yace "Inke hakan ne shi......."
Daga kafarta tai ta kara rungumeshi tace "Yaya......."
Bakinta taji a cikin nashi, wani yanayi ya shiga mata wanda ita kanta batasan sanda ta shiga maidamai ba, jitai kafafuwanta sun kasa daukarta, hannu yasa ya dagata gaba daya ya kaita kan gado, sun dade suna sumbatar juna kafin ya saketa kadan, yana wani irin numfashi yace "Jalilah banaso na zama mai tauye miki hakki........"
A hankali ta lumshe ido hawaye suka taru
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 28 Chapter of 38