Mari suna dakin da aka kwantar da ita a babban asibitin garin Kirikasamma. Abbati ya rasa me yake masa dadi a duniya. Gefe guda ya samu ya zauna ya hada kai da gwiwa cikin tunani. Tare suke da mahaifinsu Mal. Inuwa da wasu cikin Gwoggoninsu matan 'yan uwansa. Shi Mal. Inuwa yafi kowa nuna gigita saboda yadda yaga Abbati ya fito da ita waje a hannu ko motsi bata yi. Daga shi har 'yan majalisarsa sun dauka bata da rai.
Kowa yana tofa albarkacin bakinsa game da ciwon da ba a san silarsa ba likita ya dawo. Wasu gwaje gwajen jini ya sake rubutawa ya bukaci Abbati ya biyo shi waje.
Da sauri Mal. Inuwa ya ce "Fadi ko ma mene ne Dafta. Nan wajen duka babu bare. Me ya sami Mari?"
Likitan ya dubi Abbati wanda ya gyada masa kai sannan ya fada musu abin da suka gano.
"A gaskiya jininta ya hau fiye da kima har yana barazanar taba mata zuciya. Idan ba a dauki matakin da ya dace ba zata iya samun stroke (mutuwar barin jiki) ko ...."
"Allah ma Ya kiyaye" cewar Mal. Inuwa da rawar murya "indai kudi ne sha Allahu ba zai gagara ba. Ayi mata duk abin da ya dace ga danta nan."
"Malam. Malam"
Ba Mal. Inuwa da ta kira ba, duka wanda yake dakin sai da ya juya da farincikin ganin Baaba Mari ta farfado.
Da hannu ta yafito shi ya matso kusa da gadon ya duka kansa ganin tana ta motsa baki.
"Ku mayar dani gida."
Wani irin kallo ya mata cikin tashin hankali ya daga kansa ya yiwa Abbati inkiya da ya matso. Su Habi duk sai suka fice.
"Kaji taurin kan mata ko? Wai a mayar da ita gida."
Murmushi tayi masa "Idan an kaini asibitin waye zai biya kudin?"
"Wace irin magana ce wannan? Ko kin sami makuwa ne saboda ciwo?"
Muryarta ta kara dusashewa ta ce "kana da sauran kadara ne Malam da zaka sayar ka nema min magani?"
Duk da ya soma harzuka haka ya daure saboda ba lafiya gareta ba ya ce
"Wai ba ga Abbati ba? Mari lafiyarki kuwa?"
Idanun Abbatin ta lalubo da nata. Ya zabge tamkar shi ne kwance a gadon asibitin. Kalamanta na gaba a gareshi ita kanta basu yi mata dadi ba sai dai babu gudu ba ja da baya.
"Ban yafe ba idan ya sake kashe min kwandalarsa. Ban yarda kaima ka kashe min daga kudin da ya baka ba. Sannan idan ban tashi ba ka isar da sakona ga dan uwanka Sa'idu. NI MARIYA BAN YAFE MASA BA!
TARA DAGA KE SAI GOMA.
"Anya Mari baki yi gamo ba? Yaya Sa'idun kike ja wa Allah Ya isa?"
Wani bacin rai ne ya turnuke kirjinta. Wato bai ma damu da abin da tace akan dan cikinsa ba sai yayansa wanda ya zama silar rushewar rayuwar 'ya'yanta maza.
"Ko in hada da kai ne?"
Mal. Inuwa ba arziki ya saita fuskarsa daga fushin da ya yi da farko
"Ni kuma me nayi?"
Ko kula shi bata yi ba ta dubi Abbati da murmushi. Wannan karon kallon yana cike da soyayyar uwa da danta. Yadda ya koma yafi mata ciwo akan shi kansa. Dukiyarsa take son ta raba shi da ita domin babu amfani su cigaba da ninkaya cikin haram. Sabuwar rayuwa za ta tura shi da taimakon Allah wadda bai taso cikinta ba tunda ya fara sana'arsa. A yanzu yafi bukatar soyayyarta da tausayawa kuma a shirye take ta nuna masa domin yaji dadin tuba.
"Kirawo 'yan uwanka su taimaka min na tashi."
Kai ya gyada daidai da saukowar hawaye a idanunsa. Tana kallon yadda yasa bayan hannunsa ya dauke hawayen sai dai bai hana wasu gudana suna maye gurbin wanda yake sharewa ba. Haka ya fita bai yi musu akan rashin son zamanta ba. Ya fahimceta sarai. A shirye yake ya bi umarninta. Da hannu ya kara goge idanunsa sannan ya kira kannen nasa.
Da ya fita Mal. Inuwa kallon tuhuma ya dinga yi mata. Tabbas akwai abin da yake faruwa tsakaninta da Abbati. A matse yake da son ji. Sai dai yanayin fuskarta ya sanya tayi masa kwarjinin da ba zai iya yi mata titsiye ba.
Likitan da ya dubata har bakin mota ya bisu yana nanata musu gangancin dake tattare da dauketa a yanzu.
"Bai kamata ku biye mata don ta ce ba za ta zauna ba" ya dubi matan da ya tabbatar 'ya'yanta ne saboda kukan da suke da rokon yayansu akan su zauna "za ta iya shiga yanayin da dukkanku nan sai kun yi dana sanin kin karbar shawarata."
Habi sai ta koma kusa da mahaifinsu tana kuka.
"Kaji abin da yake cewa Baba. Don Allah ka tilasta mata ta zauna."
"Abbati?"
"Baba muje gidan. Da kaina zan dawo da ita asibiti in Allah Ya yarda."
Iyakar abin da yace kenan ya shiga gaban motar da zata mayar dasu gida.
*
Deluwa ce kan gaba wurin zuwa bangaren Baaba Mari bayan sun dawo. Daga ita sai daurin kirji da dankwali a ka. Tabe baki tayi tana soshe-soshen jiki.
"Yo aka ce mana ranga- ranga aka fitar dake ashe ma ciwon ba wani na azo a gani bane."
Ci-kan-ki wannan bata samu daga bakin kowa ba. Ta gaji da maganganunta ta kama hanya za ta fita.
"Ki kirawo min mijinki idan kin fita"
Wata irin juyowa Deluwa tayi ta kalli bakin Baaba Mari da ya furta wannan maganar. Har wani duka ta kaiwa kunnenta domin tabbatarwa.
"Ki ka ce?"
"Ki turo min mijinki! Da jikina da kwari da kaina zan je na same shi."
Mal. Inuwa dama ya matsu yaji me yake faruwa. To amma shi ma yadda tayi maganar ba karamin tsorata shi ya yi ba. Musamman da ta sallami duka 'ya'yanta da jama'ar gidan da suke sashen nasu ta bar Abbati shi kadai. Dadin dadawa kuma sai shi ma Abbatin ya yi wata magana da ta sabule masa kuzarinsa ya kara shiga firgici akan me yake faruwa.
Hadiyar yawu mai masifaffen daci ya yi, idanunsa duk sun shige ciki ya dubeta.
"Baaba tona min asiri zaki yi? Na rantse miki ba yau na tuba ba. Ni da Munzali har..."
Runtse idanuwa tayi da ya ambaci sunan Munzali. Allah Ya sani ko sunansa bata son ji balle ayi hirarsa. Ya fice mata a rai lokaci guda kamar anyi ruwa an dauke. Akwai laifin mijinta da yayansa dumu dumu amma nasa mai girma ne. Bata jin zata taba manta cewa shi ya koya masa....karshenta ma har yanzu suna yi. Tsigar jikinta a take ta mimmike da wannan tunanin.
"Idan ban yiwa tufkar hanci ba ka san irinka nawa zasu samar mana a dangi?"
Abin da ta ce kenan. Sai ya koma jikin bango ya tsaya tare da jingina bayansa. Babu wani abu ko digo da yake yi masa dadi a duniyar nan. Nadama iyakar nadama ya kara yi. Ya tsani ranakun da ya mika jikinsa ga marasa tsoron Allah cikin manyan mutane masu fada a ji a kasar nan. Farincikin da kudaden suka saka shi ya koma bakinciki.
Sallamar Mal. Sa'idu da kakkaurar murya mai nuni da girman bacin ransa sai da tasa hanjin cikinsa kanannadewa. Zazzabi mai zafi har cikin 'bargo ya afka masa. Daga wannan lokacin zai sanya kafa guda da sabon shafin rayuwa. Idan har zai iya cigaba da rayuwar.
Shikenan!
***
"Wa nake gani kamar Mariya?"
Asabe ta takawa kafafunta burki a daidai kofar dakin Innayo. Laluben dakin da yake sakale akan dokin kofa ta sake dagawa da hannunta ta leka ciki. Tabbas jikarta ce take hangowa zaune akan cinyar Salima tana ta zuba surutu. Ranta ya sosu ta taka cikin falon ko sallama babu sai ganin hannunta Salima tayi tana kokarin fincikar Qibdiyyan.
"Tashi ki wuce muje."
Noke kafada tayi ta kwace hannunta. Salima ta murmusa kawai ta ce mata "tashi mana Qibdiyya. Sannu da zuwa Asabe."
"Ban son munafunci. Ki rike sannunki ki sakar min jika"
Sababi ta hau yi akan dalilinsu na riketa a dakin.
"Shi ma Munzalin zai zo ya sameni. Akan me zai kawota bai fada min ba?"
Innayo da Zara duka suna falon amma yadda bata nuna ta gansu ba haka su ma basu kulata ba. Ta gaji da fadanta ta dauki Qibdiyya da karfi ta nufi bangarenta.
Ihunta suka ji da ta tura kofar ta bude ba tare da ta saka mukulli ba.
"Jar uban nan! Wallahi gidan nan baku so zaman lafiya ba. Wace mai kokarin ce ta bude min daki?"
"Daddyna ne ya budewa su Uncle Lilu."
Asabe ta gatsina fuska "waye kuma Unku Lihu?"
"Uncle Lilu da yake min doki a bayansa... " Cewar Qibdiyya da mamakinta irin na yara idan aka kasa gane abu mai mahimmanci a wurinsu.
Asabe hakura tayi da neman ba'asi. Duk inda yake ta san dole zai dawo daukan 'yarsa. Zata nemi karin bayani a wurinsa. Sannan kuma ta samu ta karbi kudin da take tunanin shi ya zo bata.
Mayafinta ta kama za ta cire Qibdiyya ta ce zata yi fitsari. Sunkutarta tayi gabadayanta ta shiga bandaki. Yarinya fes da ita amma saboda son burge mahaifinta kamar ba dan cikinta ba ta tube mata kaya.
"Wanka zan miki kada ya dawo ya ganki haka kamar wadda tayi dambe."
Bata da ruwan dumi amma don kar ya dawo bata gama ba idan ta tsaya dafawa sai tayi mata da mai sanyi. Qibdiyya harda kukanta don garin babu wannan zafin da zai sa mutum wanka da ruwan sanyi. Aka zo shafa mai tabi ta mulketa da man kadanya sai kyalli take. Ta kawo kwalli aka rambada mata a ido. Ta tafi dauko pant din da ta cire mata a bandaki Qibdiyya ta kai hannu gabanta tana susa. Wanka ne aka yi aka koro maikon jiki amma ba ayi mata tsarki ba. Dan datti da ruwan sabulun da ya wuce ta wajen da fitsarin da tayi ba a wanke ba.
Wannan susa akan idon Asabe da ta dawo daga bandakin.
"Kalau kike kartar jiki haka da karfi? Kwanta mu gani ko kurji ne a wajen."
Da kanta ta kwantar da ita ta kai hannu za ta raba kafafunta taji ta cafke mata hannun. Idanuwa Qibdiyya ke binta dasu tana yi mata kallon tsoro.
"Kema hannu zaki saka min a nan? Kiyi min a hankali ba mai zafi ba. Kuma ba zan fadawa kowa ba don kada ki yanka min Daddy da Papa."
Asabe ido kawai ta zuba mata ta kasa kwakkwaran motsi saboda firgici.
Qibdiyya kuwa tuni ta rufe ido tana jira ayi a gama. Da taji shiru sai ta bude idon a hankali. Da karamar muryarta ta ce da Asabe,
"Ni ce zan yi miki?"
Kamar wadda aka kwadawa mari sai lokacin Asabe ta dawo hayyacinta. Kuka ta kama yi ba tare da ta sani ba ga jikinta ya soma rawa kamar mazari. Furucin Qibdiyya ya matukar tayar mata da hankali fiye da tunani. Shi yasa bata ma san lokacin da ta d'aka mata wani mugun duka a cinya ba.
"Ki yi min uwar me? Na bonu ni Asabe. Kiyi min me? Tashi don uban...."
Qibdiyya ta tashi zaune a razane tana son yin kuka amma tsoro ya hana. Daddy ya hanata kuka ko taji zafi idan yana yi mata abu irin wannan. Cewa yake hawayenta na fita za a saka mamanta a rami a rufe da kasa. Tun bata iya ba har ta kware wurin danne hawayenta. Idanu tsilli tsilli ta kafe Asabe dasu babu alamar kuka duk zafin dukan.
"Daina kallona" wani tunani tayi ta sake kwantar da Qibdiyya ta soma dubata. Allah ne kadai Ya taimaketa bata suma ba akan abin da ta gani. Kankanuwar yarinya ta kusa gama budewa.
Kafafunta kasa daukarta suka yi bata ankara ba tayi zaman 'yan bori a kasa. Kai ta dago dankwalinta ya karkace saura kadan ya fadi ta kalli jikarta.
"Waye yake taba miki nan?" Ta nunawa Qibdiyya inda take tambaya da hannu.
Razanar da tayi a dalilin dukan da tayi mata dazu da kuma tsoron kada a rufe mata uwa a rami sai taki fada. Jikinta yana bata cewa idan ta fada din ma ba tsira zata yi ba.
Asabe ta gaji da tambaya ta soma dukanta. Amma ko digon hawaye babu sai ajiyar zuciya. Hargagin muryarta tana cewa "ba za ki fada min ba?" har tsakar gida. Uwani ta fito tana waya taji. Hanyar dakin ta nufa sai dai kafin ta isa Innayo ta fito daga nata dakin ta ce mata kada ta soma zuwa.
"Bana son gulma ki zo ki wuce naki uzurin kada ki ja min magana".
Komawa tayi din amma haka kawai taji ta kwadaitu da son sanin me yake faruwa. Maganar dai kamar da Qibdiyya ake yi amma bata ji ko tarin yarinyar ba.
*
"Munzali kana ina?"
Sautin muryarta banda alamun tashin hankali harda kuka yake iya ji.
"Muna asibiti da Hasiya ne amma na kusa tahowa. Wani abin ne?"
Karo na farko a rayuwar Asabe da ta dakata tayi tunani kenan da kwakwalwarta. Wannan sam ba maganar waya bace.
"Ka taho da sauri ina son ganinka yanzun nan."
Bayan ajiye wayar hankalinsa ya kasa kwanciya. Yasa rai da jin mitarta akan zuwa wurin 'ya'yan Innayo. Kudi ya damkawa Ummita kafin shigowar Hon. Habu ya ce musu zai je gida ya dawo.
Akan hanya ya dinga kiran Abbati shiru bai dauka ba. Kansa ya sake daukar chaji kamar ana buga guduma. Ya san Abbati ba yaro bane da za a zane bayan ya fadi gaskiya. To amma me ya biyo bayan fadin tunda ya tabbatar da wahala idan bai fada din ba.
***
Sanyi da daddadan kamshi ke tashi a wani katafaren falo. Duk inda ake neman ni'ima mai shiga zuci an gama samu a nan. Mazauna wurin maza ne su biyar wadanda shekarunsu suka tura. Ga kuma shaida a jikinsu na cewa sun kama kasa. Daga 'yan siyasa sai 'yan kasuwa sai kuwa masu manyan mukamai a gwomnati.
Dukkaninsu sanye suke da manyan kaya harda babbar riga illa mutum daya. Daga gani shi ne mai masaukin baki saboda yadda ya bararraje. Hula da babbar rigarsa duk suna gefe guda can nesa dashi. Bayani yake yiwa babban bakonsu. Amininsu ne ta fanin harkokin 'yan mata. Sai gashi a Kano garin yake gida ga sauran hudun.
"Yanzu sai da kana shirin komawa Kaduna zaka sanar damu zuwanka Alh. Tahir? Karramawar nan da ake yiwa manyan baki ma baka bamu damar yi maka ba."
Cewar mai gidan hutun (guest house) din da suke ciki.
Dariya Alh. Tahir ya yi masa "banda abinka ni da na taho da taurarina guda uku ina ni ina bin kwararo?"
Kwashewa suka yi da dariyar shakiyanci suna zolayar juna. Nan hira ta kacame da ciye ciyen kayan abinci na alfarma. Maigidan aka kira ya amsa ya bayar da umarni ga mai kiran da ya shigo.
Alh. Tahir na jin haka ya san ba zai wuce mace aka kawo ba. Murmushi ya yi yana gyada kai.
"Ni dai bari na gudu don na tuba."
Wani Alhaji mai tulun ciki ya tafa da na kusa dashi suka yi masa dariya "Kowa ya tuba don wuya ba lada."
Alh. Tahir ya kada kai "da lada fa. Abubuwa sun cabe min. 'Yar banzar yarinyar nan kawar Farha da nake fada muku yanzu fa Yakumbo ta rantse sai na aureta. Yarinyar da take yawonta da kananan yara kuma duk na sani."
Mai gidan yaja guntun tsaki "duk laifinka ne. Na fada maka wallahi Malamina yana aiki akansu maganar nan zata bi ruwa. Ita Yakumbon da kanta za ta ce a bar maganar. Yarinyar kuwa duk iskancinta sai an sauke mata shi. Ba za ta sake yin wani yunkuri domin bata maka suna ba."
"Wai kai Alh. Tahir tsoron me kake ne? Ka amince mana ka yar da kwallon mangwaro. Yarinyar nan a bariki ta sameka tayi kadan ta kawo maka cikas da girmanka da komai." Wani da bai ce komai ba tun dazu ya tofa albarkacin bakinsa.
Mai neman kuka ne aka jefe shi da kashin awaki. Basu wani jima ba suka shawo kansa. Nan take Maigidan wanda aka fi sani da Comared ya kira Malamin tsibbunsa a waya. Suna kan magana wani mutum sanye da kufta da wando ya zo ya shige cikin dakin Comared din da dan matashi da bai fi shekaru sha takwas ba.
Bayan ya gama wayar ne Alh. Tahir ya tsare shi da idanu yana nuni da dakin nasa.
"Comared ba dai kaima ka fara daya harkar ba da maza?"
Kkamar dazu, yanzu ma dariya sauran suka yi masa. Comared ya gyara zama yana shafar gemunsa.
"Wannan Malamin da na kira shi ya dorani a harkar nan. Naki fada maka ne kawai saboda naga kamar kana kyamar abin. Magana ta gaskiya wani aiki aka yi min shi ne yace na nemi namiji. Washegari aikin ya ci to amma abin ya zarce...." Ya kare da shu'umar dariya.
Alh. Tahir ya kada kai "kace ya hadani da mata goma ni dai akan namiji guda."
Wata dariyar Comared ya yi domin aikinsa kenan. Dariya kamar dan akuya.
"Ai kuwa ka makaro domin kuwa namiji ya ce ka nema ranar laraba kafin rana tayi zawali. Indai kayi yadda ya ce da kanka za ka nemeni. Zai aiko da magani da zaka hada kafin kayi abin."
Hula Alh. Tahir ya cire ya shafi sumar kansa wadda ta fara samun bakin furfura. Ko kadan baya son auren Yumna musamman saboda abin da ta nunawa Farha. A bangare daya kuma ko yana shan giyar wake ba zai so tsinuwar Yakumbo ba. Sau daya dai don ya nemi namiji ba zai rage shi da komai ba. Yana tunanin abin yaji tsigar jikinsa ta mike har amai na neman taso masa. Wayarsa ya dauka ya tashi yana yi musu sallama.
Comared ya dakatar dashi daga tafiya "bari nasa ayi maka booking wanda ya san me yake yi tunda kai sabon shiga ne" waya ya dauka ya sake kira sai ga mai kuftar da ya shige dakinsa ya fito.
Zubewa ya yi kamar mai rokon gafara a gabansa "Yallabai kana da wata bukatar ne?"
Kofar dakinsa ya kalla ya hadiyi yawu "yaron da ka kawo daga gani ya yi kawai. Kwararre a harkar nan nake so kayi min booking ranar laraba mai zuwa. Ina son irin wanda idan sabon kamu ya samu gobe da kansa zai koma. Daga aljihuna kadai zan baka dubu dari biyar. Shi kuma uban gayyar ba mai rowa bane. Ka sa rai da farin gani."
Shazali ya saki murmushi har hakoransa suka fito. Ya san inda zai samo musu kalar wadanda suke so. Shi da yake da shaidar da zata tarwatsa musu rayuwa, dolensu su zo ko sun ki ko sun so.
GOMA ƊAYA GOMA.
Akwai uwa kuma akwai uwa! Wadansu uwayen sun san cewa 'ya'ya amanar Allah ne kuma suna kokari wurin ganin sun sauke in nauyin. A cikinsu wasu suna yin nasara wurin aikata daidai a wannan tafiya mai dadi da wahala. Wasu kuwa kuskure suke aikatawa wanda soyayyar 'ya'yan ne yake zama sanadiyarsa. A shagwaba 'ya'ya fiye da kima. A kasa tsawatarwa kurakurensu, sannan a karshe a biyewa ra'ayoyinsu koda zuciya da kwakwalwa sun san hakan bai dace ba. Kaso na biyu cikin uwayen bayan wannan rabe raben na masu son sauke nauyi sune masu fifita kawunansu da bukatunsu akan na 'ya'yansu. Irinsu ake yiwa lakabi da ballagaza.
Kwakwalwarta kalau take balle ace lalura ke hanata bawa 'ya'yanta kulawa. Ita bata ma san cewa kuskure take aikatawa ba. A lissafinta kodayaushe ita ce farko kafin danta. Shi yasa take gabatar da farincikinta kafin na danta. Ita fa ko yunwa ke damunsu ita da 'ya'yanta sai ta fara koshi take tunawa dasu. Idan abincin babu yawa sai su kare da sudin hannu. Kulawa wadda ke karkata zukata ga nuna tausayi da damuwa ga mai bayar da ita bata fiya shiga tsakaninta da nata ba. Wannan sakacin nata zai iya zama kalubale kuma babbar jarabawa ga 'ya'yanta da duk wanda ya rab'e su. A karshe da za ta rigasu komawa ga Allah da wahala su ji kewa irin wadda 'ya'ya ke ji idan sun rasa uwa. Albarkacin wata tara, nakuda da shayarwa kadai za ta ci.
Ya ke Uwa!
Ki koyawa 'ya'yanki sonki ta hanyar kulawa, tausayi, jinkai, ladabtarwa da soyayya. Idan a gaba kin sami sabanin tarbiyar da kika yi musu ki sani cewa kowane bawa yana tafe da kaddararsa. Ke dai ki tabbatar cewa kin yi iya yinki har a gaban Allah ta yadda ba za ki zama wata Asaben ba. Kin bata naki ki bata na wasu da basu ji ba basu gani ba.
Kada ku manta laifin ba na Uwa bane ita kadai.
***
Ya dauki kimanin minti goma sha biyar a dakin bata ce komai ba. Hasali ma ko motsi daga inda take bata yi ba. Qibdiyya ce a gefenta idanunta a kumbure sun yi ja, da gani tasha kuka. Ya yi mata magana bata amsa masa ba. Tun shigowarsa da ta taso a guje Asabe tayi mata tsawa ta koma ta zauna.
Gajiya ya yi da shirun. Ya san halin mahaifiyarsa. Karshenta kudi take son karba a hannunsa take ta kirkiro wannan dabarar. Hannu ya zira a aljihu ya zaro dubu goman da ta rage a hannunsa ya dora mata a hannun kujera.
"Qibdiyya taso mu tafi" ya furta a yayinda ya mika mata hannunsa don ta kama.
Sannan Asabe ta tashi da fada bayan ta kwashe kudin "ince ka zo amma don raini baka tsaya kaji me ya faru ba za ka tafi."
Hannu yasa ya matse kansa da yake ciwo. Haka ya soma magana kamar zai yi kuka. Bai san wata damuwar da ta zarce rashin ji daga Abbati ba. Washegari yake son bin sa, ko ma me za ayi gara ayi musu tare. Ko kuma ya bishi a yau....tunaninsa ne ya katse lokacin da Asabe ta sakar masa harsashin da ya bula kwakwalwa da zuciyarsa.
"Ban san wane irin sakaci kake yi da 'yarka har wani tsinanne ya..ya" sai taji bakinta ya sarke sakamakon idanun da Munzali ya zuba mata.
"Me aka yi?" Ya furta da sautin da yafi kama da umarni. Bai ma san ya yi amfani dashi ba saboda yadda ya soma tsorata tun kafin yaji karshen zancen.
Asabe ta hadiyi yawu "ina jin fyade aka yi..."
"Qibdiyyan???" Ya tambaya a razane kafin ma ta kai karshe. 'Yarsa ya dauka da zafin nama yana neman dubata mata jiki.
Asabe tayi azamar karbeta "baka da hankali ne za ka bude mata jiki? Na riga na duba kuma wallahi namiji ya kusanci..."
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un....hawaye ne suka ballewa Munzali. Zancen ya dinga bin sassan jikinsa tamkar ana huda shi da alluran da aka kona a wuta. A wurin ya durkushe yana kuka mai sauti. Kuka irin wanda bai taba yin kwatankwacinsa ba. Da zai ci karo da ko ma waye ya tabbata sai dai ayi masa takwara a dangi domin shi kam tasa ta kare. Kashe shi zai yi idan ya so shi ma a hukunta shi.
Asabe gani tayi ya dora hannu a kahon zuci yana bugun kirjinsa. Idanunsa basu bar fitar da hawaye ba.
"Kashe kanka zaka yi ko kuwa zaka tambayeta waye ya mata wannan aikin?" Sannan ta kara da cewa "kuma ina zargin ba abin kwana daya bane domin kuwa alamu sun nuna ta soma sabawa."
Runtse idanuwansa kawai ya yi. Yawancin maza idan 'ya'yansu mata suka isa aure sai kaga suna ja wa manemansu aji. Ba don komai ba kuwa illa tunanin cewa idan ka auri 'yata fa ga abin da zaka yi mata. Wannan kishin yadda uba yake yiwa 'yarsa haka 'ya'ya maza suke yiwa uwayensu idan kaddarar sake aure ta gifta musu. Munzali yaji zuciyarsa tana suya a kirjinsa. 'Yarsa mai shekaru biyar ake cewa ta saba...ta saba da namiji a kananun shekarunta. Shi da ransa, mahaifiyarta ma da ranta. Garin yaya???
(Zina bashi ce Munzali. Kaga Allah Ya bamu 'ya. Idan bamu tuba ba wata rana ita za ta girbe abin da muka shuka)
Kalaman Abbati a wani lokaci da yake yi masa maganar tuba daga wannan alfashar suka dawo masa. A hankali ya tashi yaje gaban Qibdiyya ya durkusa. Ya mika hannuwansa gareta duk ta firgice. Asabe tayi mata dukan da ba a taba yi mata ba a dalilin kin fadan wanda yake mata. Shi yasa ta tsorata ko shi ma dukanta zai yi. Ga mamakinta da Asaben sai ya rungume Qibdiyya. Riketa ya yi sosai a jikinsa yana jin kamar ranar suka fara haduwa bayan haihuwarta. She will always be his baby duk girmanta. Kasancewarta tsatsonsa bai kara mata komai ba sai masifa. Ya cuceta cuta ta har abada domin an bar mata tabo daga barnar da ya kasance yana aikatawa.
"Ki yafe min Mariya. Ki ce kin yafe min."
A razane Asabe ta taso har tana
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 37 Chapter of 62