da yake ciki.
"Nasima bata fada maka abin da ya faru ba?" Ta ce tana shigewa daki ta kwantar da da ita akan gado. Ganinsa tayi a yamutse ba yadda ta barshi ba ta dawo falo tana labarta masa abin da ya faru. Tashi ya yi zai koma duba Farhan yana jin babu dadi da tsautsayin da ya sameta ya bashi kofar cin amanar mahaifiyarta. Zai daga labule Nasima ta fito tare dasu Suhaib. Khadija ta tashi ta kama kunnuwansu ta murde kowannensu ya saki kara.
"Ban hanaku tsalle akan gado ba? Kuna ganin tsautsayin da ya sami Farha baku tsoron ku fado."
Sai da gaban Tahir ya fadi ya kasa karasawa ciki. Yana jin Lilu ya fara rantsuwar basu bane ya juyo ya musu abin da bai taba ba. Marinsu ya yi duk su biyun saboda tsoron kada ta yarda dasu ta fara zargin wani abu.
"Ba zan yarda da rashin kunya ba. Maminku tana magana kuna karyata ta. Idan ba ku ba waye zai hau gadon ya yi mata tsalle? Na sake ji ko gani sai na zaneku. Ku wuce ku bani wuri."
Da kuka suka bar falon. Khadija tayi mamakin daukar zafinsa haka. Ta dade tana rokonsa ya dinga taimaka mata akan kwabar yaran idan sun yi laifi ya ki har ta hakura. Da ta biye masa da yanzu sun gama sangarcewa. Yau da laifin ba mai girma bane a idonta sai gashi ya yi musu marin da ko ita aka yiwa sai ta rike kumatu. Ba dai ta ce komai ba ta bar wurin. Da Nasima za ta tafi ta tambayeta me yasa bata fada masa inda taje ba.
"Naji kin ce Farha amma ban ji sauran maganar ba Anti. Wani abin ne ya faru?" Ta tambayeta tana rarraba idanu.
"Baki sani ba fa ki ka ce?"
"Anti ko dai nayi laifine? Kiyi hakuri."
Khadija bata ce komai ba. Sai yanzu ta tuna Nasima tana wurin abin ya faru amma bata juyo ba.
"Allah Ya kyauta" kawai ta iya cewa saboda rashin sanin matakin dauka ta bar zancen.
A haduwar Nasima da Tahir ta gaba ce tayi masa kukan da ya karyar masa da zuciya.
"Na san za ka yi mamakin ganin ni ba budurwa bace. Ba zan maka karya ba da kaina na sayar da mutumcina. Talauci da yunwa sunyi mana yawa. Babu mai son taimakonmu. Da mutane suka gane cewa zan iya komai domin ciyar da mahaifiyata da kanne shi ne maza suka fara nemana. Na san cewa kaima kana cikinsu amma ba yadda zanyi saboda albashina ba zai ishemu ba."
Daga ranar ya bude mata bakin aljihu sai yadda tayi. So yake ya nuna mata yafi sauran mazan. Kudi kam bata da matsalarsu. Tahir kuma ita take juya akalarsa. Khadija sun maida ta hoto suna badakalarsu a gidan bata sani ba. Kiyayyar da yake nunawa Nasima ta zame mata katangar hana hango komai a tsakaninsu. To gashi yanzu anyi aure!
***
"Mari kin ji labarin ana neman masu casa a gidan Sarkin Noma?"
Audugar da Mari take kadawa ta ajiye ta kalli kawarta Tasalla da murmushin da yafi kama da dariya.
"Ki bari don Annabi."
"Yasin da gaske nake. Wannan karon ina tsammanin mata sai sun cika tsakar gidan saboda alherin da ya yi bara."
Tsam Mari ta tashi ta shiga daki ta dauko mayafi. Tasalla tana ta tsokanarta wai ladan aikinta wannan karon harda amaryarta zasu ci.
"Ko Malam in fada miki sai dai kallo. Yaran nan zan rabewa in je in dubosu." Kwalla ce ta taho mata ta goge da habar mayafinta "Har mafarkin Sani nake Tasalla. Ya yi kankanta sosai da bara. Ga Abbati kin dai san halinsa. Duk inda ya shiga raina shi ake yi. Ba zan taba yafewa Mal Sa'adu ba."
Da sauri Tasalla ta dora hannu a bakinta "bari fada kar a ji. Wan mijinki ne fa."
"Wan miji ai ba uban miji bane. Don baki ji yadda nake nadamar haihuwar mazan ba. Da mata ne wa ya isa ya tura su almajiranci?"
"Kul Mari. Ba'a yiwa Allah tawaye akan haihuwa." Cewar Tasalla.
"Astangafirullah" Mari ta ce da sauri tare da yin tofi a gefe na neman barranta daga zunubin kalamanta.
Sun yi sa'ar samun gurbi cikin mata goman da ake nema suyi aikin casar shinkafa da masara a gidan Sarkin Noma. Mari kason mutum biyu take karba ta wuni tana aiki. Banda wannan ta cigaba da dinkinta duk da kuwa ba wani mai tsada bane ga bashi a wurin mutanen kauye. Haka take musu dinkin ta shafawa idanunta toka sai an biyata kudinta. Tuni tayi suna kuwa. Ana cewa bata da lamuni wurin kudi amma ta iya dinki. Duk abin da ta samu sayayya take yiwa Abbati da Sani. Yaran dake gabanta ba komai take basu ba saboda ganin suna gaban mahaifinsu.
Bayan sati uku ta nemi izinin Inuwa za ta je Zaria da Kano ganin 'ya'yanta. Shi kuma ya sanar da Mal Sa'adu. Nan da nan zance ya zagaye gidan aka yi ta aibata ta. Sauran matan babu wadda ta taba zuwa ganin nata. Idan lokacin komawarsu gida ya yi ana basu hutu su tafi su taimakawa iyayensu musamman da damina.
"Wai ke Mari kanki aka fara haihuwa ko naki kadai aka kai almajiranci? Wannan rashin ta ido har ina?" Mai bin Mal Sa'adu ya ce da ita yana muzurai.
Inna Mairo ce ta kawo mata dauki wannan karon.
"Bana son bakin hali. Kun dauke yaran yanzu meye aibunta don ta ce zata ganinsu? Na rantse da za'a jarabceku da laulayin kwana daya kafin ma ayi batun nakuda bana jin da mai yarda dansa ya matsa ko nan da zaure. Ba ita ba ma duk mai so a barta taje ta ga nata."
Ashe sauran ma suna so baki da zuciyar yi Mari ta fisu. Faccalolinta da suke da yara a wasu garuruwan kowacce sai ta fara shiri. Ba lokaci daya zasu je ba saboda kada a bar gidan babu mata. Kaya niki-niki haka Mari ta hadawa su Abbati. Don karfin hali harda shinkafa, kwan zabi da garin kunu. Da ta tashi kuma ta yiwa iyalan malamansu tasu tsarabar.
Zabinta hudu ta tafi dasu suka fara wucewa Zaria ita da dan rakiyarta dan wajen kanwarsu Inuwa. Duhun dare ya kawo kai suka isa unguwar da makarantar take. A cikin layin sun yi arba da almajirai sun fi goma. Yawancinsu duk daga bara suka dawo da abincinsu. Can gabansu suke hango kura tana tashi ga ihun yara da alama dambe ake yi.
Yayin da dan rakiyarta ya yi tsaki ita ido ta zuba tana tausayin yaran da karancin gata ya sa rayuwarsu walagigi irin haka.
Yaro daya ne a kasa guda uku na tumurmusarsa. Baka jin komai sai kukansa gami da tsinuwa da zagin da yake aika musu. Sauri Mari ta kara da niyar ta isa ta rabasu sai ga wani gardi (babba cikin almajiran) da dorina. Yana zuwa ya shiga sambada musu kan mai uwa da wabi. Ji kake taf-taf ga ihun yaran suna sosa inda bulalar ta sauka. Na kwancen da ya kasa tashi ya fi tafka. Ya kuma daga hannu zai zuba masa Mari ta gane ko waye. Babu wanda zai ce ga lokacin da ta motsa kafa sai ganinta suka yi ta duka ta rufe Sani. Bulalar a gadon bayanta ta sauka ta gantsare kwalla mai zafi tana taruwa a idonta.
"Baaba?" Sani ya ce da mamakin da ya gauraya da murna.
Da ka ta amsa shi saboda radadin dukan nan. Ya kuwa kankameta yana kukan dadi. Almajiran da suke wurin suka ruga ana rige rigen fadawa Malam abin da ya faru.
Ita dai Mari daga Sani tayi tana karkade masa jiki. Farinwata ya haska mata shi da kyau taga yadda ya rame kamar ba shi ba. Ya sake kankancewa sai kai shirim kamar ya kumbura. Lebensa sama da kasa a kumbure sannan karshen lebban ta kowane bari ga alamun ciwo. Wurin duk ya tsattsage. Su kauyawa ne amma ba kazamai ba. Zuciyarta tana kunci ta dauke shi yana ta warin rashin wanka. Nan kuma taji abu ya karci hannunta. Ta shafa kafarsa da kyau taji wani mummunan faso da ya mamaye 'yar kafar. Bata ma san ina za ta nufa ba a lokacin sai ga malamin makarantar tasu ya taho yana baza babbar riga.
"Baiwar Allah daga ina? Ance kin yi rabon fada tsakanin dalibai na." Kula ya yi da Sani da ta dauka ya rungume wuyanta da 'yan hannayensa ya daka masa tsawa "to tambadadde daga ganin mata ka makale mata. Ai sai ka sauko tunda ba uwar da ta sallamoka daga kauye bace." Ya mayar da hankalinsa ga Mari yana dan murmushi "haka muke fama fa. Iyaye mata kamar basu san zafin haihuwa ba. Yara da kananun shekaru a kawo a jibge mana. Ba kuma wani kudin azo a gani suke biya ba. Shi wannan ma dai mai idon mayun sam bai kwanta min ba. Kar ki raina kuruciyarsa hatsabibin gaske ne."
Ta so ace wadannan kalaman a kunnen Mal Sa'adu ake fadarsu ya ji da kyau ba ita ba. 'Ya'yan da suke haifa cikin gumi da jini ke irin wannan rayuwar kuma laifinsu ake gani. Zuciyarta ke bugawa da karfi tana son bashi amsa amma tana hango laifin nasu da ya fada.
"Don Allah zamu sami masauki zuwa wayewar gari." Mari ta katse surutun da yake ta yi da wannan tambaya.
Kallonta ya yi sama da kasa tare da dan rakiyarta ya girgiza kai. Haka kawai a wannan zamani da ake fama da 'yan yankan kai bai ga dalilin saukar bakuwar da bai sani ba.
"Sai dai nasa a raka ki gidan Mai Unguwa."
"Nagode, ina kayan Sani suke mu dauka?"
"Baiwar Allah wai daga ina kike ne?" Ganin karfin halinta ya yi na son satar dan mutane a gabansa.
"Mahaifiyar Sani ce daga Kirikasamma. In Allah Ya so ka bar ganin mai idanun mayu kamar yadda ka kira shi daga yau."
Kunya mai tsanani ce ta rufe Malamin. Gidansa ya tafi dasu yasa iyalinsa suyi musu abinci. Da aka kawo ko hannu bata saka ba sai da ta kula Sani yana ta kallo ta janyo kwanon. A baki ta bashi ya ci ya koshi. Ta fita wanke hannu kafin ta dawo bacci ya dauke shi. Shafa shi ta dinga yi tana hawaye. Wai wannan ne Saninta. Yaro mai kiba da kuzari duk ya lalace.
Kayan Sani duka sunyi datti ga wari. Wando da riga ta samu tun asuba ta roki sabulu ta wanke masa. Da yake ana zafi sosai kafin su tashi tafiya sun bushe. Da kanta tayi masa wanka ta dirje masa jiki. Suna shan koko taji ana cewa yaran da suka yi masa duka jiya biyu cikinsu sun kwana suna zawo. Ana tsammanin abincin da suke fadan a kai lalatacce ne.
"Sani ka ci abincin?" Ta tambaye shi hankali a tashe.
"Loma daya nayi suka kwace."
'Kemis zan fara zuwa na saya masa ja da yalo kafin muje tasha' ta ayyana a zuci. Da zasu tafi bata fasa ba ta ajiye musu tsarabar da ta kawo. Neman magani ta dinga yi ido rufe amma bata sami kemis ba sai a tashar ta sayi maganin zawo a wurin wani mai tallan magunguna. Irinsu kemis guda ne a kansu suna sayar da kusan kowane irin magani na bukatar yau da gobe. Ita ba ilimin abin ba haka zalika mai maganin ma sayarwa kawai yake yi. Haka ya hado mata magunguna kala biyar wai duka na zawo da ciwon ciki. Filagil kadai ta gane sai magnesium na ruwa da ake girgizawa kafin a sha. Sauran kuwa kafinol ne hade da boscopon da panadol extra. Burinta kada wani abu ya sami danta saboda haka kai tsaye ta bashi na ruwan.
Hakura tayi da zuwa ganin Abbati zata koma gida har sai Sani ya dan murmure. A hanya ya soma ciwon ciki yana ta amai. Daga baya sai zawo duk ya fita hayyacinsa. Shi yake ciwon amma Mari ke kuka. Sauran fasinjoji kuma suka dinga hantararsu saboda wari ya ishesu. Babu wanda ya san lalurar da ta kawosu wannan matsayi aka dinga cin mutumcin 'yan kauye a gaban idonsu.
Kafin su isa Kirikasamma Sani ya fara sankamewa idanunsa a waje gwanin ban tausayi. Mari tayi kuka har muryarta ta dashe wurin yi masa sannu.
"Baaba cikina zai tsinke ki kara min magani."
Sam ta manta da magungunan da ta saya ai kuwa ta roki ruwa a wurin wata da ta kulla a farar leda. Ta ballo bibbiyu kowanne kamar yadda mai maganin ya ce mata ta bashi.
Cikin zakuwa take tambayarsa "Ka fara jin sauki?"
"Eh" ya amsa idanunsa suna kakkafewa.
A zaton Mari bacci ne. Rungume shi tayi tana dan jijjiga shi har rai yayi halinsa bata sani ba. Ashe rabon su gana ne ya kaita Zaria. Da zasu fita daga motar wata ta ce mata jikinsa kamar ya saki.
Da murmushi ta ce "bacci ya samu."
Goya shi tayi ta dauko wasu kayayyakin. Sauran kuma dan rakiyarta ya dauka suka dauki hanyar gida a kafa. Lokaci lokaci take gyara goyon ta yi masa sannu. Rashin amsawarsa a wurinta saboda bacci ne.
Sun kusa isa gida ta hango Inuwa a majalisarsu ta karkashin bishiyar darbejiya. Mamakin dawowarta a yau yayi tunda kwana uku ta ce za ta yi. Silifas dinsa ya zura ya taso da sauri da ya fahimci goyo tayi.
"Ba dai Sani kika dauko ba Mari? Me kike so na cewa Malam?"
"Maganar ba ta hanya bace ka bari muje gida. Bashi da lafiya ba zan iya barin shi a can ba."
Dan murmushi ya yi sanin cewa ita ma akwai taurin kai. Yana son yin yadda take so amma ba zai iya sabawa yayansa ba.
"To kwanto min shi na dauke shi naga kema a gajiye kike."
Ba musu ta kwance goyon Inuwa ya tare zai saba shi a kafada yaji yanayin jikin wani iri. Mutum biyu cikin abokansa suka taso jin ba'asi ganin ana kwance goyo.
"Sani ne jikin ba dadi ta taho dashi gida." Inuwa ya fada musu.
"To kawo shi mana ka tayata da sauran kayan."
Mijin Tasalla ne Lukumanu ya karbe shi sai ya dago shi da sauri jin ya tafi baki daya. Hannunsa na rawa ya ce,
"Sani. Sani bude ido..."
Mari sai ta tsaya tana son cewa bacci yake taga duk sun rufa a kansa ana jijjiga shi. Inuwa da karfi yake kiransa jikinsa yana tsuma.
"Sai dai hakuri Inuwa amma Sani ya amsa kira."
Kalaman Lukumanu kenan da suka shiga kunnuwan Mari. Duniyar tsayawa tayi cak bata iya tuna komai sai ranar da ta haife shi. Ranar da taji ciwon nakudar da ya zarce na Abbati. Lokutan da ta dinga sake-saken burikanta akan kyakkyawar rayuwar da take masa fata kamar yadda ta yiwa Abbati. Fuskar Saninta wanda yake ta kuka ba zai je almajiranci ba take gani. Yaron da jiya jiyan nan ta ganshi ana turmususa a cikin kasa akan lomar abinci.
A kwana na biyu da rasuwar ta dan dawo hayyacinta. Kuka take yi ta rungume ledar magungunan da ta bashi. Muryarsa ke yi mata amsa amo tana jin lokacin da yake rokonta ta kara masa magani. A yayin da wasu zafafan hawaye ke kwarara a idanun Mari sai ta bawa Inuwa tausayi. Shi ma din zuciyarsa ta dinga raya masa lallai su dawo da Abbati gida.
Wani abin ban tausayi ga wannan mata bai wuce har ita ma ta koma ga Allah SWT ba za ta taba sanin ainihin sanadin ajalin danta ba. Komai a rayuwa yana da sila. Hakkin ran Sani yana rataye a wuyan jama'a da dama. Babban cikinsu Mal Sa'adu mai ingiza kai yara almajiranci. Ga Inuwa da ya kasa jajircewa wurin kare amanar da Allah Ya bashi ta 'ya'ya daga dan uwansa. A gefe guda ga Malamin tsangayarsu da bai rike amanar da aka bashi ba ta yaran mutane. Matar da yayi bara a gidanta ta bashi lalataccen abinci saboda rashin sanin girman hakkin bil adama. Yaran da karancin tarbiya da kulawa ya janyo suka yi masa duka akan abincin da ya samo. Mai sayar da maganin da bashi da iliminsu ga mutane saboda neman kudi. Gwamnatin da ta yarje masa yawo a tituna da kwararo yana sayarwa bayan bashi da lasisin bada magani. Kaico! Hatta Mari da ta bawa Sani magungunan nan bisa rashin sani da tsantsar soyayya irin ta uwa da ďa bata tsira ba. A takaice dai the society killed Sani!
***
Kalmar hutu kanta tana da dadin fada a baki balle kuma idan jiki zai same shi a aikace. A wurin Innayo kuwa daga mai arziki sai wanda bai san ciwon kansa ba kamar Asabe ke hutawa. 'Yan mata biyar a gabanta babu mai basu sai abin da Allah Ya hore mata daga kasuwancinta. Biki ko suna da wuya yake hanata dora tukunya. Abin da ya kama dole taje to lallai wata cikin 'yan matan za ta zauna a gida. Yau kuwa dole ta saka ta zaman gida tana hutun dole.
Ranar ta kama litinin. Ta tashi da ciwon kirjin da ya kan damketa lokaci zuwa lokaci. Yaran nata kuma duka suna makaranta. Zara da bata kaunar karatu sai gayu ta so zaman jinya amma Innayo ta kora ta. Hudu suna zango na uku a makaranta. Jarabawa ake yi ta canjin aji ba za ta so a sanadiyarta wata ta maimaita ba. Babbar kuwa shekararta ta farko kenan a School of Nursing. Ayyukan da basu zama dole ba Innayo ta dauke mata a gidan saboda kawai ta sami isasshen lokacin karatu.
Tsakar gidan nasu tsit sai ita kadai a daki. Alh Rabi'u yana kasuwa. Asabe kuma makota ta shiga saboda an kusa sauke sanwar rana. A can za ta ciko cikinta su kuma yaran ta dafa musu gurjiya kowa ya ci ya sha ruwa babu ruwanta.
Zumbur Innayo ta tashi da ta tuna ta sa a jika mata gero tun dare amma ciwo ya hana ta wanke a kai nika. Idan ta barshi zai lalace gashi har kwano uku. Tashi tayi da kyar tana dafa bango ko ruwan ne ta samu ta canja. Bandaki ta fara zagawa domin rage mara taji taku da 'yan maganganu anayi. Gida na jama'a bata wani damu ba ta kammala ta fito. Babu kowa har yanzu a tsakar gidan ta zauna tana wankin geronta.
Kwana biyu da suka wuce Munzali ya yi wata magana da dan kanwar Asabe da yazo musu hutu. Shi satin da ya gabata suka gama tasu jarabawar. Yaron mai suna Halliru ya girme shi da kusan shekara biyu.
"Idan ka yarda muka yi aradu yau abincinka da nama" ya ce saboda ya fahimci amfani da kayan kwadayi yana taimakawa wurin samun biyan bukata.
Halliru ya kai masa duka a kafada yana dariya"ashe kai gara ne ban sani ba" karkada hannu ya yi tare da jijjiga kai yana yi masa kallon rainin wayo "to bari kaji in fada maka da mata ake yi ba maza ba. Na taba gani a lungun gidan Mai kalanzir din unguwarmu."
Dan jim Munzali ya yi yana nazari daidai kwakwalwarsa kafin ya ce "kai ka taba yi da macen ne?"
A kunne Halliru ya rada masa cewa suna yi da kanwarsa idan babu kowa a gida. Ya kara da yi masa bayanin yadda suke jindadi. Shi ma 'yar makota ce da ta girme shi ta koya masa shi kuma ya koyawa kanwar. Da 'yan shekarunsu ya kwadaitawa Munzali son gwadawa.
Shi ne fa ya bawa 'yar makotansu inda Asabe ta shiga kwadayi kafi-kaza ya taho da ita gida lokacin da Innayo ta zaga.
Tare suka je gidan da Asabe ta kore shi da mugun kallo "shegen yaro kwalamamme. Ka biyoni salon taga munyi mata yawa taki zuba min abincin. Banda abinka idan ta bani ba zan rago muku ba?"
Cike da tsiwa ya ce "za dai ki rago musu. Yaushe rabona da cin abincin makiyalla."
Baki ta sake maganar ta shigeta ta daga hannu za ta kai masa mari "kut! Nice ma nake makiyalla?"
Juyawa ya yi zai tafi idonsa caraf akan 'yar gidan da bata fi shekara shida ba. Da sauri ya dago ledar kafi-kazan yana kiranta. Kafin ta iso sai da Asabe ta karba ta barbada a tafin hannunta ta lashe.
"Munzali kenan. Kai dai ba dai mutane masu insani ba. Kwanakin nan har wani kumatu ka dire." Ta kai hannu ta yi masa dukan wasa "ni ko saura ne ka dinga rago min a leda mana. Sai bakin hali irin na ubansa."
Shigewa tayi shi kuma Munzali ya sami damar hillatar yarinyar suka tafi gida. Ya zata gidan ba kowa. Dakin Asabe ya shiga da ita inda babu kowa ya ce ta zo ya koya mata wani abu.
Da kananun shekarunsa shaidanci ya shige shi har ya sami amincewarta ta cire kaya yadda ya umarceta. Karatun Halliru ya soma aiwatarwa akan yarinyar da bata san me ake yi ba.
"Kar ki fadawa kowa kinji. Zan dinga baki tsamiyar biri da kafi-kaza."
"Harda tsamiya gaye?" Ta tambaye shi da murmushi.
"Duk abin da kike so zan dinga baki indai baki fada ba."
A can gidansu kuwa Asabe tana ta sharbar faten tsakin da babarta ta bata.
Innayo tana wankin gero taji kamar ana magana kasa-kasa. Gajiya tayi da sharewa ta tashi ta nufi dakin. Duk a zatonta abokan Munzali ne. Satin da ya wuce Asabe ta tafi yawonta aka zo aka dauke mata kudin dashi. Tayi ta rantsuwa wai cikin 'ya'yan Innayo ne. Shi ne ta tashi ta leka don kada a sake sakata biyan kudin da ta san karya ake musu.
Tana daga labule tayi mummunan gamo. Da sauri ta afka dakin ta cakumi wuyan Munzali ta kifa masa wani gigitaccen mari. Tana dukansa amma jikinta ke rawa kuma ita ke fitar da hawaye. Idanunsa kyamas abin sa ya ja wandonsa ya mayar. Yarinyar kuwa ko a jikinta. Kafi-kaza ne tayi dumu-dumu dashi tana ta lasa.
Ta baya Innayo taji an riko mata wuya tana juyowa Asabe ta dauketa da mari ita ma.
"Kashe min dan zaki yi?" Ta kwance dankwali taci dammara "muguwa, makira. Ba tun yau na san magadan Alhaji sun tsole miki ido ba. Wato niyarki ki karshi a daka babu kowa ki fice."
Yau daya Innayo ba ta kishi take ba. Tausayin Asabe ma take ji saboda wannan halayya idan Munzali ya tashi da ita ba karamar masifa bace.
"Ai dai kya tambayeni me ya yi kafin ki fara sababi. Ganinsa fa nayi akan wannan yarinyar daga shi har ita ba wando...."
Wani irin bugu Asabe ta yiwa kasa da hannu ta tafa hannuwan tana hargagi "ahayyeeeee....anyi walkiya na ganki Innayo. Yau dai rigar munafunci ta sauka an miki tsirara a idona. Wato kiyayyar taki da 'ya'yana har ta kai kiyi musu irin wannan sharri mai muni."
"Asabe. Asabe ki ajiye maganar kishi ki duba tarbiyar 'ya'yanki. Meye ribata idan nayi masa sharri."
Juyo dashi Asabe tayi duk da fargabar dake zuciyarta amma sam ba za ta yarda Innayo tayi mata dariya ba.
"Kai Munzali wai da gaske ne?"
Sai da ya kumburo baki ya ce "Biyoni tayi fa shi ne ta ce in kaita bayi tayi fitsari. Kawai ina cire mata wandon ta hau dukana."
Ajiyar zuciya Asabe ta sauke ta kalli Innayo "to kin dai ji. Haka kawai za ki kulla masa sharri. Yo Allah na tuba yaron nan nawa ma yake? Me ya sani? Ko an fada miki kowa ma irin wadancan shirgin ne da ki ka tara a daka suna yawon ta zubar?"
Lokacin ya yi! Tana kai karshen maganar Innayo ta rama marin dazu. Ba lafiya gareta ba amma tuni ta manta da ciwon. Zagi ba irin wanda Asabe bata yi mata ba ta ja gefe tana kallonta. Damben da take so ta biye mata suyi ne ba za tayi ba. Munzali salin alin ya ja hannun yarinyar ya kai ta kofar gidansu ya kara gaba.
Dare ya raba Asabe ta kasa baccin kirki. Tashi tayi ta koma rumfarta ta taba Munzali.
"Ka tabbata dazu Innayo karya tayi maka?"
Sai da ya murza ido saboda bacci sannan ya ce "Halliru ne ya ce wai da mata yafi dadi."
A baya ta daka masa duka a razane "bude ido don ubanka. Kayi da gaske?"
Lokacin ya wartsake ya girgiza kai "ni ban yi mata komai ba."
Jinjina kai tayi ta ce ya kwanta. Ta san karya yake. Har kasan zuciyarta ta yarda da Innayo da subutar bakinsa ta dazu. Sai dai kuma ko ana muzuru ana shaho ba za ta taba yarda ace laifinsa bane. Wannan magana anyi an gamata daga yau
HUƊU ƘAFAFUN TEBUR.
***
Kwana goma cif da tarewar Nasima a gidan Tahir. Amarci suke irin wanda iyayen gida ke tsoron ayi musu kishiya su ga irinsa. Kullum sabon
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 62