koma gida da niyar fadawa Mami Khadija amma bata dawo daga wurin aiki ba sai bayan isha. Ta biya gidansu ne akan shirin bikin autansu da ake yi. Tana dawowa ya fada mata.
Kallonsa tayi da kyau ta kada kai "yanzu Suhaib maimakon ka kirani tun dazu sai yanzu da dare ya yi?"
"Yanzu ban burge ba? Cewa za ki yi nayi wauta ko?" Ya tambayeta yana tsuke baki.
Dariya tayi kafin ta amsa masa "ta ina ka burge? Kuma banda wauta da ka kirani ai zan ce ka tuntubesu ko suna bukatar taimako. Ba ka ce ka karbi nambobinsu shi da dan uwansa ba? Kira dayansu mu ji me zamu iya yi musu."
Da ya kira Munzali ya sanar dashi ya kama musu dakuna a Guest Inn din da ya raka shi da safe. Sannan ya riga ya sayi abinci. Suka yi sallama cikin aminci suna masu nanata godiyarsu a gare shi.
Mami Khadija tana da wani ajin da safe ranar, saboda haka sammakon tashin Sauda tayi. Mardiyya ta kwana a bangaren Nasima, dama ta saba yi mata haka tun a wancan gidan. Idan ta je wurinta kusan raba dare suke tana bugun cikinta domin ta san me da me Mami Khadija da 'ya'yanta suke ciki. Tunda da wayonta sai kawai take biye mata tayi ta hada mata zantukan da basu da kan gado tana fada.
Tsomen doya da kwai Sauda tayi wanda ya gajiyar da ita saboda yawansa. Mamin tasu tayi farfesun kaza sannan mai-aikinta ta dafa tea aka zuba a flask din gida sai na asibiti da na 'yan uwan Abbati. Ga kuma bread an hada musu dashi.
Bayan sun gama a gajiye Sauda take cewa "Mami wai waye a asibitin ne? Jiya da shekaranjiya ma an kai ga na yau kamar masu tarbar baki."
" 'Yan uwanki basu fada miki mutumin da suka gani a asibiti mara lafiya ba?"
Da dokinta ta ce "Sun fada ban san shi ake kaiwa ba" sannan ta hau bata labarin abin da ya faru kafin ta dawo gidan "Ai jiya kafin ki dawo ne Ya Farha ta fada mana ashe wanda muka yi hoto jikin motarsu ne a plazar su Mama...Mami zo ki ga ihu wurin Ya Lilu wai mutumin ya burge shi."
"Rabani da wannan mashiriricin. Karasa hada kowanne yadda na nuna miki ki taso Suhaib tunda shi ya san dakin da mara lafiyar yake."
Tsabar son ganin kwaf Sauda ta ce "Mami ki ce yaje dani don Allah. Sai na daukar masa basket din."
"A dawo lafiya. Idan ki ka yi masa rawar kai ya make ki" Mami Khadija ta furta tana yin gaba ta fita daga kitchen din.
Kafin goma na safe sun kai abincin dakin Abbati wanda ganin Suhaib ya saka masa rai da sake ganin Farha. Da ya ga fuska daban bai nuna rashin jindadinsa ba sai aikin godiya. Haka kuma Munzali ya musu rakiya har dakin Baaba Mari.
Wannan abu ya yi mata dadi fiye da zato da tsammani. Ta dinga yi musu kyawawan addu'o'i. Wani bangare na zuciyarta yana haska mata cewa karshenta Abbatinta mutumin kirki ne sabanin zarginta. Mutanen kwarai basa rasa mataimaki a inda basa zato.
A matsayinta na uwa haka yafi komai yi mata dadi. Babu mai son rab'a danta da mummunan abu ko yaya yake sai dole. Babu wata uwa dake duka ko yiwa danta fada domin rashin so. A takaice ma tsabar soyayyar ke janyowa mu dinga kwab'ar 'ya'yanmu domin su zama nagari. Habi ta saka ta dibar musu abincin sannan ta ce ta kai ragowar dakin su Deluwa. Sai da suka ci suka koshi sannan Munzali ya daukesu suka tafi asibitin. Suna zuwa ana sallamarsa.
"Baaba za ki iya sake kwanan inda na kai ku jiya ko mu kama hanyar Kano idan mun yi azahar?"
Munzali ne ya tambayi Baaba Mari bayan sun gama gaisawa da Abbati an harhada kaya.
"Mu tafi din dai zai fi."
Deluwa taji zai bata mata shiri don so tayi su kara kwanaki ko biyu ne ta cusawa Abbati 'Yashshafa kafin su tafi Kanon. A gidansa Hanne za ta iya hana ruwa gudu.
"Kai dai wannan yaro da zakalkalewa ka ke? Ai dai ka bari wadda ta fika iko dashi tayi magana?"
Baaba Mari sai ta dauke kai kamar bata ji ba, su ma sai suka yi yadda tayi din.
"Kafin mu tafi din zai kyautu muje gidan wadannan bayin Allah muyi musu godiya. Bai dace su biyomu karbar kwanukansu ba." Ta ce da Munzali.
A ransa Abbati yake cewa kamar ta shiga zuciyarsa ta san abin da yake tunani.
"Kayan shimfidar ma duka nasu ne."
"Allah Sarki. Mutanen kirki basa karewa a duniya."
Deluwa ta jinjina kai bayan sun gama kwashe komai suna shirin shiga mota ta soma sababi. Habi da 'Yashshafa suna motar Buba. Ita da Baaba Mari ne zasu shiga baya a ta Munzali.
"Dole ki wulakantani mana Mari. Baki da laifi tunda ni na nace sai nazo duba danki. Wannan cin kashin da ki ke yi min Billahillazi kaf sai na fadawa Malam" ta kare tana yi mata kashedi da hannu.
A karo na biyu Baaba Mari ta sake bawa banza ajiyar Deluwa ta ce "Na san halinka da nawa idan ka so Abbati. Don Allah ka hanzarta yin wanka ka kimtsa yadda zamu je mu kama hanya da wuri"
Munzali sai ya kama murmushi. Da can ma Abbati komai nasa da shiri cikin tsari yake yi ballantana yanzu da zasu je gidansu Farha. Waya ya daga ya kira Suhaib ya fada masa. Sai kuma ya roke shi idan zasu iya ajiye motar Abbati a gidansu. Sati mai zuwa su zo su dauka saboda ba ya son Abbati ya gwada tuki mai nisa da fitowarsa daga asibiti.
*
Mami Khadija ya fara kira ya fada mata bakin da zasu yi. Tana hanya don goma ta fito daga aji kuma bata zauna ba ta taho saboda maganar bikin gidansu. Farha ta fara kira bayan sun gama magana ya fada mata karfe nawa zasu iso.
"Idan kina jin kwarin jikinki yau kisa hannu a hada musu abincin rana. Aikin zai yiwa Sauda yawa a kankanin lokaci. Mardiyya kuma tun jiya na kula da take taken Nasima saboda haka kar ki kirata har ta sami yadda take so ayi rigima. In kuma ba za ki iya ba sai a siyo musu kawai."
Bata san cewa kafin ma ta gama bayaninta ba Farha ta mike tsaye. Wannan yanayin na farinciki mara misaltuwa ya mamaye kirjinta.
"Zan iya Mami. Sai kin iso. Allah Ya kiyaye hanya."
Babu sauran ciwo bare damuwa. Dakin Sauda ta wuce ta tasota. Karatu take yi na gwajin da take dashi washe-gari litinin.
"Ayyaaaa Ya Farha test gareni. Yaushe zamu gama nayi karatu? Ni wallahi ban iya komai ba kar naci zero."
"Yi zamanki. Amma wallahi ki baza kunnuwa don Mami tana hanya. Kina jin motarta ki taho kitchen."
Sauda tayi mamakin wannan abu. Yau yayarta da kanta take gudun dan tayi? Ba wai kyuya gareta ba amma bata son shiga kitchen ita kadai. Ko baka tayata da komai ba ta dinga jin motsi ko a ayi hira. Sai kuma ta tuna hasashensu ita da Mardiyya akan wanda Munzali ya bawa wayarsa rannan. Mutumin da Farha ta ce mata shi ne mara lafiya. Shu'umin murmushi tayi ta wurgar da littafin tana dirowa daga gado tabi bayanta. Zaman daki bai kama ta ba indai akwai wainar da ake toyawa tsakaninsu gara ayi a gabanta. Akan hanyar zuwa kitchen din ta turawa Mardiyya text ta tsegumta mata.
(Ki kirani idan sun zo please)
Ta tura mata amsa idanunta akan Mama Nasima. Fatanta kada a sami akasi akan fitar da ta ce zata yi. Ta kasa gane yawan tambayar da take yi mata yau akan Yumna kawar Farha.
A zuciyar Mardiyya bata kaunar wannan hali mai kama da gulma na mahaifiyarta. Kafin ta girma duk abin da ta tambayeta take fada mata. Sai ta kula idan ta so takalar Mami Khadija rigima da wannan take amfani tayi ta sakin maganganu. Mamin ta gane abin da Nasima take yi amma bata taba nunawa yaranta su guji Mardiyya ba. Suhaib har CID ya saka mata lokacin wanda akan idonta Mami tayi masa kaca-kaca. Da shekarunta suka karu tayi hankali sai ta fahimci illar abin da take yi ta daina.
Duk lalacewar Nasima a tata zuciyar wannan karon ba da gulma take tambayoyin ba. Laluben hanya mafi sauki da za ta fadawa 'yarta auren da mahaifinta zai yi take. Yaran duka suna son babansu a iya saninta. Wannan labarin ba komai zai yi ba sai wargaza farincikinsu. Sannan tana sane da yadda Yumna ta zame musu makusanciya a dalilim Farha. Bata sani ba ko ita ma Farha tana yawo. Kada ya zamana an koyawa 'yarta bata sani ba. She was just being a Mom a yau. Sai dai rashin sabo da rashin kyawun zuciya tun farko yasa ta kasa gabatar da niyarta.
*
Zuwan Sauda yasa aikin nasu saurin karewa. Tuwon shinkafa Saudan tayi ita kuma Farha hadaddiyar miyar agushi. Lilu ya siyo frozen springrolls da samosa aka soya da kuma lemuka. Sai kayan marmari da aka hada fruit salad.
A gurguje Farha ta shiga wanka. Kafin ta fito Mami Khadija ta dawo taje ta duba inda aka tanadi kayan tarbar bakinsu. Komai ya yi yadda take so domin 'ya'yan nata ba daga nan ba.
*
"Kai Mutumina, wannan kamshi kamar gaisuwa zamu je kai wa ba godiya ba?"
Abbati ya cigaba da fesa turare yana murmushi kafin ya bawa Munzali amsa.
"Sa ido sana'ar su waye ma?"
"Zagina za ka yi saboda ka warke?" Cewar Munzali yana tasowa ya karbe turaren ya shiga fesawa "wai ma da kananan kaya za ka je gidan surukai?"
Abbati ya kalli kayan jikinsa ya dan hade gira. Jeans ya saka baki da jar riga shirt. Agogonsa na fata da takalmi covershoe duka bakake.
"So ka ke ka rage min farincikin da nake ciki shi ne za ka fara korafi akan kayana?"
"Rashin dacewa na gani. Tunda babu a kayanka idan ka amince kawai mu wuce Kano sai mu dawo daga baya idan an sami lokaci..."
Sauran maganar tasa bata sami fita ba a dalilin kansa da Abbati ya taho shi kuwa ya ja da baya yana dariya. Sauran kiris su fara halin nasu na kokawa kamar yara Buba ya kwankwasa kofar.
"Baaba ta ce in duba ku taji shiru."
Sai da Abbati ya harari Munzali sannan ya bude kofar yana cewa "ka ci sa a."
"Kai dai ka ci sa a ba don haka ba yau da sai nayi maka John Cena (sunan dan wasan wrestling ne) a gadon baya."
Yana fadin haka ya fice da sauri suna dariya harda Buba da yawan tsokanar junansu ke matukar burge shi.
Kamar yadda suka dawo masaukinsu haka suka sake shiga mota da kayayyakinsu yanzu. Habi da 'Yashshafa suna motar Buba. Habi tayi shigarta fes ita kuwa yallab'iyar kwalliyarta ta rambada tayi bajau. Banda uwar hoda da foundation wanda suka mayar da ita mutum mutumi ta kawo wata foundation din mai haske ta zana tun daga tsakanin girarta har karshen karan hanci. Irin abin nan da masu make up suke yi domin a karawa hanci tsini. Sai fuskar tayi daban daban. Jambakinta kuwa purple ne an zagaye shi da jar jagira. Abin dai sai godiya kawai. A son ranta Abbati ya karbi tukin sai ta shiga gaba. Sauran su taru a motar Buba. Deluwa da Baaba Mari suna motar Munzali a baya. Abbati yana gefensa suna ji ya gama waya da Suhaib wanda ya ce su je asibitin Doctors Haven yana jiransu a waje. Da isarsu kuwa suka hango shi a mota ya tayar su kuma suna bin bayansa.
Maganar Munzali game da kayan jikinsa ta dawowa Abbati ya dubi Munzali wanda hankalinsa yake titi don kada Suhaib ya bace masa. Yadi ne a jikinsa wanda yasa domin tsokana ga Abbati.
"Idan mun je ka zauna a mota kawai"
Munzali ya karkace kai ya ce "saboda?"
"Saboda na isa. Ko so ka ke a dinga yabonka shigarka ace tawa bata yi ba?" ya bashi amsa.
Dan waigawa baya Munzali ya yi ya ce da Baaba Mari "ki shiga tsakanina da mutumin nan. Cin zalina yake yi duk sanda ya sami dama."
Dariya suka bata ta murmusa "haka dai ku ka iya kamar kananan yara."
"Haba Baaba ina da kamar Qibdiyya ki ke ce min yaro?" Inji Abbati
"A baki ba! Kodayake gara ma kai wannan karon. Kai kuwa Munzali dama taraka nake yi. Kai baka mayar da mahaifiyar Mariya (sunan gaskiyarta take kiran Qibdiyya) ba kuma baka nemi wata ba..."
Caraf Deluwa wadda tun dazu take neman shiga hirar ta ce "shi ma Abbatin ai sammakal. Har ma gara Munzali tunda ya ajiye kwai duniya ta shaida. Kai kuwa ka ajiye juya a gida bata komai sai ta ci ta sha tayi kashi. Ai Mari aure ya kamata ya kara ko Allah zai sa ya sami magaji."
"Ku ne 'yan birni. Me ya kamata mu kaiwa mutanen nan ne a matsayin tukwicin kyautatawarsu?" Baaba Mari tayi tambayar ga 'ya'yanta tana mai kawar da kai ga maganar Deluwa a karo na uku. Ranta yana baci ne idan tayi maganganunta to amma bata son ta biye mata. Yin hakan zai zubar musu da kima a idanun 'ya'yansu da wadanda suke tare. Ba ta son tayi abin da ko da wasa Buba zai gorantawa Habi idan sabanin yau da gobe ya hada shi da ita. Sannan ga Munzali da uwa uba 'Yashshafa wadda tayi imanin komai rashin kan gadonta, idan taga ana saitawa mahaifiyarta zama sai taji babu dadi.
Abbati ne ya amsa mata da cewa sai dai su ajiye musu kudi tunda sun riga sun biyo bayan Suhaib babu damar tsayuwa. Ita kuma ta ce ba kowa ke karbar kudi ba siyayyar za ta fi. Basu ankara ba suna shawara sai gani suka yi Suhaib ya saka trafficator ta bangaren dama. Munzali sai ya ce mata kada ta damu in Allah Ya yarda zasu kawo tukwicin ko ba yau ba.
Deluwa aka hangame baki da kofofin hanci ana kallon tafkeken gida irin wanda bata taba gani ba. To Baaba Mari ma dai sai da taji faduwar gaba. Masu kudi irin haka ne suka taimakawa danta. Anya in sun san cewa su kauyawa ne zasu kallesu ma kuwa?
"Baaba fito mana"
Muryar Abbati ce ta katse mata tunanin da bata san ma ta dulmiya a duniyar yinsa ba. Shi ma kuma suna fitowar hada ido suka yi da Munzali kowanne ya jinjina kai. Basa bukatar furta zantukan da zukatansu suke yi. Maganar daya ce tak. Gidan nan yafi karfinsu.
*
"Ya Farha sun iso."
Cikinta ya sake bada sauti bayan na farko da ya yi lokacin da taji an bude gate. Waskewa tayi don jikinta har wani dan rawa yake yi kamar mai shirin kamuwa da masassara.
"To kuma sai aka ce idan sun zo ki fada min? Bakin Mami ne ki je ki sanar da ita mana."
Sauda ta kama dariya "gani nayi wai kin sha wahalar yi musu girki."
Farha ta sha kunu "to biyana za su yi?"
"Eh mana. Ko dan murmushi aka cillo miki na san za ki kwana kina juyi." Tana kare magana ta fita da sauri kafin Farha ta iskota.
A can waje bangaren da aka yi domin ajiye motoci Mama Nasima ce za ta shiga motarta. Mardiyya tana gefenta ta dauko mata jaka. Suna wurin su Abbati suka shigo. Suhaib ya ajiye motarsa a inda ya saba sannan ya tafi inda suka tsaya baya kadan dashi suna jiransa. Kamar da wasa Mama Nasima ta kalli bakin da take tunanin na makiyarta ne sai idanunta suka sauka akan Munzali sannan Abbati.
Motar da bata shiga ba kenan ta bude baki ta soma cewa "Alh. Munzali" kamar ita ta rada masa sunan.
Su duka suka waiga har ta karaso wurin tana kallon mutanen da suka zo tare.
Kan Mardiyya ta dungure wadda tana jin ta kira sunan Munzali hankalinta ya tashi ta biyo bayanta.
"Wai yarinyar nan sai yanzu take fada min kuna tafe kuma harda manyanka. Shi ne fa na fito da kaina zan tarbeku." Ta dubi su Baaba Mari jikinta a dan sanyaye da yanayinsu da ya fallasa rangwamen wayewa a tare dasu. "Sannunku da zuwa Inna." Suka amsa fuska a sake don basu san wurin wa suka zo ba dama.
Mardiyya tayi karfin halin cewa "Mama ba fa..."
"Wuce muje ki hado musu juice sannan ki dora abu mai sauki (bata taba daukar mai-aiki ba saboda gudun kar a ramawa kura aniyarta)."
Duk abin da ake yi Munzali kallon Mardiyya yake wadda idanuwanta suka cicciko da kwalla. Tana magana hawaye na kokarin sauka.
"Mama kinga tare da Ya Suhaib..."
Munzali sai ya girgiza kai da sauri saboda fahimtar halin da mahaifiyarta ta sakata. Irin wannan ai ba bakonsa bane tunda ya tashi a gaban Asabe.
"Abbati ku je da Suhaib zan shigo daga baya."
Mama Nasima ta yamutsa fuska tana hararar Suhaib "au, kun sansu ne?"
Hanya kawai Suhaib ya nunawa su Abbati "Bismillah muje."
Abbati sai ya kalli Mardiyya ya yi mata alama da tayi murmushi ga Munzali nan. Murmushin kuwa tayi ya hado da zubowar hawaye.
"Mama muje dama zan kawo miki karar Diamond girl"
Munzali ya ce domin kawar da hankalin Mama Nasima daga kansu Abbati. Ai kuwa ya yi nasara domin yana kiran 'yarta Diamond girl ta soma dariya.
"Yaran yanzu ba kwa kunyar kowa. Duk da dai kamar ma zamu yi sa'anni da kai Alhaji. Amma babu komai. Aure babu inda ba ya kai mutum. Abbanta ya girmeni sosai. Kusan kamar kai da ita."
Kallon ban hakuri Mardiyya take yi masa. Shi kuma ya nuna mata ko kadan bai shiga damuwa ba. Da ido kadai yake karfafa mata gwiwa har taji saukin zuciyarta akan abin da mahaifiyarta tayi. Basu sani ba ashe kallonsu Mama Nasima take. Ta sake kallon motar da Munzalin ya tuko taji sanyi a ranta. Watanni kalilan suka ragewa Mardiyya da Sauda su gama secondary. Ranar jarabawar karshe in sha Allahu za ayi kamun 'yarta. Aurar da ita zata yi ga kamilallan mutum ko hankalinta ya kwanta. Bangaren zuciyarta da bai manta rayuwarta da ta mahaifin Mardiyya ta baya ba yana cike fal da tsoron kada wata rana kaddara ta giftawa tilon 'yarta.
Suna shiga falonta ta yar da mayafi akan kujera ta fada kitchen. Sai lokacin Mardiyya ta iya yi masa magana.
"Ni wallahi ban ma san me zan ce maka ba. Don Allah kayi hakuri."
Kashe mata ido ya yi fuskarsa a sake ya ce "Kar ki damu Diamond girl. Ina jin fa gara wannan maman tamu akan wadda na baro a Kano."
Abin sai yaje mata bambarakwai. A iya saninta mahaifiyarta ce kadai me wannan halin.
"Da gaske?"
"Zan kaiki ki ganta sai ki tabbatar."
'Yar dariya tayi, yaji wani irin sanyi a ruhinsa sai da ya kai ga lumshe ido. Kamar da wasa ya cewa Abbati zai nemeta sai dai bai taba zaton zai ji komai a ransa ba game da ita. Ya zata tausayi ne kawai...
"Ka kaini ka ce mata wa? Bamu da 'yan uwa a Kano na san ma Abba ba zai bari muje ba."
Muryar Mama Nasima suka ji tana cewa "kina nan kin saka shi a gaba da zance maimakon ki biyoni kitchen ko? Wannan ni kike son ki tozarta a zaci ban miki tarbiyya ba. Alh. Munzali sai kayi hakuri fa. Matar taka akwai kuruciya ga autanci yana damunta."
Tamkar Mardiyya ta nutse a kasa don kunyar mahaifiyarta. Sai gashi Munzali ya kara mata da cewa "kinji Mama ta bada amsar idan na kaiki Kano da wane suna zan gabatar dake ga iyaye da 'yan uwana."
*
"Sannunku da zuwa. Sannunku. Ku zauna don Allah"
Mami Khadija kenan take yiwa su Baaba Mari barka da zuwa cike da fara'a da kyautatawa. Baaba ta saki fuska ita kuwa Deluwa duk ta gigice da sanyin falon. Haushin shareta da Baaba Mari ta dinga yi ya bace a lokacin. Suhaib take kallo tana sake kallon zinariyar 'yarta wani abu yana darsuwa a zuciyarta.
"Shafa'a (tana jin kamar idan ta kara 'tu' din sunan zai yi kauyanci) koma motar ki shigo da kwanukan da suka yi ta mana hidima dasu mana."
'Yashshafa ta tashi ta fara zumbura baki sai ji tayi Deluwa ta ce da Suhaib "Sha'aib rakata kaji dan albarka."
Abbati ya harbo jirgin ya ce 'Allah Ya 'yantani' a ransa sannan ya mike kafin ta sake magana.
"Muje na tayaki."
Deluwa ta hade rai kamar ta rufe shi da duka. Sanda taso ya kula 'yarta yaki, yanzu ta sami wani zata cusawa yana neman hana ruwa gudu.
'Yashshafa tayi waje tana ta karairaya sai ka rantse kugunta bai zauna daidai ba. Abbati ya tabe baki yana dariya a ransa. Banda rigimar Deluwa daga ganin mutum ta fara tunanin hada shi da 'yarta. Kafin ta karasa kunyatasu gara ma suyi su bar gidan. Sai da suka isa jikin motar Suhaib ya fito ya karbi mukullin motar Abbati dake asibiti. Lilu zai dauko a gidansu abokinsa sai ya kai shi ya dauko motar. Bakin Abbati baya gajiya da yi musu godiya. Bayan ya tafi ne ya mikowa 'Yashshafa tissue.
"Goge fuskarki kafin mu koma. Da ace naga wannan adon bararojin tun kafin mu fito ba zan yardi ki biyomu a haka ba."
"Ni dai gaskiya Yaya Abbati ka bar min kayana ina so. Duk wata mace da ta amsa sunanta yanzu sai da me-uf (make up)."
Magana zai sake yi mata kawai ya hango Farha ta fito daga wata kofa da bata da nisa da wadda suka fito. Doguwar rigar atampa ce a jikinta sai mayafin mai kauri wanda ta dora a ka ba tare da ta saka dankwali ba. Bata san ya ganta ba tayi saurin buya a bayan wasu fulawoyi masu tsayi da suka cike tazarar dake tsakanin bangarensu da na Mami Khadija.
Kwando daya ya mika mata ya ce "jeki, iyaka dai duk wanda ya yi mafarkin fuskarki a gidan nan yau alhaki a kanki."
Tana soma tafiya ya hango Farha ta kuma lekawa sannan ta buya a zatonta tare zasu koma ciki. Har ya lallabo ta gefen bangaren Mami Khadija ya tsaya a bayanta bata sani ba. Kallonta ya dinga yi kamar babu kowa a duniya sai su kadai.
Farha da bata san yana wurin ba ta sake lekawa sai bata ga kowa ba. Sauke ajiyar zuciya tayi kanta cunkushe da tarin tambayoyi. Bata san ma'anar wannan bakon yanayi da take tsintar kanta game da Abbati ba. Sai tuhumar zuciyarta ma da take yi wurin azalzalarta da yawan tunaninsa.
Kafa ta daga za ta bar wurin ta bangaren nasu dakin Abbati ya yi mata magana da sauri.
"Abin da muke buyarwa din har ya tafi ne?"
Ba karamin tsorata tayi ba harda ja baya. Tabbas taji kamshin turare mai ratsa zuciya amma bata kawo cewa a bayanta mai shi yake ba. Ga kunya ga kuma mamakin yadda yazo wurin bata sani ba, basarwa tayi ta ce masa,
"Me kake yi a nan?"
Takowa ya dinga yi a hankali zuwa inda take. Ta rufe ido har ya karaso domin tamkar a tsakiyar kanta take jin sautin duk takunsa.
"Naga kin buya ne shi ne nima na taho kar abin da kike gudu ya kamani."
Tura baki tayi don ta boye kunyar da ta kama ta ta ce "babu abin da nake gudu ni."
"Da gaske? To ko ni ki ke kallo?"
Ba shiri ta daga kai ta zuba masa kyawawan idanunta "me zai sani kallonka?"
Hannuwansa duka biyu suna aljihun wando, ya jikina da bango ya dubeta da kyau kafin ya ce
"Nima haka nacewa kaina. Me zai sa ki kallona?"
Karkata kai tayi ta dan kalli yanayinsa da ido daya sai taji babu dadi.
"Wai haushi kaji?"
Shi da zai yi fushin wasa tana neman saka shi dariya. Da kalma daya ya amsa mata kada dariyar ta subuce masa
"Eh"
Farha ta sake ware idanu wanda ya fahimci tana yin hakan cikin mamaki ko tsoro. Yadda yake ji a ransa a lokacin zai iya rantsuwa babu wanda ya taba son wata mace kwatankwacin yadda yake jin Farha a ransa.
"Fushin gaske ko na wasa?"
Ya marairaice mata fuska "na gaske mana. Abbati bashi da abin da zai sa Ya Farha ta kalle shi ai dole in ji babu dadi."
"Ni yaushe nace maka haka?" Ta fada hankalinta yana neman tashi. Abbati kuwa kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha saboda ya amince ba haukansa yake shi kadai ba.
"Kin yarda ni ki ke kallon? Uhmm?"
Yadda ya tsareta da ido sai taji kamar tayi tsuntsuwa ta bar wurin. Motarsu ta nuna da hannu ta fice daga wurin yana bin bayanta.
"Motar nan nake kallo ina tunanin kafin ku fito na zo na dauki hoto..."
"Cewa za ki yi baki manta alkawarinmu ba. Ina fata
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 62