ta soma hamdala. Tafiya zasu yi yanzu yanzu in Allah Ya yarda. Bata bukatar Hanne ta zo ta bar nata abin fadin kamar na Deluwa da 'Yashshafa.
Kafin ta shigo tun a waje Lilu ya tareta ya bata labarin gamonsa da 'yar tashe. Dariya taso yi aka kuma bude gate Abbati ya shigo. Zuciyarta tayi wani irin dokawa mai wuyar fassara. Abin sai ya bata mamaki tunda a hanya ta san Munzali ke jan motar. Bata ga alamun Munzalin ba sai mace. Shi ne ta shige bangaren Mami da sauri don ma kada su hadu.
Ya kula da irin saurin da take yi wanda yake da nasaba da gudun haduwa da Hanne. Da gaskiyar Munzali dai da ya ce masa kishinsa take.
"Wai shiga ka ke so nayi na kirasu? To wane bangaren zan je?"
Hanne ta katse masa tunani da ta bude kofa za ta fita.
"Don Allah Hanne ki kama kanki. Kin san abubuwan da bana so. Kar ki gwada musu a gidan nan. Godiya kawai muka zo yi musu na kyautatar da suka yi mana."
Ya san halinta. Ko babu komai tsakaninsa da Farha ba zai so ta shiga tayi abin da zai zubar mata da kima a idonsu ba. Idan Farha rabonsa ce zai so ta shigo gidansa tana ganin mutumcin wadda ta tarar kuma kanwa gareshi.
"Naji" ta amsa da kunkuni.
Abbati dakatawa ya yi aka yi musu izinin shiga bayan ya yi sallama. Yana saka kafarsa Farha na shigewa wata kofa da yake tunanin kitchen ne. Murmushi kawai ya yi sannan aka gabatar da Hanne ga Mami. Anyi sa a Mami Khadija tayi mata kwarjini shi yasa ta gaisheta a mutumce.
Da kyar Mami Khadija ta samu suka ci abincin don sun matsu su tafi Kano a ranar. Basu dade suna jiran Munzali ba ya iso. Wurin Mardiyya ya fara zuwa suka yi sallama. Mama Nasima tana son tambayarsa alakarsa da abokan tafiyarsa da Mami Khadija amma yau ba hali. Ciwon karyar Mardiyya duk ya tsaya mata a rai.
Da zasu bar gidan Abbati ya so Farha ta fito ko yaya ya sake ganin fuskarta amma taki. Tsoron ganin matarsa take yi. A yadda ta ganshi hadadde dan gayu da wuya ace matarsa ba haka take ba. Idan kuwa haka ne kila sai ta raina kanta. Karshenta kuma tafiyar da bata taba irinta da wani d'a namiji ba ta sami tangarda. Gara dai kada ta kai kanta kallon abin da zai iya tada mata hankali.
***
Fitar su Hasiya ba dadewa Ale Gambo ya dawo. Salima na durkushe bakin murhu tana faman hura wutar itace cike da tashin hankali saboda daren da girkin ya yi. Gashi itacen danyene, yaki kamawa sai hayaki yake ta fitarwa. Daga bakin rariyarsu 'yan matanta ne suke wanke wanke.
Takunsa dif-dif tamkar wani doki mai ji da karfi ya shigo tsakar gidan. Sannu da zuwan da yaran suke yi masa ma bai ji ba sai kira yake kwalawa Salima. A razane ta fito domin da wuya suke wanyewa lafiya idan ya shigo a wannan yanayin. Cikin tsananin fushi da mamakin rainin da ya soma shiga tsakaninsu ya nuna ta da dan allinsa. Har wani haki yake ga feshin yawun da ya kan yi in yana magana cikin fushi.
"Hasiya na gani ta fita."
"Wani abin ne ya sameta?" Salima ta tambaye shi da firgici.
"Nawa ta baki?"
Maganar ta doketa sosai ba kuma don yau aka fara ba. Mijin aurenta ne, uban 'ya'yanta, wanda bai taba sanin darajarta ba yake yi mata wannan tambayar. Duk inda mutumci yake sun dade da yin hannun riga da Ale Gambo. Maganganunsu dasu Hasiya na dazu suka dawo mata. Tabbas zancen Ayaah gaskiya ne, babu wanda zai iya k'watar mata 'yanci a wannan yanayi sai ita da kanta. Tana jin tsoronsa har cikin kasusuwanta domin dukanta yake kamar ya sami gardi daidai dashi. Amma haka ta daure ta yatsina fuska tana magana cikin bacin rai ita ma.
"Ajiya ka bata ko bashi?"
Hagu da damansa ya waiga babu kowa sai yaransu suna kallonsa. Ya dawo da idonsa kanta tare da nuna kirjinsa.
"Wai dani kike Salima?"
Haka kawai taji kwarin gwiwa yana ciccibata. Daurin zaninta da yake neman kwancewa ta gyara tana cewa,
"Idan akwai wani Gambon a gidan nan bayan kai to dashi nake."
Jikinsa sai ya hau tsuma kamar mazari. A zatonsa ko hauka take bata isa ta maida masa magana haka ba. Daga shi har ita sun ji karar kwanukan wanke wanken domin a tsorace yaran suka mike. Sun tabbata sai ya dakar musu uwa. Hularsa ya cire ya yar a gefe. Kodaddiyar babbar rigarsa tabi bayanta.
"Baba kayi hakuri"
Ko kallonsu bai yi ba ya dubeta yana jinjina kai. A firgice take sosai amma tayi alkawarin daukar mataki.
"Dama ina da labarin Hasiya" ya ce yana kumfar baka "ance tafi kowa rashin kunya a cikinku. Wato zuwa tayi ta kitsa miki gaibu tace kiyi min rashin kunya ko? Tunda baki da hankali har ki ka karbi shawararta za ki ga abin da zai biyo baya. Wallahi Salima daga yau ko daga ido ki kalleni kin daina.."
"Idan ka isa ka kasheni kawai ka huta." Ta bashi amsa da kuka.
"Mama kiyi shiru don Allah" cewar autarta.
Ita da yaran babu wanda ya kula da lokacin da ya hanyo igiyar gugar rijiya. Murdeta kawai ya yi ya kama daidai inda zai masa dadin riko ya shiga lafta mata.
Salima taki yin ihu kamar yadda ta saba. Tsayuwa tayi kyam dukan yana sauka a jikinta amma zuciyarta ke karbar zafinsa.
Shi kuma gogan rashin jin magiyarta ya sake tunzura shi. Hannu ya daga ya kai mata dukan da yafi kama da naushi a gefen fuska. A lokaci ne kuma ta aiwatar da shawarar Ayaah. Tafiya tayi luuu ta zube a kasa. Yaran suka yo kanta suna kuka. Ale Gambo ya soma masifa yana jiran ta tashi yaji shiru.
"Ke Salima. Salima? Tashi mana" ya ce jikinsa na yin sanyi. Igiyar ya saki ya dan ja baya.
Babbar 'yar tasu mai shekaru sha uku Ihsan tana ganin ta fadi ta ruga makota a guje tana kuka. Duk da haka Ayaah ta ce suyi amma a tsorace take ko suman gaske Ummanta tayi. Kuka take tana kururuwa kamar yadda Ayaah ta fada mata a dan tsukin lungunsu.
"Wayyo Allah. Baba ya kashe mana Umma"
Hankalin Ale Gambo ya tashi sosai da yaji me take cewa. Girgiza Salima ya shiga yi yana faman kiranta kamar mahaukaci. Durkushe a wurin makotan da suka fara shigowa suka same shi.
"Haka kawai naga ta fadi nima." Ya dubi yaransa a darare "ai ban mata komai ba ko?"
Basu amsa masa ba sai ihun da suka cigaba da yi.
"Baba ya kashe Ummanmu da duka."
Salati kawai ake ji sai matan da suke neman taimaka wa Salima.
Shi kuma Ale Gambo sai huci yake da surutai mara sa kan gado. Duk wanda ya gan shi a wannan lokacin ya san ya shiga rudani, amma yana kokarin boyewa don kada ya tonawa kansa asiri. Hannuwa yake ta dagawa kamar mai shirin tashi sama.
"Ni ban mata komai ba! Daga maganar fatar baki sai mutum ya suma? Salima ki ji tsoron Allah ki mike. Wai me nayi miki?"
Ba a dauki lokaci ba ta dan farfado musu amma taki ta sha ko da ruwa ne ga kuma baki duk sai fitar da jini yake. Gefen fuskar nan inda ya daka ya kumburo suntum kamar alkubus. Kan a ce me gida ya kacame da 'yan jaje cikin daren, daman makotan ta da dama suna da masaniyar ba yau ya fara bugun ta ba.
Wani dan tsoho da yake yawan zama nan gindin bishiyar kofar gidan nasu ne yace to ya zama tilas su nemo iyayenta a sanar dasu kafin ya kashe musu 'ya wataran sai dai a kai musu gawa.
Kowa ya yi na'am da zancen. Shi ya saka wasu magidanta biyu tare da Ihsan suka hau adaidata zasu je a fada wa iyayenta halin da ake ciki. Ale Gambo yana neman yi musu taurin kai domin ya gudu samarin layin suka kama shi. An tsayar da magana cewa da an dawo da iyayenta zasu wuce dashi ofishin 'yan sanda.
***
Idanu ta runtse tana mai jin haushin kanta. Shigowar Innayo ta bakwai kenan dakin amma ta kasa motsa baki tayi mata tambayar dake cin ranta. Dangin Babansu da makota da dama sun zo mata barka. Amma yadda babu kowa daga gidan mijinta haka nan babu daga dangin Innayo. Hatta na cikin Kanon babu wadda ta zo. Abin ya yi mata ciwo. Indai ba su ma din sun tsaneta ba me zai hanasu zuwa? Ga yaranta da take masifar kewa kamar tayi hauka.
Sallamar Uwani ta jiyo tayi saurin share kwallarta. Sai dai tuni Uwanin ta gani lokacin da ta bankado labulen dakin.
"Kuka Zara? Naga uban kayan abinci su akarambana (Hasiya) suna gyarawa wai na suna. Ba dai rigima ku ka yi da Alh. Unais ba?"
Bangare daya na fatan haka ne ko don tayi mata dariya. Ta jima tana fada mata kudin miji ba a tinkaho dashi. Burgewa shi ne ki tashi ki nemi na kanki. Daya bangaren kuma mai sauran imani yana fatan ba haka bane. Shi ma kuma domin kada 'yan bani-bani su kara yi mata yawa idan Zaran ta durkushe ita ma.
"Bama waya ma" ta amsa mata muryarta tana karyewa "sai dai matsalarsa bata gabana. Na san yadda zan yi na rama duk abubuwan da suka yi min shi da Haj. Fatakwal."
"To meye kike hawaye?"
*
A waje Maimuna, Hasiya, da Murja da Ummita wadanda daga gida suka wuto nan din kai tsaye ke ta aikin kayan miya da nama. Yaran Maimuna duka maza ne. Biyu cikinsu, manyan sune masu yayyanka nama. Hira suke yi cike da nishadi Ayaah sai ta dinga jin kanta kamar bare. Gefe ta koma tana daddanna waya amma ko kadan abin baya burgeta. So take ayi da ita amma bata san kan hirar ba. Zantuka ne da dukkansu suka san wani abu a kai.
Hasiya tana ta lura da ita. Yanzu kam tana sane ta ki sakota cikin hirar saboda ta kara gaskata maganar Salima. Ta kuma samu abin da take so. Ayaah ta bata rai sai wani karkada kafa take wanda ta san da wata cikin yayyenta za ta yi mata magana karshenta a kare da rigima.
"Ayaah."
Kamar jira take ta amsa kiran Antinsu Maimuna da sauri.
"Na'am"
"Jeki ki karbo jaririyar nan wurin Zara na goya miki ita. Kin dai iya goyo ko?"
Yanzu ma da saurinta ta gyada kai "na iya"
"Dan wa ki ka taba goyawa?"
"Aji tsoron Allah dai banda karya"
Cewar Ummita da Murja suna mamakin yadda ma ta amsa mata a ladabce. A zatonsu gefen da ta kebe kanta tana danna waya duk cikin rashin kunyarta ne.
"Ku kuma don baku taba gani ba sai ku yanke mata hukunci da rashin iyawa?"
Mamaki ya kara kamasu. Anti Hasiya ce fa ta kare mata! Anya yau lafiya kuwa? Kara musu mamakin tayi ta hanyar kallon Antin tasu suka yiwa juna murmushi sannan ta kallesu ta murguda baki. Da sauri ta ta juya ganin Anti Hasiyan ta bude baki. Bata so tayi mata fada yau. Kullum ita ce mai laifi idan abu ya hada da yayunta. Yau dai ita aka tarewa. Duniya tayi mata dadi.
*
Innayo ta fito daga bandaki ta jiyo muryar Uwani da Zara a cikin daki. Bata ji shigowar Uwanin ba ta shiga wanka bayan ta gama hadin sabulun salo na jaririyar da take nuna bata damu da ita ba. Hannun kofar ta kama za ta bude ta ji zancen da suke yi wanda ya sake tsinka mata zuciya game da sha'anin 'ya'ya.
"Yo don dangin Innayo basu zo miki barka ba sai ki hau kuka? To ko dai kin ji wata magana ne?" Uwani ta furta da bacin ran ashe duk kukan Zaran ma mara dalili ne a ganinta.
"A cikin gidan fa nake amma ko mutum daya ban ji ta kira ta fada musu haihuwar ba. Ai dole abin ya yi min ciwo. Kuma ita ma bata taba daukan yarinyar nan duk kukan da za ta yi."
"Kinga Zara bana son munafunci fa. Ni ce ba wata ba da za ki fake da rashin zuwan dangin Innayo don ki boye 'yar tsamar dake tsakaninki da mijinki. Daukar jika kuma ina ce haka kike so?"
Daidai lokacin Ayaah ta shigo. Murmushi ta yiwa Innayo tunda sun gaisa lokacin da suka zo. Tashin maganganun da ta ji ita ma sai ta kasa karasawa dakin. Fita ya kamata tayi amma ta kasa lokacin da ta kula idanun Innayo a birkice suke. Akwai boyayyen bacin rai da damuwa a cikinsu. Sai kuma kwallar da ta cika shi taf amma taki bari ta zubo.
"...ba har gidanki ki ka kirani akan in zo in karbarwa su Innayo tsofaffin kayan da baki dinka ba don kada su zama abin kallo wurin taron suna ba?Ko baki dinga yamutsa fuska da na baki labarin tana ciwon hakori ki ka ce kazanta bace? Shi ne yanzu za ki dinga kukan karya kamar kin fi kowa damuwa da ita..wai ma da kin taba gayyayarsu suna ne?"
"Meye na daga muryar? Kuma duk abin da ki ka fada ai bai canjata daga zama uwata ba." Zara ta ce da sanyin muryar wanda hankali ya fara ziyarta.
Uwani tayi wata irin dariya ganin kamar rainin hankali Zara take yi mata.
"Daga baya kenan amma kin san sai dai ki fadawa wanda bai sani ba ko? Na san Innayo za ta ji dadi. Ko ba komai yadda ta dade tana son ki dinga rabarta sosai yau ta samu tunda baki da tudun dafawa."
Allah Sarki Innayo, kwallar sai ta sauko a guje. 'Ya'yan cikinka su yi maka irin haka ba karamin ciwo gare shi ba. Ji tayi kafafunta suna neman sakinta a kasa sai hannuwan Ayaah suka tareta.
Tausayin Innayo ya tsirga mata. Tunda suka shigo matar nan tana kan kafafunta. Amma ita ce 'ya'yanta suke yiwa haka.
Daga ciki suka ji Zara na cewa "Ko ma me za ki fada kiyi ta fada. Na riga na fara ganin nawa sakamakon, ki jira naki."
"Ba zan ga komai ba sai alheri. Wato rashin kunyar da ki ka kwana biyu baki yi ba saboda kin dawo gida mai soro ce tasa ki cewa nazo dama?"
Zara ta share kwallar da ba za ta ce ga aihinin dalilinta ba.
"Ki barshi kawai."
Ayaah kasa jurewa ganin hawayen Innayo tayi ta juya za ta fita. A yau ta fahimci me yasa a gida ake bukatar wanda ba ya shakkar kowa.
"Ina za ki?" Innayo ta tambayeta cikin dusashewar murya.
Kofar dakinta ta harara tukunna sannan ta ce "Anti Hasiya zan kira."
Innayo ta murmusa ganin ran Ayaah yana neman fin nata baci
"Dawo abinki Hajara. Idan babarki ta zo raina sai yafi yanzu baci. Ba wani hakuri gareta ba bare jin magana a irin wannan yanayin."
Ayaah bata san lokacin da tayi murmushi ba "da gaske ita ma bata jin magana?"
"Ban ce ba" Innayo ta amsata cike da kulawa.
Sautin tsakin Uwani wadda ta mike suka jiyo tana mai cewa
"Aikin banza. Kin san abubuwan da na katse na zo? To wallahi sai kin biyani tunda a bakin aiki nake ki ka sani fitowa."
Zara ta auna ta ga a neman lafiya babu ji da kai. Idan tayi shiru kanta za ta cuta. A yadda ta wahala kwanakin farkon haihuwarta ba za ta so a maimaita ba.
"Wurin dinkin nan nake so ki duba min. Ina jin kamar bai yi ba."
Metiron Uwani ba mutumci. Banda tana tsoron kada kasuwar ta watse da sai tayi dariya. Ai tun ranar da Innayo ta saka ta duba Zaran ta kula dinkin zai iya samun matsala saboda rashin kulawar da ya samu. Duk da cewa a ranar a tsorace take amma ta san muddin Hasiya tana wurin bata isa ta karbi kwandalar Innayo ba. Ashe kuwa tana da rabo. Tunda Zara ta sake kawo kanta wallahi sai taci kudinta.
Tashi tayi kamar za ta fita daga dakin a zuwan bata damu ba ta ce "Aiki ne na kuďi Zara. Sannan dole ki san karyar da zaki yi ki zo ki sameni a gida. A nan Innayo..."
Innayo kawai ta bude kofar. Su biyun kowacce ta zaro idanu. Jaririyar ta nunawa Ayaah.
"Dauki kanwarki ki fita kuma kada ki manta abin da na fada miki."
Umarni ta bi ta koma tsakar gida da 'yar jaririyar wadda ta sake nannadewa a shawul.
"Uwani"
Cikin Uwani sai da ya tsirga don tsoro ne ya cika mata zuciya. Yanayin Innayo yasa taji kamar tayi tsuntsuwa ta ganta a nata gidan.
"Ba dake nake ba?" Innayo ta yi mata tsawa.
"Na'am" Muryarta har rawa take da ta amsa.
"Ban ce ki duba min Zara zan biya ki ba rannan?"
"Kin ce."
"Isa ne ban yi ba ko? Saboda bani da wannan mutumcin a idonki."
Maganarta ta biyu babu hargagi balle daga murya. Amma zukatan fitinannu cikin 'ya'yan nata sun girgiza. Duk abinsu bata taba nuna musu wannan bangaren nata ba. Sai suka zata duk wani rashin albarkarsu za ta karba saboda tana son su.
"Wallahi Inn..."
Katseta tayi da cewa "Duba ta."
Zara ta kwanta da tsoron kada fadan ya dawo kanta. Uwani na dubawa ta ce sai an sake dinkin. Hawaye ta soma fitarwa kawai saboda tuna irin azabar da tasha a 'yan kwanakin da suka wuce. Tana ji Innayo ta ce da Uwani ta je ta dauko kayan aikinta. A gurguje ta fice. Duk da dan akwatin tafi da gidanka da take yawo dashi yana mota ita dai burinta ta ganta a waje. Bayan fitarta ne Zara ta kasa daurewa ta kira Innayo a raunane.
"Innayo."
Bata amsa ba ta fita daga dakin. Wurinsu Hasiya ta tafi ta ce komai suka gyara su adana shi suna sai wani satin.
"Wani abin ne ya faru?" Cewar Maimuna.
"Maijego babu lafiya. Banda ma sun dorawa kansu waye yake wani taron suna a haihuwa ta biyar?"
Hasiya kamar bata yarda ba. Dama ta kula da wani irin yanayi da Ayaah ta fito dashi kamar tayi kuka. Ana haka Uwani ta dawo. Bata cewa kowa komai ba ta shige ciki.
Innayo ta bi bayanta ta rufe kofar falonta. Kafin a fara tasa Zara kiran Alh. Unais. Sai da tayi masa kira hudu sannan ya dauka a wulakance.
"Ina fata ba cewa za ki yi kayan abincin sun yi kadan ba. Sannan ki fadawa Innayo dinnan don Allah ayi abinci maidadi saboda dangina da zasu zo da na Laurat. Ayi abin fita kunya."
Taji zafi kwarai da jin kalamansa. Sai dai kuma har duniya ta nade Zara bata da wata uwar sama da ita. Babu mai daukar wannan bakin halin duk son da yake mata ya ce zai jure ya cigaba da kulawa da ita irin na uwa da 'ya. Ita din cw dai dolenta.
"Innayo dinnan ce ba Zara ba. Ka fadawa danginka suna sai wani satin. Idan kuma za ku iya hakura gabadaya zai ma fi."
A hanyar komawa gida yake daga kasuwa. Yana baya direbansa yana ja. Jin muryar Innayo ba shiri ya tashi zaune daga kashingidar da ya yi.
"Wani abin ne ya faru?"
"Ba ta da lafiya."
Ya san Haj. Fatakwal ba za ta lamunce ba shi yasa ya ce zai sanar dasu yadda idan sun zo ba za su takura mata ba.
Gaban Zara yana dukan uku uku ta ji Innayo ta cigaba da cewa
"Baka fahimceni ba kenan. Kwata kwata bana son danginka su zo gidan nan gobe. Bayan wulakancin da ku ka yi min akan zamanta a asibiti da rashin lekowar waninku dubata sai ace za a zo suna? Ga kayan abincinku nan 'yan uwanta sun muku kara sun gyara. Ka aiko a dauka tunda matar taka bata nuna maka mutumcin mazaunan gidan nan ba balle ka zo da kanka. Sannan kasa a kawo mata 'ya'yanta su dubata."
Dammmm...Zara da Alh. Unais da ma Uwani dake tsaye a gefe kowa yaji gabansa ya fadi.
Tsoro ya ji kada ta ce ya sakar mata 'ya ya soma bata hakuri. Yana son Zara har yanzu.
"Kiyi hakuri zan zo. Amma don Allah ayi sunan saboda Hajiyata."
Wato saboda Hajiyarsa. Matar da bata san ciwon tata 'yar ba.
"Suna kam babu shi Unaisu. Idan kun zo ma ba za ku sameta a gidan ba"
Ta kashe wayar ta ce da Uwani tayi aikinta.
"Kinga ya soma warwarewa ne Innayo. Ko in ware duka na sake sabo?" Uwani ta tambaya gudun yin laifi.
"Ni da ban taba shiga aji ba ina zan sani? Ke dai kiyi aikinki zan biya."
Uwani ta san gatse ne. Yau bata san me ya faru ba amma tsoron bacin ran Innayo take irin wanda bata taba ji ba a baya. Haka nan dai ta duka tayi aikinta gabanta yana faduwar da bata san musabbabinsa ba.
Kafin a gama Zara ta kusa suma. Ihu ko surutu irin na mai jin jiyo bata sami zarafin yinsa ba. Tsoron sake batawa mahaifiyarta rai take yi. Wani abu da ya dade bai ziyarci zuciyarta ba. Innayo na ganin yadda take cije lebe da damkar gefen katifa sai ta matsa kusa da gadon. Hannunta kadai ta rike tana girgiza mata kai da rarrashi amma sai taji salama. Ciwon ya ragu sai wani irin abu da take ji game da matar da ta kawota duniya. Hawaye ne ya balle mata bata sharesu ba kuma babu niyar tsayuwarsu. Fuskar nan da ta tashi tana gani a bakin murhu a yau ta maye mata gurbin duk wata allurar kashe ciwo. Bata sani ba ko rashin kula ne amma kamar yau ta fara tantace komai na fuskar Innayo. Idanuwanta sun fada ciki ana gani za a gane wahalar rayuwa ce ta kawosu. Farar fatar da suka gada ta dusashe sosai. Wanda ya san kuruciyarta kadai zai iya bada shaidar ita din fara ce a da. Ga layukan girma don ba a ce tsufa ba sun zane mata fuska. Hannun da ta riketa dashi kuwa ba ka ce na mace bane. Babu kanta kamar da tunda ta daina kaso tamanin cikin ayyukan da take a baya. Amma fatar ayi wani irin tauri kamar na kakkarfan namijin da ya sha aikin hannu. Hannuwa ne da suka raini tare da aurar da mata har guda tara! Mata da masu kudin cikinsu suka juyawa hannun alkhairi baya. Matan da ita Zara take cikinsu! Kawai sai ta fashe da kuka. Ta sake yiwa hannun Innayo wani irin riko tamkar tare da rayuwarta yake tafe. A haka baccin wahala ya dauketa ga gumi ya wanke mata fuska.
Uwani ta gama tattara kayanta ta ajiye pain reliever din da Zara za ta sha idan bukatarsa ta taso. Tsakar gida ta fito za ta tafi daidai lokacin da Ummakati ta shigo gidan da sallama. Ita ma tunda Munzali ya yi mata magana akan gyaran zumuntarsu da 'yan uwansu ba karamin dadi taji ba. Baudadden miji gareta sai da kyar da sudin goshi ya barta ta fito barka da yamman nan.
Ta tsaya suna gaisawa Asabe ta jiyo muryarta tayo waje. Bata ga dalilin wannan shishshigi da 'ya'yanta suka fara ba cikin kwanakin nan. Fadan da ta taso yiwa Ummakati bai samu ba ta tsaya kallon wasan kwaikwayo a cewarta.
Innayo ce tayi saurin fitowa kafin Uwani ta bar gidan.
"Nawa ne kudinki?"
Sai taji kunyar idanun dake kansu. Ko babu su ita yau tsoron Innayo din ma take.
"Ki barshi ba zan karba ba."
Innayo ta hade rai sosai ta ce "Idan baki tsaya kin karba ba daga yau in kin zo gidan nan kar ki kuma shigar min daki."
Maimuna sai ta tashi da sauri "Subhanallahi. Innayo me ya yi zafi?"
"Kar ku saka min baki." Ta kuma kallon Uwani wadda duk ta tsure "nawa ne?"
"Dubu shabiyar. Don Allah ki barshi Innayo." Ta ce kamar za tayi kuka. Kowa ita yake kallo kamar basu santa ba.
Innayo bata saurareta ba ta kwance gefen zaninta. Dubu takwas ta hado dama ta san bata da shabiyar din. A rashin hankali na Uwani idan ta so kin karba da sai ta yanko kudin kasa sosai. Ita dai Innayo sai ta kalli Hasiya da Maimuna,
"Nawa zan samu wurinku?"
Hasiya ta so cewa kar ta biya sai dai ta kama bakinta. Dubu uku ta bayar ta bar dari biyu da zasu yi kudin adaidaita sahu ita da Ayaah. Maimuna ta bada dubu biyun da Innayo din ta bata dazu. Samarin 'ya'yanta kamar hadin baki kowa ya ciro dari biyar kudin da aka basu sallama na aikin kafinta da suke koyo. Murja ta dauko jakarta ta mika dubu daya. Ummita dari bakwai gareta a hannu ita ma ta mika. Ummakati ma da bata san silar abin ba ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 26 Chapter of 62