wayar amma bai samu ba. Ya taba hannun babu wadda ta bude. Ya dawo da sauri ya tambaye shi ,
"Wacce ce a ciki? Duka a rufe suke."
Maimakon ya bashi amsa sai yaji ya ce "Zina bata yarda taci bashi bata biya ba komai daren dadewa. Naji dadi da kunnuwana suka jiye min kalaman tuba daga gareka wanda yanzu na tabbatar baka fadesu domin ka san ina ciki ba."
Yana gama magana cikin gidan ya koma. Abbati ya sake taba jikin Qibdiyya sau daya bayan ya shiga mota ya zauna sannan ya tayar ya tafi.
***
Wani irin ihu Zakiyya tayi da Abbati ya shigo da Qibdiyya cikin falon Munzali tamkar bata da rai. Ya manta ta zo gidan da bai shigo kai tsaye ba. Munzalin ma hankalinsa ba karamin tashi ya yi ba da yaga hannuwanta suna kadawa su kadai.
"Me ya sameta kuma? Tare da Asaben ka daukosu? Ko ita kadai ta biyoka bayan ka ajiye su Innayo?"
Akan doguwar kujerar da Zakiyya ta tashi ya kwantar da ita.
"Maganin bacci aka shaka mata. Nan da. .."ya dubi agogon hannunsa "minti talatin idan bata tashi bane zamu nemi likita"
"Ka kara sakani a duhu. Me yake faruwa ne?" Cewar Munzali yana tattaba jikin Qibdiyya.
"Zakiyya bamu wuri don Allah"
Gyara zama tayi abinta a kusa da Qibdiyya tare da rike mata hannu.
"Gara ma ka fadi ko ma mene ne don babu inda zani alhali akan 'yata zaka yi magana."
"Zaki tashi ko sai na mugun bata miki rai"
Tsawar Munzali ta tsorata ta amma bai kai yadda zata iya bin umarninsa ba. Zai sake magana Abbati ya ce,
"Zakiyya ki dauketa ku je sama ki yi mata wanka. Nayi miki alkawari zaki ji duk wani abu da ya kamata idan na gama magana dashi."
Ba haka taso ba sai dai kuma a yau din Abbati ya yi mata kwarjinin da bata taba gani a tare dashi ba. Tashi tayi da Qibdiyya a kafadarta sai Munzali ya zo ya karbeta. Dakinsa ya kaisu ya fito ya rufe kofar. Da sauri ya dawo ya zauna a gaban Abbati. Shi kuma sai ya kama hannunsa suka fito waje ya bude mota suka shiga. Tafiyar kimanin minti goma suka yi wadda ta dan nesantasu da gida sannan Abbati ya tsaya.
"Ina so ka saurareni da kyau Munzali."
"Don Allah ka daina ja min rai haka. Wallahi kiris nake jira zuciyata ta buga kawai. Me ya faru?"
Tiryan tiryan Abbati ya shiga labarta masa abin da ya faru a daren jiya da yana kwance a asibiti har zuwa yanzu. Kai ya rike wanda yake azabtar dashi da bala'in ciwo da yaji karfin halin Shazali na daukar musu 'ya. Ga kuma bacin ran son tilasta Abbati ya koma ruwa. Murfin motar ya kama ya ji ta a rufe.
"Bude min Abbati. Ina jin nine ajalin Shazali." Ya furta a fusace idanunsa sun kankance sun kara yin jazur.
"Munzali ka daina magana irin wannan" Abbati ya ce dashi a tausashe.
Kallon takaici Munzali ya bishi da shi yana taune labbansa.
"Wacce iri ya kamata in yi? Fatan alkhairi zan masa ko me? Da ka amince fa? Da shegen ubangidan nasa ya taba Qibdiyya fa? Da me zan ji? Da me zan ji??" Karshen maganar muryarsa karyewa tayi sakamakon hawayen da ya soma bin fuskarsa.
"Idan kana irin wannan abin bana jin zan sami kwarin gwiwar karasa maka labarin nan."
Idanunsa fayau kamar fanko ya dubi Abbati ya ce "ina jin ka. Har akwai wani mummunan labari da zai kara tayar min da hankali makamancin wannan?"
Abbati bai bar komai ba game da haduwarsu da Alh. Tahir da kuma abin da Innayo ta fada masa na Ayaah da Suhaib. Sai ga Munzali ya kasa cewa komai sama da bude baki da rufe shi. Mamaki da kaduwarsa suka ninku dari bisa dari da ya fada masa abin da Innayo ta ce Suhaib ya yi na taimakon Ayaah. Da kuma wayarsa da Farha.
"Tabbas akwai kudurin Allah a cikin haduwarmu da iyalin nan. Ka duba kaga alakarmu da 'ya'yan gidan, da haduwata da babansu wanda ba don shi ba kila da Allah kadai Ya san halin da zamu shiga yau. Sannan ga taimakon tsare mutumcin Ayaah da ...
Yana cikin magana kawai yaga Munzali ya zura hannu ta gabansa ya bude lock. Hakan ya bashi damar bude bangarensa ya fita da sauri ya zagaya ya bude shi.
"Fito in tuka"
"Ina zamu je?"
"Don Allah ka fito. Wannan labarin ya bude min tunanina akan abubuwa da dama"
A zaton Abbati tunanin Munzali ya tafi daidai da nasa akan ganin akwai abin da Allah Ya yi nufi da Ya hadasu da mutanen nan. Bai san cewa a nasa lissafin ya kara gaskata cewa lallai Lilu ne ya bata masa 'ya ba.
***
Anti Hasiya da kanta ta hada kayan Abbas dana Honourable na tafiya asibiti. Ranakun farkon aikin ne zai dinga kwana. Daga nan kuma sai dan mai bin A'i ya cigaba da kwana. Larai ce ta dage bata yarda ya nemo mai kwana da jikanta ba a cikin danginsa. Mutanen da basu iya taimaka musu da hatsi ba a lokacin da komai ya jagule masa. Ita ma Anti Hasiya tayi na'am da shawarar. Ta san yaron ba zai kuskura ya yi wasa da lafiyar dan uwansa ba ko don gudun fadan kakarsa. Sun gama ta kira Innayo ta fada mata karfe nawa duka zasu rankaya asibitin. Ba za su dawo gida ba a cewarta sai an fito dashi.
"Inji waye ya ce ba za ku dawo gida ba? Ke fa na lura ganin kanki kike yi daidai da kowa" Honourable ya ce yana mai daure mata fuska da wasa bayan ta gama wayar. Tuni ta gano korafin nasa bai rasa nasaba da cikinta ba.
"Don Allah kada ka koroni gida wallahi fargaba ba za ta barni ba"
Illolin zaman asibiti da yanzun nan ya tattarasu a kansa saboda rashin son ta wahala ya shiga jero mata. Daga karshe ya hada da rarrashi.
"Hasiya bana son mu yi sakaci da taki lafiyar. Allah bai hana ni 'ya'ya ba kuma nagode Masa akan wannan ni'ima. Hakan bai hana ni kwadayin son ganin irin da zaki haifa min ba."
Murmushi ta bige da yi don ta riga ta san cewa ya gama cin wannan yakin. Da lokacin tafiya asibitin ya yi baki dayansu suka tafi aka rufe gida. Larai ma iyalanta a asibitin suka riskesu.
***
Ba karamin dadi Suhaib yaji ba da zuwan su Mami. Abin da bai saba yi mata ba ma ya dinga yi lokacin, wato raki da shagwaba. Damuwa da kulawar da take nuna masa ne bai gaji da gani ba. Ko yaya ya motsa kafar sai ya ce wash. Ita kuwa jiki na rawa ta dinga ambaton sannu, ko ta ce a koma asibiti. Mayafi ta yafa ta riga kowa mikewa tana cewa gara dai a je ayi x-ray a kafar. Matan gidan dasu Farha suka taru suna yi mata dariya da suka fahimci yana yi ne da gangan.
"Ki yi zamanki Mami tsokanarki kawai yake yi." Cewar Farha bayan kowa ya fita daga dakin an bar uwa da 'ya'yanta.
Kan Suhaib ta shafa cike da kulawa ta ce "idan ma karyar ciwo yake babu ruwanku. In yana so yau har goyo zamu yi."
Lilu da Farha basu san lokacin da suka sake kwashewa da dariya ba. Suhaib kuwa pillow ya dauka ya kare fuskarsa yana cewa,
"Haba Mami a gaban yara ki ke kiramin goyo don su raina ni?"
Daure fuska tayi cikin wasa ta ce "Kai ba a gaban yaran ka ke ta wash-wash ba saboda samun wuri?"
'Yan uwansa ya kalla suna ta dariya ya wulla pillow din saitinsu "Da daya daga cikinsu ne ba za ki ce suna yi don samun wuri ba"
Sai da suka gama zolayarsa ita da Farha da Lilu sannan ta dawo gefen gadon ta zauna. A ranta take kara jin cewa tabbas haihuwa kyautace daga falalar Ubangiji. Duk tarin bacin ran da babansu yake haddasa mata da ta kebe da yaranta sai ta manta da wanzuwarsa. Murmushi ta sakar masa tare da mika masa wayarsa.
"Saki ranka ka kira wadda tayi nasarar canja min kai daga sarkin zafin kai zuwa wannan Suhaib din dake gabana."
"Ummmmm"
Lilu da Farha suka fitar da sautin shakiyanci a tare. Mami babu bata lokaci ta nuna musu kofa tana shan kunu. Ficewa suka yi ana jiyo dariyarsu. Sai da suka rufo kofar sannan ta ce,
"Ayaah ce ko?"
Kallon rashin fahimta Suhaib ya yi mata ya amsa da cewa "tayi me?"
"Ta taba zuciyarka har kake yi min abin da ban taba gani ba tun tasowarka."
Kai ya shiga sosawa irin na marasa gaskiya "nifa babu komai a tsakaninmu"
"Sai ka dage ka gina abu a tsakanin naku kafin wani ya riga ka."
"Kai Mami..." Suhaib ya furta a kunyace yana kawar da kai. Da kafarsa kalau take ma da ficewa zai yi daga dakin a guje.
Zuciyarta tamkar an zuba ruwan sanyi ta dube shi ba tare da alamun wasa ba.
"Suhaib ka cinye kuruciyarka wurin dauke damuwata da kulawa da 'yan uwanka. Shi yasa ba ka san wasa ba balle yadda ake yinsa. You were too serious. Yau gashi Allah Ya amshi addu'ata. Da kan ka kake kirkiro wasa a tsakaninmu ba tare da ka san kana yi ba. Na san ba zai wuce haduwarka da niece din Munzali ba. Kana sonta ko?"
"Mami sa'ar su Sauda ce fa. Yanzu
take shirin gama secondary school"
"And so?"
Kada kai ya yi yana dariya ya ce "wannan hirar tayi min nauyi Mami a canja wata"
"An canja Suhaib. Ai ni yarinyar nan ta gama min komai. Allah dai Ya rabaka da sharrin late-comer. Idan ka tsaya wasa labari zai sha bamban."
"Allah ma Ya kiyaye"
Sai da maganar ta fito ya kama bakinsa. Karo na biyu kenan da ya fadi kalmar nan garera akan Ayaah. Tare suka yi murmushin farinciki. Mami ta sake dubansa, shi ma sai ya nutsu da ya gane magana take son su yi. Wayarta ta mika masa daidai sakon da ta turawa Abbansa. Ya karanta sau daya ya ajiye wayar a sanyaye ya ambaci sunanta
"Mami?"
"Na taba yunkurin neman sakin har sau biyu amma iyaye suka hana ni. Sai dai wannan karon kamar yadda na tura masa text dinnan to in sha Allahu babu gudu babu ja da baya."
"Su Yakumbo zasu amince?"
"Da Allah kadai na dogara. Shi ne Ya haramta zama tsakaninmu. Allah ne shaidata ban taba kusantar kowa a waje ba. Na killace kaina da taimakonSa. Kuma nayi imanin zai taimakeni akan kudirina."
Hannunta kawai ya rike yana jin wani irin nauyi a zuciyarsa. Ba don rabon haihuwarsu ba da wannan baiwar Allah bata zauna ta kwashi bakinciki irin wannan ba.
"Na rasa kalmar da zan yi amfani da ita domin kwantar miki da hankali Mami"
"Kayi mana addu'a ni da ku Allah Yasa hakan alkhairi ne a garemu baki daya. Zaman da ake ta cewa nayi domin ku bai amfana komai ba sai tonon silili. Farha da Lilu na fada maka sun san komai. Da ace na tafi tun kuna yara da har yanzu kuna ganin mutumcin Abbanku. Akwai ciwo a dan da zai san mahaifinsa yana yawo a waje. Har gara mata akan dan cikinka."
Kwalla ce ta zubo mata Suhaib ya soma bata hakuri. Lokacin kuma Farha ta bude kofar saboda ta manta wayarta. Halin da ta riskesu ya daga mata hankali. Da sauri ta shigo tana kukan da ta riga ta gane musabbabinsa.
Wayar Danliti dake gefensa Suhaib ya budo ya mikawa Mami.
"Kinga sakayyar Allah. Ki daina damun kanki. Gara mu tafi kafin muma wata rana dattin ya shafemu."
Da ta karanta irin kazaman chats din Danliti da Jiddo bata san lokacin da ta kankame Suhaib da Farha ba.
"Kada ku kusanci zina. Wallahi a cikinta akwai tozarci da kaskanci. Ko da raina ko babu don Allah kada ku yarda shaidan yaci galaba akanku. Ba zan yafewa duk wanda ya aikata ta ba cikinku."
Suna cikin wannan yanayin Prof. Zuwaira aminiyar Mami Khadija ta kirata. Sai a kira na uku bayan ta saita kanta ta iya daukar wayar.
"Dr. Khadija kun iso?"
"Eh, a nan shadaya tayi mana."
"Kin ganni mun gama shiri zan bar Kanon yanzu ni kuma. Kwatanta min gidan sai na biyo na duba d'ana kafin mu wuce"
Cikin yaran gidan Mami ta samu aka turawa Prof. Zuwaira text na kwatancen gidan. A falo suka hadu da kowa ana taba hira. Suhaib kuwa zamansa ya yi a daki ya dauki wayarsa yana jujjuyawa. Muryar Ayaah yake son ji tana tsiwar nan. Har zai kira ya tuna ta ce babansu ya karbe mata waya. Komai tsaya masa ya yi da tunaninta. Anya zai iya barin Kano bai ganta ba?
Waya Mami ta cigaba da yi da Prof. Zuwaira inda take kara yi mata kwatance saboda sun kasa gane layin. Ta nemi Lilu domin ya fita hanya bata gan shi ba. Sauran yaran cikin gidan duka mata ne.
"Gidan shi ne mai bakin gate a close din. Bari na fito waje kila ku hango ni"
Tashi tayi ana cewa ta bari a tura wata cikin yan matan ta ce babu komai. Da wayar a kunnenta ta taho bakin gate din suna waya da Prof. Zuwaira. Zuwan Lilu ne ya taimaka wurin saukaka musu. Location dinsu ya turawa Prof. Zuwaira ta whatsapp din Mami. Ba jimawa kuwa sai ga kiranta ta ce layi daban suka shiga amma yanzu zasu juyo. Tare suka tsaya jiran isowarsu a bakin gate ta ciki yana ta tsokanarta wai zamani ya canja waye yake zaman cewa a bi hagu a karkata dama.
***
Saboda mugun gudun da Munzali yake saura kadan ya wuce gidan Kawunsu Suhaib sannan ya farga. Da sauri ya taka wani wawan burki sai da taya tayi kara sannan shi da Abbati suka yo gaba kamar an hankado su. Cikin fushi kuwa Abbati ya hau shi da fada.
"Lafiyarka kuwa Munzali? Wane irin tukin ganganci ne kake yi?"
"Kira Farha ka ce mata ta turo Lilu ya zo ya shiga damu."
Abbati ya kalle shi a tsanake ya adana bacin ransa domin son fahimtar inda matsalar take.
"Me yake faruwa? Don zamu zo duba Suhaib sai mu fito a haka? Jallabiya ce fa a jikinka. Kalli yadda Shazali ya yi min da riga." Ya nuna masa kayansa da suka dukunkune kamar sun fito daga rami.
Ficewa Munzali ya yi daga motar idanunsa a rufe da bacin rai ya nufi gate din gidan ko kallonsa bai yi ba. Yana fita Abbati ma ya fito. Yana ganin ya daga hannu har ya buga gate din sau daya yayi saurin riko masa hannuwa.
"Munzali meye haka wai?"
"Sake ni Abbati. Ka sakeni in kamo dan iskan yaron nan..."
Gaban Mami Khadija yankewa yayi ya fadi ta damki hannun Lilu a tsorace.
"Muryoyin nan ba na Munzali da Abbati bane?"
Kafin ya iya cewa komai Abbati ya sake yin magana. Ransa a bace yake matuka don duka kafadun Munzali ya riko ya juyo dashi suka fuskanci juna. Zuciya ta tunzura shi ya daga murya yana fada.
"Wane yaro? Sai tambayarka me yake faruwa nake ka ki kayi magana. Me muke yi a kofar gidan nan?"
"Lilu zan kashe."
"Me???" Abbati ya sake shi babu shiri yana yi masa kallon mara hankali.
"Yadda bai iya tausayawa Qibdiyya ba nima..."
Da sauri Abbati ya dora hannunsa ya toshe bakin Munzali sannan ya ce,
"Shi ne? Qibdiyya ce ta fada maka?"
Munzali ya gyada kai hawaye yana zubo masa.
Mamaki ya kama Abbati ya ce "A yaushe? Duka duka sau nawa suka taba haduwa? Kaga zo mu koma gida..."
Zuciya da bata da kashi. A take ta Munzali ta shiga kuncin ganin kokonto a fuskar Abbati. Bai san lokacin da ya fuzge hannunsa daga gareshi ba ya ja baya.
"Nufinka karya nake yi?"
Sassauta murya Abbati ya sake yi saboda ko kadan baya so wani yaji sirrinsu. Da lallashi ya ce,
"Ba haka nake nufi ba Munzali. Wannan maganar tana da girma. Ka zo mu tafi mu fara yin shawara a gida."
Zuciyar Munzali ta kara zuwa wuya. Wace irin shawara kuma zasu yi a gida bayan gasu a kofar gidan da zasu sami Lilu? A tunaninsa jin sunan wanda ya bata Qibdiyya sai ya batawa Abbati rai fiye dashi. Me Abbati yake nufi da nuna sanya akan lalurar 'yarsu? Sai yanzu ma ya tuna cewa tun zuwan Abbati jiya ko sau daya bai tambaye shi waye ya keta mata haddi ba. Wani hawayen ne ya zubo daga idanunsa da suka rine kamar garwashi ya yiwa Abbati kallon takaici. Kallo irin wanda bai taba tsammanin zai gifta tsakaninsu ba.
"Sanin waye ubansu da kayi a yau dinnan bai isheka hujjar yarda da maganata ba? Ko soyayyar da kake yiwa Farha ce tasa kake kokarin kare kaninta ko kuwa don baka san zafin haihu.."
Tsayuwar gaggawa ce ta kama numfashin Abbati da bugawar zuciyarsa. Jikinsa ya hau bari saboda tsananin bacin ran sanin abin da Munzali yake shirin fada. Gumi ne kawai yake zubo masa kamar ruwa ga wani uban sanyi da yake ratsa kasusuwansa. Bai barshi ya karasa maganar ba ya dakatar dashi cikin zafin rai.
"KAR KA SOMA WALLAHI! Kada ka kuskura kayi min gorin haihuwar Qibdiyya don bacin ran da zamu shiga sai ya ninka wanda muke ciki a yanzu"
Munzali kasa motsawa ya yi ko kadan sai idanu da ya kafe Abbati dasu.
Shi kuwa Abbati jikinsa sai karkarwa yake kamar wanda zazzabi ya yiwa mummunan kamu. Bai haifa ba ya sani. Qibdiyya ba jininsa bace wannan ma ya sani. Fargabar da ya shiga ba komai ya janyota ba sai tsoron kada wannan masifar ta zama silar watsewar alakarsu da dan uwansa don ya wuce amini. Zai iya daukar komai banda gorin haihuwarta. Domin da zarar ya fito daga bakin mahaifinta kai tsaye zuwa gare shi, ya tabbata babu sauran zama a tsakaninsu. Munzali ba zai taba yi masa furuci irin wannan a halin rashin sani. Idan ya yi to tabbas daga zuciyarsa ne. Cikin sanyin gwiwa ya juya ya fara nufar motar.
"Ina za ka?"
Munzali ya fada da wata irin murya tamkar ba tasa ba. Yawun bakinsa ma daci yake yi masa saboda masifar halin da yake ciki.
"Ka same ni a gida idan ka aiwatar da abin da zuciyarka ta raya maka."
Yana rufe baki wani adaidaita sahu ya tsaya a gabansa wanda Munzali bai kula da lokacin da ya daga masa hannu domin ya karaso ba. A guje kuwa ya bi bayansa yana kwala kiran Abbati. Da suka ki tsayawa ya durkushe a wajen ya dauki hannu ya dinga dukan goshinsa da cikin tafin. Idan bai yi a hankali ba yana jin yana daf da zarewa. Banda haka me ya kai shi furta wandannan kalamai ga Abbati?
*
Gudun jinin Mami Khadija ya ninku, bugun zuciyarta ya zarce ka'ida. Tashin hankalin da ta shiga ya zarce tunani balle a fade shi. Duk wata kalma da ta fito daga bakin Abbati da Munzali ta sami damar shiga kunnuwansu ita da Lilu. Ma'anar zantukan nasu ya fita dalla-dalla basa bukatar karin bayani.
Daga gabar da suka fahimci inda maganganun suka dosa Lilu ya saki wayarsa a fusace ya nufi gate din. Kunnuwansa sun kurmance, haka nan idanunsa sun makance. Abu daya kawai yake hangowa shi ne hannuwansa a wuyan Munzali a yayinda zai tuhume shi dalilinsa na yi masa sharri.
"Me kake shirin yi? Ina za ka?" Mami ta tambaye shi a firgice lokaci guda ta riko hannun shi domin hana shi bude gate. Sa'arsu daya maigadin ya zaga bayan gidan zai cirowa matar gidan zogale.
Muryarsa tamkar ba tashi ba saboda tashin hankali ya dube ta da mamakin tambayar da tayi masa.
"Baki ji me ya ce ba? Ki barni in je..."
"Kada ka fita" ta furta tana girgiza masa kai.
Shi ma kan ya girgiza kuma sai lokacin hawaye ya sauko masa ya ce "idan ki ka hana ni fita zuciyata za ta iya bugawa Mami. Wallahi baki san yadda nake ji ba. Zan iya mutuwa...Mami ni ba Abbanmu bane. Ba zan taba yarda ko da wasa wani ya jefeni da irin abin da ya dade yana sanyaki kuka akan Abba ba. Kina ji fa akan sanin halinsa aka dogara da cewa ni nayi."
Daga nan bai kuma sauraronta ba ya fita da sauri. Cikin sa'a yana fita ya sami Munzali ya shiga mota kenan har ya tayar. Ba tare da bata lokaci ba kuwa ya zagaya daya barin ya bude.
Kallo daya Munzali wanda idanunsa suka yi masa nauyi saboda tsabar zubar hawayen da suke ya yi masa ya kashe motar. Mamakin karfin halinsa ya ma hana shi cewa komai. Sai Lilu ne da kansa ya ce,
"Ka kaini gidanka. Ka kaini gaban Qibdiyya in ji yadda aka yi na yi mata fyade."
"Kada ka sake ambaton sunanta. Kuma ka fice min daga mota don ban san me zan maka ba."
Wata irin dariya Lilu ya yi yace "kaga nayi kama da matsoraci ne?"
Domin samun damar wanke kansa a gaban Abbati ya fizgi motar a guje. Tashin motar ya faru akan idon Farha, Mami Khadija da Suhaib wanda ya fito yana jan kafa. Sai Prof Zuwaira da suka iso lokacin. Jama'ar gidan da suka biyosu bayan shigar Mami tana kiran Farha duka sun shiga tashin hankali. Da ta bawa Farhan mukullin mota akan su bi bayansu sai da matar kawun nasu ta ce ga direba ko ma mene ne gara wani ya kai su.
"Kiyi hakuri Anti. Idan Allah Yasa wutar ta mutu da kaina zan baki labari. Ki ara min yau ta zama sirrin gidana don Allah." Ta juya ta bawa Prof. Zuwaira hakuri da alkawarin zasu yi magana a waya in Allah Ya yarda.
Dole kowa ya hakura. Suna kallo Mami ta taimakawa Suhaib suka shiga baya, Farha taja mota da gudu. Kafin ta karasa kan titi ta kira Abbati bisa umarnin Mami. Da yake shima suna tsaye a junction ba a basu hannu ba shi yasa yaji kiran. Ganin sunan Farha ya bashi tsoro ko Munzali ya yi wani abu. Yana amsawa yaji muryar Mami.
"Kwatanta min gidanku"
"Lafiya kuwa Mami?" Ya ce a razane.
" Munzali ya tafi da Lilu."
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Kuna ina yanzu? Bari na juyo. Ko dan gari ne zai kawo ku?"
"Mu kadai ne"
Inda suke kawai ya bukaci sani ya ce su jira shi a nan. Tsayuwar minti goma sha biyar suka yi domin ya hadu da goslow a hanyar dawowa. Kafin isowarsa ne Mami ta sami damar sanar dasu Suhaib abin da suka ji ita da Lilu. Hankulansu duk a tashe har Abbati ya iso. Yana zuwa bangaren direba ya nufa ya bude kofar. Farha tayi masa wani irin kallo wanda ko kusa bai bata masa rai ba.
"Ki bashi wuri ya tuka" taji muryar Mami a kunnuwanta.
Ba don ta so ba ta fita ta koma daya barin. Abbati ya dinga tukin 'yan Kano saboda tsoron abin da zai iya faruwa a gidan kafin su isa.
BABI NA SHIRIN DA ƊAYA.
***
Fitar su Munzali ba jimawa su Mal. Inuwa suka iso. Maigadi ya bisu har bangaren Abbati yana yi musu maraba bayan ya rufe gate din. Bai gane Mal. Inuwa da Mal. Sa'idu ba. Amma Habu ba bakonsa bane tunda yana yawan zuwa gidan. Sannan ya hadu da Baaba Mari sau biyu. A wurinsa suka ji cewa Abbati da Munzali basa gida amma Hanne tana nan. Da murnarsa ya dinga kwada sallama a kofar gidan tare da bubbuga dan hannun kwankwasa kofa da yake daga wajen.
Hanne tana tsakar cin abinci taji bugu. Tsaki ta jejjera sun kai goma sannan ta mike ta ajiye plate din da ta gama shakarewa da abinci.
"Waye ne?" Ta ce bayan sautin wani tsakin nata ya karade kunnuwan su Baaba Mari.
A gajiye suke su duka musamman ita da Mal. Sa'idu saboda yanayi na rashin lafiya.
"Iyayenki ne" Mal. Sa'idu ya furta da fada.
Faduwar da gabanta ya yi a lokacin ba na wasa bane. A iya saninta idan ka cire tafiyarsu Hajji bata taba ganin kawun nasu a Kano ba. Mantawa tayi da hannu ta fara cin abinci ta damki hannun kofar ta bude. Da d'ai-d'ai ta bisu da ido har suka shiga suka zazzauna. Habu ne kawai bai biyo su ciki ba ya tsaya suna sake gaisawa da maigadin. Hanne ta rufo kofar ta durkusa ta gaishesu. Babu yabo babu fallasa suka amsa. Na iyaye mazan bai dameta ba sai na Baaba Mari. Tunda suke bata taba ganin ta canja mata fuska daga faram-faram ba. Shi yasa taji gabanta ya soma faduwa ta fara tunane tunane barkatai.
Gauron numfashi da Mal. Sa'idu ya sauke da kyar na ciwon jiki ne yasa ta mayar da hankali gareshi a k'agauce.
"Ina yayan naki"
"Ya fita"
Mal. Inuwa ya ce
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 51 Chapter of 62