gida. Saura wata daya suspension dinta ya kare. Sannan ba tare da sanin kowa ba sai mijinta ta dauki Zakiyya da Qibdiyya sun je asibiti. Duk wani abu da ya dace ayi Salihi ne ya dauki nauyin biyan kudin. Ita da 'yan uwanta duk sun karbi zancen da yabi bakin kowa na cewa karayar arziki ce ta sami su Munzali. Asabe ta gina zancen akan wanda Mami Khadija tace mata taji a wurin Alh. Tahir lokacin da ta kira tayi musu jaje.
Salima dai aure ya mutu murus. Ale Gambo ya yi rantsuwar idan bata koma ba cikin kayadadden lokacin da ya bata tana da damar sake aure domin babu shi babu ita. Innayo ta lamunce mata tayi abin da zuciyarta take so. Cikin farinciki don har ta murmure ta ce ta gama zama dashi. Kwanaki kadan da suka wuce ta gama iddarta.
Abbas ya warke ya koma gida. Sauki ya samu don ya fara magana kuma yana tafiya da kansa. Tsakanin su Honourable da Abdulkarim sai tarin godiya. Shi da Ummita soyayya suke yi mai ban sha'awa. Biki saura sati biyu. Ayaah ma ta gama NECO sauran WAEC wadda jarabawa biyu suka rage su kammala baki daya. Anti Hasiya ciki ya fito. Laulayi ya yi sauki sosai. Tana samun riritawa daga mijinta, mahaifiya, 'yan uwa da 'ya'ya. Haihuwa kawai ake jira. Karshen abin farinciki shine kulle Danliti da Shazali da Alh. Sadisu yasa aka yi. Duka malamai da masu gadin makarantar da sukw da hannu su ma an rufe su. Shi Shazali ma a kurkukun bai tsira ba domin kusan kullum sai an yi masa duka.
Tunda Baaba Mari take bata taba samun kwanciyar hankali dari bisa dari ba sai yanzu. Alkawarin Allah Ya cika. Bayan kowanne tsanani akwai sauki tafe. Damuwarta ta shekara da shekaru ta kau. Sauran 'ya'yanta dama basu da matsala irin wadda ta jima tana damunta akan Abbati. Yanzu da komai ya daidaita ta sami nutsuwa.
Mal. Sa'idu ya soke karatun Allah. Sauran 'ya'ya da jikoki duk yasa an dawo dasu gaban iyayensu. Ya kuma aurar da 'Yashshafa ga wani tsohon saurayinta. Deluwa kamar ta hadiyi zuciya. Tana ta mitar yaya zasu yi ida Sha'aib ya zo. Hanne ma ta gama idda har manema sun fara kawo caffa. Ta cigaba da rayuwarta sannan ta rike sirrin Abbati.
***
Wata biyu kenan Abbati da Munzali suna karbar treatment akan hanyoyin tsira daga komawa tsohuwar rayuwarsu. Kafin su taho duk wani abu da suka mallaka sun damka shi a hannun Dr. Abdallah Saraki. Zunzurutun kudi da kadarori. Sutura da takalma kadai ne basu bayar duka ba. Amma hatta zobe da agogo basu bari ba. Motocinsu sun sayar. Gidan ma a satin aka sami mai saya. Sauran abin da basu kammala ba suka bar masa amanar sayarwa. Cikin kankanin lokaci aka dinga gina rijiyoyin burtsatse a kauyukan da suke tsananin bukata. Aka biyawa marasa lafiya da yawa kudin asibiti. Kudi ya zaga inds ya kamata. Dr. Abdallah ya taimaka musu kwarai wurin sauke nauyin da yake wuyansu. Hankulansu kwance a inda suke. Wayoyin hannunsu ma shi ya saya musu kafin su tafi.
Bayan tafiyarsu Alh. Sadisu ya neme su a waya shiru. Sai ya tuntubi Alh. Tahir. Shi ma bai san inda suke ba. A wurin Mami Khadija ya sami numbar Baaba Mari. Takanas ya tafi Kano inda suka hadu shi da Alh. Sadisu suka kirata. Ta hadasu da Mal. Inuwa shi kuma ya faygace musu halin da ake ciki.
"Alhaji da zuciya daya nake kaunar yaran nan. Idan suka dawo kana ganin zasu yarda in saka su cikin siyasa? Ba wai 'yan banga ko makamancin haka ba. Ina so in daga su a idon duniya. Su fara da zama PA dina ko Secretary. Ta yadda duk inda nasa kafa muna tare. A hankali har a sansu wata rana idan muna raye in daga hannuwansu a zaben manyan mukamai" Alh. Sadisu ya ce da Alh. Tahir bayan sun koma gidan Alh. Sadisun.
"Nima nayi tunanin janyo su aikin kwangilata. Amma ina gudun kada su ki amincewa saboda yarana da suka nema a baya. Sannan bani da wani mutumci a tunani a idanunsu. Dama auren zai yiwu da naji dadi. Musamman na Farha." Shi ma Alh. Tahir ya fadi nasa kudirin. Jari zai basu mai tsoka da zai ishesu tsayuwa akan kafafunsu. Amma kuma Alh. Sadisu zai bawa "ina gudun kada su ki karba. Ko kuma su ga kamar nayi ne da wata manufa"
"Hakika haduwarka da yaran nan izina ce garemu baki daya Alh. Tahir. Duba ka gani yadda rayuwarka ta canja. Ina fada ba don izgilanci ba. Yadda ka rabu da harkar mata haka idanuna suka bude na rabu da duk wani abu na haramci a siyasata. Don gani nake kamar hakki ne ya kama Abdul. Kuma naga fa'ida domin na kara samun masoya. Kwarjinin da nake fata na kara yinsa ba tare da na bawa kowa tsoro saboda cin zali ba."
***
Garin Parioli wanda yake cikin babban birnin Italy wato Rome shi ne inda ake da babban masallacin kasar. Saboda girmansa zai iya daukar masallata dubu goma sha biyu a lokaci guda. A daya daga cikin wuraren alwalar maza Abbati da Munzali ne suke alwala. Sun cika burinsu na ziyartarsa kafin su bar kasar. Abbati sanye yake da shudin wando da shudiyar shet wadda ya dorawa jacket sea green. Munzali kuwa bakin wando ne da polo shet ruwan madara a jikinsa. Su biyun sun yi kumari sosai. Ashe duk yadda jikinsu yake wannan abu yana tsotsesu basu sani ba. Sai yanzu suka kara zama cikakkun maza masu cikar kamala. Kowanne ya ajiye gashi a fuska wanda ya kara musu haiba. Alwala suke Munzali yana ta rawar dari. Abbati da ya gama ya koma gefe yana yi masa dariya.
"Nace maka ka k'ara riga akan ta jikinka amma ka dage wai da alamun rana a waje. Yanzu kuma ka zo ka sani a gaba kana makyarkyata kamar wanda ya kulla abota da DJ"
Munzali ya ciko hannu da ruwa zai watsa masa ya kauce yana kara yi masa dariya. A hasale Munzali ya ce,
"Ka dai ji kunya. Wai a matsayin wa na kake amma ka kasa sadaukar min da rigar sanyi. Sai surutu kake min kamar ..."
Kunnensu Abbati ya kamo yana cewa "ban hanaka rashin kunya ba?"
Munzali ya karkace kai saboda zafi yana magiya "me yasa baka san wasa bane. Don Allah ka saki kada kayi min kunne daya"
Zungure masa kai Abbati ya yi sannan ya cire rigar ya mika masa.
"Minti talatin zata yi a jikinka ka bani"
Da farinciki Munzali ya karba ya saka suka shiga masallacin domin yin sallar azahar.
Da suka idar hotuna suka dinga dauka domin tarihi. Ba su suka tafi ba sai da suka yi sallar la'asar. Lokacin jacket din ta koma jikin Abbati. Kowa minti talatin din yake ya bawa dan uwansa. Suna ta atishawa. Abbati ya yi ta mita. Munzali yana tunzura shi da cewa don kada ya barshi da jinya ne ma fa yake karbar aron rigar sanyin. Da zasu tafi addu'a kowannensu ya yi. Kusan abu daya suke roko. Cigaba da samun rufin asiri akan abin da ya gabata na rayuwarsu. Samun sana'ar yi sai kuma kowa ya yiwa dan uwansa fatan samun abokiyar zama tagari ba tare da sanin dayan ba.
Ranar da zasu tafi a airport dukkaninsu dokin ganin Qibdiyya suke yi. Sabo da rigima kamar yara harda fadan waye zai fara daukarta.
"Bayan ma yau baka kira mana ita ba" Abbati ya harari Munzali.
Zama suka yi akan kujerunsu daga jikin juna a jirgi sannan Munzali ya ce "na fada maka kashe min murya Zakiyya take yi. Sai ta kusa cinye kudin da surutu. Kai kuma ka wani dage ba za ka dinga kiranta ba sai kace surukarka"
"Ka sani ko ayi kome?"
Seatbelt din da yake kokarin sakawa ya saki ba shiri ya kalli Abbati.
"Kome a ina? Ni nace maka ina son aure ne ko kuwa ina son Zakiyya?"
Abbati ya ce "ko daya. Aure dolenmu ne Munzali. Indai ba so kake iyaye su sake fara zargin ko mun koma ruwa ne. Ba don na san mun rabu kenan dasu Diamond girl dinka ba ai da ita zan ce ka aura. To amma kaga babu wadda ya dace ka zauna da ita kamar Zakiyya. Ita ce ta haifi Qibdiyya. Ita ta san me ya faru da ita. Ita ce kuma zata san hanyar hana maimaici."
"Shawara ce kake bani?"
"Eh"
"Kana ganin akwai alkhairi idan aka daina rabawa Qibdiyya hankali?"
"Tana bukatar tsayayyen gida da uwa da uba."
"To kai yaushe za ka yi auren?"
"Wa yake ta tawa? Da Hanne tana nan da yanzu bakina alaikum. Yanzu kuwa dole in nema can nesa da gida."
Zancen Farha ya so yi masa amma ya fasa saboda baya son yi masa fami.
"To Allah Ya kawo tagari. Amma ka daina zancen Hanne baiwar Allah. Ni na san ko kadan baka sonta. Shi yasa kana samun dama ka sallameta" cewar Munzali yana dariya.
Shi ma Abbatin dariya ya yi yace "Cutar juna muke kawai. Tana jin haushina ina jin nata."
Jirgin na shirin tashi suka kira Dr. Abdallah, Alh. Sadisu wanda yanzu yake yawan kiransu sannan kowa ya kira iyayensa. Munzali kadaran kadahan suka gaisa da babansa. A hakan ma sun sami cigaba ne a alakarsu saboda jajircewar Munzalin.
***
Tafiyar awa biyar da minti hudu ce ta kawosu Nnamdi Azikiwe International Airport Abuja. Suna fitowa daga ciki mota tazo ta daukesu kamar yadda Alh. Sadisu ya ce musu ya bada umarni da suka yi waya.
"Zai kai ku hotel. Gobe zan zo garin ganin party chairman. Sai mu juya jibi tare. Ina fatan hakan ba zai zama takura a gareku ba"
Wannan shi ne abin da ya fada musu a wayar. Cike da girmamawa suka yi masa godiya. Da zasu fita daga motar bayan sun isa hotel din kudi direban ya basu a envelop.
"Yallabai ya ce ku rike kafin ya iso"
Suka sake yin godiya sannan kamar lokacin tasowarsu duk da dare ya yi sai da suka kira iyayensu. Cikin daren suka tattauna yadda zasu yi idan Alhaji Sadisu ya zo musu da wani abu da zai iya bata musu rayuwa. A yanzu sun hankalta suna matukar tsoron shigewa masu kudi. Babu dangin Iya babu na Baba. Watakila wani abin ake nema a garesu.
Washegari sai bayan isha Alh. Sadisu ya iso. Tare suka je suka ci abinci. Dakinsa a hotel din yace su biyo shi. Gabansu ya fadi amma suka daure.
Yana zaune a kan kujera suna kasa a gefensa ya yi musu magana.
"Na san cewa zukatanku suna cike da tambayoyi da fargabar manufar janyoku da nayi a jiki. Dom Allah ku kwantar da hankalinku. Ko babu komai ceton rayuwar Abdul da ku ka yi ya isheni dalilin son saka musu da abin alkhairi. A dalilinku ya sami sauki har ina shirye shiryen tura shi kasa mai tsarki da biyu cikin iyayensa mata. Sai ya yi a kalla shekara guda yana karatun addini zai dawo gabana ya karasa sakandire. "
Murna suka taya shi yaji dadi kuwa
"Magana ta gaskiya labarinku ya tsaya min a zuciya. Ban taba ganin almara irin wannan ba. Giyar kudi bala'i ce. Musamman ga matasa irinku wadanda kuruciya take diba. Yaran yanzu zasu yi komai domin kudi. Sai gaku na hadu daku zahiri ba labari ba. Kun bude min ido da kusanto da tunanin lahira a dukkan lamurana. A takaice rayuwata duka na canjata kuma duka kune sila. Wannan yasa na daukarwa kaina alkawarin ba zan bari ku tagayyara ba. Rashin abin yi da rashin kudi a hannun wanda ya saba rikewa ba karamar jarabawa bace. Tsananin rabo da tsoron Allah ne kadai zai dakushe zukatanku daga tunanin hanyoyin samun kudi ko ta wace siga. Saboda haka idan kuna da ra'ayi ni Alh. Sadisu Nakano nayi muku alkawarin muddin ina raye da rai da lafiya, zan yi iya yina domin ganin kun zama wasu ababen misali da alkhairi a cikin al'ummarmu. Ina burin duniya ta amfana da alkhairin da nake da yakinin Allah Ya wanzar muku sakamakon mika wuya gareShi. Me ku ka ce?"
Basu ce komai ba sai kwalla. Ikon Allah akwai ban tsoro. Duka duka awanni nawa da suka wuce ne suka zauna suna tunanin yadda zasu yi da rayuwarsu yanzu? Sai gashi mafita tazo daga inda basu tsammani.
Alh. Sadisu ya yi murmushi "in dauki shirunku a matsayin amincewa?"
"Alhaji ko za ka bamu zuwa gobe domin mu shawarci iyayenmu"
"Ka cika babba Abbati. Dama gaggawa daga shaidan take. Ku yi shawara da duk wanda ya dace. Fatana Allah Yasa ku bani damar zame muku uwa da ubs a siyasance. Da yardar Allah ni daku babu mai yin nadama."
Dr. Abdallah suka fara kira. Ya ce idan sun shigo Kano gobe su zo su same shi a gida. Da makomar tattaunawarsu da shi zasu yiwa iyayensu bayani. Daga nan su nemi amincewarsu.
Direban da ya daukosu daga airport shi ne ya kuma zuwa daukarsu. Alh. Sadisu ya sanar dasu cewa zasu tsaya a Kaduna zai ga abokinsa kafin su wuce. Haka suka jera suna biye dashi a baya.
***
Suhaib, Farha, Lilu, Sauda da Mardiyya ne suka fito daga wani babban shopping mall wanda yake makwabtaka da ofishin Alh. Tahir. Mami Khadija ya kuma roka akan burinsa na daidaitawa da yaran. Tayi musu magana harma da fada akan lallai su cire abin da yake ransu su kyautatawa mahaifinsu.
"Shi kadai gareku. Ba zai yiwu don ya auri Yumna kowa ya dauki gaba dashi ba. Duk alkhairinsa gareku bai kyautu ku manta ba saboda wani abu guda daya da bai sabawa shari'a ba"
Fadan a gaban kannensu ne. Su manyan sun san me take nufi. Hakuri suka bata tace to tana so bishi office su nuna masa komai ya wuce. Da yake kullum cikin kokarin janyosu jiki yake suna yakicewa sai kowa yaji babu dadi. Shi ne Suhaib ya ce su fara zuwa kowa ya sayi gift guda daya su bashi.
Sauda da Mardiyya sai tsalle da murna. Ji suke kamar sun dade basu ga Abbansu ba. Kowa ya yi kewarsa. Harda Suhaib kuwa.
Abbati da Munzali a hadadden reception din office din suka zauna suna hira. Alh. Sadisu ya shiga wurin Alh. Tahir ba tare da sun san wurinwa ya zo ba. Yana ciki suna tattauna makomar rayuwar yaran. Niyarsu sai sun gama magana sannan Alh. Sadisu zai kirasu ciki domin su sami fahimta da Alh. Tahir. Yana so su dauke shi a matsayin makusancinsu.
Waya suke yi da Qibdiyya ta cikasu da surutu mai bude kofar ya hangameta. Basu dago sun kalli su waye suka shigo ba koda suka ji ma'aikatan dake wucewa suna ta yi musu maraba.
"Oga yana tare da bako." Wani masinja ya fada musu.
"Bari mu jira shi a nan" Suhaib ya nuna kujerun reception din.
Kafin su karasa duka su biyar din sun ga su waye a zaune. Farha ji tayi kamar zazzabi zai kama ta. Kujerar farko ta gabanta ta dafa yayinda Suhaib da Lilu suka karasa gabansu.
Earpiece ne a kunnen Abbati yana kallon video din Qibdiyya
BABI NA ASHIRIN DA BIYAR.
***
48
Zaune yake gaban likita na goma sha uku cikin jerin likitocin da ya ziyarta domin magance matsalarsa. Amsa yake nema don ya san a wane babi zai ajiye lafiyar kwakwalwa da tunaninsa.
Ya gama bayani tsaf akan yadda ya dauki Abbati da zargin da mutane makusantansa suke yi masa kamar yadda ya yiwa sauran likitocin. Ya kare da cewa,
"Bayani nake so a mahanga ta addini. Idan bani da rabon samun rahama ne saboda irin tunanina gara..."
"Subhanallahi" cewar likitan da sauri "Munzali wannan magana taka bata dace da dan musulmi ba. Ni ba malamim addini bane. Amma tabbas har yau ban bar gaban malamai ba. Na kuma godewa Allah da malumanmu na yanzu suka kasance masu ilimin boko wanda yake taimaka musu wurin warware matsalolin da suke tafe da zamani. Idan za ka iya gobe ka zo nan da la'asar. In sha Allah zan kai ka wurin Dr. Abdallah Saraki. Kawu ne kuma siriki a wurin abokina Dr. Huzaifa."
Tun bayan zaman nan da aka yi a gidan Abbati sati biyu da suka wuce, sai yau Munzali ya yi murmushi. Da ya tashi zai tafi likitan nasa ya ce su taho tare da Abbati da iyayensa.
"Hakan ne zai sa kowa ya sami gamsuwa akan amsar da zai baka"
Yana shiga mota ya kira Abbati. A lokacin shi kuma yana cikin ofishin Alh. Sadisu. Kiran na shiga ya dauka da sauri.
"Munzali lafiya dai ko?"
"Lafiya kalau. Kana gida ne?"
"Ina office din Alh. Sadisu ne. Yanzu muka dawo daga duba Abdul"
Munzali yaji kunya ta kama shi. Ba irin lallashi, fada da nasihar da Abbati bai yi masa ba amma kememe ya daina yarda ko zaman minti biyar suyi a wuri daya. Abbati ya yi fushi sosai saboda ya fuskanci akwai abin da yake boye masa. Shi kuma baya son fada saboda a take Abbatin zai soke masa zargin. Gashi zuciyarsa ta riga ta fara rawa akan maganganun iyayensa. Ya zama wajibi ya san me yake ciki.
"Kwatanta min wurin zan zo na same ka"
Minti ashirin ya kaishi. Suka zauna tare da Alh. Sadisu. A yau godiya mai tarin yawa ya sake yi musu sannan ya koma kan batun abubuwan da yaji a police station din.
"Kuna ganin da gaske zaku iya dainawa? Nayi bimcike ance da wahala rabuwa da wannan dabi'ar. Idan Abdul ya tashi a haka ban san yadda zan yi ba"
Munzali bai yi kasa a gwiwa ba ya fada masa shirinsu na zuwa asibiti a Italy. Rashin zuwa a duba lafiyarsu da kuma neman hanyar rabuwa da lalurar har abada ba karamin kalubale bane ga tubansu. Ita wannan dabi'a tana tattare da matsaloli da yawa ga lafiya. Ciki kuwa harda kasa jurewa rashin samun biyan bukata ta inda aka saba. Wannan abu ya kan fi karfin furtawar baki da yakinin zuci. Wani duk dauriyarsa idan abin ya ciwo shi sai ya biya bukatar yake jin dadi.
"Abdul yaro ne. Sake komawarsa ba abu bane mai wahala. Mafi a'ala shi ma ka kai shi asibiti" inji Abbati.
Godiya ya yi musu da zasu tafi da alkawarin tsaya musu a duk lokacin da suke da bukatar taimakonsa.
"Magana nake son muyi Abbati." Munzali ya ce da suka fito waje.
"Dama jikina ya bani tunda ka kira. Ka gaji da yajin ne kazo biko da kanka?"
Da sauri Munzali ya ce "don Allah ka bar amfani da kalmar yaji da biko kamar wasu mata da miji"
Abbati na jin haka ya gano inda matsalar take. Motarsa ya bude suka shiga ya tayar. Gida ya wuce kai tsaye. Yanzu babu kowa daga kuku sai Maigadi. Iya Kande bata dawo ba tun tafiyar Qibdiyya gida.
A waje suka zauna wurin wasu kujeru da 'yar rumfa. Munzali ya fadawa Abbati dukkanin damuwarsa.
"Na san za ka iya cewa ba komai bane. To amma hankalina ba zai taba kwanciya ba. Don Allah gobe ka zo muje wurin malamin."
Kamar uwa da d'a. Tausayin Munzali ya kama Abbati sosai. Don gudun kara masa damuwa sai bai yi masa yadda ya saba ba idan yana cikin yanayi mara dadi. Lokutan da yake yi masa fada ko nasiha da rarrashi har sai ya sauko.
"Allah Ya kaimu goben. Dama nima ina son yi maka magana akan mu nemi fatawa kan dukiyarmu. Goben sai muje masa da komai muji me zai ce."
Munzali ya mike zai shiga ciki. Abbati ya kai hannu zai taba kafadarsa don ya tsaya sai ya fasa.
"Munzali."
Juyowa ya yi fuskarsa duk ta rame kamar ya dade yana ciwo.
"Ina so ka sani cewa ko yaya makomar alakarmu ta kasance gobe ba zan taba barinka ba"
"Ko da ya tabbata wannan kazantar bata barni ba"
"Zama da kazanta fa sai ka so. A matsayin kani kuma amini na daukeka. Banda an riga an dasa maka wani irin tunani a zuciyarka da na fada maka matsayinka a wurina. Yanzu kuwa ina magana za ka iya tsoron kada nace gobe zan kawo sadaki"
Murmushi suka yi a tare sannan kowa ya nufi gidansa.
***
Washegari basu hadu da safe ba. Munzali ya tafi gida dauko su Asabe. Ya sami gidan a cike makil. Larai da su Fati sun zo dukkaninsu kwai da kwarkwata. Gaban Innayo ta zauna ta roki gafararta na rashin kyautawa da tasa 'ya'yanta yi mata. Ta karbi laifinta kamar yadda 'ya'yanta su ma suka karba. Aka yafi juna tare da alkawarin sabunta zumumci.
Hasiya ce kadai bai samu ba. Hakan ya yi masa dadi domin yana jin kunyarta saboda rashin samun sukunin zuwa duba Abbas. Uwani kuwa tana jin muryarsa ta fito ta tare shi a gefe. Mita ta soma yi masa na rashin kiranta da ya ce zai yi domin ta duba Qibdiyya. Hakuri zai bata sai ta kula da ramar da ya yi. Mantawa tayi da fadan ta koma tambayarsa damuwarsa.
"Na manta gidanmu ba irin da bane, da na sani ban zauna abubuwa suna ta damuna ba a cikin kwanakin nan" yace ba tare da wasa a fuskarsa ba.
"Komai mai wucewa ne Munzali. Tunda muka dinke da Innayo kaima kawai ka jira lokaci. Kafin ka farga zaka ga ya koma tarihi. Ko ka bayar dashi ko rike abinka a zuci"
Karfin gwiwa ya samu daga gareta wadda da ita ya yi amfani wajen jajircewa iyayensa suka bi shi.
***
Sheikh Dr. Abdallah Saraki ya saurari jawabin Munzali da Abbati da dukkan nutsuwar da ake bukata daga malami. Labarinsu gabadaya izina ce kuma babban darasi ga iyaye da su kansu 'ya'yan.
(Ni din ba Malamar addini bace. Daliba ce mai koyo har yanzu. Bakin gwargwado ina nazari da bincike kafin na kawo wani batu mai girma cikin labaraina. A nan ma na duba matsayar malamai na kuma hada da tawa fahimtar. Saboda haka idan mai karatu yaci karo da abin da ya sabawa nasa ilimin, kada a manta cewa wannan labari ne. Abin da ya shafi fatawa a nemi sahihancinsa a wajen maluma. Rabbi Yasa mu dace da khairi duniya da lahira. Amin)
Da Alh. Rabi'u ya ga zai fara magana, hankalinsa kacokan ya mika masa. Yana so yaji malamin ya wanke shi daga abin da Munzali ya ce, wato yana da hannu a cikin lalacewar rayuwarsa.
Dr. Abdallah ya fara jawabinsa da sallama tare da addu'ar bude taro ko wani zama da za a tattauna abu mai mahimmanci. Sannan ya karkare da yiwa fiyayyen halitta salati SAW.
"Da farko zan fara da yaba muku tare da kara muku karfin gwiwa. Duk wanda ya nufi Allah SWT da kyakkyawar zuciya, to ya sani cewa Allah ba zai tab'ar dashi ba. Saboda haka ku cigaba akan niyyarku. Ko a duniya ko a lahira sai kun yi mamakin falala da girman Mahaliccinmu. Zai baku fiye da rokonku. Ya yafe fiye da tubanku domin Shi din gagara misali ne wajen jink'ai da tausayi."
Ya gyara zama saboda su san cewa zancena gaba yana da mahimmanci.
"Munzali ina so kai da iyayenka ku sani cewa tsaftatacciyar soyayya ce tsakaninka da Abbati. Irin soyayyar da Allah SWT Yayi alkawarin inuwar Al'arshi rana gobe kiyama ga ma'abotanta. Wato mutum biyu masu kaunar juna domin Allah Shi kadai."
Munzali ya hau murmushi yayinda Abbati ya dinga kiran sunan Allah a iya a lebbensa.
"Malam baka ji inda ya ce yana son Abbati fiye da kowa ba? Ma'ana fa harda mu. Babu jin nauyi ko kadan yake nuna min cewa yaron nan ya fini a wurinsa." Cewar Alh. Rabi'u yana huci.
Dr. Abdallah ya ayyana a ransa cewa lallai Alh. Rabi'u akwai gagarumin gyara a lamarinsa.
"Aikin sab'o sakamako ne na raunin dan Adam. Shi kuma rauni ana gane shi ne daga zuciya. Idan aka haneta ga barin abin da take so sai ta ce ta kasa. Idan aka umarceta da abin da bata so nan ma ta nuna gazawarta. To da zarar mamallakinta ya biyewa ra'ayinta ba tare da dora shi a mizanin hankali, dabi'a da addini ba, dole nadama ta saukar masa watarana. Alh Rabi'u, ka yi godiya muddin rai ga Allah da Ya bawa yaran nan damar fin karfin zukatansu a lokaci irin wannan. Gurbacewar zamanin nan ta kai ta kawo. An kawata zina ana tallatawa mutane. Tserewa tarkonta wallahi sai wanda Allah Ya azurta da jarumar zuciya. Wadda tana so din kuma tana tsoron mummunar makoma. Zuciya ta ma'abota tsoron Allah da kwadayin rahamarSa."
Asabe ta dinga gyada kai tana yiwa Munzali da Abbati kallon tausayi. Alh. Rabi'u kuwa cikin kosawa ya ce,
"Nifa so nake naji inda aka halattawa baligin namiji kaunar kato kamarsa har ma kake ganin cewa hakan ba laifi bane.
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 59 Chapter of 62