cikowa.
Hassan ya kamo hannunta, da sauri ta kalleshi, yace "in bakyasan na rikike wallahi ki hadiye hawayen nan."
Da sauri ta zare hannunta tare da kokarin hadiye kukanta.
Ya guntse dariyarsa,nan suka karayin sallama da Abba suka wuce ciki.
(Nace a sauka lafiya🕊)
***********
Ghali ne ya kalli Abba yace "inalilahi, ita kuma haka tata kaddarar take?lalai taga bakincikin rayuwa."
Abba yace "ai abin ba'a cewa komai."
Fuskarsa ya shafa sannan yace "amma wannan kwai dan iska, menene laifina dazai wulakantaa haka? Mace kamar ta haka?"
Abba yai shiru cikin takaici.
Yace "to ya shi ya saketa ne?"
Abba ya kalleshi yana dariya yace "kana so ne?"
Yace "naga kai kace in kula da patient ya kake neman canza shawara?"
Abba yai dariya yace "kabar komai a hanuna ni kaina babban burinane maga matarnan na cikin farinciki."
Haka sukai ta hirar Goggo har dare yaja, Ghali yace zai wuce gida.
*********
Zaune yake a kofar gidan sanyi sai ratsashi yakeyi, yanata kiran number Jalila bata shiga, sanyi sai kara kadashi yakeyi ga azabar yunwa dake damunsa, tun safiyar jiya har yau bai ci abinci ba, hasken daya dalleshi ne yasa ya rufe fuskarsa, tsayar da motar yai maimakon ya shiga gidan, ya fito sannan ya kunna fitilar wayarsa yana haska shi.
Dady ya mike da sauri yana neman yin gaba.
Abakar? Abinda ya fada kenan, gaban Dady ya fadi dan yanzu ya gane Abba ne, kasa juyowa yai saboda tsananin kunyar yanda kayan jikinsa da yanda duk ya canza yake.
Abba da sauri ya karaso ya jawoshi, Dady ya juyo tare da yake baki yace "Taura!"
Abba cikin tsananin mamaki yake kallansa yace "menene hakan?"
Ya fada yana kallan jikinsa, Dady ya dan zare hannunsa yace "bakomai."
Abba yace "daga ina kake haka?"
"Daga ina ma zance? Dama zuwa nai ko zanga Jalila inata kiranta bansameta ba."
Abba yace "Jalila ai bata kasar ita da mijinta."
Da sauri Dady ya kalleshi yace "batanan?"
"Suna Kuwait, amma kai meya faru naganka haka? Kwanaki inata nemanka har gidanka naje akacr kum tashi."
Yai shiru yana kallan Abba, Abba yace "Abakar?"
Dady ya kalleshi, idanunsa suka canza yace "dama inasan ganin Jalila ne ta bani dan wasu kudi wanda zan koma kauyen mu dan na gaji da kwana a masallaci ko karkashin gada."
Abba cikin mamaki yace "bangane ba?"
Nan Dady ya sanar dashi abinda ke faruwa, Abba yai shiru yana kallansa kafin yace "Abakar kaga yanda rayuwa take ko? Shiyasa akesan mutum yayi dakyau, yanzu gashinan bakada wani wanda zaka nemi taimako agunsa, bakada wanda zai ji tausayinka, kanada 'ya'ya amma ka banzatar dasu, yanzu meka mora a duniyar nan?"
Dady cikin raunaniyar murya yace "nikam ai banga wani abun dana mora ba...." hawaye suka zobo masa yai saurin gogewa.
Abba ya kalleshi yace "menene matsayin mahaifiyar Jalila a gurinka?"
Kallan Abba yai yace " nikaina ban sani ba."
Abba yamai wani kallo yace "kai kana tunanin da hakkin ta kadai ma zai barka? Ka saketa ne ko me?"
Dady yace "nikaina bansan halin kaina ba, amma ni tun farko ban dauketa a matsayin mata ba."
Abba ya runtsr ido cikin wani irin kunar rai yace "yanzu ba aurenta kenan a kanka?"
Dady da sauri ya kalli Abba, yace "ko akwai?"
Dady yace "bangane nufinka bane."
Abba yace "in ba auranka akanta ka bata takardarta ta nemi miji ta aura, saboda wannan abinda kake yi ba karamar tauye mata hakkin rayuwa kakeyi ba, ayanzu ma danaji baka dauketa a matsayin mata ba, in na sanar da ita auranku ya rabu sai dai nafisan ka rubuta saboda abinda zai iya faruwa nan gaba."
Dady yace "amma ni.:......."
Abba ya katseshi "akwai sauran cin zarafi ne dakake kokarin yi mata?"
Dady yai shiru yana tuno irin wulakancin dayama Goggo, Abba yace "akwai mai santa inhar kanaso wani ya gyara abinda ka bata sai ka rubuta min yanzu ka bani."
Dady ya kara goge kwallar data zubomai sannan yace "to zan rubuta yanzu, dan na tabbatarban camcanci zama mijinta ba."
Abba ya wuce mota Dady ya biyoshi, paper ya dauko da biro ya mikamai, Dady ya rubuta saki daya yaba Abba.
Gaba daya sai ya kara ba Abba tausayi, Abba ya koma cikin mota yana tunanin ya taimaka mai ne? Sai dai in ya tuno abubuwa marasa kyau da Dady ya aikata sai yaji inaa bazai iya ba gwara ya kara sanin duniya ta garashi tukunna, wallet dinsa ya dauko ya duba ciki, dubu takwas ne a ciki, yasa hannu a aljihunsa yaji dubu biyu ya mikamai yace "gashi kai kudin mota sannan ka nemi na abinci."
Dady ya fara godiya, Abba ya shige ciki da sauri.
Yana parking ya fito jiki a sanyaye..........
#OneLove💕[1/11, 10:17 PM] El-hajj: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
🥰🥰
*80*
*************
Bayan wata takwas.
Jalila ce ta turo kofar falon, tana shigowa ta zube a kasan carpet din falon ta kwanta.
Hassan na kitchen yana jinta ya fito falo yana cewa "Hajiya an dawo?"
Harararsa tai tace "wallahi daga yanzu na daina yarda da wannan wayan ace wai ni kadai xan dinga zuwa siyayya."
Kusa da inda take kwance yazo ya kwanta shima yace "kefa kikace ayi game, wanda ya zabi zuwa siyayya shizai dinga zuwa cefani."
Tace "amma ai wayau kamin, kasan wanda ka rubuta hakan, tunda kana dauka ka zabi abinda kake so."
Juyowa yai ya kalleta tare da jawota kafadarsa yace "baby ba wayau, ya zakiyi? Tunda kin zaba ai ba yanda zakiyi."
Ta turo baki tace "ni gaskiya a sake."
Yace "inaaa ban yarda ba."
Tace "Allah ga yunwa, na dawo daga makaranta ansani wucewa cefani."
Ya dan bubugata alamar lalashi yace "karki damu wannan ur Hubby ya shirya miki sai dai kawai kici."
Da sauri ta kalleshi tace "Allah?"
Ya mike yana daga mata gira alamar yes, da sauri ta bishi kitchen ta bude tukunya tana murna, hade ran datai ta juyo ta kalleshi ne yasashi yin dariya yace "Surprise!"
Kallan Indomien dake cikin tukunyar tai tace "Yaya Allah ni nagaji dacin indomie."
Yace "ah haba? Ta kalleshi tace "nisaidai kamin dan wake."
Dan wake? Tayaya akeyi? Badani ba."
Tace "Allah yau inbanci ba banaji zan iya bacci."
Yace"baban magana, sai ki dafa mana muci."
Nanta shigayindan wake, sai dai tana gamawa sunzo ci ta kasa, da sauri ta mike tai toilet ta shiga kela amai, Hassan cikin mamaki ya kalleta tare da dafa goshinga yace "Baby stress ne ya miki yawa? "
Ta kalleshi tace "bakai bane ka sani?"
Mikar da ita yai yace "muje gari ki duba wani abin kichi."
Ta kalleshi kamar zatai magana sannan sai yaga kuma ta tsaya, yace "ya akai?"
Kallansa tai tace "Yaya yaushe rabon nai period?"
Yace "period? Na manta, badai shi bane? Ahh nikam gaskiya....."
Yanda yaga tana irge da hannunta ne yasa ya kalleta yace "oh gaskiyarki fa kin dade bakiyi ba."
Ta kalleshi tare da saurin rikimai hannu tace "muna ta fama da skul ga murnar zani nigeria bikin Ya Sageer next month inaji shiyasa sam ban kula ba."
Yace "da matsala ne?"
Tace "a'a sai dai inaji......"
Sai kuma tai shiru, yace "me?"
Ta kalleshi ta nunamai yatsa guda biyu, yace "baby?"
Tace "maybe."
Da sauri ya sureta sama yana wani irin farinciki, Jalila ta hade rai tace "yaya murna ma kakeyi? Karatu na fa?"
Ya sauketa yace "menene aciki? Sai muje mu taho da ko Amira tunda ta gama secondary tazo ta zauna mana."
Ta kalleshi cikin gamsuwa tace "amma saifa munje anyi test karka sa rai dayawa."
Hannunta ya rike kawai yanata tsalle kamar wani yaro, dariya kawai ya shiga bata.....
************
Yanda aketa shirye shirye a gidan ne zai kayatar dakai, Goggo da Ummy na kitchen suna ta shirya abinci kala kala, Ameera da Aina'u suna gefe suna aiki suma, Goggo ta kalli Ummy tace "Oh na tabbatar jiya Jalila batai bacci ba."
Ummy tai dariya tace "inafa zatai zata zo taga na gida, malam Hassan dai na tabbatar ya shari baccinsa."
Goggo tai dariya, Ummy ta kalleta tace "Dr dai yau zai bar mana ke ki kwana ko?"
Goggo tai dariya tace " bazan bar Nabila da Muftahu ba a gidan, shima cemin yai in kwanab amma nikam badani za'ai wannan abin kunyar ba, anjiman nan zan koma, suna zuwa zamu tafi."
Ummy tai dariya tace "ya labarin su Mumy kuwa?"
Goggo tace "suna nan, ai kun gama musu komai, tunda kukace su dawo gidan danake ciki inyaso su sa dayan haya."
Ummy tai murmushi tace "kinsan da ke naso a dinga ba ma rabin kudin hayar dazasu dinga samu, sai dai ke yanzu kinyi gaba, tunda Allah ya dagaki."
Goggo tai murmushi tare da cewa "Ummy Dr ba karamin kyautatamin yakeyi ba, 'ya'yansa ma basida hayaniya, sai godiyar Allah, duk abinda nakeso kafin ma in nema yamin, sannan kinga akwai gidansa na haya da ya barmin, mezan nema nikuwa yanzu a duniyarnan, inba kuma san zuciya nake neman bi ba?"
Ummy ta jinjina kai tace "Alhamdulila ala kulli hal, hakurinki me ya biya miki, Allah ya dubi zuciyarki ne."
Goggo tai dariya sannan tace "Ai duk haduwata da ku shine ya ja min haka, daga ni har Jalila,/ shiyasa akoda yaushe nake gode ma Allah daya hadanu daku."
A tare sukai murmushi.
Lantana ce ta shigo da kaya da sauri ta ajiye tamatso gun Goggo tace "Goggo gashi, kiranki akai."
Goggo ta amsa tare da fitowa daga kitchen din dan tasan Dr ne.
*************
Juye yake akan gado yana ta zuba waya sam bai kula yazo karshen gadon ba, Maimuna tace "nikam kunya nake ji."
Yace "Kunya ko? Ki jira......."
Dim ya tiko daga kan gadon, Maimuna tasa dariya, yace "wayyo Allah na." Dan kam Sageer yaji zafin faduwar, budar kofar Ameera tai dauke da kayan guga, kallansa tai a kasa yana shoshe soshe, dariya ta saka ganin alamar waya yakeyi tace "Yaya anji jiki, ka fito za'a tafi airport."
Ta ajiye kayan ta fita.
******^^^*
Ya dage sosai yanata wanke dakin, sai daya gama tass ya fita sosai sannan ya maida katifar ya shifida ya zauna akai tare dasa kansa a cikin cinyoyinsa yana tunanin rayuwa, tunda ya dawo kauyen nasu mahaifinsa ke kwance ba lafiya, haka ya shiga jinyarsa, baya iya komai sannan komai a kwance yakeyi, haka yai ta kula dashi har Allah ya dau ransa a daren jiya.
Gaba daya rayuwa tamai zafi, yai shiru yanzu shikam baisan ina zai nufa ba dan yan uwansa duk ba wanda yake sanshi, kowa kyararsa yakeyi, yau ya samu ma su barshi ya zauna a waje gun amsar gaisuwa sun hana sun koroshi ciki.
Jakarsa ya dauka dan baiga amfani zamansa ba, dan dama sun sanar dashi mai tarar mai fada wato mahaifinsu ya rasu ya tattara nasa ya nasa ya bar musu gida.
Haka ya fito yana neman zama a tabirmar yayansa yasa kafa agun yace "malam kama gabanka."
Dady ya fito daga kauyen gaba daya abin duniya ya dameshi, balle waccen watan daya wuce yana garin Goggo tazo itada mijinta, haka tazo da kaya kala kala taita rabawa, yanaji zatazo gidansu yabar gidan, haka ta kawo kaya dayawa, haka ya tsaya ta bayan gari yana lekensu.
(Ranar kam ko ni sai da dady yaban tausayi.....lol)
***********
Gida ya cika sosai anata hira da dariya abin gwanin ban sha'awa kana ganinsu kaga mutanen dake cikin farinciki.
Jalila na kankame da Goggonta, Ummy ta kalli Hassan yace "nikam Hassan sai naga Jalila ta rame, ko Goggo?"
Goggo ta kalleta tace "bangani ba nikam."
Hassan yai dariya yace "wato Ummy so kike kice banaba 'yarki abinci ko?"
Ummy ta kalli Jalila tace "Jalila? Anya ana kila dake kuwa?"
Jalila tai dariya tana kallan Hassan, yana kallanta yace "da alama zuciya zatai kafin Sageer yai aure tana so ta maidani babba saboda kar a rainani."
Ummy tace "babba? Oh Hassan kaikam dai......"
Sai kuma ta tsaya tare da kallansa da sauri tace "Jalila ciki ne da ita?"
Da sauri Jalila ta kalleshi tana mai alamar yai shoru.
Ya kalli Abba yace "Abba ya ka gani na kusa zama baba fa."
Nan fa murna ta karu, Sageer yace "gaskiya ne yaya."
Hassan yai dariya yace "ya? A ina zaka zaunane?"
Yace kasan layin nan, muka samu gida."
Hassan yasa dariya tare da dafashi ya matso kusa dashi yace "wato ni kakesan yima wayau ko? Inyi ta zama anan kenan ko?"
Sageer shima cikin rada yace "ai naji fadanka ne."
A tare sukai dariya Abba yace "ai da kun daina rada dan nikam ina jinku."
Dariya sukai su duka.......
Jalila ce ta kalli Goggo bayan sun shiga dakin Ameera tace "Goggo kinganki kuwa?"
Goggo ta harareta tace "bansan gulma fa, bari na kira Dr yanata san ku gaisa."
Tai murmushi tace " Goggo ya labarin Dady?"
Goggo ta kalleta tace "ina zan sani?"
Jalila tai shiru kafin tace "Yaran sa fa? Duk kuna zaune lafiya?"
Goggo tace "sosai Jalila, har mamaki nakeyi, a farkon auranmu basu saki jiki dani ba saboda ziga na yan uwan mahaifiyarsu, amma daga baya abin kam har mamaki yake bani."
Jalila tai murmushin jin dadi tace "ai gashinan na gani a jikinki."
Haka sukai ta yan hira kafin su fito dan Goggo zata koma gida sai kuma wani satin in za'ai bikin Sageer.
*********
#OneLove💕
[1/11, 10:23 PM] El-hajj: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
_Last Page😘_
An daura auran Sageer da Maimuna sun tare a gidansu dake karshen layin su Ummy, gidan ba babba bane sosai sai dai ya tsaru iya tsaruwa.
Ansha shagali kala kala, amarya ta tare a gidanta.
Mumy kam dasu Safeena komawa sukai 'Yan kallo dan yanda Goggo da Jalila suka saje a cikin manyan masu kudi, gaba daya ji sukai bikin yafi karfinsu.
********
Har ta wuce ta layin a cikin adaidaita sahu ta dawo daga dan karamin aikin data samu a company din inna, dan bayan rasuwar inna daga filin da Inna ta bar musu da shares din duk kudin sun kare, saboda batsan yanda zata juya su ba, sai da Allah ya taimaketa da Goggo zatai aure Ummy ta tausaya musu, yanzu kam suna cancanawa dan aikin ba wani babba bane dan bata san abubuwa dayawa ba, tadaiyi karatun ne.
Tsaida mai adaidaitar tai ta fita da sauri, yana zaune a bakin masallaci yana alwala, daga dan nesa kadan ta kura mai ido,meya sameshi? Dab taga duk ya canza, juyawa tai ta tsaya idanunta duk sun ciciko, taku uku tai taji ance "Fatima!"
Tsayawa tai cak ta kasa juyawa, yace "ashe dagaske kece? Nayi zatan gizo kika min."
Yanzu kam ta daure ta juyo ta kalleshi, ido suka kurama juna ta daure ta dauke idanunta dan inta tuno abinda ya mata ji take ta tsaneshi gaba daya, juyawa tai kawai ta fara tafiya.
Da gudu yazo yasha gabanta yace "Fatima!"
Karabin dayar hanyar tai tawuce, tai sa'a mai adaidaita ya taho tagun kawai ta tsayar da sauri ta shige.
Shima a hanzarce yaga wani awai ya tsayar yace "dan bimin adaidaitarcan dan Allah."
Nan ya bi bayan su, da yake dama ta kusa zuwa gida bata dade ba ta sauka, zata biya kudi kawai taganshi ya fito, batai mamaki ba sai dai tayi saurin bada kudin da neman juyawa, Yasmeen ce ta leko ta gate din tana ganin itace ta taho da gudu tana murna.
Mumy ta rumgumeta tace "wayace adinga lekowa."
Zata bata amsa ta hango Dady, Yasmeen ta kalleshi cikin mamaki tace "Dady?"
Dan kwanakin ba kadan ba, Dady wanda idanunsa suka ciciko ya tako a hankali ya bude hannayensa, rugawa tai da gudu inda yake ta rungumeshi tace "Dady sai yau ka dawo daga tafiyar? Ta fada tana kuka."
Gaba daya jikinsa ne yai sanyi hawaye suka zubomai, kenan shi da daya koresu ina yake sa ran su zauna? Mikewa yai ya dauketa yace "Yasmeen angirma."
Sannan ya kalli Mumy wacce ta wuce ciki, Tsayawa yai yana kallan gate din gidan, Yasmeen tace "dady muje."
Haka suka shiga cikin gidan Safeena na shara sai ga Mumy tana shigowa ta wuce daki, Safeena zatai magana ta hango dady da Yasmeen.
Gaba daya yanayin fuskarta ne ya canza, Dady ya kalleta yacee "Safeena?"
Dakyar ya lalabata ta shiga ta kiramai Sultan wanda yana fitowa yaga shine ya koma ciki yasa key.
Mumy ma dakyar Safeena tasata ta fito, Dady kam tana fitowa ya sulale ya tsugunna a gabanta, kallansa tai da sauri, Safeena ma ta kalleshi tace "Dady!"
Idanunsa na zubar da hawaye yace "ki yafemin Fatima, ita kadai ce kalmar dazan iya fada miki."
Mumy tai shiru tana kallan yanda yake zubar da hawaye.
Kallansa tai tace "ka tashi mayi maganar."
Yace "ban isa tashi ba harsai kin yafemin."
Mumy tai shiru tana kallansa, tace "gidan ka fa? Naga ka koma haka?"
Nan ya sanar da ita yanda aka kwacemai gidan da komawarsa kauye."
Tausayinsa ne ya kamata dan tana masifar sanshi, abinda ya mata ne yasa ta tsaneshi.
Tai shiru kafin tace "ta yafemai."
Dady yace "nagode."
Na dawo daga baya lokacin da Sultan ya huce."
Ya mike zai tafi, kasa jurewa tai tace " a ina kake kwana?"
Juyowa yai ya kalleta yace "inda ya samu, masallaci ko..." sai kuma yai shiru ganin Safeena na kallansa cikin tausayawa.
Mumy ta juya baya tace "inzaka iya sai ka dinga kwana a falo, kafin ka samu abinyi, sannan in rana tayi sai ka fita.
Kallanta yai kamar yace a'a saboda kunya sai dai inyace ina zai zauna? Yana shirin magana yaga ta shige ciki.
Idanunsa ya runtse dan yasan bai kyauta ba a rayuwarsa.
***********
Yana fitowa daga gidan yaje ya dauko jakarsa sannan ya wuce gidansu Jalila, dan har ya fito zai taho dazu Safeena ta biyoshi gate, ya tsaya yana kallanta, kafin yace "Safeena ki yafemin dan gaba dayanku na cutar daku."
Nine silar dayasa duk abinda ya faru daku ya faru.
Tace "bakomai Dady dukanmu munyi laifi,
sannan bamu bane ya kamata ka fara neman yafiya a gunsu ba, Goggo da Jalila ya kamata ka fara nema."
Yace "Safeena na sani sai dai bansan inda zan samesu ba, ita Jalila ance batanan...."
Da sauri ta katseshi tace "ta dawo, ana bikin kanin mijinta."
Da sauri Dady yace "haba? Bari naje."
Bai jira mai zata ce ba yai waje da sauri, Safeena tai murmushi tace ban fadama Goggo tayi aure ba.
*********
Mika tai tare da yin juye, Hassan ta gani tsaye a kanta.
Idanu ta zare sannan ta mike tace "Yaya?"
Rufto da kansa yai kanta ya sumbaci bakinta, yace "Hajiya Baby kin farka?"
Tace "Yaya yaushe ka tashi? Naga ina rigakafa tashi."
Ya kalleta sannan ya danna wayarsa hasken agoggo ya bayyana, da sauri ta mike zaune tace "11? Inalilahi da alama bana cikin hayacina, ko yaya?ko duk gajiyar bikin ne?
Ya zauna kusa da ita tare da dan sa kansa kadan saman cikinta yace "ya zakiyi? Twins sun sa kin makara?"
Hannu tasa tadan ture kansa daga cikinta tace "yaya da gaske Twins ne?"
Yai ajiyar zuciya yace " maganar gaskiya Jalila banaso na tsorata kine amma 'yan uku ma likita yace zaki haifa, ya gano wani daga nan, wani anan sannan wani a kwance tanan." Ya fada yana wani taba cikinta.
Gabanta ne ya fadi tace "yan uku?"
Yace "eh shiyasa banasan ki sani dan nasan hankalinki tashi zaiyi, kinga Amira kadai mana kadan sai mun hada da Aina'u."
Kallansa tai ta hade rai tace "abinda yafi Aina'u."
Yadan saki fuska yace "yanzu Jalila ya zamuyi? Ga karatu?"
Idanunta ne suka fara rau rau, dariya ya sa harda kyakyatawa yana nunata, tana ganin haka tasan tsokanarsa ce ta motsa.
Kafa tasa ta tureshi daga kan hadon ya fadi a kasa, amma duk da haka dariya yake, ta hade rai tace "Allah zan rama."
Yace "a yaushe kenan? Bayan kullum haka ake cewa?"
Ta turo baki, yace "tashi kiyi wanka Baba Ghali zaizo gaida 'yarsa."
Da sauri tace "haba?"
Yace "kin manta Goggo ta fada miki yau zasu zo dashi? Dasu Nabila? Kafin mums muje?"
Tace "inalilahi nikam naga ta kaina wallahi na manta."
Ta mike da sauri tai toilet ya bita da kallo yana
Murmushi.
Tana shiryawa yana taimaka mata tasa kaya da sauri dan tana fitowa daga wanka akace sun iso
Nan suka fito mayafinta a hannu.
Neman gudu takeyi gun sauka daga kan steps, Hassan yasa hannu ya rik kugunta, kallansa tai tace "yaya karfa suga mun dade."
Yace "gwara suga laifina na basu hhskuri akan kijin asara."
Dariya tai sannan ta sauko a hankali.
Nabila na zaune yarinya yar shekara 12, tana ganin Jalila ta saki fuska dan sun hadu a biki.
Dr na ganinta yace "masha Allah ana ganinki anganta."
Ummy tace "ah haba? Anya ba san kai kuwa?"
Dr yace "inafa sankai? Sai dai inkece kike sanyi."
Abba yai dariya, nan ta karasa kusa da Ummy ta tsugunna ta gaishesu, fuska a sake ya amsa sannan ta gaida Goggo, dasu Ummy da Abba.
Nabila ta dawo kusa da ita ta zauna.
Hira suke sosai har lokacin yingirki yai, Jalila, Amira suka shiga kitchen Nabila ma tabi bayan Jalila dan ko ina Jalila tai binta take.
Bayan sun gama cin abinci akai sallah sannan aka karasa wani hira.
Can yanma wajen magrib suka fito dan tafiya, dukansu suka fita harabar gidan ana karayin hira.
Mai gadi ne yazo ya sanar dasu zuwan Dady.
Jalila naji gabanta ya fadi,Hassan ta kalla da sauri.
Hassan yace "abarshi ya shigo.
Yana shigowa ya tsaya turus, ganin mutane, sai daiduk da haka ya gano Jalila.
Cire kunyarsa yai ya nufosu.
Dr ya kalli Goggo yace "shine baban nata?"
Tace "eh."
Dady ya karaso jiki a sanyaye, hannu ya mika musu suka gaisa dukansu, sai dayazo kan Dr sannan ma yaga Goggo ce ashe dan da sam bai gaje taba.
Dr yace "barka da haduwarmu, nine mahaifin Jalila na yanzu, mijin mamanta kenan."
Dady ya kalli Goggo yaga yanda ta canza, ya kalli motar da suke jin gine agun dan alama ce ta motarsa ce.
Jiki a sanyaye ya kalli Jalila da Goggo, kamar zaiyi magana sai sukaga yasa gwiwowinsa a kasa, da sauri Hassan yaje ya sa hannu ya dagashi.
Dady ya kasa magana kawai sai kuka..........
Gaba daya tausayinsa ya kamasu, dan kam Dady yaga rayuwa adan lokacin nan.
Idanun Jalila ne suma suka ciciko.
Gaba daya Dady yama kasa magana kawai sai kuka.........
**********
Gidan ya cika sosai anata shirye shirye, Jalila na zaune a daki tayi rau rau da ido kamar zatai kuka, Hassan yace "wai da zafi sosai?"
Tace "nidai wallahi da zafi."
Bude kofar da akai bayan an kwankwasa ne yasa Hassan juyowa.
Goggo ta kalleshi tace "Hassan jeka gidan Sadiq ankai muku abincinku can."
Yace "Goggo har gidan Sadiq cin abincin? In tafi in barta?"
Mumy tace "ai kuwa dai tafiya zakai, dan na kula Jalila neman raki takeyi dan taga yau ka dawo, ai sanda tana nakudar bata dinga zabga mana raki haka ba, amma yau dan ta ganka shine takesan fanshewa, dama ai suna na mata ne, kaje kaci abincin amarya."
Jalila ya kalla wacce ta shagwave, haka ya fita.
Goggo tana zuwa ta dungurema Jalila goshi tace "ko kunya? Shayarwar akema raki haka?"
Jalila ta turo baki, tace sai fa yau yazo?
Basu san Ummy tazo ba sai ji sukai tace "abarta tai abinta wayace kar ya dawo da wuri? Wai shi a sole yanajin haushin na daukota da cikinta yakai wata tara? Itama ku barta ta fanshe."
Mumy tace "dama dai Ummy ke shagwabata."
Sukasa dariya, Safeena ce ta shigo da kaya tace "gashi inji Wata tace dole dole wannan za'a sama jariri."
Ummy ta girgiza kai tace "Aunty Nana kenan, sam ba dama."
Nan Ummy ta dauki yaran wanda yake jin yunwa tace "Jalila bashi yasha asamai kaya."
Dan nasan mijin nan naki dakyar zai bari ki kara sati biyu anan.
Sukasa dariya.
Ameera ce ta shigo da flask na ruwan zafi ta ajiye kusa da Jalila.
Jalila ta daga mata gira, Ameera ta hade fuska tace "bamu shirya ba."
Jalila ta jawota tace "badai ruwana in naji kina lalabashi a waya cikin dare.
Ummy tace " gulmar ce?"
Jalila tai dariya......
A kasa kuwa falon Abba, dady na zaune daga dan gefe
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 37 Chapter of 38