Hukunci ya zama wajibi sannan shi din bashi da hurumin hanawa.
"Bari na baku wuri"
Bai jira yaji abin da zasu ce ba ya fita daga falon. Haka Ayaah ta rarrafa gaban babanta ta kama kafafunsa tana kuka. Hakan bai hana shi tureta ba ya daga hannu zai mareta Abdulkarim ya hana.
"Bata kyauta ba amma don Allah kayi hakuri. Mace kamar wannan ta wuce ladabtarwa da duka"
"Inji wa?" Cewar Larai tana face majina "yau ba don yaron can dan albarka ba da yanzu muna cizon yatsa"
"Duk da haka dukan bashi da amfani. Kamata ya yi mu godewa Allah da Ya tsare mutumcinta"
"Sai kuma ayi mata me bayan addu'ar? In kyaleta gobe ma ta bi wani katon banzan?" Honourable ya tambaya cikin fushi.
Kafafunsa Ayaah ta sake dafawa ta ce "Don Allah kayi hakuri Baba ka yafe min. Wallahi ba zan kara ba."
Girgiza kai ya yi da disappointment karara a fuskarsa "kin bani mamaki Ayaah. Kamarki ace kin iya hada baki da namiji ya zo makaranta ya daukeki. To ma wa ya san tun yaushe hakan take faruwa?"
A gigice ta dora hannu a baki tana rantsuwa "wallahi yau ne kadai."
"Kina tunanin zan yarda ne?"
Bata fuska Larai tayi "ban gane ba Habu, me kake son cewa? Tun dazu nake ta bata laifi tunda na san bata kyauta ba. Amma ba zan zuba ido ka jefeta da kazafi ba." Ta juya bangaren Anti Hasiya "dama na fada da sa hannunki akan abin da Ayaah tayi. Banda haka wace uwa ce zata kasa gane irin wadannan abubuwan? Da ace kina kula da marayun nan ai da kin fahimci abin da take yi tun kafin ya yi nisa. Ki bari ki haihu din kafin ki wargaza rayuwar 'ya'yan gidan."
"Maganganu irin wadannan basu dace da gab'ar da muke kai ba Larai." Innayo ta furta cikin lumana. Na farko Honourable Habu suruki ne sannan ga bakonsa. Bai dace magana irin wannan ma ta raso a yanayin da ake ciki ba. Sannan ta gaji da daure zuciyarta kan kalaman Larai akan Hasiya. Tana tsoron kada a kai ta bango ta rama duk su taru su bawa kansu kunya.
Mayar da kallonta tayi ga Ayaah ta ce "ina ji a jikina abin da ya faru yau ya isheki darasi da ishara akan rayuwar da kika so jefa kanki a baya. Ki kiyayi maimaituwar yau din a rayuwarki domin duk ranar da namiji a sami galaba a kanki walau da son ranki ko babu indai babu aure a tsakaninku ya cuceki har abada. Wani tsautsayin kirawo shi ake yi da sakaci. Allah Ya kiyaye gaba."
Amin suka amsa su duka har Larai din. Abdulkarim ya yi murmushi a ransa yana kara yabawa da tsatson da Hasiya ta fito wanda ya yi tasiri akan 'ya'yan Honourable. Dolensa ma ya zage damtse akan Ummita don bai ga wadda ta dace ya nema da gaske ba kamar ita.
Innayo sallama ta yi musu ta ce zata tafi. Honourable sai ya ce yana son su zama shaida akan hukuncin da zai yankewa Ayaah. Jin batunsa Anti Hasiya da Ayaan suka dinga bashi hakuri. Suna cike da tsoron abin da zai ce. Sun san shi mutum ne mai hakuri da kawaici amma bashi da dadi idan ya kai bango. Ummita da Murja yasa Ayaah ta fita ta kirawo masa. Babu bata lokaci sai gasu duka a tare kowacce ciki ya duri ruwa. Fadan baban nasu bashi da dadi ko kadan.
"Ku zama shaida" ya ce dasu Innayo, "ban yarda Ayaah ta sake fita in ba tare da wani daga cikin gidan nan ba. Makaranta ma in sha Allahu ta bar zuwa sai ranakun jarabawa. Shi ma da kaina zan dinga rakata na daukota. Sannan in sha Allahu sati daya da gama jarabawar Ayaah zan aurar dasu. Duk wadda bata da manemi zan samar mata kafin lokacin. Ke kuma..." Ya nuna Murja "ki fadawa Mahiru tunda dama ni suke jira. Ku tashi ku tafi."
Murja ta mike. Ayaah da Ummita suka kasa kwakkwaran motsi. Maganar abin da bai fi wata uku ake ba. Kuma basu da maneman a hannu. Anti Hasiya ma maganar dirar mikiya tayi mata. Ayaah kam tayi laifi mai girma sai dai ko kusa ba za ta yarda ya yiwa yaran nan auren dole ba. Ita da nata mahaifin ya yi mata, Allah ne kawai Ya dubi zukatansu ita da mahaifiyarta Ya daidaita zaman. Sai ya kasance Honourable din ya zarce duka tunaninsu a fagen kyautatawa sabanin sanin da suke tunanin sun yi masa lokacin yana auren A'i.
"Ku tashi mu tafi" ta ce da 'ya'yan nata ganin hatta Ummita ita ma kukan take. Suka bi bayanta kuwa suna tafe kamar kwai ya fashe musu a ciki.
Da fitarsu Honourable ya bawa kowa mamaki da ya yi 'yar dariya. Innayo ma da Abdulkarim sai da suka murmusa. Ita nata ya dace da na Honourable. Fushi ne suke gani muraran Hasiya tana yi na sanya mata yara a tsaka mai wuya. Shi kuwa Abdulkarim na farincikin fahimtar cewa Ummita bata da kowa a hannu yake. Lallai zai ci karensa babu babbaka. Tunda babu wani yaro a hannu da zai masa shigar sauri ya hure mata kunne.
Dakin da suka baro su Maimuna suka shiga, Ummita da Ayaah suna kuka babar tasu ma tana yi. Maimuna ta gaji da rarrashinsu ta koma fada.
"Tunda baku san hakuri ba sai kuyi ta yi. Amma ki sa Ayaah ta cire rigar d'an mutane ta mika masa"
Sai a lokacin ta tuna da rigar. Da sauri ta shiga balle maballan ta cire ta mikawa Murja.
"Don Allah ki kai masa"
Anti Hasiya ta kai mata duka ta kauce
"Amma baki da kirki Ayaah. Mutum ya yi miki irin wannan taimakon amma godiya ta kasa shiga tsakaninku. Tashi maza ki kai masa da kanki."
Hijab ta dora ta fita tana jiyo muryar Larai tana bada labarin abin da ya faru. Duk inda take tunanin ganinsa kama daga tsakar gidan, soro da kofar gida. Bata manta da gargadin babanta ba saboda haka bata yarda ta fita ba. Ciki ta dawo da niyar daukar wayarta ta kira shi sai ta kula da takalminsa a kofar falon. Kenan Baba ne ya sake kiransa ta ambata a zuciyarta. Kamar wadda tayi magana da karfi sai ji tayi Babanta ya kwala mata kira.
Da hanzari ta shiga don yanzu bata kaunar abin da zai bata masa rai.
"Dama rigarsa zan ce ki kawo ashe ma kin dauko."
Abdulkarim sai cewa yayi "muje waje in ganka kafin na wuce Honourable."
Hon. Habu ya dan yi turus sai da ya sake maimaitawa ya mike. Suna fita Abdulkarim din ya ce da Suhaib idan ya fito zasu yi sallah don har biyu da rabi.
Rigar ta mika masa bayan sun fita ta furta kalmar godiya a hankali.
"Ya naga duk kin yi laushi ne? Ko hukuncin da Baba ya ce min ya yanke ne bai yi miki ba?"
Dago rinannun idanunta tayj da sauri ta ce "yanzu sai da ya fada maka zai min auren dole?"
"A'a" ya ce yana mai girgiza kansa "cewa ya yi kawai za ki daina fita har zuwa school sai kina da paper" ya kare da dan murmushi.
"Auren dolen ka ke yiwa dariya ko hanani fita?"
"Kina da rigima" Suhaib ya furta da wani irin yanayi sannan ya tashi tsaye "ni zan wuce. Sai in ce sai mun zo biki ko?"
Shiru tayi bata kula shi ba don ta kula yana jindadin zolayarta.
"Au ba za ki amsa ba?"
"Kana farinciki da auren dolen da za ayi min ya za ayi na amsa?"
Sai da ya je bakin kofa sannan ya juyo ya kalleta cikin ido ya ce "dazun nan ki ka yi warning dina da cewa ko ina sonki kada na fada domin ba za ki yarda ba. Ba don haka ba da na sake introducing kaina a wurinsa a matsayin...." Ya lumshe ido ya budesu a gajiye "idan kin bani matsayin da ya dace na sake gabatar da kaina a wurinsa ki kirani kafin lokaci ya kure mana. Take care."
Har ya fita su Ummita suka shigo bata sani ba don ba karamin kashe mata jiki da zuciya kalamansa suka yi ba.
Sallah ya tsaya suka yi sannan ya ce zai tafi. Ba yadda Honourable bai yi dashi ba akan ya zauna yaci abinci yace ya koshi. Da fitarsa bai zame ko ina ba sai garejin su Danliti. Ogansu ne ya kira shi yana shiga mota zai bar unguwarsu Ayaah.
"Mal. Suhaib muna kara godiya akan taimakon da kayi mana. Dalilin kiran naka kuwa yanzu ba wani abu bane illa wayarsa da nake son baka kafin 'yan sanda su nema."
"Waya kuma?" Suhaib ya furta yana yamutsa fuska saboda son sanin dalili.
Mutumin ya ce "Kwarai kuwa. 'Yan sandan da suka zo basu kula da ita ba sai wani cikin yarana ne ya dauko. Yanzu suka budeta har sun cire lock din ma. A garin bibiyar hirarrakinsa na chatting muka ci karo da hirarsa da wata mata suna kuma yawan ambaton sunanka. Matar har tana cewa idan ka zo Kano ya sake maka kamanni da duka. Shi ne nace gara dai ka zo ka gani kada ya cuci wata"
'Alhamdulillah' Suhaib ya ce yana mai fadada murmushin fuskarsa domin wannan batu ba karamin taimako zai yi masa ba. Shaida ce guda da zai samu ya nunawa Abbansu akan Jiddo. In anyi sa'a yaga cewa matarsa ma tana yin yadda yake ko kusa da kila ya canja hali. Da wannan tunanin ya wuce garejin.
Kafin ya karasa kafarsa ta dama ta soma wani irin tsukku kamar ana cakarta da allura. Da kyar ya iya karasawa sai dai yana fitowa ya kasa takata da kyau. Ogansu Danliti yana ganin yanayin tafiyarsa ya ce,
"Dama na san a rina. Wannan duka da ka yiwa kofar dakin nan da wuya idan baka bugu ba ko targade. Don da karaya ce da wuri zaka fara jin ciwon."
Wasa-wasa Suhaib kasa jan motar ya yi. Shi da ya yi niyar komawa Kaduna a lokacin sai gashi wani aka samu ya mayar dashi gidan kawunsu inda aka yi zaman biki. Abinci ma kasa ci yayi dole suka tafi wani asibitin kashi na kudi. Har x-ray aka yi masa saboda kafar ta fara kumbura ta wurin idon sawu. Dunduniyar kuma tana ciwo. Babu karaya yadda suke tsammani sai tsabar buguwa. Irin leg brace dinnan aka daura masa bayan an yi mata gashi sannan suka koma gida. Matan gidan suna can suna kiran Mami Khadija su sanar da ita shi kuwa ya kira Lilu ya ce ya taho washegari su koma tare.
***
Zara taga ikon Allah zamansu da Uwani bayan fitar su Innayo. Surutai take yi ita kadai kamar wadda ta sami tabin hankali. Kalma ko daya ba za ta iya cewa ta gane ba amma ga bakinta nan yana ta motsi da sauri-sauri. Abin tsoro ya soma bata ta tashi daga dakin ta koma falo. Kafin ta zauna Uwani ta fito tana mai cigaba da maganganunta. Babu zato taji ta ce mata,
"Kiyayyar da kuke min har ta kai a rasa mai tambayata damuwata Zara?"
"Idan na tambaya za ki fada min ne?"
Uwani na jin haka ta dawo kusa da ita ta zauna. Da gaske neman wanda zata saukewa damuwarta take. Innayo din da ta zata har abada ba za ta taba juya mata baya ba yau gashi tana magana taki sauraronta da kyau. Kanta ta dinga dunguri da yatsanta manuni.
"Zara ina ji wadansu notina suna kwancewa a kwakwalwata wallahi. Daf nake da zarewa idan Habibu bai dauki wayata ba"
"Habibu kuma ko Salihi?"
Uwani ta maimaita sunan da karfi "Habibu nace. Ai ce miki nayi kaina zai kwance ba wai ya kwance din ba"
Mikewa Zara tayi "me yayi zafi za ki sauke min fadanki. A kira Habibu lafiya"
Da sauri Uwani ta riko hannunta ta dawo ta zauna. Bata boye mata komai ba cikin matsalolin da suka fuskantota a dan kankanin lokaci.
"Idan na rasa komai wallahi zuciyata za ta iya bugawa. Zara gabadaya rayuwata fa akan yadda zan gujewa rayuwa irin ta Innayo na yita. Sai yanzu bayan na gama shan wahalar har ina hango soma cin arzikin sai komai ya rushe? Meye marabata da Innayo yanzu? Karatun da aikin duka babu riba."
Kwalla ce ta taru a idon Zara saboda ita kanta ta hango tsagwaron rashin hankali a zantukan Uwani.
"Ko kadan baki yi kuskure ba don kin yi fatan gujewa irin rayuwar Innayo. Babu wani mai hankali da zai so bayan ya tashi a wahale ya cigaba da rayuwa a haka. To amma kuskurenmu daya ne ni da ke. Mun so gujewa rayuwar ne mu kadai ba tare da tunanin wadda tayi sanadiyar rabamu da ita ba. Da gumin wa muka rayu? Wa ya ciyar dake? Waye ya kai ki makaranta? Wa ya aurar dake? Addu'ar waye ya zame miki garkuwa tsahon rayuwarki? Sai ace kuma da kika sami dadi ita ce mutum ta farko da kike gudu tamkar ita ta zabawa kanta kuncin da take ciki. Ke din wayonki ne yasa ki ka sami duka nasarorin da kike tinkaho dasu? Idan wayonki ne to ki sake tsallake wannan ramin dake gabanki. Ni dai na dawo daga rakiyar shaidanin da ya taba min zuciya. Uwata ita ce madubin rayuwata. Ranar da kika gane haka kuma ki ka roketa gafara shi ne lokacin da zaki fara ganin haske."
Tun zuwanta gidan ta kula da yadda Zara take neman shiri da Innayo. A zatonta abin na ganin ido ne kadai. Sai gashi taji daga bakinta. Wannan yasa tayi wata irin dariya. So take ta san waye mara hankali tsakanin ita da kanwar ta ta.
"Da bambanci sosai tsakanin matsalata da taki. Baki san juya kudi ba sai dai a dauka a baki. Shi yasa da miji ya juya miki baya ki ka yi saurin laushi a hannun Innayo tunda arzikinta kike ci. Ni kuwa gumina ne. Nafi karfin tozarcin da namiji wallahi."
"Hakka!" Cewar Zara da gatsali.
"Don kin ganni a gida ki ke min magana haka? Hala baki ji na fada miki ina da gidan kaina ba?"
"Kan ki kuma ake ji"
Zara dama ba kyalle bace. Da ta fuskanci Uwani bata da niyyar bin hanyar da take nuna mata sai taji gara a bar maganar kafin su fara fada. Tashi tayi ta fito falo. Uwani sai ta biyota rai a bace.
"Ni kike cewa kaina ake ji saboda ga 'yar macukule ko? Har kina da bakin fadawa wani magana ma ke da kike goyon 'ya mara suna?"
"Wai in tambayeki Uwani. Anya kin taba zama kin karewa Innayo kallo kuwa? Kin ma santa kuwa? Sani na wace ce ita a matsayin 'yar Adam ba na matsayinta na uwa a gareki ba." Shiru Uwani tayi tana sauraron zancen da Zara ta dauko.
"Innayo bata sami gatan uwa da uba ba a dalilin maraici amma mu ta zame mana uwa da uba harda kari. Mu tara ta aurar Uwani. Mata tara wata na bin wata. Ta sadaukar da lafiyarta da jindadinta domin rayuwarmu ta inganta. Amma cikinmu banda Hasiya waye take jindadi a jikinsa? Salima da Maimuna suna kyautata mata amma ai har yau guminta suke ci. Su Hasina dama tun zamanin marigayiya Allah Ya jikanta suka juya mata baya. Me tayi mana da zafi Uwani? Saboda ta auri ubanmu ta haifemu shi ne laifi? Ko don ta jure wahalar gidansa domin ta zauna damu don kada rayuwarmu ta tagayyara? Kiyi tunani idan har kina da rabon jindadin duniya da lahira. Innayo jininta ne kadai bata zubar domin mu ci, mu sha kuma mu sami ilimi ba. Tun karfe hudu take tashi amma babu ita babu sake kwanciya sai wuraren shadaya ko shabiyun dare. Hannunta kullum a ruwa, ido a gaban murhu. Haba Uwani? Kamar baki rike ciki kin yi nakuda ba? UWA, UWACE komai lalacewarta. Balle kyautar Allah irin Innayo."
Bata kara tofa komai ba bayan haka ta shige daki saboda kukan da yaci karfinta. Uwani kuwa zama tayi dabas akan kujera duka jikinta babu kwari. Ta kwashi kusan minti ashirin tana juyayin maganganun Zara kafin wani irin bacci ya dauketa. Tabbas sau tari mutum yana ganin abin dake zuciyarsa ne a cikin bacci. A yadda take a zaunen ko gyara zama bata yi ba baccin nata ya dauketa zuwa duniyar mafarki mai ban tsoro. A cikin baccin take fatan Allah Ya kawo mai tashinta saboda firgicin da ba za ta ce ga abin da ya kawo mata shi ba.
*
"Shazali ya maganarmu ne? Ranar laraba muka yi da Alh. Tahir gashi har yau litinin baka ce min komai ba"
Gefen titi Shazali ya gangara da motarsa domin maganar da zai yi da Comared tana bukatar nutsuwarsa sosai.
"Ranka ya dade akwai shirin da nake yi ne. Hatsaniya ta shiga tsakanina da mutumin da nake son kawo masa ne, saboda haka sai na lallaba shi a hankali."
Tsaki Comared ya ja ya kuma kama yi nasa fada harda zagi.
"Ka tabbata yaron ya zo domin idan aka sami akasi raina da naka duk sai sun baci"
Hakuri Shazali ya bashi a ransa yana ta tufka da warwarar yadda zai yi ya sami kan Abbati cikin lumana. Aikin Comared din da ya yi masa bayani ya wuce biyawa Alhajin da zai zo bukata kadai. Aiki ne na sihiri wanda Alh. Tahir ya zata za ayi ne domin toshiyar baki (Yumna). Bai san cewa Comared tasa tukunyar yake son gyarawa ba. Sharri yake son kulla masa ya watsa hotunansa ta yadda zai rasa duk wata kwangilar dake hannunsa. Sai a bawa Comared don dama irin sana'arsu daya. Lokaci guda Alh. Tahir din ya yi musu zarra, sunansa kadai ake ji. Abotar sai ta koma murmushin gaban ido da gulmar bayan ido, batare da saninsa ba.
To shi ma Shazali burinsa ya yi amfani da wannan damar ya tozarta Abbati. Duk da cewa a gaskiyar lamari yafi jin haushin Munzali saboda yafi baki. To amma wulakantar Abbati sai tafi ta Munzali ciwo kamar yadda ya yi hasashen tonon asirinsu. Abbati dan dangi ne. Munzali kuwa da danginsa da babu duk daya a tunaninsa. Sannan son da Munzali yake yiwa Abbati zai sa yaji ciwon abin sosai. Dama ce ya samu da zai nuna musu shi din ba kanwar lasa bane. A matsayinsa na silar arzikinsu bai kamata su juya masa baya ba. Sai da suke ganiyar samun kudi kamar hauka sannan zasu ce wai sun tuba. Ko waye ya fada musu cewa shi baya son samun rahama bai sani ba. Lokacin tubansu idan ya zo ba sai kowa ya fada musu ba. Tsufansu ya ishesu sanin cewa ya kamata a koma ga Allah. Su gina masallatai su dinga bayar da sadaka. A haka zasu koma lahira kamar jarirai. (Babu bawan da Allah Ya yiwa alkawarin jinkirta masa rayuwa zuwa wani wa'adi. Lokaci yana zuwa ne ko da tsufa ko babu. Ko an tuba ko ba a tuba ba sai an tafi. Ya Rabbi Ka yafe mana zunubanmu na zahiri da badini. Amin)
Da waccan magana ya katse kiran Comared ya shiga laluben layin Abbati. Cikin sa'a kuwa ta shiga sai fatan a dauka. Abbati na ganin sunansa a jikin wayarsa ya ja tsaki ya mayar da ita aljihu. Sun kusa Jogana motar tasu ta soma hayaki suka tsaya. Abin duniya ya taru ya yi masa yawa domin ya kasa samun mota mai tsayuwa ta dauke shi. Ga yamma ta kawo kai. A gefe guda kuma ya kasa samun Munzali. Hanne da yake tunanin zata hadasu ita ma wayarta a kashe. Daga baya ne ya yi tunanin kiran Kukunsu. Cikin sa'a kuwa ya sameta. Shazali da bai hakura da nemansa ba ya dinga jin wayar tana shiga number busy.
Kalmar lafiya kalau kadai Abbati ya iya cewa ga dukkan tarin kalaman gaisuwa da kukun yake jefa masa. Jin zai fara tambayarsa mutanen gida ya yi saurin katse shi.
"Don Allah hadani da Munzali"
Kuku ya dubi hanyar bene ya ce "yau ko sau daya bai fito ba. Sannan yaki barin Qibdiyya ma ta sauko. Abincinsu ma ni ban sani ba ko sun ci don ya kulle kofarsa"
Dunkule hannu Abbati ya yi ya daddaki goshinsa cikin rashin sanin abin yi. Can dai ya ce masa yana zuwa ya kashe wayarsa. Hannunsa yana rawa ga gumin tashin hankali ya shiga scrolling din sunaye a wayarsa. So yake ya gani ko zai yi dacen samun nambar 'yan uwan Munzali amma babu ko daya. Tsoronsa kada ya dauki mummunan mataki musamman da Kukun yace yana tare da Qibdiyya. Kiran kukun ya sake yi da wata shawara ta zo ransa.
"Ka san gidan iyayen Munzali ko?"
"Na sani ranka ya dade"
"Ka je gidan ka nemi mahaifiyarsa Asabe ka fada mata. Ita zata san me ya kamata ayi kafin na iso. Ka tabbatar ita ka samu"
A kofar gidan Alh. Rabi'u kukun ya tsayar da mashin dinsa ya sauka ya dinga kwada sallama.
A cikin gidan Asabe tana kuryar dakinta abin duniya ya yi mata yawa. Zantukan Munzali basu da ma'anar da zata iya cewa ga dalilin da yasa yake rokon Qibdiyya gafara don an mata fyade. Ta so tahowa ma da ita a jiya a hana. Yau kuma yaki daukar wayarta. Daga baya ita ma bata samunsa. Ga sunan yaron da Qibdiyya ta ambata ma ya kwanta mata don bata taba jinsa ba. Shawara tayi tafi dari akan ta kira su Ummakati ta fada musu ko tayi shiru. She was never a Mom to all of them. Ta dai san wahalar daukar ciki da nakuda. Ta kuma dan san wahalar raino musamman kafin yaro ya fara zama. Daga nan kuma sai abin da hali ya yi. Allah Mai rayawa Shi ya raya mata zuri'arta cikin mugun sakaci da rashin sanin ciwon kai.
Da Innayo ce tabbas ta san da tuni ta lalubo abin da ya dace har ma ta aiwatar. Yinin ranar bata tsinana komai ba sai kullawa da kwancewa. Ga ranar da duk girman d'a yake bukatar mahaifiyarsa. Gata da rai da lafiya amma bata san me ya kamata ta yiwa Munzali ba.
*
Tashin da Uwani tayi daga firgitaccen baccinta yana da alaka da karfin sallamar Kuku. A razane ta tashi tayi hanyar kofa da sauri. Zara ta kalleta ta girgiza kai. Ita ma sallamar ce ta fito da ita.
Kallon ina-na-sanka Uwani ta dinga yiwa masa. Shi bai ma ganeta ba sai Asabe da ya tambayeta.
Juyawa tayi kamar ta koma daki sai dai ta karasa ta fadawa Asaben. Tare suka dawo bakin kofar. A gabanta ya fada mata halin da Munzali yake ciki. Cikin tsantsar rudani kuwa Asabe ta soma kuka. Ita kuma Uwani wani case ta tuna a asibitinsu inda uba ya kusa kashe 'yarsa saboda bakincikin an mata fyade a kauye. Ya ce gara ta mutu akan duniya taji wannan labari. Ba tare da tunanin komai ba sama da ran kaninta da 'yarsa ta koma daki da gudu. Mayafin dake jikin Zara wanda ta lulluba zata fito tun zuwan Kuku ta warware ta yafa. Ta ruga daki ta dauko jakarta mai dauke da kayan aikin gaggawa ta fito.
"Ki fadawa Innayo na tafi gidan Munzali"
Zara ta bita da sauri "gidan Munzali kuma? Me ya faru?"
Uwani bata ce komai ba ta fita. Asabe har lokacin tana tsaye tana koke koke bata iya cewa komai ba ga kuku. Isowar Uwani ce ma ta ankarar da its cewa ya kamata tayi wani abu.
"Malam muje don ba gane gidan zanyi ba"
Kuku ya dan ja baya "ke ce Asaben?"
Rai a bace da ganin yana bata mata lokaci ta ce "ni yayar Munzali ce. Ka wuce mu tafi"
Asabe sai ta gyada masa kai ta koma ciki da zummar dauko mayafi. Kafin ta fito sun bar wurin. Duk da tsoro irin na Uwani haka ta hau mashin din tana salati har suka isa.
BABI NA SHA SHIDA.
Karfe goma na safe Habibu ya shigo cikin ministry da wata 'yar jaka a hannunsa. Kayan sawarsa ne da abubuwan bukata na kurkusa ya hada a ciki. Zaman Kano ba nasa bane ya sani tun ranar da Salihi ya titsiye shi. Babu shakka bayani ya kai kunnen Uwani. Sanin da ya yi mata na son kudi ba na yau bane. Abu mafi karanci da zata yi masa shi ne ta hada shi da 'yan sanda. Shi yasa zai yiwa tufkar hanci ya gudu. Ba kudinta ne kadai ya jike a hannunsa ba, harda na wasu da dama. Da ace kudaden suna da albarka a hannun macuci kuma maha'inci irinsa da tuni ya zama wani. Shekara da shekaru da 'yan dabaru yake kwatar kudi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 45 Chapter of 62