Share this page
fada ba ya san cewa Abbati ya gama sarewa da komai. Yau din rana ce da za ta zama mafarin wani abu da bashi da suna a rayuwarsu. Kuma har ga Allah Yafi kowa sanin cewa tonowar asirin Abbati ba kamar nasa bane. Abbati ya tashi cikin dangi da iyaye. Duk wani rikicin cikin gida bai raba kan iyayensa ba. Shi kuwa ko yau iyayensa suka ji bashi da abin da ya wuce dora musu alhakin komai. Darajar Qibdiyya da kuma 'yan uwansa da ya fara sabunta zumunci dasu ne ababen dubawa. Sai kuma masoyiyarsa Mardiyya wadda ko kadan baya son abin da zai shata layi tsakaninsu. Mafi girman damuwarsa kuwa tana tattare da bakincikin shi ya batawa Abbati rayuwa. Numfasawa ya yi bayan ya dan yi nazari. "Kana nufin za ka je ka tonawa kanka asiri ne ni kuma na zauna? Waye silar shigarka wannan rayuwa." Hannu Abbati ya nuna masa "kada muje nan wajen." Rai ya soma baci Munzali ya ce "to ina zamu je? Ba ni bane? Ba don ka hadu dani ba da yanzu kana rayuwarka cikin kwanciyar hankali." Kafin ya gama maganar idanunsa sun yi jajir. Zuciyarsa a kuntacce take yana jin yadda take zafi. Ya sake bude baki zai yi magana Abbati ya dakatar dashi da cewa, "Don Allah kayi tuki a hankali." Duk yadda Munzali yake son yi masa musu haka ya hakura ya tafi bayan shigar Abbatin motar haya. *** Mummunan faduwar gaba ne ya sami Baaba Mari har ta saki butar hannunta da taji muryar yaran gidan suna yiwa Abbati barka da zuwa. Sake dibar ruwa tayi cikin rawar jiki duk tana zuzzubarwa ma ta kuma cika botar ta zauna za tayi alwalar Isha'i. Jikinta har wani karkawa yake saboda tashin hankali. Tunda ya iya biyo dare ya taho garin a yau da basu kwana da shirin zuwansa ba ta san babu lafiya. Tabbas babu ko tantama Abbatinta bashi da gaskiya. Da babu wata a kasa tun dazu zai kirata ya karyata zantukan da taji sunyi a waya da Shazali. A yadda zuciyarta take dakan lugude a kirjinta kuwa a lokacin ko me ya fada a waya zata amince. Yardar ta zame mata wajibi ko don kada bakincikin jin gaskiya ya kwantar da ita. Shi kuwa a bakin kofar da zata sada shi da sashen mahaifinsa ya tsaya tun shigowarsa. Idanunsa da suke cike da kwalla suka sauka akan Baaba Mari tana alwala. Ya gama karanta da fahimtar duk wani motsinta. A firgice take! Alwala take yi amma sam hankalinta baya jikinta. Shafar kai kadai wadda da wuya ake kuskure adadinta saboda sau daya ce sai da tayi biyar akan idonsa. Ya lura duk gabar da ta kama sai ta dawo hayyacinta take tafiya ta gabanta. Bai san kuka yake ba sai da yaji ruwan da zafinsa yafi wuta a zuciyarsa yana bin kumatunsa. Asalin kunci da damuwa ne suka rufe shi ya juya a hankali ya fita daga gidan. Kofar gidansa yaje tun daga dan nesa yake hango hasken tocilan din wayoyi guda uku a wurin. Bai yi mamakin ganin 'Yashshafa da wasu 'yan mata sa'o'inta biyu ba. Su ma duka kannensa ne kowcce da tsintsiya a hannu. "Gwaggo Deluwa ce ta aikomu muyi maka shara kafin a kawo abinci." Guda cikinsu ta fada bayan ta gaishe shi. Mukullin kawai ya mika musu ya juya masallaci. 'Yashshafa bata manta gargadin Deluwa ba tayi saurin cewa a dawo lafiya. "Ki kwantar da kai ki kyautata masa domin mu sami biyan bukata." Cewar Deluwa mintuna kalilan da sallamar Abbati cikin gidan. 'Yashshafa tana dirzar kafarta da dutsen goge kaushi ta daga kai tana zumburo baki. "To wai ni Inna haka za kiyi ta min ne? Yau ki ce in daina sakar masa fuska gobe in saki? Yaushe zai soni a haka?" Deluwa ta murmusa tana wani jijjiga kai "Yaro man kaza. Banda abin ki 'Yashshafa idan baki kwantar da kan ba ta yaya zamu samu ya baki lambar shi Sha'aib din cikin sauki?" Cigaba da dirzar kafarta tayi cikin yanayin ko in kula ta ce "Inna ki bar batunsa don a ranar ko kallo ban ishe shi ba." Harara mai kyau ta samu kuwa sannan cikin fushi Deluwa ta ce mata, "Ta yaya zaki san me yake faruwa a lokacin nan kina can kina kukan shanu? Kar ma ki zata dominki na damu. Tausayin yaron da mutumcin uwar tasa ne yasa nake ta kokari. Ni kadai na san me na gano a kwayar idanunsa game dake. Jikina ya bani suna ta nemanki ta wurin Abbati. Amma don mugunta yaki hadaku. Su kuma 'yan birni ba wuya ciwon zuciya ya kwantar dasu saboda da gaske suke soyayya." Tabe baki 'Yashshafa tayi bayan tafiyarsa tabi 'yan uwanta cikin gidan. Daga Abbatin har Suhaib ta san bata gabansu. Ita din ma ta turesu daga gabanta. Kwanakin nan mutum daya take yawan tunawa tana jin ina ma zasu hadu ta rama dariyar da ya yi mata. Da Abbati ya dawo bai koma gidansu ba. A waje ya gaisa da sauran iyayensa maza ya ce kansa ne yake ciwo zai kwanta. Harda nanatawa Mal. Inuwa ya sanar da Baaba bashi da lafiya kada ta ji shi shiru. Nan kuwa karfin gwiwar hada ido da ita a daren ne bashi dashi. Abinci kala biyu ya gani a falonsa. Wanda ya tabbata daga wurin Baaba Mari aka turo ya tsakura kadan ya yi shirin bacci. Sun dan taba shawarwari da Munzali a waya sannan ya kwanta. *** Tafiyarsu Munzali ta gaggawa ta dagawa iyaye da 'yan uwan Alh Tahir wadanda Allah Yasa suka gamu dasu jiya hankali. Saboda haka suka dinga kiransa ana tambayar ko yaji daga garesu. Shi ma ya damu haka Mami Khadija da Mama Nasima. Wuraren tara na safe yaci sa'a Munzali ya dauki waya. TAKWAS GOMA BA BIYU. Tafiyarsu Munzali ta gaggawa ta dagawa iyaye da 'yan uwan Alh Tahir wadanda Allah Yasa suka gamu dasu jiya hankali. Saboda haka suka dinga kiran Alhajin ana tambayar ko yaji daga garesu. Shi ma ya damu haka Mami Khadija da Mama Nasima. Wuraren tara na safe yaci sa'a Munzali ya dauki waya. Munzalin kwanan zaune yayi inda yake ta tufka da warwara. An wayi gari kansa yana wani irin ciwo saboda rashin bacci da alhinin me zai faru tsakanin Abbati da Baaba Mari. Irin wannan lokacin sallah da kankantar da kai a gaban Allah SWT shi ne yafi dacewa da bawa. Sai aka yi rashin sa a munin dabi'ar da suka rayu cikinta ya danne tunaninsu daga shi har Abbati. Asalin kalmar da bature yake kira despire ita ce ta wanzu a kawunansu. Suna jin tamkar basu da sauran rabo. A duniyar sai sun ji kunya sannan a lahira da wuya su sami dacewa da rahama. Wannan shi ne tunanin kowannensu. Shi ne fargabar da suke da yakinin ganin ranar faruwarsa. Da farko bai yi niyar amsa wayar kowa ba sai ta Abbati. Amma karar kiran da ya shigo tamkar ana kada kararrawa a cikin kansa ya saka shi mika hannu ya daukota a gefensa. Katse kiran yaso yi tunda bai san nambar ba, bisa kuskure sai ya zamana ya amsa ne. "Alhamdulillahi ya dauka" Shi ne abin da Munzali yaji an fada daga dayan bangaren. Bai sha wahalar gane mamallakin muryar ba. Hakan ya tilasta masa tattaro duk wata nutsuwarsa ya gyara murya suka gaisa sosai. "Me ya faru jiya Munzali? Kun tafi kun barmu da fargaba. Ina shi Abbatin?" Murmushin fatar baki Munzali ya yi da ya hasko tonuwar asirinsu da irin yadda zasu wulakanta bayan rabuwa da masoyansu. Karya ce kadai rufin asirinsu kuma ita ya gilla kamar yadda suka saba domin kare kai. "Ku yi hakuri. Wan Baban Abbati ne aka kira babu lafiya ...." Alh. Tahir ya katse shi tun kafin ya gama da cewa "Subhanallahi, ciwon ya yi tsanani kenan duba da yadda ku ka tafi." "Eh suma yake yi kamar ba zai tashi ba." "Kuna ina ne yanzu?" Munzali sai da ya dauke wuta na wucin gadi kafin ya iya bayar da gamsashiyar amsa. A yadda suke dai bai kamata ya ce Abbati ne kadai ya tafi ba. Sannan idan ya yi gaggawar binsa yanzu bai san me hakan zai janyo ba. A takaice ma dai dole ya zauna domin ya dakile yunkurin da yake hasashen Alh. Tahir ya fara. "Muna Gumel nima aka kirani Qibdiyya ta fadi ana zaton karaya ce." (Da safe ranar ta fadi amma ko kuka bata yi ba) "Sannunku kaji. Ya jikin nasu?" "Kawu Sa'idu ya fara samun sauki. Qibdiyya kuwa mai kula da ita ce ta firgita. Buguwa ce kawai." Nutsuwar da Alh. Tahir ya rasa tun jiya ce ta dawo masa. Ya sake jajantawa Munzalin sannan suka yi sallama. Munzali har ya fara jin sanyi a ransa na rabuwa dashi lafiya sai ya sake kira. Bayan ya fada musu me yake faruwa ne Mama Nasima ta ce ayi musu kwatance zasu je dubiya. Ita a nufinta taje har gidan Munzali ta kara gane ina zata kai Mardiyya. Alh Tahir bai ki ba saboda shi ma baya son wadannan zaratan matasa su kufcewa zuri'arsa. Tunda Allah Yasa suna Kanon gara ma da aka yi haka. Sai suje domin a karfafa magana. "Amma ya dace muje gidansa? Babu mace fa a ciki. Idan akwai ma kuma ai bai kyauta iyayen wadda yake son aure suje duba mata 'ya ba." Mami Khadija ce taja hankulansu kan kuskuren zuwa gidansa. Mama Nasima sai ta hau borin kunya. "Mutum kullum burinsa ya nuna yafi mu sani da iyawa. Da an fimu din kuma da bamu zo gidan ba. Ki kwantar da hankalinki bance sai kinje ba. Yanzu nake shirin cewa a fada masa ya kaita gidan iyayensa sai muje can." Mami Khadija sai ta girgiza kai kawai. Ba don tayi magana ba tsaf gidansa zasu je. Yanzu kuwa ko don a bata kunya dole a canja salo. Ba bata lokaci Alh. Tahir ya kuma kiransa ya fada masa shawararsu. Suna gama wayar Munzali ya tashi a gaggauce ya fada bandaki. Cikin mintuna biyar har kaya ya saka. Yana makala links din hannun riga wayarsa tana gefen kunne ya danneta da kafada. Asabe ya fara kira ya tambayeta ko tana gida ta ce ta tafi sunan wata 'yar uwarsu a kauyen Kuyen Ta'inna da sassafe. "Idan zuwa zaka yi bari in taho gida yanzu. Ka san kauyen a cikin gari yake zan iso da wuri." "A'a yi zamanki. Zan zo da daddare ko gobe." A wurinsa gara ta zauna kada su hadu da Mama Nasima ayi abin da shi da Mardiyya zasu dade basu manta ba. Zara ya kira ya fada mata bakin da zai yi da matsayinsu. Asabe kuwa sai ta kasa zama. Idan kudi ne gara ta koma gida tayi masa waya ya zo ya kawo mata. Kada tayi sake goben ya ce ya taba. Takalmanta ta saka ta sallami maijego ta fito neman abin hawa. *** Yau ma Abbati ya kasa shiga bangaren Baaba Mari. Ya leka ya gaisar da kawunnansa. Ita kuwa yana zuwa kofar dakinta ya tambayi wani yaro dan wajen Habi ko ta tashi. "Ta tashi tun dazu. Kunu take sha." Kirjin Abbati ya sake matse zuciyarsa saboda tsoron hada ido da ita. Cikin hanzari ya ce da yaron "Tunda kunu take sha ka ce ina gaishe ta. Bana son shiga in katseta. Zan dawo anjima." Daga cikin dakin Baaba Mari tana sauraronsu tun farkon tsayuwarsa a wurin. Maganarsa ta karshe tasa ludayin hannunta ya yi mata nauyi a hannu. Abbatin da ko wanka take yi yana jiranta shi ne mai cewa baya son katse mata shan kunu? So take ya bata dalilin karyata duk wani zargi da ya darsu a zuciyarta amma ya kasa. Daga wayarsu ta jiya kafin yazo zuwa yanzu bai yi komai ba sai tarwatsa mata zuciya da fargaba. Akwai matsala ta riga ta sani sai dai bata san girmanta ba. Wannan shi ne tashin hankalinta. Tsayuwa Abbati ya yi a jikin bangon dakin ya kasa tafiya. Komai na duniya ya tsaya masa cak. Baaba Mari kawai yake so ta dube shi, duba na tsausayi da soyayyar uwa ta ce masa ta yafe. Ta roka masa rahamar Allah wadda a yanzu yake taraddadin samu. Idanunsa ya rufe sa'ilin da kwala ta cikasu har tasa suke zafi. A sanyaye ya juya zai tafi sai yaji wayar Baaba Mari tana ruri. Sautin ne ya dawo da ita daga duniyar tunani tayi saurin share kwallarta sannan ta dauka da sallama. Muryar mace mai kamala ce ta amsa mata cikin walwala da son janta a jiki. "Wa alaikum salam wa rahmatullah. Allah Yasa baki manta Khadija kanwarki ta Kaduna ba." Baaba Mari tayi murmushin jindadi "yaushe zan manta mace mai kirki da mutuntunta dan Adam kamar ki Mami Khadija?" Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Cikin sakan daya Abbati ya bayyana a gaban Baaba Mari a hargitse. Kallo guda taji ya matukar bata tausayi. Duk ya sauya babu komai a idanuwansa sai fargaba da tashin hankali. Bakinsa na rawa saboda bai san me aka ce musu ba tunda ya gama tsorata da Shazali ya ce, "Baaba kashe wayar don Allah" a hankali. Dauke kai tayi kamar bata ganshi ba tana tambayar Mami Khadija yara. "Kowa lafiya kalau Alhamdulillah. Ya mai jiki kuma? Jiya Abbati ya tafi ya barmu da fargaba. Ashe kawunsa ne babu lafiya." Kallonsa Baaba Mari tayi ta tabe baki. Abin har ya kai ga karya kenan. Shi da bai ma san abin da Munzali ya fada musu ba sai ya daburce ganin tana masa kallon tuhuma. Da bakinsa ya kasa hada kwakkwarar kalma balle ya yi magana sai ta cigaba da wayar. Rufa masa asiri tayi kamar yadda kowace uwa za ta yi ta ce "Ai jiki ya yi kyau sai hamdala. Tsorata muka yi shi yasa aka kira shi." Cikin jimami Mami Khadija ta ce "haka Munzali ya ce. An kira an ce yana suma ai dole hankula su tashi. Don Allah kiyi masa sannu." "In sha Allahu Mami. Mun gode sosai." "Haba ai an zama daya. Allah Ya kara hada kawunansu." Amin ta ce sannan suka yi sallama. Abbati ya kalleta cikin sauri ya sauke ido. Inda ya tashi ya koma ya gurfana gabanta hankalinsa ya sake tashi. Baaba Mari ta kasa tambayarsa komai. Tsoron amsarsa take ji ga kuma tausayin yadda ya firgice mata. A hasashenta ma daga maganganun Mami Khadija ta fahimci akwai alaka tsakaninsa da daya daga cikin 'yan matanta. Wayarsu ta karshe kafin zuwan Shazali dama ya fada mata akwai maganar da yake son yi da ita. Kawar da tunanin tayi domin bashi da muhalli a yanzu cikin damuwarsu. Can ta nisa tayi masa tambaya amma a sakaye. "Kai da Munzali sana'arku daya?" Sai da taji hadiyar yawunsa tare da hawa da saukar Adam's apple dinsa kafin ya iya bata amsa. "Eh" ya dora da cewa "amma wallahi Allah mun tuba mun daina" yana mai nunin girman maganar da yatsansa. Hannu ta daga ta dakatar dashi nata jikin yayi sanyi kalau. Kunnuwanta kuwa kamar an toshesu domin bata jin komai sai karar bugun fargabar zuciyarta. "Bana son jin koma mene ne Abbati. Duk wanda yake kan tafarkin gaskiya ya sani. Wanda ya saba ma yana sane. Ka tashi ka koma gida. Zamanka a nan ba zai karemu da komai ba." Samun kansa ya yi da fashe mata da kuka. Babu sauti sai dai ilahirin jikinsa duka rawa yake kamar an kwara masa ruwan sanyi. "A tare dake aljannata take Baaba. Idan kin yafe min ina sa ran samun gafarar Ubangijina." Nata kukan ta danne. Ya zama wajibi a gareta ta karfafi zuciyarta indai tana son danta ya sami karfin gwiwar tuban da yace ya yi. "Na yafe hakkina idan akwai a cikin sana'arka. Sai dai ban san yadda zaku yi da hakkin mutane ba." "Baaba ban fahimta ba." Ya tambayeta da dukkan gaskiyarsa. Rikicewarsa ta kai ya manta bata san ainihin sana'ar ba. "Ba da sana'arku ku ka yi kudi ba?" "Da ita ne." Ya amsa kansa a kasa. "Kuma sana'ar haramtacciya ce?" Kai ya sunkuyar ya gyada shi a hankali. Yanayinsa sai ya soma bata haushi. Yafi ta sanin me suke aikatawa to don me zai nuna mata rashin sanin girman laifin? Duk mai daukar kayan da ba nasa ba yafi kowa sanin hakkin wasu ne yake dannewa. Hakkin da sai an tambayeshi ranar lahira. "Kafi ni sanin cewa dukiyar haram ce kake kwance a kai. Idan akwai halin ka mayarwa wasu cikinsu dukiyoyinsu gara ka gaggauta yin hakan." Abinka da dan fari kuma mutum wanda tun asali bashi da saurin fahimtar abubuwa makamantan wannan. Da Munzali ne tabbas zai cigaba da tafiyar da Baaba Mari ne akan zarginta na cewa sata ce suke yi. Abbati kuwa cikin kidima da tsoron zargin da take musu sai cewa ya yi bai taba satar kudin kowa ba. Baaba Mari taji zuciyarta ta daka wani mugun tsalle a kirjinta yana fadin haka. Da sassarfa ta tashi ta tura kofar dakinta ta saki labule sannan ta dawo ta kama hannunsa suka zauna. Kallon ido cikin ido take yi masa cikin yanayi na fargaba da taraddadi. Muryarta a shake ta fito saboda nauyin tambayar da take shirin yi masa. "Yankan. Yankan? Kai? Yankan kai? Abbati ku 'yan yankan kai ne?" Bata jira amsarsa ba ta shiga yarfe hannuwa "na shiga ukuna ni Mariya. Abbati rashin imanin naku ya tsallake sata ya hada da zubar da jini?" Sakin hannuwansa tayi ta hanyar bigesu daga cikin nata tayi baya a zabure. Hakan yasa shi yaji kamar ba za ta kara son ya kusanta gareta ba. Ita kuwa zafi ta soma ji fiye da kima ga gumi yana tsatstsafo mata kamar an kunna famfo. Wannan kaddara da nauyi take. Dan cikinta ne a gabanta amma bata san shi ba. Tana tuhumarsa da daya daga cikin masifun wannan zamani amma yaki cewa komai sai ido da yake binta dasu. Tana hawaye ta doki gefen kirjinsa, cikin gunjin kuka ta ce, "Bakinka zaka bude kayi min magana. Wato da baka da niyar fadin gaskiya sai ranar da aka bukaci jininmu a kungiyar ...." "Baaba ki yarda dani wallahil Azeem bana cikin kowacce irin kungiyar asiri ko yankan kai" ya fada dalla dalla duk da kukan da yake cinsa domin ta yarda da gaskiyarsa. Komai ya kulle mata. Ta rasa tudun dafawa. Tsoron abin da zai fada yasa take jin gara ma ace satar ce. Sassauta murya tayi ta sake mika hannu ta damko hannunsa daya. Da dayan hannun nata ta share kwallarta sannan ta fuskance shi da kallo na tausayi garesu baki daya. "Fada min sana'arka!" Saukar aradu yaji. Zuciyarsa ta tsaya na 'yan dakiku kafin ta cigaba da bugu cikin yanayi na faduwar gaba. "Baaba...." Sai kuka. Kuka. Kuka...sannan ya fayyace mata komai tun daga haduwarsa da Munzali. Ko da ya gama ya sake kiran sunanta bata amsa ba. Dama kansa a duke yake sai ya dago a hankali. Shi take fuskanta amma ba shi take kallo ba. Bakin kwayar idanunta a birkice ya gansu, sun juye kamar babu su. Suman zaune tayi bai sani ba. *** Datar MTN ta dari uku wadda suke bayar da 1GB na kwana daya Danliti ya saka a wayarsa. Whatsapp ya bude cikin rashin sa'a bai ga sunan Ayaah ba. Guntun tsaki ya yi domin ya so ganin hotunanta yau. Kwana biyu kenan da zuwansa wurin dinner inda ya hadu da Suhaib amma har yanzu bai manta da fuskarsa ba. Sai da ya koma gida haushi ya ishe shi. Da gani ya girme shi wai amma shi ne ya yi masa barazanar da ta tsorata shi haka. "Idona idon matsiyaci sai na nuna masa tashancin 'yan Kano." Danliti ya yi kwafa gami da jinjina kai cikin bacin rai. Duk da cewa baya jin akwai wata mace da ta kama kafar Ayaah cikin matan da yake son mu'amala dasu, amma yaci burin samun hajiyar Kadunan nan wato Jiddo. Da bukata bata samu ba. Ya laluba babu halin ganin hoton Ayaah a yau. Sai kawai ya saka katin dari biyu ya kirata. Shirin fita suke ita da Murja zuwa gidan Innayo. Murja ce za ta yiwa Zara kitso kamar yadda ta fadawa Hasiya jiya. Shi ne ita kuma ta hadasu da Ayaah ta ce su tafi tare. Shake murya ya yi yana magana ciki ciki irin na mayaudara. "Baby nayi missing dinki da yawa. Anjima zan zo. Me ki ke so na taho miki dashi?" Ya fada a karshe don ya san ba za ta ce komai ba. Ita kuwa sanyi taji a ranta da sabon sunan da ya rada mata. "Babu komai. Fita ma za muyi da Murja." "Ina zaku je baki fada min ba? Nifa gaskiya bana son kina fita ana gane min ke. Da kin fada min sai na zo na kai ku. Anywhere dai ku jirani please zan taho now now." Satar kallon Murja tayi ta bar wurin da sauri kafin taji me yake cewa. "Ka barshi bani kadai bace. A gida fada za ayi min. Gidan kakanninmu zamu." A lissafinsa anci rabin kudin wayar sai kawai ya fake da nuna bacin rai ya mata sallama. Hankalinta sai ya tashi tayi maza ta kira shi da ragowar canjinta. "Kayi hakuri mana don Allah." Kamar ba zai ce komai ba har ta fara kosawa sannan ya ce "Naji. Amma har ku isa muna chatting. Ki kwatanta min gidan sai na sameku a can ko fuskarki na gani naji dadi. Da kudi a wayar ko na turo miki?" "Akwai" ta bashi amsa duk da ta san sun kare. A danja ta sayi kati ita ma na dari biyu ta saka ta tura masa amsar sakonsa wanda ya rubuta kamar haka, (Wane kaya ki ka saka?) (Atampa ce) (Kwatanta min daga sama har kasa domin naji kamar kina gabana.) Kwatancen tayi masa na riga da skirt da hijabin da ta saka mai hannu wanda ya zarta gwiwarta kadan. Abin bai yi masa armashi yadda yake so ba. Wanda a idon namiji mai mutumci zai ga tayi matukar kyau. Canja salo ya yi cikin kwarewa da iya hillata. (Da wane irin kaya ki ka fi son yin bacci?) Kallon wayar tayi kamar ba tata ba na dan lokaci har sai da Murja ta tambayeta ko akwai matsala ne. Dena juya wayar tayi a kasan ranta tana yi masa uzuri da cewa kila lefe yake tunanin fara hadawa. (Doguwar riga) Danliti yaja tsaki ganin taki daukar haske. (Ni kuwa kinga nafi son kwanciya da wandon bacci kadai. Idan ma sanyi ake nan gaba kadan na san kina kusa dani ba zai dameni ba. Kema ki shirya ba zaki zo min da doguwar riga bed ba.) Wani dumi dumi Ayaah ta fara ji. Ita kadai ta dinga tsarguwa ko Murja ta fahimci irin sakwanin da yake turo mata. Hirar ta daina yi mata dadi amma ta rasa me ya hanata dakatar dashi ko ta daina bashi amsa. Wani sakon ne ya sake shigowa sai da ta dan zabura da ta karanta. (Ina son mace mai kunya. Shirunki yasa na kara sonki. Amma fa ki sani nan gaba kadan zaki nemi kunyar ki rasa. Zaki fara rungumeni da kanki ba sai na nema ba. Kafin aurenmu ina son mu sake da juna sosai ta yadda tun yanzu zamu san abubuwan da zasu faranta mana.) Ayaah bata iya sake tura masa amsa ba. Tambayoyin nauyi suka yi mata. 'Yar fara'ar da ta soma ta nema ta rasa. Danliti da kansa ya gano zai yiwa kansa sagegeduwa ta wannan hanyar. Kifin rijiya ce ba kamar yadda ya yi zaton irin makwadaitan 'yan matan nan bane masu mummunar wayewar zamani a soro. (Kiyi hakuri Baby. Ina jin kamar na dauko hirar da bata kamata mu fara tun yanzu ba. Ina tsananin kewar irin wannan kusancin da iyalina. Ke kadai ce zan iya fitowa da damuwata hankali kwance domin nayi imanin zaki saurareni kuma ki fahimceni. I love you) Shi kenan! Kyakkyawan tunanin da ya fara ginuwa a zuciyarta ya rugurguje da sakonsa na karshe. Tausayinsa ya sake kamata. Ta kara jinsa a rai fiye da kullum. Matarsa kuma ta sha bakaken addu'o'i domin har gani take ba don haduwarsa da ita ba kila da yanzu ya fara bin matan titi. * Dubu ashirin Alh. Tahir ya baiwa Mama Nasima domin yiwa Qibdiyya sayayyar dubiya. Ita da Mami Khadija zasu je. Sai 'ya'yansu. An nemi Jiddo a waya bata dauka. Tana can gidan wata 'yar kungiyarsu 'yar Kano an kawo musu samari suna keta dokar Allah. Ta gama tsara karyar da zata yi idan ta dawo kafin lokacin tafiyarsu Kaduna. Mota biyu suka yi. Daya direban gidan da ake bikin ne yake jan Mama Nasima da Mami Khadija tund shi dan gari ne.Ta bayan kuwa motar gidan Alh. Tahir ce. Suhaib ke tuka kannensa suna biye dasu a baya. A son ran Mami Khadija su

Chapter 35 of 62