lafiyarta gun sata tayi abinda sukeso?"
Goggo ta share hawayenta tace " duk nice suka raina, nice suka maida abin zuba shara, nice basa ganin mutunci, nagode sosai da kaunar da kuka nuna ma yarinyar nan, ko ba'a fada ba na san akwai kulawa mai karfi datake samu a gidannan fiye da gidan da za'a kirashi da sunan gidan mahaifinta."
Abba yai ajiyar zuciya yace "yanzu tunda nasan meke faruwa bazan barsu haka ba."
Ummy ta kalleshi da sauri tace "me zakayi?"
Ya mike cikin takaici yace "don't u understand what's happening? Sun daukemu a matsayin joke ne, kenan sun maidamu fools, duk abinda suka tsara shi muke bi."
Ummy ta kalli Hassan wanda kamar ma baisan abinda ake a falon ba, sannan ta kalli Abba tace " ni kuma ina ganin ka kyalesu kawai."
Abba yace " In mun kyalesu kina tunanin zasuyi dana sani?"
Goggo ta kallesu tace "amma dan Allah inada tambaya, me ka musu ne da harsuke tunanin ko za'a mutu sai sun kawo Jalila cikin gidan nan?"
Sageer ya kalli Abba yace "Abba ni kaina ina wannan tunanin."
Abba ya kalli Ummy yace " kasuwanci......."
Ummy tamai alama dayai shiru, yace " yanzu ke Jalila kiyi hakuri, nasan an shiga hakkinki, sannan an shiga hakkin mahaifiyar data haifeki, kuyi hakuri wannan harda laifin mu."
Goggo da sauri tace "ba laifinku bane, masu laifin daban, zan iya yafe duk wani abu da za'amin ko na wulakanci ko na tozarci amma bazan yafemusu ba akan abinda sukama Jalila, tayaya zasuyi amfani dani wajen ganin sun sata abinda sukeso? Yanzu da ace mugun hannu ta fada fa???? Ta fada cikin raunaniyar murya.
Hassan ya bude idanunsa ya kalli Jalila wacce ke kuka tana zaune kusa da Goggonta.
A hankali ya mike kawai yabi ta bayan kujera yai hanyar waje.
Jalila ta kalleshi, shima kallanta yai sannan ya dauke idanunsa da sauri.
Ummy ta mike tace "Hassan ya akai?"
Yace "bakomai...."
Kawai yai kofa, kallan Abba tai cikin wani yanayi, hannunta ya yadan dafa alamar ba komai.
Sannan ya kalli Goggo wacce gaba daya ita da Jalila tausayi suke bashi, yace "Sageer kai dasu Jalila ku shiga ciki, ni zanyi magana da mahaifiyar Jalila."
Sageer ya mike ya fita, Jalila ta mike ta fito.
Abba ya kalli Goggo yace " garin yaya kika bari aka maidake kamar baiwa? Ko bakida yan uwa ne?"
Tace "inadasu sai dai a matsayin babu suke."
Ummy tace "kamar ya?"
Tace "bayan anmin auren dole da Abakar aka umarceni da karna kara tako garin sai dashi tin daga lokacin ban sake zuwa ba, dan banida darajar da zai kaini."
Ummy tace "kamar ya? Baki sake neman mahaifiyarki da yan uwanki ba?"
Tace "ina zan nemisu bayan umarni mahaifina ya bani....."
Abba yace "wani umarni ne hakan?"
Ummy tai saurin cewa "Auranki fa?" Dan ta fahimci rashin ilimin addini ne ya sa ta dauka biyayya takeyi.
Goggo tace "ban sani ba nima dan rabona dashi tun ranar da aka kaini, lokacin Allah yai dabon Jalila."
A tare sukace "me?"
Goggo tai kasa dakai tana murmushin takaici.
Ummy tace "Goggo muje kici abinci ki kwanta."
Abba ya kalleta cikin mamaki dan akwai tambayoyin da yake san jin amsarsu.
********
Jalila na fitowa ta nufi hanyar sama, Sageer da sauri yace "Jalila!"
Tsayawa tai bata juyo ba tana share kwallarta, Sageer ya matso ya mika mata handkerchief kallansa tai kamar zata karba sai kuma naga ta fasa, kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa tace "nagode." Kawai tace ta juya ta hau saman.
Tsayawa yai yana kallanta cikin tsananin tausayi, har saida tai kwana sannan ya juya zuwa dakinsa, yana shiga ya zauna a bakin gado yana tunani, haka rayuwarta take? Shiyasa ashe ake barinta a makaranta ita kadai? Shiyasa sukasata a government?
*******
Ummy ta taso tazo kusa da ita, suka fita tare, ina saurayin Jalila? Ta tabbatar Jalila.......... tunowa datai a inda tasan Sageer ne yasa ta kalli Ummy da sauri tace "ya sunan mijin Jalila?"
Ummy tace "Hassan!"
Goggo tace "wanda na gani dazu fa?"
Ummy tace "Sageer? Kaninsa ne."
Goggo tace "kaninsa?"
Ummy ta daga kai alamar eh, Goggo a ranta tace "to ko ba shi bane?"
Dakin Ameera ta kaita sannan tace "kici abinci ki kwanta, dan Allah karkiyi tunanin komai, Jalila yanzu 'yatace bazan kara bari wani abu ya sameta ba, sannan mu zamu san abinyi, ke dai ki kwantar da hankalinki ko dan lalurarki."
Goggo ta riko hannun Ummy tace "Nagode, nagode har bansan iya godiyar daya kamata nai miki ba."
Ummy tai murmushi tace "muma mungode, da kika fahimcemu, yanzu sai kisama auransu albarka."
Tace "insha Allah."
Nan ta shiga ciki.....
Ummy ta bita da kallan tausayi.
Jalila kam kamar zata shiga ciki sai kuma ta fasa, zama tai a falo kawai tana kuka ko kwanwutar bata kunna ba.
Shima zama yai a kasa ya kwanatar da kansa akan kujerar dakin, wace irin rayuwa yarinyar nan tai? Amma duk da haka akwai laifinsa a ciki, ya tabbatar dabadan shi ba da baza'a mata auran dole haka ba, wadan nan tunani sune suke tayimai zirya a ransa, tarinta yaji hakan yasa ya kalli kofar falon.
Mikewa naga yayi ya jingina kansa da jikin kofar, sheshekar kukanta yaji wanda yasashi rufe ido cikin tausayawa.
Jin kukan yake har zuciyarsa, a hankali ya bude kofar.
Dayake makunin fitilar falon a kusa da kofar take kawai sai ya kunna ta.
Haske ne ya baibaye falon, da sauri ta dago.
Jingina kansa yai da jikin kkatangar falon yana kallanta tare da sa hannunsa na hagu cikin aljihunsa.
Kallansa itama takeyi, sun dade a haka kafin ta sauke idanunta kasa.
Yace " yau ma hobby din naki ya motsa ne?"
Ta kalleshi da idanunta da suka sha kuka, yace "a rana kuka nawa kikeyi?"
Baki tadan motsa tanasan magana, yace " in zakiyi kuka kiyi a gurin daba kowa, dan ni ba hobby dina bane sauraransa."
Ya juya bai rufe kofar ba ya zauna akan kujera, me yasa yace haka? Shi dayaje dan ya lalasheta?
Mikewa yai yai sallar Isha'i, ganin batada niyyar shigowa yasa yaki mikewa daga kan sallayar, yana jiranta.
Kofar yake lekawa, yaga ba alama.
Pillow ya janyo yasa kansa akai yana kallan kofar.
Abincin su ya kalla, bataci abinci ba, shiru yai yana tunanin shigowarta.
Yana nan a kwance har karfe 10, baisan sanda bacci yai gaba dashi ba.
Jalila kam bayan ya juya kawai ta kwanta akan kujerar tana yan mitoci, kasan baka damu da hawayena ba me yasa dazu kazo? Nikam Yaya me yasa baya magana mai sanyi? Tadan turo baki ta kwanta tana tunanin rayuwarsu.
Batasan bacci ya dauketa ba, sai karfe 11 ta farka, batai isha'i ba ya akai bacci ya dauketa?
Da sauri ta sauko daga kan kujera ta nufi dakin, a kwance ta ganshi a kasa, batai mamaki ba dan taga yanayi, kawai ta wuce toilet.
Tai alwala tazo tai sallah, jitai cikinta na karar yunwa, ta zo ta bude abinci zataci, gani tai ba alamar taba abincin, baici abincin dare ba kenan?
Kadan ta zuba a plate ta faraci.
Lomarta uku taji kakarinsa, wani sankamewa yakeyi, da sauri ta ajiye abincin ta matso inda yake.
Gaba daya ya sai juye juye yake, yana girgiza kai alamar a'a, ga zufa tanata keto mai.
Hannunsa ta riko tana tabashi, Yayah! Yayah!
Gaba daya ba alamun yanajinta, kansa ta kwantar a kan cinyarya dan murkususun dayake yasa kansa ya sauka daga kan pillow din, tasa hannu ta rike kansa dayan hannun kuma tasa a saman kirjinsa tana dan tabashi tare da kiran sunansa.
Can kuma sai tadanyi kulhuwalahu da falaq da Nasi sai tadan tofa mai.
A hankali taji ya daina motsumutson.
Idanunta na kansa ya ciciko saboda da tausayinsa, wannan wani irin abu ne ke damunshi? Me ya sameshi abaya?
A hankali ya bude idanunsa, daidai lokacin kwalarta ta zubo ta zubu saiti idanunsa, wanda yana rufe ido ta zubo a bayan idansa.
Idanunsa ya sake budewa ya kalleta, dayan hannun data rike kansa dashi ta saki ta share hawayenta sannan ta kalleshi tace "Yayah!"
Idanunsa ya lumshe yana kallanta kamar yanda take kallansa cikin sansanyiyar murya mai kamma da rada yace "sai yaushe ne zaki daina saurin kuka?"
Tace " kukan ne bakaso nayi?" Itama a hankali tai maganar tana kallansa.
Mamaki ne ya kamata dataga ya daga kai alamar eh, tace "meyasa?"
Ya dan girgiza kai kadan yace "ban sani ba nima, sai dai I don't like it."
Kallansa tai tare da neman zare hannunta daga kan kirjinsa.
Hannu yasa ya tsayar da hannu yana kallanta yace " yanzu kukan me kikeyi?"
Tace "meyasa kakesan sani?"
Yace "Hmm kawai, saboda sai naji ne zansan abinda ya dace nai."
Hannunta ta nemi janyewa tana cewa "me ya faru dakai? Duk sanda kake abin nan kamar wani abu kake tunani."
Shiru yai bai bata amsa ba, kafin can yace " izinki nawa?"
Tace "mene?"
Yace "tambayarki nai, so nake nasan karatunki, na kula kamar bakiyi nisa ba."
Tadan sosa wuyanta da dayan hannun tace "bankai izu ko daya ba, a gida Goggo tadan koyamin na sallah."
Idanu ya kura mata, wanda yasatai saurin juya kai yace "bakyajin zafin mahaifinki?"
Tai shiru kafin tace "inaji, inaji sosai da har wani sa'in ganinsa ma banaso."
Yace "kenan ko me ya faru bazakiji haushi ba?"
Tace "me zakamai?"
Mikewa yai daga kan cinyarta sannan ya saki hannunta yahau kan gado....
Da sauri ta taso tace "me zakayi?"
Yace "bakomai, fada kawai nai."
Jalila ta kalleshi alamar rashin gamsuwa.........
********
Dady kuwa yana saukowa daga gun Inna ya shiga daki kawai ya hau hada kayansa, Mumy ta shigo da sauri zatai magana taga yana hada kaya, a rikice ta rike hannunsa tace "Dear menene?"
Ture ta yai yace " menene? Da alama karshen zamana dake yazo."
Da sauri ta rungumeshi tace "menene? Kafi kowa sanin bazan iya rabuwa dakai ba, Inna ce? Itace?"
Yai shiru wai shi a dole ransa ya baci.
Da sauri ta fito ta nufi dakin Inna da gudu rai a bace.........
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*45*
Da karfi ta banko kofar dakin Inna, lokacin Inna na zaune tasa hannu tayi tagumi tana tunanin abinyi, yanda Mumy ta banko kofar ne yasa ta zabura ta kalleta tace "Lafiya?"
Mumy cikin bacin rai ta zauna a gaban Inna tace "Inna so kike kiyi ajalina?"
"Ajalinki kamar ya kenan?"
Tace "in ba so kike in mutu ba taya zaki nemi halakamin aure? Sanin kanki ne yanzu kinsan bazan iya rayuwar ba Abubakar ba, a da ma da 'ya'ya basu hadamu ba na kasa rabuwa dashi bare yanzu."
Inna ta katseta cikin fada tace "me ya fadamiki?"
Tace "ba damuwa ta bace da duk abinda kike tunani sai dai kiyi abinki ke kadai, dan wallahi bazan bari wani abu ya sameshi ba, in kuma so kike mu bar miki gidan to....."
Mamaki ya kama Inna ta kalleta cikin wani yanayi tace "Fatima ni kike fadama haka? Ni wacce ma sadaukar da komai dan ganin farincikin ki?"
Cikin masifa tace "kika sadaukar dame? Me kika sadaukar? Duk abinda kikeyi ba saboda kanki kikeyi ba? In har saboda nine ai da kin daraja Abakar kin bashi company din kamar........."
Marin data kifa mata ne yasa Mumy yin shiru, ta kalleta tare da rike kuncinta.
Inna ta kalli Hannunta dake rawa, dan ita kanta batasan ta mareta ba, cikin dana sani tace "Fatima......"
Mumy ta mike tsaye tana kallanta, hawaye sun cika mata ido tace " in har bakyasan in bar gidan nan ki ajiye duk abinda kike shirin yi." Ta juya tanaji tana kiranta bata amsa ba tai waje.
Inna ta bita da kallo jiki a sanyaye.....
Shikam Dady tana fita yai wata dariyar mugunta yace "Inna i am sry sai dai kin riga kin makaro akaina 'yarki da kikafiso a duniya zata iya juya miki baya."
Yanajin alamun bude kofar ya shiga kokarin zuge jaka, Mumy na shigowa ta sa hannu da karfi ta fincike jakar sannan ta rungumeshi tace "Dadyn Yasmeen me yasa baka tunani na in zaka aikata abu?"
Yace "tunanin naki ne yasani yanke wannan hukuncin, taya zan zubarma kaina mutunci? Bayan nasan ina zubar da mutunci na naki na zubar? Da ace kome zai faru zai tsaya akaina ni kadai bazai shafeki ko yaranmu ba wlh ba abinda bazan iya ba, amma ta yaya zan yarda in zubar da mutuncinki dana 'ya'yanmu."
Dagowa tai tana kallansa tace "to kamin alkawari ko me zai faru bazaka sake tunanin rabuwa dani ba."
Yace "na miki, yanzun ma ba'a san raina nake shirin tafiya ba."
Ta kara kankameshi tace "barni da Inna bazan kara bari ta wulakantamin kai ba"
Ya shafa kanta yana wani murmushin mugunta yace " taya zan yarda na zama sillan fada tsakaninki da mahaifiyarki?"
Tace " ba kaine silla ba dan dama na gaji da yanda take ma kamar wani bawanta."
Nan ya sumbaceta a kunci yace "i luv u Zarah."
Ta sakarmai murmushin so......
Nace ansha kauna😏
Inna kuwa Mumy na fita ta ture littatafan dake kan tabir din gabanta cikin takaici tace "Abakar how dare you!"
Kwafa tai tace " kana tunanin ka samu abinda kakeso? Inji wa?"
Ta sakeyin wata kwafa........
********
Zama tai a kusa dashi a kan gado yana kwance yana tunanin Zaliha, ji yake zuciyarsa kamar zata fashe da rashinta.
Ganin baimasan ta zo bane yasa tasa hannu ta tabashi.
Kallanta yai sannan ya kakaro murmushi yace "Yaushe kika shigo?"
Tace "me kake tunani?"
Kallanta yai jiki a sanyaye, murmushi tamai sannan ta kauda kai, a hankali yace "I am sry, i am really sry."
Kallansa ta sakeyi tace "me kake tunani game da mutanen nan?"
Ya mike ya zauna yace "amsar kudinmu zamuyi, inyaso company din nasu ya nukushe."
Tace "ayi haka kuwa?"
Yace " baki kula da rainin hankalin da suka mana ba? Sannan yarinyar nan da mahaifiyarta, gaba daya ba tausayi a harkarsu, Hajiya taban mamaki duk da nasan macece wace kanta yake a waye amma i didn't expect that from her."
Tace "na sani sai dai in muka duba abin ta wata fuska zamuga mu taimakonmu sukai, da farko dabadan sun yaudaremu ba da bamu san wacce zamu aurana Hassan ba, in muka duba saukin da muka dade muna nema akansa yanzu gashi abinda likitoci da dama suka kasa yi yarinyarnan a ciki wata daya ta mana, duk da bawai ya warke ne ba sai dai canjin daya samu nada yawa."
Abba yai shiru yana kallanta zuciyarshi na dana sanin abinda ya aikata mata, yace "yanzu me kike tunani?"
Tace "just live them."
Yace "kina nufin duk abinda sukai ya tashi a banza?"
Tace "ko daya sai dai ina tunanin mu barma Allah, yanda suka cutar da Jalila da mahaifiyarta Allah bazai barsu ba, mu murikesu, gatan da basu samu ba mu basu, mu jira hukunci Allah akan su."
Abba yai shiru sai kallanta kawai da yakeyi, tace "kallan fa? Shawarar batai ba?"
Yace "akoda yaushe in kina abu sai na dinga yin wani tunani, sau dayawa akance mata basukai maza zurfin tunani ba, sannan sai kaji namiji na ta aibata mace, in naji haka a koda yaushe sai insan Allah yamin baiwar da ba ko wani namiji yama ba, samunki a matsayin matata yana daya daga cikin abubuwan da nake alfahari dasu a rayuwata."
Kallansa tai sannan tai murmushi tace " Kasan abinda yaban mamaki? Ban taba tunanin Hassan zai sauko kasa ba wlh, kasan kawai nama Jalila zancen ne amma a raina nasan bamai yiwuwa bane?"
Abba ya kalli yanda taketa farinciki yace "ni kaina nayi mamaki, kinsan rabon da Hassan ya shigo falona kuwa harya zauna ya dade haka?"
Tace " kasan ya sauko ya gaida baban Jalila ran nan?"
Abba yai murmushi yace "da alama yanda nai dace da mata haka Hassan yai dace, sai muyi addu'a Allah yaba Sageer mace shima ta gari."
Tace "insha Allah."
Washegari.
Dakin Sageer ta nufa tasa hannu tai knocking.
Yana kwance akan gado ya taso ya bude mata.
Kallansa tai cikin kulawa tace "Sageer lafiya? Naga baka fito ba."
Ya kalleta yace "Ummy...."
A rikice ta kalleshi tace "menene? Bakajin dadi ne?"
Yace "a'a kawai dai..."
Tace "na kula ma gaba daya yanzu kadan canza, Sageer menene ke faruwa?"
Yace "kai Ummy wacce canzawa?"
Tura kofar tai ta shiga dakin, binta yai ciki da sauri yana cewa "Ummy."
Hannu tasa ta zuge labulen dakin ta zauna akan kujera.
Ya matso yana cewa "Ummy!!!"
Cikin shagwaba ya kirata, ta harareshi tare da hard'e hannayenta tace " In baka fadaminba ba inda zani."
Dariya ya saka sannan ya zauna a kasa kusa da ita yace "shikenan sai muyi hira."
Tace "Sageer dan Allah meke damunka? Sai yanzu na fahimta sam da yake banda nutsuwa ban kula da canzawar dakai ba."
Yace "Ummy wlh ba komai, muje na tayaki aikin kitchen kafin sirikarki ta sauko."
Kallansa tai sannan tai murmushi ta mike ta fito, yabiyo ta.
Dakin Ameera ta kalla tace "bari in nakai musu breakfast sai mu gaisa."
Shima dakin ya kalla sannan ya matso yace "Ummy me kukai da Abba akan su?"
Tace "Goggonta zata zauna anan kamar yanda Hassan yace, su kuma su suka sani."
Sageer yai murmushi zaiyi magana ya hangota a kitchen.
Tsayawa yai yana kallanta, Jalila ta juyo jin motsin mutane, kallan Ummy tai sannan ta matso fuskarta dauke da fara'a tace "Ummy ina kwana?"
Ummu ta kalleta cikin jin dadi tace "Jalila kin tashi lafiya?"
Tace "lafiya kalau Ummy."
Sannan tadan kalli Sageer a hankali tace "Ina kwana?"
Sageer yace "kin tashi lafiya?ya yaya?"
Lafiya kawai tace.
Ummy tace "Jalila naji dadin ganinki haka kamar ba abinda ya faru."
Jalila tai kasa dakai tana murmushi, a zahiri itakam ganin Goggonta yasa takejin kamar duk wani abu daga baya kenan, sannan ta rasa me yasa takejinta haka.
Sageer ya zauna a falo su kuma suka nufi kitchen, suna aiki suna yar hira, Ummy tace "Hassan abin nashi na tashi sosai yanzu?"
Jalila tace "ba sosai ba sai yai kwana biyu zuwa uku lafiya."
Ummy tai murmushin jin dadi ta kalli kular data suko dashi ta bude, kallan Jalila tai tace "jiya bakuci abinci bane?"
Tace "yayane baici ba, inaji bacci ne ya daukeshi."
Ummy tace "ba matsala tunda ya fara bude zuciyarsa nasan komai zai daidaita a hankali."
Jalila ta kalleta cikin rashin fahimta tace "bude zuciya?"
Ummy ta dauko kukar tana cewa " eh mana akanki ba."
Jalila tace "ni?" Ta fada cikin mamaki da alamar tambaya, Ummy bata tanka mata ba ta cigaba da aiki.
Jalila tai shiru tana nazarin abinda Ummy ke nufi, ba dai so take tace wai Hassan ya fara santa ba? Tab shi wannan har akwai zuciyar soyayya ma a ransa?lalai Ummy.
Haka suka gama ta kaima Goggo ya zauna suka gaisa da dan hira, Ummy na shigowa ta mike ta dawo kitchen ta dau nasu.
Sageer na zaune kan dinning shi kadai yana cin abinci, waya yakeyi da alama da Ameera yake waya dan yana cewa "In bazata biyoki ba sai ki dawo kindai san ran monday zaku koma makaranta."
Jalila ta wuce ta hau sama, a hankali tasa hannu tadan murda kofar, tadan fara kokarin budewa a hankali.
Jitai an jawo kofar da karfi har ya hado da ita data rike kofar, ta taho ciki da dan gudu ga tire a hannunta.
Da sauri ya rike tiren yana kallanta.
Daidaita tsayuwarta tai sannan tace "yaya irin wannan fizgar kofar fa?"
Yace "ke kuma irin wannan bude kofar fa? Kamar wata munafuka? Ko laifi kikai?"yai maganar da alamar tuhuma.
Da sauri ta ajiye abin hannunta tace "laifin me? Ni wlh ba laifin danai."
Baisan yanzu ma bakinsa yadan motsa ba yace " kin tabbatar?" Ya fada tare da matsowa.
Da sauri tai baya tana cewa "ni wlh banyi komai ba, kawai dan na murdo kofa a hankali."
Yadan kalli idanunta yace "why do i have this kind of feeling?"
Tace "ikon Allah, dama dai fada kakesan yi, daga shigowata?"
Ya zauna akan gado yana cewa " ramawa nai."
Tace "me nai da zaka rama?"
Bai tanka taba ya dau littafinsa tare da gyara zama, ido ta kuramai a ranta tace "so? Hahh lalai Ummy wannan mutumin nan?"
Bai kalleta ba yace "kallan fa?"
Ta dauke idanta da sauri tace "sauko kaci abinci."
Yace "banaci."
Tace "bakaci jiya da daddare fa?"
Yace "shiyasa ai bazanci yanzun ba."
Tace "ban gane ba???"
Ya shareta.
Ta matso tana neman amsar littafinta, wani kallo ya mata yace "littafin kike san amsa ko rikeni kike sanyi?"
Da sauri ta matsa baya tace "rike ka kamar ya?"
Yace "kamar yanda kika saba."
Mamaki ne ya kamata tace "kaima ai kana rike ni."
Wai meke damun mutan nan? Jiya da daddare kamar bashi ba.
Kallanta yai kamar bazai yi magana ba sai jitai yace "inma na rikeki ai ke matatace."
Mamaki me ya kamata ta saki baki tana kallan ikon Allah, shikuwa kamar baiyi maganar ba ya cigaba da karatunsa.
Tace "dan Allah ka sauko kaci abinci."
Yace "Allah bazan ci ba."
Tace "bangane hakan ba."
Mikewa ma taga yayi ya ajiye littafib ya nufi toilet, mamaki ne ya kamata ta bishi da kallo.
Haryaje zai shiga toilet sai taji yace "inkin gama ki shirya muje a siyoma Goggo kayan dakinta da abin bukata." Ya shiga ciki yana cewa jiya dana jira kizo muci ai shareni kikai kema kiji ko da dadi......
Duk da taji dadin abinda yace sai dai wulakancin daya mata yasa tama rasa abinyi.
Da kyar tasha ruwan tea, duk kuwa da tanajin yunwa amma takaici ya hanata, wai Allah bazanci ba, kalmar nan ta bata haushi.
Tana nan a zaune ya fito daga wanka daure da towel, da sauri ta juya baya.
Ko kallan inda take baiyi ba ya fara shiryawa.
Yana gamawa ya dau key yace "ina jiranki a mota."yai waje.
Da kallo ta bishi tai tunanin jiya bayan ya warke, kamar ba shiba yana mata magana a hankali, to yanzu me ya sameshi kuma? Ramawa? Me tamai?
Haka ta mike tai wanka duk ranta ba dadi, ta fito tana kokarin sa bra a saman towel din jikinta ya turo kofar.
Idanunsa ne ya sauka a kanta, zaro ido tai tana kallansa, da sauri tasa hannu ta rufe kirjinta.
Ganinsa tai ha fara matsowa inda take, idanu ta runtse tana tsoron abinda zai biyo baya, sai dayazo daf da ita har tana jiyo numfashinsa yasa hannu cikin wardrobe ya dauko abu, kallanta yai yace "Wallet."
Ya fada tare da nuna mata wallet din, ya juya ya futa.
Wani nanauyan numfashi ta saki........
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*46*
Hassan na saukowa kasa ya nufi hanyar fita da sauri "Hassan!" Juyowa yai da sauri kamar mara gaskiya ya kalleta.
Karasowa yai inda take sannan ya gaisheta, fuskarta dauke da murmushi tace "fita zakai?"
Yace "eh ni da...." sai kuma yai shiru, murmushi ta sakeyi tace "ya zaka fita baka gaida sirikarka ba?"
Yace "sirika?"
Nunamai dakin Ameera tai da hannu, Hassan ya kalleta alamar rashin fahimta, tace "badai bazaka ba?"
Kallan dakin ya kuma yi sannan taga ya nufi dakin, da kallo ta bishi cikin jin dadi.
Hassan ya kwankwasa kofar dakin, daga ciki Lantana ta mike ta bude.
Tsayawa yai yana tunanin me ma zaice inya shiga?
Goggo dake zaune a kasan carpet tana ganin shine ta mike tace "Hassan? Shigo mana."
Shigowa yai ya zauna daga gefe yace "Ina kwana?" Kansa na kasa.
Goggo tace "ka tashi lafiya? Ya dawainiya da mu?"
Hassan yai shiru dan bai san me zaice ba, Goggo tadanyi shiru haryana shirin mikewa.
Tace "Hassan."
Komawa yai ya zauna tare da kallanta, Goggo tace "in ba damuwa magana nakeso muyi."
Yace " ba komai, menene?"
Tadanyi shiru kafin tace "da farko dai nasan kafi karfin Jalila, saboda ita ba gata gareta ba, ba kudi gareta ba sannan ba 'yan uwa dake santa take dashi ba, yarinyar tasha wahala agidan mahaifinta wanda har bata iya cewa ko kawo kawarta da sunan gidansu, tunda nake da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 38