gobe a sabon office dina." Ya juya ya fita.
Dady ya saki wani irin ihu wanda ya kara razana Mumy.
Sani ma juyawa yai ya fita dan shikam hankalinsa ya kasa jawomai cikaken abinda ke faruwa.
Dady ya matso kusa da Mumy ya daga hannu ya sharara mata mari, ya kara daga hannu ya sake mata wani sannan ya nunata da yatsa yace "ke har kin isa ki sa wannan dan iskan yaran yacimin mutunci?"
Kallansa tai tana hawaye tace "Dear."e
Da yatsa ya kara nunata yace "don't you dare call my name like that."
Ya matso kusa da ita sosai yace "ni kika ci amana saboda bakyasan na zama wani abun ko? Na miki saki daya."
Kawai taga ya juya ya fita, gaba daya jitai kanta na wani irin juyawa dan ta kasa tantance takamaimai meke faruwa.
Batasan yawan mintinan da ta kwashe a tsaye ba kamar mara numfashi.
Yanda wayarta ke ta zuba kara ne yasa ta farga, daga wayar tai ba tare data dubama wanda ya kira ta ba.
"Mumy ki zo gida yanzu." Muryar Sultan taji a rikice yana fadar haka.
Da sauri ta fito ta fada mota sukai gida, wasu gardawa ta gani a cikin harabar gidan, gefe kuma Sultan ne a tsaye.
Tana zuwa ta karasa gunsu tace "lafiya?"
Turo mu akai akan ku tattara kayanku ku bar gidan nan.
Cikin mamaki tace "mu bar gidan kamar ya kenan?"
Yace "ko ku bar gidan gaba daya ko kuma yace ku koma boys quaters."
Yanzu kam ta gane wanene ya turo su, waya ta daga ta kirashi.
Kamar bazai daga ba sai taji ya daga, cikin mamaki tace "Abakar me kake nufi akan munar gidan da mahaifina ya gina?"
Yace "kema kiji in aka kwacema abinda yake naka ya kakeji."
Tace "ni menene naka dana kwata?"
Tambaya kike?
Tace "badai company dinmu kakeso kace ba?"
Yace "ko ma menene magana ta kare, ke kika bani gidan nan da kanki sai kisan inda dare ya miki."
Tace "zan san inda dare yamin amma 'ya'yanka fa?"
"'Ya'ya? Ki tabbatar kin kwashesu."
Hawayenta dake zubowa ne ya karo, tace "nikam Abakar tunda nake dakai ka taba min so na tsakani da Allah kuwa?"
"So? Wasan yara kika koma yi kuma?"
Mumy ta toshe bakinta saboda kuka na neman cin karfinta, kawai kashe wayar tai ta kalli Sultan tace "wuce kaje gidan Kawu, ni zan koma asibiti."
Yace "wai mumy meke faruwa ne?"
Tace "jeka in na dawo mayi magana."
Shiru yai kamar ya sake magana sai kuma yace "to."
Tana ganin ya fita kawai ta tsuguna tasa kuka, ba kowa a wajen sai ita dan mutanen ma sun tafi, itakam me tayi? Laifin me tayi da rana daya rayuwa ta juya mata haka? Hakkin bayin Allah da kukaitaci.
Kuka ta sake sawa, ta dade tana kuka kafin ta mike ta tafi asibiti.
Safeena na ganinta ta taso tace "Mumy menene?"
Mumy hawaye ne yazubo mata tace "Safeena ya zamuyi?"
Hankalin Safeena ne ya tashi tace "menene?"
Nan mumy ta kwashe komai ta fada mata tana kuka, sam basu san kafin su fara labarin Inna ta farfado ba.
Kuka sosai sukeyi itada Safeena, Safeena tana kuka tana cewa "yanzu Mumy haka Dady ya mana? Kema Mumy kamar baki da wayau kina ganin yanda ya banzatar da abinda ya haifa duk rashin mutuncin mutun ko duk mutuncinsa indai har bai daraja abinda Allah ya bashi ba banaji zuciyarshi a tsarkake take, kina ganin duk abinda za'ama Jalila bai taba sa baki ba, bai kuma taba nuna damuwa ba, tunda kikaga haka ai kema kinsan Dady ba mutumin kwarai bane."
Mumy tana kuka tace "duk laifinane Safeena, Inna tasha nunamin gaskiya amma banaji, yanzu gashinan ai."
Yanda Inna ke yi ne yasa suka juya inda take da sauri, hankalin Mumy ya tashi tace "Safeena kira likita."
Da gudu ta fita, Mumy ta kamo hannunta kawai ta sa kuka.
Inna ta fizge abin hancinta cikin wani irin murya tace "Fatima!"
Mumy ta dago da sauri tana kuka, Inna tace "ki daina kuka, ni nasan tawa tazo karshe, ke nakeji Fatima bansan wace rayuwa zakiyi ba."
Mumy tana kuka tana girgiza kai tana cewa "Inna ki daina fadar haka."
Inna ta girgiza kai cikin tsananin ban tausayi tace " ki duba kasan katifa ta akwai key na safe dina akwai takardun gida dana siya kwanaki can da suka wuce, kisa Sani ya kaiku gidan.
Fatima kiyi hakuri duk nice na cuceki, duk nice na dauraki akan rayuwar da kikeyi, san kaina da sanki yasa bana tunanin komai, Fatima bansan ya zakuyi ba, shares dina basuda yawa sai dai nasan zasu rage muku na cin abinci.
Yanda numfashinta ke kara sama ne yasa hankalin Mumy ya kara tashi, Inna tace "karkima Abakar magana, kar kuma ki nemi kwatar gidan, ki barshi rayuwa ce, gashinan nima na gani dayawa sun gani shima kuma zai gani, sai dai ki taimakeni da abu daya.
Mumy ta kara runtse ido hawaye na kara zubo mata "Jalila! Da Mamanta!"
Idanunta ne suka shiga lumshewa tace "Fatima ki nemarmin yafiyar........."
Yanda ta kara birkicewa ne abu na ta zubowa daga bakinta ne yasa ta kasa magana, Dr ne ta shigo da sauri ta matso kusa da Inna.
Kafin ta yi wani abu har rai yayi halinsa.
Wani irin kuka Mumy ta saka, Safeena ma ta sa kuka abin tausayi.
***********
Abubakar kam yana zaune a dakin hotel din daya kama, idanunsa sunyi jaa in ya tuna abinda aka mai sai yajii zuciyarsa na kara tafasa, Fatima? Sai kaga ya naushi gefen da yake zaune, can ma sai gani nai ya mike a zuciye ya nude window kawai yana kallan waje.
Bai taba tunanin wani abu zai kawo mai cikas ba a wannan lokacin, ihu ya saka tare da cizar lebe.
************
Goggo kam hankalinta ya kwanta dan yanzu kam taje taga yan uwanta data dade tana kewa, sun dan dade suna waya da yayanta wanda ta amshi numbersa sukai ta gaisawa da yan uwa suka mata ban gajiya sannan ta kashe, wai yanzu itace yan uwanta ke nuna mata kauna haka? Lalai duniya juye juye.
***********
Suna shiga mota Sageer yace "Yaya wannan mutumin kansa daya kuwa?"
Hassan yace "kansa daya kawai tsabar greediness ne ke damunsa."
Sageer yai tsaki yace "ji fa abinda ya maka?"
Murmushi yai yace "kar ka damu ba komai, sannan dan Allah mu bar abin nan mu biyu."
Sageer yai dan tsaki sannan ya cigaba da tukinsa.
Suna isa gida ya kalleshi ya mai alamar zip da bakinsa.
Sageer ya bishi da kallo, shikam da sauri ya shiga ciki, Sageer kam juya kan mota yai ya fita dan dama akwai abinda zaiyi.
Hassan na shiga ya wuce kitchen da sauri, ba kowa a ciki, da alama harta kammala yanda yaga har kitchen din ta gama gyarawa, juyowa yai ya wuce sama.
Kallan kanta tai a madubi tace "kai inaa.... bazan iya sa kayan nan da Ameera ta ban ba."
Rigace iya gwiwa, ba dogon wando, tace dama taban wando ne kila dana saka.
Ta juya jikin wardrobe tana neman cirewa ya turo kofar dakin.
Ta manta kayan dake jikinta, gani tai ya taho inda take da sauri, yana karasowa ya rungumeta tsam a jikinsa.
Shiru tai a hankali yace "Baby wannan shigar fa?"
Tunowa tai, ta kasa cewa komai, dagota yai ya kalleta daga sama har kasa, kunya tasa ta juya baya da sauri, kara juyo da ita ya rungumeta yace "saura kadan fa na fadi."
Kallansa tai tace "kai Yaya."
Sumbatarta yai zaiyi magana sai ya fasa yanda yaga ta kura mai ido.
Yace "menene?"
A hankali takai hannunta gefen bakinsa tace "me ya faru?"
Hannunta yadan ture yace "ba wani abun bane ina sauri ne ban kula ba na danji."
Idanunsa ta kalla sai dai ta rasa me yasa bata yarda ba.
Kamar zatai magana sai kuma ta fasa, gani yai idanunta sun fara cicikowa yace "Menene kuma?"
Ta fara kokarin shanye kwallar tace "ba saboda fitar dakai bane wani yama haka? Ko dad......"
Kara jawota yai ya rungume yace "ki bani abinci, yunwa nake ji."
Shiru tai cikin rada yace "mu biyu ne a gidan, na dauka Sageer zai shigo sai naga ya juya, kinga yau sai mu....."
Sai ya kara matsowa kusa da kunneta yace "sai a biyani bashina duka."
Dagowa tai ta kalleshi, kamar zatai magana kuma sai yaga tayi murmushi tace "ka dainajin yunwar ne?"
Cikin shagwaba yace "ina fa? Ai ni yau a nan ma za'a bani indai anaso inci." Ya fada yana nuna bakinsa.
Dariya tai, ya ja hannunta suka nufi kasa.
#OneLuv💕🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
*74*
Haka ya jawo hannunta har kasa, dinning ya nufa ya zauna akan kujera yace "anan."
Kai ta daga alamar to sannan ta nufi kitchen, tana zuba abinci tana tunanin abinda ya faru har aka bigemai baki dan kana gani kasan ba faduwa bane.
Haka ta zuba ta nufi dinning, tana ajiye wa ya dagata ya daurata akan saman dinning din inda yake, kallansa tai tana dariya tace "karfa nai barna, inya fashe fa yaji nauyi."
Baki ya bude alamar mamaki yace "kuma fa haka ne, kar muje muji abu ya fashe ba shiri."
Fuska ta hade tace "yanzu ni har katuwa ce dazan fasa wannan table din?" Ta fada tana bubuga table din."
Ya dan canza fuska yace "kuma fa haka ne, taya ma za'ace babyna guda zata karya wannan katan abin? Wai waye ma ya fada?"
Ido ta kafeshi dashi, waige waige ya shiga yi yace "ni wai waye ya fara maganar nan?"
Serving spoon ta mikamai tace "zubama da kanka."
Kwanciya yai a kan cinyarta yace "ni kam in ba'a ban abinci ba nan da minti biyar Allah inaji za'a samu matsala."
Dayake rigar karama ce daya kwanta sai ya zama kasansa kadan rigar ta tsaya, hannu yasa ta cikin cinyoyinta da sauri tace "zan zuba wallahi, ni wallahi tsoron zama anan nake, in wani ya shigo fa?
Dauke kansa yai daga cinyarta yana dariya yace "in suka ganmu kinga sai suyi gaggawar bamu namu muhallin."
Jalila ta kalleshi cikin mamaki tace "lalai yaya." Ta karasa da dariya tare da fara zubamai abincin.
Shiru yai yana tunanin mahaifinta, Jalila ta kalleshi tace "Yayah!"
Kallanta yai yace "yah?"
Tace "me kake tunani?"
"Me kika gani?"
Tace "bakomai."
Fork ta mikamai, ya kalleta sannan ya dan shagwabe yace "ni faduwar danai dazu ma kamar na bige hannuna."
Murmushi tai sannan tace "ba sai kayi pretending ba." Ta karasa tana debo abincin.
Murmushi yai sannan ya shiga karba, yaci sosai sannan yasha tea, kwantar da kansa ya sake yi a cinyarta tace "yaya....."
Jitai cikin sanyin murya yace "Jalilah?"
A hankali tace "Naam."
"Ki dinga ma mahaifinki addu'a yayi nisan da sai dai a kwatoshi da addu'a, da fatan nemar masa shiriya agurin mahalicci."
Jalila tai shiru tana kallansa, dago da kansa yai amma kan na kan cinyarta yace "bawai wani abun bane, kawai dai ina tunani addu'arku ita yafi bukata. Ya karasa da murmushi wai dan ya nuna mata bakomai.
Yanda take kallansa ne yasa yace "ba wani abun bane kawai dai........"
Katseshi tai tace "shi yama haka ko?" Ta fada tana taba gefen bakinsa."
"Oh wai akan me babban mutum zai daki kamar ni? Ni ba dan yaro ba nima?"
Jalila tace "abinda Mumy ta fada hakan ne ko?"
"Name kenan?"
Na Dady zai kwace musu company dinsu da gidansu?"
Kai kawai ya juyar ya kara kwanciya yace "bansani ba."
Hannu tasa ta dagoshi tace "Yayah?"
Yanda ya kalleta yasa ta sakeshi tana murmushi tace "hakan ne , yanzu ya kukai?"
Yace "mun samu an kwace company din daga gunsa yana gunmu yanzu sai dai bansan maganar gidansu ba."
Jalila ta fara neman hadiye kwallarta tace "Yaya ta ina dan Adam zaiyi haka? Taya mutum zaiyi haka? Kuma mutum din ma wanda yake mahaifi? Miji?........"
Hawayenta ne suka nemi fitowa yasa ta shiga motsa baki tana neman hadiye kukanta.
Hassan ya jawota kan cinyarsa yana kallanta, kallansa tai sannan ta sunkuyar da kanta hawaye suka fara zubo mata.
Yace "to ke yanzu kukan me kike a takaice? Ke kikai? Shifa yai sannan a yanda mahaifinki ya nuna kamar ba wanda ya isa ya....."
Sai kuma yai shiru, hawayenta ta shiga sharewa suna sake zubowa tace "ni da wani ido zan kalli mutanen gidan nan? Da wani ido zan kalli wadanda suke jinina?"
Hassan ya jawota jikinsa yana lalashi, yace "mubar kasar nan a dan kwanakin nan, naga alama in ba barin kasar nan mukai ba bazan daina ganin kina kuka akai akai haka ba."
Dagowa tai ta kalleshi, yace "ni kila zan dan saki kuka amma kadan, dan haka." Ya fada yana nuna tsagun karamar dan yatsansa.
Jalila tace "ashedai zaka sani kaima."
Yace "kardai inyi karya ne ai.
Murmushi tai sannan ta kalli gefenta da wayarta ke ta kara.
Ganin sabuwar number yasa "ta daga jiki a sanyaye."
Jalilah? Cikin mamaki tace "Safeenah"
Safeena tana abin kuka tace "Jalila Allah yayima Inna rasuwa."
Gaban Jalila ne ya fadi, ta mike tsaye daga jikinshi jikinta duk ya fara rawa tace "Inalilahi wa Ina Ilaihi Raji'un, yaushe?"
Safeena tana kuka tace "dazun nan, yanzu muna hanyar kaita gida ne za'a mata wanka."
Jalila hawaye ne ya zubo mata tace "bari nima ganinan zuwa."
Safeena tace "Gidan kawu zamu kaita, acan za'ayi zaman makoki, dan Dady ya koremu."
Jalila jitai kanta yayi dum kafin tace "ya koreku kamar ya?"
Safeena tana kuka tace " sai kinzo."
Dan batasan me zatace ba acikin wannan yanayin, gaba daya Jalila ta juyo tace "Yaya? Inna ta rasu."
Hassan wanda tundayaji yanda take magana jikinshi ya bashi Inna ce ya matso ya rike hannunta wanda keta rawa yace " Jalilah?"
Kallansa tai tana zare ido tace "yaya ina Dady yake?"
Yace "wallahi bansani ba, menene?"
Tace "Yaya meke damun Dady? Taya zai kori mutane daga gidansu?"
Hassan yace " bangane kora ba?"
Tace "nima bansani ba amma kome ya faru wannan abinda dan adam ya kamata ya aikata ne? Gidansu ne fa?"
Ta fada a rikice, Hassan yace "yanzu kizo muje in kaiki gidan gaisuwa komai ya biyo daga baya, sannan mutanen nan sumafa sun cutar dake."
Hawaye ya sake zubo mata tace "sun cutar dani amma ba kamar shi wanda ya haifeni ba, ya banzatar dani da mahaifiyata duk abinda ya faru damu ba ruwansa........."
Rungumentan dayai ne yasa tai shiru, yace "ya isa haka nan, ki kira Goggo ki sanar mata sai mu biyo mu dauketa."
Ta daga kai alamat to.
Nan ta kira ta sanar mata, Hankalin Goggo ya tsahi tsantsa dan gaba daya ma kasa magana tai, Jalila ta koma ta shirya suka fito suka shiga mota, gaba daya haryanzu hankalinta ya kasa kwanciya dajin abubuwan nan biyu.
Gidan Goggo suka wuce suka daukota suka fito, Hassan yace "kamar ya kamata asai wani abun ko?"
Jalila tace "abu kamar me?"
Yace "bari na tambayi Abba."
Shiru tai ya kira Abba sukai magana, itakam sai cewa take "Goggo nikam dama Inna batada lfy ne? Ni gaba daya na kasa gane abinda ke........"
Tabota da Hassan yai ne yasa ta kalleshi, magana yai mara sauti yace "Karki kauce hanya."
Shiru tai itakam gaba daya....
Goggo kam dama tundaga gaisuwa batasake magana ba, gaba daya mutuwar tazo mata a ba zata.
**********
Kallan kansa yai a madubi "me ya kawoshi nan?"
Hannu yasa yana shafa kirjinsa yace "Sageer da alama ziyara zaka gidan Aunty Nana."
Wata zuciyar tace "kaine kake zuwa gidan haka kawai?"
Can yai sauri ya kara cewa "ai yanzu haka na koma."
Kallan layin da yake yai yace "ai dubata zanyi a musulunci kuma ziyarar mara lafiya akwai lada mai yawan gaske."
Kara tada motar yai yana dan hango gidan shikam yaje yace me?
Inaa bada shi ba, gaba yai kadan ya juya kan motar, yana neman yin gaba mai adaidaiti na parking, fitowa tai daga ciki sanye da kayan makaranta na health school, kudi ta mikamai ta juya, hartayi gaba sai kuma ta tsaya ta juyo ta kalli motar, girman idanta ta rage dan ganin mutumin dake ciki.
Kunya ta kara kama Sageer ya daure ya fito tare da dan daga mata hannu kadan, yana yake.
Maimuna ta dan fara takowa shima yana takowa, sai da suka matso kusa da juna sannan tace "Ina yini?"
Yadan sosa keya kadan yace "lafiya, nazo wucewa ne sai na hango gidanku, naji kamar ya kamata na tambayi jikinki."
Kallansa tai dan taga sanda ake juya motar tana hanya, tace "na gane shine kake neman juyawa?"
Yace "hmm daga bayane nai tunani kamar kuma na tafi, kar kiji abin banbarakwai."
Murmushi tai tace "yanzu fa?"
"Yanzu kam tunda naga kingani naga kuma kamar dai kamar dai."
Tace "to yanzu nagode zance?"
"Ba nagode kadai ba kinga saboda kar asani tunani dawowa inaji number kawai za'a bani yanda zan kira."
Batai mamaki ba, dan yanda fuskarsa take da idanunsa yasa ta fahimceshi, tadai gane ta baya yakesan biyo mata.
Murmushi tai kafin ta mikamai hannunta, wayarsa yamika mata yana murmushi.
Amsa tai ta saka mai, nan suka danyi hira kadan kafin ta shiga ciki.
Tana shiga ya washe baki yace "ahhh Malam Sageer da alama kaima......"
*************
Kayan abincin da ake ta shigowa dashi ne yasa mutanen dake zaune suka mike suna cewa "daga ina??"
Jalila ce ta shigo itada Goggo bayan masu ajiye abincin sun ajiye, Safeena na hango Jalila ta mike da gudu tazo ta rungumeta tare da fashewa da kuka....
Itama Jalila hawaye ne ya zubo mata, Yasmeen dake kwance jikin Mumy ce itama ta mike da gudu ta taho gun Jalila.
Hawaye ne ya kara zuboma Mumy aranta tsantsar nadama ce fal, Goggo Safeena ta kalla tana kuka tace "Goggo sannu da zuwa." Dan da bata ganeta ba saboda canzawar datai.
Mumy ta mike tacema "Goggo tazo ta zauna."
Mutanen gun kuwa mamakin kayan da aka shigo dashi da kuma sunan Jalilah da suka jine yasa kuwa ya kunshe gulmar dake ransa, dan tabbas sunsan sunan wasu kuma sunsanta.
(Balle dama a wannan lokacin da gidan mutuwa ya zama gidan gulma, gidan sa ido, gidan hira da gidan cika ciki, mutuwa kuma anbarma wanda akayima)
********
Tsaki yai tare da cillar da wayar kan gado dayaga sakon Safeena akan cewa Inna ta rasu, a fili yace "Ankarama kasa nauyi."
Ya kwanta kawai tare da neman yin bacci.
Sai dai duk yanda yaso yai baccin nan ya kasa, daga ya kwanta sai ya farka a razane, mikewa yai ya dara bankan ruwa, tare da komawa kan kujera ya zauna......
#OneLuv💕🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
_Gaisuwa tare da sakon godiya gareku Mom Farhan, Haske da Meela Adeel wanna shafin naku ne 🥰🥰🥰🥰Much Luv
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
Tuba nake jiyaan jini dif kamar wutar nepa🙈
*75*
Tana shiga daki ta jingina da jikin kofa tana maida ajiyar zuciya, itakam Hassan nema yake ya maidata mara kunya.
Jin an murda kofar yasa ta kalli jikin kofar inda take a jingine, yace "wallahi ko a bude ko kuma in na shigo in wahalar da mutum."
Jalila tace "menene wahalar?"
Yace "Ayya wallahi in na irga uku ba'a budemin ba? Hmm ban masan ta ina zan fara ba."
Guntse dariyar ta tai tace "nima sai na kira Ummy."
Yace "wacce Ummyn? Ai kema kinsan Ummy tawa ce, ko kwace akesan min ne dama ban sani ba."
"Zan faea irgawa fa, kuma ko wacce number na kira tana dauke da babban bashi wanda kiss kadai bazai biyashi ba."
Daga kofar tai ta shige can cikin dakin, yana shigowa ya bita da inda tai, da sauri ta haye gado tare da saukowa daya bangaren, tana kokarin nufa kofar yai gudu ya rufe kofar sannan ya fizgota suka fadi kan carpet.
Wani irin dan kara yai tare da cewa "shikenan an karyani."
Dagowa tai da sauri gabanta na faduwa, ta lleahi idanunta sun firfito.
Cikin tsananin tsoro tace " Yaya? Ina ne? Nashiga ukuna."
Hannunsa ya langwabar yace "nan ne, nikam kamar kashin gun ma ya karye."
Gabanta ne ya kara faduwa a tsorace ta kalleshi sannan ta shiga taba hannnun, tsabar tsoro sai ma taji kamar ya karye din, tana tabawa yana cewa "wash Allah na...."
Jalila ta kar rikicewa tace "Yaya tashi muje asibiti, nashiga ukuna."
Idanunta duk sun canza, yadan karkace kai irin abin zafin nan yace "Jalila kaini na kwanta kawai ba sai naje asibiti ba."
"Yaya kargun yai tsami gobe azo kasha wahala."
Yadan kara raunane fuska yace "yanzu insu Ummy sukaji kin karya musu d'a mai zasu ce? Ki bari gobe sai mu fita ba tare da kowa ya sani ba."
Jalila tai shiru tana tunani, yace " kinsan dai in Ummy taji kin karya mata d'a akwai karamin matsala ko?"
Jalila tai shiru tana tunanin yanda Ummy ke san Hassan, yawo ta hadiya sannan ta kalleshi.
Yace "kaini na kwanta bakomai insha Allah."
Jalila idanunta sukai raurau gaba daya itakam batasan ma ya zatai ba, yace "ni nace ki kaini na kwanta ba wani abun."
Jalila ta dagashi yanata wani wash, ta kwantar dashi.
Yace "dan bani ruwa nasha."
Da sauri ta juya ta dauko mai ruwa a fridge ta matso ta bashi, yace "bazan iya mikewa ba."
Da sauri ta ajiye ruwan ta shiga kokarin dan jinginar da shi, sannan ta miko mai ruwan ya amsa da dayan hannun ya fara kokarin yanda zaiyi ya bude, da sauri ta amsa ta bude mai sannan ta mikamai, amsa yai da hagu yasha.
Yana gamawa ya mika mata jarkar ta amsa, yace "bari na kwanta dan buguwar tasamin ciwon kai, idanunta suka kara raunana tace "yaya Allah muje asibiti naba su Ummy hakuri."
Yace "karki damu Baby, Kinga Ummy tanada hakuri tana kuma da sanyi sai dai bata kyale wanda ya tabani ko kadan, kinga mubar maganarnan."
Jalila ta kalleshi sannan tace "to."
Gyaramai kwanciya tai sannan ta zauna a gefenshi, tare da rike mai dayan hannun.
Yace " banfa ci abinci ba tun na safen nan ga yanzu har an kusa magrib."
Tace "bari naje kasa na zuboma nasan tunda Ameera ta dawo tayi girki."
Ya daga kai kamar wanda baya magana, tace "sannu." Sannan ta mike ta fita, tana fita yai dariya yace "ahh baby nah." Ya jawo pillow ya rungume.
**********
Kallansa yai kafin yace "kana nufin bazaka bani kudina ba kenan ko me? Ni na kasa fahimtar inda ka dosa ne."
Wani mugun murmushi yai yace "wai kai da a haukarka kana tunani ni zan bi wadanda muka rabama kudi ince su dawo dashi ne ko me?"
Cikin zafin rai Dady yace "dama ba sun amshi kudin bane dan su bani mukami? To tunda bai samu ba basai su dawo dashi ba?"
Wata dariya yasa mai wanda ya kara kular da Dady yace "stop dreaming Abakar, dama nine na damu mu baka wannan mukamin ko saboda nima na samu abinda nake so, ko da dan haukarka da karamin tunani ka dauka 'yan board din ne suka amince a kawo ka a baka matsayin nan?"
Kallan mamaki Dady yakemai kafin yace "ba hakan bane?"
Director din yasa dariyar mugunta yace "ah haba? Abinda ka dauka kenan? Saboda na basu kudinka na lalabasu ne yasa kaga suna daga wuya akan a baka mulkin nan, kudin daka raba musu ne yasa suka bi bayanka bba wani abun ba."
Dady ya matso a zuciye ya cakumeshi yace "ni zaka wulakanta? Kasan ko ni wanene?"
Cikin karfi ya fincikeshi hakan yasa dady ya fadi kasa, board director din ya nunashi da yatsa yace "kai wanene? Mtsw ni zaka maida karamin mutum? Ko ni nace ma ka kwaso kudi dayawa? Ni dai nasan cema nai kawai ka kawo kudi a basu, ko nace ma ga yawon kudin da zaka ciro? Shashashan banza kawai, har kai ka isa ka maidani karamin mutum? Ashe da babban kuskure na kusa tafkawa.
Yai tsaki sannan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 34 Chapter of 38