a dawo a kwashe kayan gidan.
Hankalin Ale Gambo sai lokacin ya tashi da yaga sun fara fita. Mutane irinsa masu mulkin mallaka ga wadanda suka fi karfi basu fiye son a gudu a barsu ba. Duk wannan power din da yake takama da ita dama na samun wuri ne a jikin Salima. Yau da tayi bore sai yake jin yafi kowa kaskanci. Kiran sunanta ya dinga yi da karfi da kalaman tsoratarwa akan irin hukuncin da zaiyi mata idan ta dawo.
Babu wanda ya waiwaye shi har 'ya'yansa. Innayo ce kadai ta dakata sai da iyalinta suka fice sannan ta dawo inda yake tsaye an daure masa hannuwa ta wanka masa wani irin gigitaccen mari. Kamar an dauke wuta haka mazan da suka yi saura a wajen suka dauke numfashi. Shi kuwa hantar cikinsa sai da ta kada domin bai taba zaton za ta iya yi masa wani abu sama da mugun kallo ba.
"Idan takamarka wanda ya baka aurenta bai san darajarta ba shi yasa kaima kake takawa to kayi karya. Muddin ina numfashi da yardar Allah ka gama taba lafiyar Salima. Shari'a kuma akan hakkinta da ka dade kana dauka ko zamu shekara anayi in Allah Ya so ba za mu karaya ba."
Juyawa tayi ta fita ran ta yana kuna. A bakin kofa suka yi kicibis da 'yan sandan da aka kira. Haka suka bi bayansu domin sun ce dole Salima taje ta bada statement kafin su daure shi.
*
Daki guda Abbati ya zage da kansa yana gyarawa Baaba Mari. Gidansa kato ne. Akwai rashin adalci idan aka ce matar gidan kullum sai ta bi dakuna da bandaki ta gyara. Shi yasa ya sa rai da ganin kura kadai ta rashin amfani. Shi ma kuma ko don kada kaya su lalace a kalla ko sau daya a sati ne ya kamata ace an share. Sai ya sha mugun mamaki. Datti dakal-dakal ya tarar da kura harda yana. Basu fiye bakin kwana ba saboda kishinta duk da masu zuwan duka 'yan uwansu ne. Bandakin kuwa harda kwari suna yawo wasu kuma sun mutu. Bawan Allah bai hango laifin kowa ba sai nasa. Da bai salwantar da rayuwarsa wurin yawo ba kila da yafi kula da lamuran gidansa. Yanzu kuwa ko sannu bai samu ba daga Hanne tayi hayewarta sama.
'Yashshafa ma duk shirmenta sai da taga rashin dacewar haka. Dukkaninsu sun gaji musamman Hannen da tayi jeka ka dawo a rana daya. To amma har ace ta manta mijinta a ranar aka sallamo shi daga asibiti? Akalla ko da ba yi za ta yi ba ai ta nuna masa cewa tana da hankali ta hanyar cewa ya bata tsintsiyar ta share. A yadda ta fahimti Abbati ta san da kansa zai ce taje ta huta. Jinjina kai tayi ta tashi daga kan doguwar kujerar da ta dan kwanta tabi bayansa bayan ya wuce da tsumman goge-goge.
"Ina zaki kuma?" Deluwa ta tambayeta da sauri.
"Karbar gyaran dakin zan yi."
"Dawo ki zauna ai ba sanin darajarki ya yi ba. Na gano miki miji dan gidan arziki ba taka haye irin na wasu ba."
Ta furta tana kai dubanta ga Baaba Mari wadda maganar ta yiwa dirar mikiya. Ko a farcenta don Deluwa ta hana 'yarta taya Abbati gyaran daki. Abin da ya tsaya mata bai wuce kiransa wanda ya yiwa arziki taka haye ba. Kenan ba ita kadai sauri da habbakar arzikinsa yake yiwa kai kawo a kirji ba? Kamar Deluwa taji tunaninta ta bata amsa tana faman tabe baki.
"Kar fa kiji haushin maganata Mari kin san ba karya nayi ba. Almajiri da tamfatsetsen gida irin wannan akwai ayar tambaya. Anata cewa yana kasuwanci gashi har rana irin ta yau bamu taba ganin samfurin hajar tasu ba."
Baaba Mari bata iya cewa uffan ba har Habi ta shigo daga bangaren Munzali inda aka yi musu masauki. Daki ya basu a cewarsa bai yarda su dawo tare a barshi a nasa gidan shi kadai ba. Iya Kande ba zama take sosai ba indai Qibdiyya bata nan.
Habi ce ta karbi gyaran dakin a wurin Abbati shi kuma ya hau sama. Deluwa ma da 'Yashshafa suka shige dakin da aka basu suna jiran kuku ya gama girki.
Tunani, damuwa da zancen zuci aka bar Baaba Mari tana yi akan tarin dukiyar Abbati. Kasantuwarsa dan fari ba shi ne ya sanya soyayyarsa tafi ta 'yan uwansa a zuciyarta ba. Saukin kansa wanda mutane musamman na gidan suke amfani dashi wurin cusguna masa tun kuruciya ne. Tunda aka gane lagonsa ake saka shi kuka. Tun tana kawaici har ta koma musayar yawo da duk wanda zai taba shi saboda bashi da baki. Wannan saukin kan yasa ta guji ya tafi almajiranci. In an barta ma za ta ce wannan halin zai janyo masa wahalar rayuwa fiye da a gabanta. Sai gashi abin mamaki maimakon ci baya sai ya yi gaba. A gaban ma ya yiwa da yawa fintinkau. Wata irin zabura tayi ta mike lokacin da taji takunsa yana saukowa daga sama. Haka ta kura masa idanu tana kallonsa cike da firgici. Tsoron yarda da hasashenta take yi. A cikin zuciyarta take addu'a kamar haka.
"Ya Allah Kasa ba sata ko fashi yaron nan yake yi ba."
BIYU IDANUN...
***
Su uku ne zaune a dakin Alh. Rabi'u. Shi, Innayo da Asabe. Tray din abinci ne a gabansa yana ta kwasar girki yana gumi. Hannun malum-malum dinsa yasa ya goge shi bayan gama ya janyo tsintsiyar kwakwa a gefen gadonsa. Dan tsinke ya karyo ya danna a baki yana sakato naman da ya makale yana tofarwa.
Magana ya kirasu suyi wadda gabadaya akan 'ya'yan Innayo ne. Shi yasa taji haushin kiran Asabe da ya yi dakin nasa. Ta san ya yi ne domin neman fada a wurin Munzali tunda dan Asabe ne. Duk tsiya idan ya kyautata mata ta hanyar nuna mata gazawar Innayo za ta yiwa Munzali magana akan bukatunsa. Ya kula yanzu bakin gwargwado Munzali yana dan yi mata magana da tattausan lafazi.
Hirar arzikin Munzalin ya dauko suke ta yi da Asabe har sai da Innayo ta magantu.
"Zan koma idan kun gama tadin ayi min magana."
Mikewa tayi abinta za ta fita Alh. Rabi'u ya dubeta fuska a hade kamar ba shi ya gama yiwa Asabe dariya ba.
"Bakin halin da ki ka koyawa 'ya'yanki za ki gwada min?"
Dadi ya kama Asabe ta karbe zancen don ta kara zuga shi.
"Ka dai bi a sannu kar ka manta da bakinka ka fada min Ale Gambo ya ce ta mare shi."
Kamar an kunno shi kuwa ya hau masifa yana fadawa Innayo maganganu.
"Banda lalacewa ace har kin iya dora hannuwanki a fuskar baligi kamar Ale Gambo kamar baki san haramcin yin hakan ba?"
Saboda yadda take jin ta muzanta sai take gani kamar tsirara ya yi mata a gaban matarsa. Jikinta ya yi sanyi kalau yayinda zuciyarta take tafarfasa. Haka nan idanunta suka rine da bacin rai mara misaltuwa.
"Yanzu Alhaji me ya kawo magana irin wannan? Gambo tamkar dan cikina fa yake tunda ya auri Salima."
"Tamkar 'yar cikinki dai...ke da baki san ma'anar haihuwar namiji ba ina ke ina kwatanta dan wata da naki?"
Asabe ce tayi maganar dankwalinta a gaba tana neman takalar fada. Haushin yadda su Munzali ke bin Innayo take son fanshewa.
"Fada mata dai. 'Ya'yan da ta cusawa kiyayyata basa ganin girmana. Gashi tun ba aje ko ina ba an fara dawo min gida."
Asabe ta murmusa cike da jindadi.
"A'a fa Alhaji. Kar kayi butulci. Nima shaida ce ana kawo maka dari da kwabo idan Hasiya mai lalle tayi ciniki. Su kankamoji (Zara da Uwani) dai ko ita sha-wuyar basa bawa."
Dariya suka kwashe da ita wadda tayi sanadiyar zubowar hawayen da Innayo take ta kokarin dannewa. Habar zaninta ta saka ta goge idanunta amma haka wani hawayen ya maye gurbinsa. Dan kuka mai ja wa mahaifiyarsa jifa. A haka ta fita tana jiyo sautin dariyarsu.
Bata karasa dakinta ba ta juyo a fusace ta koma dakin Alh. Rabi'u. Tuni ta fahimci cewa sadaukarwa da hakuri daban suke da kawar da kai. Ta sadaukar da kuruciya, lafiya da jindadinta a bautar aure da kula da yara. Tayi hakuri da rashin kyautatawar miji da wasu cikin 'ya'yanta. Duka wadannan akwai riba a duniya da lahira. Amma kawar da kai akan abubuwa na bacin rai kam cutarwa ne gareta dasu wadanda take kyalewa. Anyi abin da aka yi a baya. Yanzu kuwa daidai take da kowa. Bata da nufin cutar da kowa, sai dai ba za ta yarda tayi ta hadiyar bakincikin kowa ba.
Bankada labulen tayi ta shiga ta zauna a gaban Alh. Rabi'u. Hannayensa duka biyu ta kamo ta shimfida tafukan akan fuskarta. Asabe mamaki ne ya kamata na zuci da zahiri. Shi kuwa sai ya sami kansa da shiga taitayinsa ya kasa yi mata magana.
Cikin muryar lumana babu wani hargagi kamar yadda ta yiwa su Zara ta soma magana.
"Kaji dumin hawayena?"
Ya gyada kai kamar sakarai.
"Bai kama kafar zafin zuciyata da barazanar bugawar da take a kirjina ba. Alhaji...."
"Na'am" ya amsa da rawar baki.
"Allah zai bi min hakkin hawayen da na zubar maka ba da hakki ba."
Ta tashi ta juya za ta fita sai ta tsaya ta kara da cewa " 'ya'ya amana ne kuma daidai iyawata nayi kokarin sauke wannan amanar. Ba komai da nayi bane zai zama daidai amma nayi imanin Allah zai sakawa kokarina. Zai shirya min 'ya'yana. Zai daidaita min lamurana."
Da ta koma dakinta duka 'ya'yanta suna nan harda Uwani da ta shigo bayan fitarta. Kare musu kallo tayi daya bayan daya tana tuna ranar da ta haifi kowacce. Uwar dakin ta shiga ta barsu ba tare da ta amsa maganganun da suke yi mata ba. Hannu na rawa ta tura kofar ta rufe da sauri sannan ta zube a kasa saboda zafin kirji. Miji babu dadi, kishiya ba zaman lafiya, 'ya'yanta kuma kowacce da tata matsalar. Matsalolin nasu da suka zame mata abin tunani da shiga damuwa.
Kwana biyar kenan da ta dauko Salima. Ga Zara har yau mijinta bai zo ba. Maimuna nata mijin ya ce ya gaji da yawan zarya da take yi zuwa gidan iyayenta, ga talaucinsa da yafi na Ale Gambo. Uwani tun washegarin zuwan Ummule ta fada mata anyi mata kishiya. Gabadaya ta sauya tana neman susucewa. Sai dai taki fada mata ba zuwan kishiyar bane kadai damuwarta ba. Kudin da take yawan cewa babu ta nema ta rasa. Ta kuma kasa cigiya a gida saboda babu wanda ya san dasu. Hasiya kuma nauyi ya mata yawa. Bata morar kudin sana'arta ko kadan yanzu. Duk ta rame saboda wahala da rashin isasshen bacci. Sannan rashin haihuwarta yana matukar damunta.
Ita ce uwa garesu. Bata hango ranar hutun jiki da na zuciya ba kila sai ta bar duniyar.
Alh. Rabi'u da Asabe kuwa har Innayo ta ware a dakinta basu dawo daidai ba. Maganarta takaitacciya ce amma ta zauna saram a kwakwalensu.
***
"Kace masa Habu ne."
Masinjan ya bishi da wani irin kallon kwaf kafin ya ce "Habun ai da yawa. Baka da inkiya ko cikakken suna?"
Honorable ya yi dan murmushi don fushi ba nasa bane. Satinsa guda yana zuwa ma'aikatar wurin shugabansu Alh. Bala ana jirga shi. Ba kuma zuwan kansa bane. Mutumin ya kasance abokinsa lokacin da yake da abin hannu. Tunda ya sami karayar arziki bai taba bibiyar tsofaffin abokan huldarsa neman taimako ba. Wulakanci ne baya so. Yanzu ma dole ce ta kawo shi. Ya boyewa duka iyalinsa ne musamman Hasiya amma likitan da yake duba Abbas a asibitin kwakwalwa na Dawanau ya tabbatar masa da cewa idan ba ayi masa aiki cikin kankanin lokaci ba da wuya ya warke ko anyi. Jijiyoyin da suka sami matsala sun fara gajiya a yanayin da suke ciki. A wannan yanayin ne ya hadu da tsohon abokin nasa a wajen daurin aure. Bai yi kasa a gwiwa ba ya nemi taimako kuma ya yi sa a ya amsa masa. Fatan samun warakar Abbas din shi ne albishir din da yake ta boyewa Hasiya. Sai gashi har yau ko ciki bai sami shiga ba. Kullum da abin da ake fada masa. Yau ne ma ya yi sa'ar haduwa da masinjan Alh. Bala din shi ne har aka tambayi sunansa.
"Habu Danmalam za ka ce masa. "
Masinjan ya sake kura masa ido kamar me neman wani abu. Cikin 'yan dakiku ya sanya hannu ya bugi kansa da takaicin rashin gane shi da wuri. Sakin fuska ya yi sosai ga mamakin yanayin da ya ganshi.
"Habu Danmalam dai da na sani?"
"Ni ne" ya amsa da murmushi.
"Ikon Allah. Ai wallahi da na san kaine da tun zuwan farko nayi cuku-cukun hada ka da Yallabai" Hannu ya mika masa suka gaisa ya ce " Amma ina zuwa. Bari naje na fada masa idan Minista ya tafi sai ka shiga."
Wani karamin ma'aikaci a wurin yana jin furucin masinjan ya janyo shi gefe.
"Yallabai fa ya ce kada a bar kowa ya shiga yau. Idan Ministan ya tafi shi ma tashi zai yi."
Honorable Habu yana jinsu ya ja gefe da nauyin zuciya. Gwargwadon iyawarsa bai yi amfani da mukamansa na baya ya wulakanta kowa ba. Amma duk da haka yanzu idanunsa sun kara budewa da bambancin masu mukami da talakawa. Mafi yawan masu kawo korafi basu da yadda zasu yi ne. In an barsu ba za sy zabi kaskantar da kai suna roko ba. Amma sai su keta billensu suyi rokon bayan an hanasu a kara da wulakanci.
Masinjan ya amsawa mutumin da cewa "Honorable Habu Danmalam ne fa."
"Kai ka san shi" cewar wancan irin 'yan rijiya ta bayar guga ta hana dinnan.
"Ni kuwa na san shi. Kuma Yallabai ma ya san shi domin tare suka yi siyasa."
Bai kara saurarar mutumin ba ya wuce cikin ofishin Alh. Bala. Ya san suna tare da Ministan (Land, Housing and Urban Development) sai dai kuma idan har bai sanar dashi bakon nasa ba karshenta ya fice ta baya idan sun gama tattaunawa.
Sallama ya yi ya sake gaishe da Ministan kamar ba shi ya yi masa rakiya har nan din ba.
"Yallabai dama na ce bari na leko ko kuna bukatar wani abu."
"Idan ina bukata ma ai ka san Surayya (sakatariyarsa) tana nan."
Masinja ya gyada kai
"Eh haka ne kuma. To ku tashi lafiya." Juyawa ya yi kamar zai tafi sai kuma ya dawo "af...Yallabai kar na manta kana da bako fa."
Alh. Bala ya kirne fuska saboda wannan shishigi zai iya sawa ya rasa alkhairin da Ministan ya zo dashi. Hannuwansa ya dora akan teburin gabansa yana maganar da babu kofar ja'inja cikinta.
"Ba zan ga kowa ba idan mun gama tafiya zan yi. Ko waye ka ce ya dawo gobe."
Ya san za a rina shi yasa ya ce "babu komai. Yau da gobe duk daya ne. Don ya kara kwana daya akan ragowar kwanakin da ya yi yana zuwa babu matsala."
Wani mugun kallo Alh. Bala ya jefa masa kafin ya kai ga ambaton sunan bakon a dole ya fita. Addu'a yake shi kadai yana fatan bai yiwa kansa sanadin aiki ba.
Sai bayan fitar Masinjan Minista ya ajiye karamin kyakkyawan kofin shayin da yake rike dashi tun shigowarsa. Yadda ya buga kofin ya tayar da hankalin Alh. Bala domin alama ce ta bacin rai.
"Kayi hakuri Ranka ya dade. Na san ka ma fini haduwa da 'yan maula masu hana mutane hutawa. Mutumin da ya zo din na san ba kowa bane illa wani tsohon dan siyasa da muka zauna jam'iyya guda a baya. Gwamnatin da ta maye gurbin tamu tun a wancan lokacin tayi watsi dasu. Shi kuma bai iya kwantar da kai irinmu ba...hahahhha"
Har lokacin fuskar Minista babu wani annuri sai ya dora da,
"Harda laifinsa gaskiya da ya kasa samun wani mukami da aka sake samun canji tsohuwar gwamnatinmu ta dawo. Ya dauki girman kai da dagawa shi a dole mai tsantseni. Ashe abin nasa duk buge ne, gashi daga haduwa wurin daurin aure ya makale min."
'Allah na gode Maka da Ka nuna min waye Alh. Bala tun kafin na sanar dashi makasudin zuwana.' Furucin Minista kenan a zuciyarsa.
Idan yawan aiki ne da yawan 'yan maula ya ninka Alh. Bala nesa ba kusa ba. Sai dai shi mutum ne da ya tsani wulakanci. Tarba mai kyau wadda ta dace da matsayinsa ya samu kuma akan idonsa wani ya sami kishiyarta. Wannan abu ne da ba zai iya dauke kai ba. Maganar aure ce ta kawo shi. Ya hadu da wata yarinya a gidan abokinsa wadda bayan gajeren bincike aka fada masa 'yar Alh. Balan ce. Muradinsa na son auren mata biyu yaso cikewa akanta. Dalilinsa kenan na zuwa ya same shi saboda shi mutum ne mai tsari. Ba ya son ya fara yi mata magana a waje ta amince saboda mukaminsa bayan akwai wani. Halin mahaifin nata da ya gani yasa shi yanke shawarar zurfafa tunani da bincike.
Tashi ya yi ya gyara zaman babbar rigarsa.
"Ba dai tafiya ba? Bamu tattauna maganar da ka ce mai mahimmanci bace ba ma" Cewar Alh. Bala shi ma yana tashi tsaye.
"Kada ka damu zan kira ka a waya. Ina da appointment ne da naso mantawa dashi gashi har lokaci ya kusa."
"Au tohhh..." Alh. Bala ya ce yana sakin fuska "ai na zata zuwan dan anacen can ne ya bata maka rai."
Minista bai ce komai ba har suka fito waje. Alh. Bala kuwa sai zuba masa surutu yake yana ta kwantar da kai kamar ya durkusa masa.
*
Da Masinjan nan ya fito bai iya komawa wurin Honorable Habu ba. Zaman jiran bai dame shi ba. Ya zabi ya fadawa zuciyarsa aiki ne ya yiwa Alh. Bala yawa ba wai da gangan yaki ganinsa ba.
Tashin wasu security da sassarfa suna komawa wurin jerin wasu bakaken motoci da ya samu a wurin yasa shi kallon hanya. Farinciki ya wadatu a fuskarsa yayinda ya yi tozali da Alh. Bala. Da sauri ya tashi yana son yi masa magana kafin ya shiga mota. Da ya tashi sai yaga ba shi kadai bane ya nufi Alh. Bala din da wanda suke tare. Sai kalaman fadanci ake ta zubawa ana cewa
"Allah Ya kiyayeka"
Da dai ya gane ba da ubangidansu suke ba sai ya kalli abokin tafiyar sosai wanda shi ma kallonsa yake yi. Baki ya hangame sai kuma dariya da murna suka hana shi magana.
Ministan ne da kansa ya ambaci sunansa cikin wani irin shauki da kewa.
"Habu Kansila? Honorable Namu? Kai ne?"
Honorable ya dinga gyada kai har suka cimma juna. Hannuwansa Minista ya rike yana ta murmushi.
"Abdulkarim kaine haka?"
Sunkuyar da kai ya yi na kunyar rashin kyautawarsa kafin ya ce,
"Naji kunya sosai Honorable duk da dai wallahi na nemeka sosai bayan dawowata aka ce ka bar unguwar. Laifina shi ne na rashin mayar da hankali wurin binciken inda ka koma din."
Alh. Bala sai yaji kamar an sare masa gwiwoyi. Alamun sanayyar dake tsakaninsu barazana ce a gareshi. Hanyar da suka baro ya nuna da hannu yana kiransu.
"Ku zo mu koma ciki don da alamu kuna bukatar zantawa cikin sirri."
Minista Abdulkarim Mamman Diso bai bashi amsa ba sai nunawa Honorable motar da zasu shiga ya yi.
"Bismillah. Kodayake ban tsaya naji uzurin da ya kawoka nan din ba."
Honorable ya kalli Alh. Bala ya kawar da kai
"Wanda nazo gani bai saurareni ba"
Da haka Minista ya gane shi ne wanda yazo ganin Alh. Bala.
A motar suna tafiya Minista yake sake bashi hakurin yankewar zumuntarsu. Ba abokai bane domin kuwa Honorable ya girme shi nesa ba kusa ba. Lokacin da yake ganiyar cin zamarsa ne su Abdulkarim suka fitini unguwa. Rashin kudi ya hana iyayensa tura shi makarantar gaba da sakandire. Kafin wani ya kai zancen kunnuwan Honorable Habu shi ya gani da idanunsa. Har gida ya tura aka kira masa iyayensu maza ya ce zai dauki nauyin karatunsu shi da abokansa su uku. Haka kuwa aka yi. Suka sake JAMB cikin ikon Allah shi kadai ya haye. Yaji dadi sosai ya biya masa kudin karatun. Abokan masa kuma ya basu jari.
Rayuwa tayi ta tafiya har ya kammala digirinsa na farko. Honourable Habu ya soma cuku cukun nema masa aiki sai ya sami tallafi na zuwa kasar waje karo karatu. A can ya zauna ya yi masters da Phd. Kuma nan ne dai ya hadu da dan wani mai bawa shugaban kasa shawara. Da taimakonsa aka sama masa aiki ya fara yana dawowa. Ya nemi Honorable Habu a ranar da ya sanya kafarsa a unguwarsu Diso sai ya sami labarin ya tashi. Da zuci zucin ya kara nemansa ya koma Abuja. Daga nan kuma kujiba kujibar duniya da kai kawo suka dauke masa hankali. Sai gashi sun sake haduwa a inda bai yi zato ba.
"Ina su Abbas kuwa? Ya gama karatu yanzu ko?"
Tambayar sai ta zama fami ga Honorable. Nan ya labarta masa halin da suke ciki.
Abdulkarim sai ya kara jin haushin kansa. Bai ce masa komai ba amma tuni ya gama yanke shawarar irin taimakon da zai yiwa Hoborable da iyalinsa.
***
A gidan Alh. Tahir kuwa Mami Khadija ta cigaba da shirye shiryen bikin autansu. Mama Nasima kuma ta matsawa Mardiyya lamba da tambayar yaushe Munzali zai dawo.
"Kinga ya tafi kafin mu samu ayi maganar da ta dace. Ni ba so nake kuyi ta batawa juna lokaci da hirar waya ba." Ire iren zantukanta kenan kullum.
Ita kuwa Jiddo ta shiga tsaka mai wuya a wurin kawaye. Karyar da ta zuga musu akan hadin kai da jindadi da ta samu a wurin Danliti makanike ce take neman tarar da ita. Mutum biyu cikinsu kuma harda shugabarsu a ciki sun nemi ta hadasu dashi. A cewarsu harka da talakawa marasa galihu tafi dadi. Komai kika yi musu yanzu sai su ji kamar duniya babu kamar ki. Ladabi da biyayya da kuma bin hanyoyin farantawa mace sai kin zaba kin darje. Sannan uwa uba sun fi rike sirri.
Zancen da ake yanzu dai shugabar tasu tana son yaje Abuja ya sameta sati mai zuwa. Mijinta zai yi tafiya kasar waje kuma tana da yakinin da daya daga cikin 'yan matansa zai tafi. To ita ma ta kirkiri tata tafiyar ya kuma amince. Nan kuwa dan gidan holewa ta saya ba tare da saninsa ba inda take kai kwartayenta. Dubu hamsin ta turawa Jiddo ta ce ta bashi ya yi kudin mota.
Jiddo ta rasa inda za ta saka kanta. Tun ranar da ta tura masa hotuna bai kara nemanta ba. Ta saka masa kati na dubu goma babu godi bare na gode. Yanzu kuma har shugabar wadda ake yiwa lakabi da Sarauniya ta fara cewa idan ma taki hadasu ne saboda tana kishinsa zasu saita mata zama. Ai ta san dokarsu babu rowa. Kowacce tana da damar neman saurayin 'yar uwarta. Shi yasa ma suke fadawa juna yadda ta kaya ko wata za ta so.
Uban gayya Alh. Tahir kuwa yana cikin fushin Yakumbo. Ya tsayar da duk wata magana ta auren Yumna saboda abin da tayi masa. A yadda ya tsara idan an fasa akalla nauyin Farha zai ragu a ransa har ya samu su yi magana. Rabin hankalinsa a kwance yake tunda sauran 'ya'yansa babu wanda ya canja masa fuska. Ya san bata fada ba. Ita kadai ce dai har yau bata yarda sun hadu ba. Motsin motarsa ma idan taji daki take shigewa ta kulle kofa.
Yakumbo kuma tayi rantsuwar idan bai auri Yumna ba to ya shirya ganin bacin rai domin babu shi babu ita.
A can wani bangare na zuciyarsa wanda soyayyar 'ya'ya ta rinjaya sai yake jin gara fushin Yakumbo akan na 'ya'yansa. Yakumbo uwa ce. Uwa kuwa a saninsa za ta iya jure komai kuma ta hadiyi komai domin 'ya'yanta. Idan ta kama ya yi mata kuka ne ma zai yi don ya san za ta yafe masa ta janye zancenta.
*
Dan madaidaicin akwati mai taya hudu Farha ta daga ta saka a booth din motarta. Idanunta ta kai kan motar Abbati wadda take lullube a wurin ajiye motocin gidan taji zuciyarta ta harba. Zai yau zai zo gidan daukar motar amma ba zai sameta kamar yadda tayi masa alkawari ba. Sakon da ya turo mata jiya da daddare ta sake maimaitawa a cikin kanta a hanyarta ta zuwa wurin Maminta.
(Zan zo mu yi magana Ya Farha. Maganar baki da baki kafin nayi shirin daukar mataki na gaba wurin mallakawa Auwal muradinsa. Kin mamaye ko'ina a tare dani. Allah Yasa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 28 Chapter of 62