tace “me kuke tunani? Kuna tunanin nima a san raina ne?”
Mumy zatai magana sukaji an kwankwasa kofa.
Inna tace “waye?”
Jalila tace “nice, abinci na kawo.”
Inna tace shigo.
Shiga tai ta ajiye abincin a inda tasaba ajiyewa sannan ta gaisheta, ta gaidasu Dady sannan ta mike tai waje.
Tana rufe kofa naga idanun Mumy dana Inna sun kalli juna, Inna ta hade rai ta kalli Dady tace “ da Taura ya kira cewa yai yanasan hadin aure tsakanin babban dansa da babbar jikata.”
Dady yace “ to yazamuyi?”
Tace “baka fahimceni ba kenan?”
Yace “kamar ya kenan?”
Inna tace “a ka’ida wacece babbar yarka?”
Da sauri ya kalleta dan yanzu ya fahimce me take san fad’a, jiki a sanyaye yace “Jalilah.”
Tace “wa kake tunanin Taura na nufi?”
Dady ya kalleta sai dai bai iya cewa komai ba.
Mumy cikin kissa tace “Yanzu Inna ta ya zamu aurana Jalila mahaukaci? Gaskiya nikam ban yarda ba.”
Inna tace “ to sai shi Abbakar din ya duba ya gani, da company dinmu ya durkushe mu rasa kudin mu, da mu daure mu aurama Jalila yaran wanne yafi? Sannan yaushe kikaji ance miki mahaukaci ne?”
Dady yai shiru yama rasa me zaice, can yace “amma ai suna ganinta zasusan ba yar cikin gidan nan bace.”
Inna tace “karka damu da wannan zansa yau din nan a maga dinkuna kala kala, sannan zansa a dauko mai aiki, ai dama na dade ina tunanin cewa ta bar aikin da takeyi, kuma yaran nan tunda yana da matsalar kwakwalwa gani nake bazai zama wani abu ba, gidan kudi zata sannan in haukar ta juyo mai zai iya sakintama a ranar kaga shikenan kowa ya huta.”
Kallan mamaki ya shiga yima Inna, tabbas wannan kalaman nata sunzo da rainin hankali sai dai bayaji zai iya bijirewa domin shima ya tsani talauci a rayuwar sa, menene dan ya sadaukar da rayuwar yarinya d’aya?
Inna tace “in kuma baka yarda ba.......”
Yace “Inna waec.....”
Tace “zanyima Taura magana a barta sai ta gama karatunta, sannan a gida ma banasan kowa ya sani har sai ta kammala karatunta yanda hankalinta zai kwanta.”
Dady ya jinjina kai alamar gamsuwa.
Haka suka cigaba da tsare tsarensu shidai Dady kome sukace yarda yakeyi.
Kiran Taura Inna tai ta sanar dashi amincewarsu.
Yaji dadi sosai ya ce zaizo karshen satin nan ya kawo kudi sannan su sa hannu akan contract din da sukai.
Ummy dai batace komai ba, sai dai Abba yace “in zaije sai suje tare ta ganta.” Da haka ya rufe mata baki.
*********
Jalila tayi mamaki sosai ran lahadi da yamma da Mumy ta nuna mata wata mata a matsayin mai aikinsu, sannan tace mata daga yau karta kara yin aikin gida.
Abinci ma mai raia da lafiya aka aiko musu.
Yau kam cike da mamaki tabar gidan.
Da zata tafi har dari biyu Mumy ta bata wai kudin kashewa, yanda ake ba su Safeena.
Suna isa makaranta ta sauko tana tafiya, tunani takeyi wannan kuma wani sabon salon ne ke faruwa?
Sam bata kula dashi ba wanda missing dinta ya sashi fitowa da wuri.
Yana kallanta har ta wuce bata kula dashi ba, sai datai nisa yace “Jalilah!”
Juyowa tai ta kalleshi, jitai duk damuwar dake ranta ya tafi, wani sansanyan murmushi ne ya bayyana a fuskarta.
Tace “Uncle.”
Fuska ya daure sannan yace “ what are u thinking?”
Tace “Something suspicious.”
Ganin Zarah ta taho yasa yace “See u later.”
Sannan ya juya.
Da kallo ta bishi dashi tana murmushi.
Zarah ta daka mata duka a baya tace “Anya Jalila bakida crush akan Uncle Sagir kuwa?”
Jalila ta ture hannunta tace “to uwar sa ido, in ma inada shi laifi ne?”
Zarah tai dariya tace “in shigar dake?”
Jalila a ranta tace na shigar da kaina tuni, amma a fili tace “ ni banasan love one side.”
Haka suka tafi suna hira.
Sai da aka tashe aka watse tana tsaye, sai leken kofa take ko zataga fitowarsa, sai can ta hangoshi ya taho.
Da sauri ta juya kamar bata kallan gun, har sai daya iso.
Jitai yace “ Hajiyar tunani an cigaba ne?”
Kallansa tai tace “Uncle kaine?”
Murmushi yai sannan yace “bakima ji alamun na iso ba?”
Tace “sry na tafi tunani ne.”
Fuska ya dan canza yace “anya kuwa kinyi missing dina?”
Idanu ta rufe wai ita kunya sannan tace” sosai ma.”
Yace “ to kunyar ita kuma ta menene? Ni bude idanunki ki fadamin meke damunki?”
Idanunta ta bude tace “Uncle me zakace ingaka wanda ya tsaneka ya fara nuna maka yana sanka?”
Sagir yai shiru kafin yace “ya danganta da irin tsanar da kuma irin san.”
Tace “ da ba wanda ya damu dakai haka kawai sai kuma kaga kowa yana ma mutunci yana kula da kai.”
Yace cikin dayan biyu ne, ko sun fara santa da gaske ko kuma suna san wani abu daga gunta.”
Jalila tai shiru tana tunani, itakam bataji akwai na biyun, to ko santa sukeyi yanzu? Da sauri ta girgiza kai tace “tunda aka haifen basa sona sai yanzu?????
Nima nace gaskiya kam😝
#Oneluv💕
[07/10, 21:26] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 10*
Gabanta ya dawo yace " Me kike tunani kuma?"
Kai ta girgiza tace "ba komai."
Ya dan canza fuska yace " inata farin ciki zamu hadu yau amma ke naga kamar har yanzu hankalinki baya kaina."
Jalila ta sunkuyar da kanta kasa tace "Uncle wlh ba haka bane."
Yace " to menene?"
Murmushi ta shiga yi tana sunkuyar da kanta, yace "Murmushi?"
Tace " a'a."
Yace "ni to gaskiya a sanar dani"
Kasa ta kara yi dakai tana wasa da hannunta, yace "Ahhh na kula dai dan ina malaminki ne yasa ake kunyata haka, gaskiya zansa a canzamin gun service yanda zanzo har gida kinga lokacin sai a cire kunyar."
D'agowa tai ta kalleshi tace "a'a gaskiya."
Yace " bakyasan in canza?"
Tace "eh."
Ya da n yi kasa da murya yace " kinfisan ki dinga ganina kullum?"
Kunya ce ta kamata dan kuwa abinda take nufi kenan, bata kula ba ashe motarsu har tazo, horn taji anyi, kallan motar tai sannan ta kalleshi tace "Uncle zan tafi."
Ta fada cikin sauri tare da fara tafiya, juyowa yai yana kallanta dan kar ga farga har ta bude mota.
Safeena tunda ta hangosu a tsaye ta hade fuska, Jalila na shigowa ta kara kallan Sagir wanda har a lokacin idansa na kallan motar sai da suka wuce.
Safeena ta kalleta tace "na fada nace iskanci kike zama yi a makaranta kin nemi karyatani yanzu me zakice? Zance da mai mata?"
Jalila tace "Zance kikace ai ba a d'aki kika ganmu ba, a iya sanina kuma shine mijin auren ba ni ba."
Safeena ta kulu tai kwafa tace "wlh zaki fadama Mumy uban me kikeyi a makaranta."
Jalila ta juya kai tanama Yasmeen wasa.
Suna shiga gida da gudu Safeena ta je tana kaima Mumy gulma, Mumy ta ce "ya isheni menene damuwarki dan tayi zance a makaranta?"
Safeena tace "Mumy?"
"Banasan gulma, karki kuskura ki kara kawon gulmar Jalila ba yayarki bace?"
Mamaki ya kama Safeena, me Mumy take nufi?
Ita kuwa Jalila tana cire kaya tana leke ko za'azo a mata duka ko aci mutuncinta, sai dai har ta gama cire kaya bataga Mumy ba.
Goggo ce ta fito daga bandaki ta zauna da kyar tace "Jalila kin dawo?"
Jalila tace "na dawo kina bandaki."
"Wlh cikina ke mirdamin tun jiya, da alama yanayin cin abincin da muka samu ne yasa cikina ya hargitse."
Jalila cikin kulawa tace "Goggo in anso miki magani ne?"
Goggo tace "barshi kawai."
Hijab ta zara tadau dari biyun da Mumy tabata dazu tai waje da sauri.
Tana zuwa ta sai mata magani ta fito, a hanya taga mai d'ata shima ta siyi na hamsin, tana shiga gida Dady na shigowa.
Sai data jira yai parking ta karasa ta gaisheshi.
Leda taga ya miko mata yace "Gashi."
Kallan mamaki tamai tace "ciki za'a shiga dashi?"
Yace "a'a naki ne."
Kallan mamaki ta mai tace "nawa?"
Baice komai ba ya fito yai ciki.
Mamaki ne ya kamata ta bude ledar, doguwar rigace a ciki da mayafinta, sai kayan kwalliya da turare.
Kallan Dady ta sakeyi wanda yai nisa, mamaki ya kara kamata, me kenan?
Haka ta shiga bangarensu tana mamaki, tana shiga ta mikama Goggo magani sannan ta ce kinga.
Kayan Goggo ta amsa tace "daga ina?"
Jalila tace "Dady ne ya bani."
Shiru Goggo tai tana tunani, tabbas tafi kowa sanin halin mutumin nan, tunda aka haifi yarinyar nan ya bata dan kayan jarirai daga nan bai sake bata ko da da falan atamfa ba, sai sallah ne Mumy zata jefeta da atamfa mai arha, sai kuma wani sa'in in kayan Safeena sun tsufa sai a bata, meke faruwa?"
Yanda Jalila taga Mumy ta nustu tana tunani yasa tace " Goggo in maida?"
"Ba haka bane Jalila, kawai dai ina mamaki ne."
Jalila tace "Goggo ni kaina mamaki abinda ke faruwa nakeyi, kinga an hanani yin aikin gida, sannan jiya Mumy tace wai tabada dinkuna a dinkamin, sannan Inna ma yanzu sakemin fuska take, yanzu kuma Dady, bansan me hakan yake nufi ba"
Goggo dan kar Jalila ta damu sai tace mata "kila sun duba sunga yanda kike musu ne yasa suka sauko."
Jalila tace "ko?"
Tace "sosai ma."
Murmushi sukai Jalila ta mike ta wanko musu d'ata suka fara ci, basu gama cinyewa ba aka kawomusu abinci mai rai da lafiya.
Wannan sabbabin al'amari haka sukai ta faruwa a kwanan nan, Mumy da kanta tasa aka kwashe tsofaffin kayan Jalila aka sa mata sababbi, sannan tace ta dinga zuwa cikin gida tana kallo, sannan kafin su nemi abu an aiko musu.
Itakam Goggo haryanzu bata daina mamakin wannan al'amarin ba, itakuwa Jalila hankalinta a kwance sai soyayya mai karfi da take kara shiga tsakaninta da Sagir.
Kullum da daddare sai ta ba Goggo labarinsa.
Shikansa Sagir ji yake a yanzu babban burinsa bai wuce ya ganshi da Jalila ba.
**********
Yau Juma'a tun safe Mumy ta aika Jalila tazo, tare sukaje gun wanke kai aka wanke mata, sannan suka taho a hanya sai wani janta da hira takeyi, cikin hirar ne ta riko mata hannu tace "Jalila!"
Jalila ta maida hankalinta kan Mumy.
Mumy tace "Jalila kiyi hakuri abubuwan da muka muku a baya, bamu kyauta ba na nuna banbanci tsakaninki da Safeena da mukeyi, ke ce babba sai dai zuciya tasa mun tauye miki hakkinki, mun maidake kamar mai aikin gida."
Ta kara raunana murya tace "kiyi hakuri Jalila."
Jalila jikinta ne yai sanyi tace "ba komai Mumy sannan ni bakumin komai ba, Goggo itace za'a ba hakuri, ni dama 'yace a gunku kome kuka min dama hakkinane na 'ya inyi abinda kuka sa ni."
A ran mumy tace 'Ya?
Amma a fili tace "Nagode Jalila, sannan zan ba Goggon hakuri itama, inaso ki cigaba da nuna matsayinki na babba a gidan nan, karki nunama kowa ke din ba 'yata bace, da ke da Safeena duk daya kuke a gurina."
Jalila tace "nagode Mumy."
Haka suka isa gida cikin farin ciki.
Goggo kuwa bayan sun fita ta fito da kanta ta kwankwasa kofar falon cikin gida, Yasmeen ce ta bude kofar.
Goggo tana dan dingisa kafarta da take mata ciwo, tace "Yasmeen Dadynku na nan?"
Tace eh, sannan tai ciki da gudu tana kwallamai kira, dady ne yadan fito ba da dadewa ba.
Goggo ta kalleshi sannan ta gaisheshi.
Mamaki tai dataga ya amsa, tace magana nakesan muyi.
Yace ina jinki.
Sai datai dan shiru kafin tace "meke faruwa?"
Yace "name fa?"
Tace "na canzama Jalila da kukai kai da zuri'arka, nasanka nasan bazaka taba canzawa dan kanka ba sai dai in dakwai abinda kake nufi damu, domin kai da kanka kasanar dani hakan." Yace "ban ganeba?"
Tace "ka manta da bakinka kacemi kai a rayuwarka ba so, in har kuwa naga kanasan abu to lalai akwai abinda zai kareka ne."
Dady yace " kema kinsan wannan zancene na da, sannan me ya kawo wannan maganar da yar cikina?"
Kallan zargi tamai tace" tuni nazo na maka dan baxan taba tafema ba in har ka cutarmin da 'ya ta."
Ta juya ba tare da ta nemi amsarsa ba, ko ajikinsa ya juyawarsa ciki.
********
Yau tun safe ake hidima a cikin gida,Mumy ta aika aka kira mata Jalila, tare dukansu suka hadu a kitchen sukai ta aiki, Safeena kuwa tana gidan Kanin Inna a cikin gari, suna gamawa Mumy tace ma Jalila tace tai wanka a toilet din Safeena.
Wani had'ad'en material ta dauko mata ta saka, Jalila kam yau tayi mamakin kyan da tai, dan tayi kyau sosai, Mumy da kanta ta daura mata dankwali sannan ta sa mata turare.
Wajen azahar motar Taura tai parking a gida.
Ummy ce ta fara futowa sannan shikuma ya kashe motar ya fito.
Kallo d'aya zakama Ummy kasan macece mai class ba wani shigar karya tai ba sai dai kana ganinta kasan matar manya ce.
Taura ya matso sannan ya nuna mata hanyar.
Dady ne ya fito ya shigar dasu falon baki, sai wani washe baki yakeyi, Inna ta sauko suka gaisa, nan suka dan tattaba magana akan harkar business, Mumy ta mike ta shigo dakin Safeena inda Jalila take a zaune,tace "Jalila zo ki kai musu abinsha."
Jalila ta mike tana cewa "Mumy kunya nake."
Mumy ta yafa mata mayafi tana cewa "abokana Dadynki ne gaisawa kawai zakuyi."
Haka ta fito ta amshi tiren ta nufi falon, ta rasa me yasa gabanta ke faduwa, yaye labulen tai ta shiga da sallama.
Ummy tana shigowa ta kura mata ido, haka kawai taji yarinyar ta shiga ranta, yanayin nutsuwarta ne ya kara burgeta, Jalila ta ajiye tiren kanta na kasa dan ji take kamar kallanta akeyi.
Kanta na kasa ta gaishesu, Ummy ta fara amsawa sannan Taura ya amsa ya daura da cewa " Ya karatu?"
Tace "Alhamdulila."
Yace "ance kun kusa fara jarabawa sai a dage ko?"
Tace "insha Allah."
Ganin yanda take tsugunne a gun yasa Ummy tace "tashi kije."
Nan Jalila ta mike ta fita.
Inna ta kalli Ummy tace "kun ganta?"
Ummy tace " Mun ganta sai fatan Allah ya kaimu lokacin, sannan muna fatan bazaku mata maganar auren ba har sai ta gama karatunta kamar yanda aka tsara."
Inna tace "dama hakan shine daidai."
Ummy tai shiru kafin can tace "sai dai ni banasan auren dole, a matsayina na mace banasan tauye hakkin mace yar uwata, kar muje akwai wanda takeso."
Mumy tace "in dai wannan ne ba matsala dan Jalila ba ruwanta da kula kowa, ita kunya ma bazata barta ta kula saurayi ba."
Ummy ta jinjina kai na gamsuwa, haka suka sa hannu a takarda na yarjejeniya.......
Sannan sukai sallama.
Nace uhm hmm..........
[07/10, 21:28] +234 803 222 1758: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 11*
Ummy har ta sa hannu zata kwankwasa kofar Hassan sai kuma naga ta sauke hannunta sannan ta bi kofar da kallo, juyawa tai jiki a sanyaye tana neman sauka.
Sagir ne ya fito daga dakinsa, kallan Ummy yai sannan ya matso gunta, yace "Ummy menene?"
Tace " Sagir ashe kana ciki?"
Ya kalli shima kofar Hassan sannan yace "Ummy in koma dakin yaya ta karfi?"
Harararsa tai na wasa tace "kana tunanin zai barka ne?"
Yace "sai in zauna ta karfi ince bazan fita ba."
Ummy tai murmushi tace "karka damu insha Allah na kusa samun mai tayashi kwana."
Cikin zumudi yace "haba?wanene?"
Ummy ta fara sauka daga matatakalar tana cewa " watace."
Sagir cikin mamaki yace " Aure?"
Nan ta shiga bashi labarin abinda ke faruwa sannan ta daura da cewa " Sagir ni na rasa me yasa tunda na ga yarinyar nan nakeji kamar akwai alamun tauye hakki acikin wannan lamarin."
Sagir yace "ba wani tauye hakki Ummy, na farko Yaya ba mahaukaci bane, ba kuma nakasashe bane, sannan a zamanin da ai mace ma ance ba sanin wanda zata aura take ba har sai anyi mata auren."
Kallansa tai tace " hakane nima dan Abbanku sai da aka gama komai na ganshi."
Tana fada tana dariya.
Yace "kinji ma ko? Wow Ummy harna kosa naga yarinyar, tunda ta kwanta miki ma tabbatar yarinyar ta gaske ce."
Ummy tace "kai sai yaushe zaka nunamin taka budurwar?"
Yace "nan gaba kadan nafisan ne sai mun rabu ta gama makaranta sai na fara zuwa gidansu a matsayin saurayinta ba malami ba, kinga sai na kawo miki ita kiganta."
Ummy tai murmushi tace "babban burina a duniyarnan bai wuce abubuwa uku ba Sagir, na farko naga yayanka ya warke ya dawo kamar da, na biyu naga ya samu macen da zata kula dashi na uku kuma na ganka kaima da matar da kakeso kuna rayuwar farin ciki."
Sagir yai murmushin jin dadi yace "insha Allah Ummy duka burikan nan naki zasu cika ba da dadewa ba."
Haka suka sauko kasa suna hira.
*****
Kansa yaji yamai gingirin gim, gaba daya dakin yamai zafi, mikewa yai ya fito daga d'akin ya sauko kasa.
Yana jin muryar Ummy dasu Ameera a kitchen, waje yai ya fada motarsa yai waje...........
Wani irin farinciki kwanan nan takeji, ga gida yanzu ana santa sosai, ga tsananin soyayya dake kara shiga tsakaninta da Sagir, jiya suka gama waec zasu fara neco, shine yau ta fita da kanta ta hau mota tace gidansu Zarah ta amso aran wasu litattafanta.
Tana zaune cikin adaidaita tana murmushi suka dan tsaya saboda dan karamin go slow dake gun, gefenta ta kalla motarsa ce a gun, kallan motar tai sannan tai dan tsaki tace " irin motar wannan dan iskan."
Kallan motar ta sakeyi sannan, da yake motar mai tint ce sannan bata ganshi ba a wancan ranar shiyasa bazata iya ganewa ba.
Sa'a akai ya juyo da fuskarsa inda take, kawai ya hangota tana murguda baki da hararar motar, mamaki ya kamashi dan ya tabbatar bata ganinsa bare tace wani abin ya mata.
Har ya dauke idanunsa sai ya kara juyawa, baki ta kara tabewa sannan ta juya kanta tana yan guna guni, kai ya girgiza sannan ya juya fuskarsa.
Jalila tana dan masifa tana cewa ai indai na kama mutumin nan ko ban mai komai ba sai na harareshi irin taimakon nan ma bai iya ba, ba kunya ranar ya mata rashin mutunci.
Hassan kam gaba yai ya tafi can inda ya saba zama, ya kashe motar sannan ya kwantar da kansa a jikin kujera tare da kunna karatun al-qur'ani, kira'ar Malam Abdullahi Abba ne ya zagaye cikin motar.
Jalila an samu jin dadi, yanzu kayanta kala kala, sannan haka zata zauna wani sa'in a falo itafa Yasmeen suyi ta kallansu, duk sanda suke kallan india in ana soyayya itada Sagir dinta kawai take hangowa, ba shakka bata san sanda san Sagir yai nisa a zuciyarta ba.
Goggo najin dadin yanda Jalila yanzu ta murmure duk da ba kiba tai ba amma inka ganta zakaga ba wahala a jikinta.
A kasan zuciyar Goggo har yau hankalinta ya kasa kwanciya da yanda su Mumy da Dady ke jan Jalila a jiki, sai dai duk sanda Goggo ta nemi Jalila data rage zuwa gunsu Jalila sai tace "Goggo Allah ba abinda sukemin sai mutunci."
Jalila an dage sosai ana ta karatun Neco saboda Sagir yace tai karatu sosai dan yanasan yaga matarsa ta cigaba da karatu.
Duk sanda yai wannan maganar sai Jalila ta sunkuyar da kai wai ita kunya, sai dai a kasan ranta wani dadi take ji.
Goggo har ta gaji da labarin Sagir dan kusan kullum sai ta mata tadin shi.
Su kuwa a bangaren su Inner company ya kara habaka saboda sun samu kudi sosai a gun Taura, yanzu company din ma yafi da karfi.
Su uku suke tsara abin biki dan har kayan daki sun fara siya, Safeena kuma suna ta shirye shiryen kaita Egypt wai ta cigaba da karatunta.
Sai dai ni nasan suna kokarin fita da ita ne dan karma a san da zamanta har sai anyi auren.
A can gidan su Ummy kuwa, suma ita da Ameera da Aina'u suna zuwa siyayyar kayan lefe, sanda Aunty nana taji zancen nan har gida tazo tacema Ummy wai tayi dabara ai gwara da suka nemarmai mata ta kudi wai sai yafi daraja.
Sanda tai maganar nan Ummy bata tanka ba dan haryau kalaman Aunty Nana na mata ciwo.
Yau suke zane paper karshe ta neco, suna fitowa suka hau ihon gama makaranta.
Jalila ma zaune itada Zarah a can gefe, Zarah tace "Jalila ni tun jiya nakesan fada miki wani abu."
Jalila tace "menene? Fada kukai da Nasir?"
Zarah ta juyo saitin Jalila sosai tace "Jalila tsoron abinda na aikata nakeyi."
Jalila ta mata kallan tuhuma.
Zarah tace "Jalila jiya Nasir ya sani yin abinda na ke ta tsoro."
Jalila tace " me ya saki yi?"
Idanun Zarah ne suka canza suka ciciko da kwalla tace "Jalila jiya muna tare da Nasir kinsan in zaizo kasan layinmu yake tsayawa sai ni kuma naje saboda tsoron kar yayana ya ganmu, jiya sai na ganshi a mota sai yake cemin motar babansa ce aka aikeshi, bayan mun gama hirarmu a cikin mota zai tafi sai cemin yai wai sai na mai kiss."
Jalila cikin tsantsar mamaki tace "kiss?"
Zarah ta runtse ido cikin dana sani tace "Jalila kinsan yanda nake tsananin san Nasir ganin ransa ya baci dana tsaya ina tunani yasa na matso kusa dashi na sumbaceshi a kunci, shine yace shi sai na mai a baki, nan na kai bakina saitin bakinsa shine ya rikoni ya dinga tsotsar leb'ena bansan sanda na bude mai cikin bakina ba, Jalila bansan ya akai ba na kasa kwacewa sai bashi hadin kai danai, dakyar na kwavi zuciyata na fizge jikina da sauri na fito daga motar nai gida da gudu........."
Kuka ne ya zo mata wanda yasa ta kasa karasa abinda takesan fada, Jalila kam sam tama kasa magana sai inalilahi kawai da take cewa........
Ganin yanda Zarah ke kuka yasa Jalila ta riko hannunta tace "Zarah it's okay! Kinyi laifi babba ma kuwa sai dai tunda harkin fahimci kinyi laifi sai ki nemi yafiya a gun Allah ki kuma kiyayi aikata makamancin abinda kika aikata."
Zarah ta rungume Jalila tana kuka, Jalila tace "Sai dai magana daya zan fada miki gaskiya ki bincike san da Nasir yake miki, so ne ko sha'awa, in so ne sai ku tuba ga Allah ku nemi kariya daga shedan in kusa sha'awa ne sai kisan zaman da zakiyi dashi."
(_Gareku 'yan mata da samari masu irin wannan soyayyar, sai kaga saurayi yazo gun budurwa in zai tafi sai yace sai ta mai kiss ko sai ya rungumeta, ko kuma ya nemi tamai abinda bai kamata ba, wanda ke da kike aikatawa kinsan haramun ne, sannan shi da yake saki shima yasan haramun ne._
_Dan Allah mu guji fadawa halaka saboda wani buri na zuciyar mu, Allah ya mana tsari ya kare mu daga sharrin zuciya_Ameen suma Ameen)
Jalila na zaune itada Zarah tana kara mata fada aka aiko tazo inji Uncle Sagir.
Kallan Zarah tai tace "Zarah ina zuwa."
Zarah tace " Ba sai kin dawo ba dan na san ba ganinki zanyi yanzu ba."
Jalila ta kalleta tace " har kin dago?"
Zarah ta harareta tace " yanda kike nunawa ta ya ya zan kasa ganewa? Ba ni ba na tabbatar yawancin mutane sun sani."
Jalila ta matso tace "da gaske? Ina nunawa a fili?"
Zarah tai dariya tace gashi nan kin rubuta a goshinki da jan biro."
Jalila ta dan daket tace "bansan iskanci."
Zarah tace "daga ke har shi ai kun gama sanar ma mutane dan ni a bakin
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 38