ko da na aure su sai dai idan biyayya zan yi. A zahirin gaskiya ba wata macen da na ji ta kwanta Mani a rai."
Dam dam haka ƙirjin Uncle Adam da Mom yake bugawa, sakamakon jin zancen da Asad ɗin ke faɗa.
"Ki yi haƙuri Mom wallahi biyayyar uwa ce kawai za ta ni zuwa wajen yarinyar da kika zaɓa mani, ga Uncle shi ma ya bijiro da zancen auren ƴarsa. Kin ga idan na bi ra'ayin ki na zaɓi yarinyar da kika zaɓa mani zai ji ba dad'i ganin ga ƴar uwata ƴarsa na ƙi ta. Kamar yadda idan na zaɓi ƴarsa na san ke ma za ki ji ba dad'i ne ki ce n watsa maki ƙasa a idanu. So ku yi hakuri Please."
Ya karasa maganar yana haɗe hannayensa alamar roƙo.
Dad ya kalle shi ya ce.
"Ba zai yiwu ba dole ka zaɓi ɗaya daga cikinsu."
Ɗan jim ya yi kafin ya ce.
"To Dad ka bani lokaci kadan zan yi nazari kafin na zaɓi daya daga cikinsu."
Mom ta yi saurin cewa
"Ka je ka ga waccen saboda ka san ta don yaran kawun naka ba ɓoyayyu ba ne."
Jinjina kai ya yi sannan ya fice daga falon. Sulaiman bodyguard ɗin sa ya tarar a ƙofar yana jiransa.
Gaba yayin da s shik kuka take masa bayan fitarsa ne Uncle Adam kalli Mom ya ce.
'Yar bakin ciki hankalin ki ya kwanta burinki ya cika , hankali ki ya kwanta wato bai auri ɗaya daga ɗaya daga cikin ƴaƴana ba. To bari na fada maki kamar yadda bai sure ki ba Hakazalika ba zai auri kowace yarinya da kika kawo ba idan kuma kika matsa to mutuwar kasko zamu yi, dan Wallahi sai dai kowa ya rasa."
Yana gama fadar haka ya fita fuu yana cika kar ɗanwaken da zai yi juyin farko a wuta.
Dad kam gabaɗaya sun daure masa kai, yadda kowa ke nuna cewa sai ta hanyarsa Ajmal zai samu mata .
Jidderh ce ta yi sallama ta shigo cikin falon, cikin girmamawa ta durkusa ta gaida Dad, ya amsa cikin sakin fuskar tare da tambayar ta mutanen gidan, ta amsa da Alhamdulillah.
Nan ta gaida Mom ta amsa mata ba walwala, har ta mike ta nufi kitchen dai ta ji Mom ta ce
" Jidder?"
"Na'am gani nan zuwa."
Ta fadada tana dawowa in ga Mom take.
"Mom ga ni."
"Ki fara shga cikin ɗakina ki ɗauko Maganin da zan sha."
"To Hajiya."
Ta fada tana tashi daga Wajen.
_Asadullahi_
Yana zaune. Bayan motar yana kallon Togo da jama'ar sai dai hmhanafaya hankalinsa na wani wajen can daban, don a zahiri ba titin yake kallo ba ya lula can duniyar tunani.
Al'amarin Uncle Adam da Mom.
Fitowa ya yi daga cikin motar, ƙamshin tutarensa kawai ya tabbatar wa ma'aikatan kamfanin ya ya iso.
Wunin ranar da na dai Asadullah ya yji shi gabaɗaya ya kada gane meke damuwa.
Da wuri ranar ya dawo gida .
Ƙofar Sualaima ne ya yi saurib fitowa daga motar ya zo ya buɗewa Asadullah . Yana fitowa ya nufi cikin gida.
Ba kowa a falon ƙasa, don haka kai tsaye ya nufi upstairs. Direct ɗakinsa. Bayan ya shiga ne ya ji kamar motsi.
Yana juyowa kafin ya samu damar ganin ko waye ya ji an fesa masa abu a fuska. Daga ranar bai sake gane komai ba, sai dai ya farka ya ga ne a in da yake. Sai dai an ɗaure shi da sarƙa.
*Cigaban labari*
_Hilal_
Shaƙo Idanunta ya yi ta fara zaro idsnu tana kakari.
"Waye ya maki ciki?"
Daidai lokacin ne Dr ya shigo yana ganin abunda an Hilal ke ƙoƙarin aikatawa. Da ƙurar ya kwace Zahra daga hannunsa.
Take ta zube a wajen tana ta faman tari.
"Za ki fara fadi ko sai na illata rayuwar ki?"
Ita dai sam ta kasa gane me yake nufi da wai tun yaushe ta fara harka, sannan kuma wani ciki yake magana akai, sam ta kasa gane manufarsa.
Doctor ne ya yi magana yana cewa
Ka duba halin halin da take ciki mana, ka bari ta huta abi komai a sannu."
Tashi ta yi ta zauna bakin gadon tana mayar da numfashi.
Babu abinda Hilal ke aika mata da shi sai mugun kallo, bakin ciki ne a a cikin zuciyarsa.
Zuwa ya yi ya samu Dr akan ya basu sallama. Tsoronsa da Doctor ya ji ne ya saka ya basu sallama.
Yana shiga ɗakin ya tsuke fuska .
"Tashi mu tafi kafin na ɓalla ki a wajen nan."
Haka ta dinga rawar jiki tana ɗaukar dankwalinta da takalmi ta saka.
A tare suka fice kowa zuciyarsa ba dad'i. Wajen parking motocin da aka tanada a asibitin suka nufa. Mazaunin direba ya shiga yayin da ya shiga ta zauna a gefensa.
"Wa ya yi maki ciki? Kuma yaushe kika fara mu'amalar banza da maza?"
Hawayen da take riƙrwa ne suka samu nasarar zubowa daga idanunta.
Ita tun da take a rayuwarta babu wani ɗa namiji da ya taɓa rike ko da hannunta ballantana suka kai ga mu'amalar banza da shi. Amma wai yake mata zancen ciki har da ma tambaya wai yaushe ta fara
Tsawar da ya daka mata ne ya saka ta sakin wani marayan kuka.
Bai ce mata komai ba, ta cigaba da kukan nata, kasancewar baya son hayaniya da kuka ya saka shi yin parking a gefen hanya.
Kallon gefen fuskanta ya yi ya ga shatin yatsunsa biyar a fuskarta sakamakon marin da ya yi mata a asibitin. Tsawa ya daka mata tare da cewa
"Za ki rufe Mani baki ne ko dai na sauya maki kamanni a wajen nan, wallahi idan ba ki kiyaye ni ba sai na ɓallaki a wajen nan."
Tana jin haka ta san muguntarsa don haka ta haɗiye kukan da take yi. Sai dai zuciyar ta mata zugi bisa kalamansa gare ta na cewa yaushe ta fara mu'amala da maza."
A haka suka ƙarasa gidan ran kowa a jagule, bayan ya yi parking a parking space ne ta kai hannu dan buɗe murfin motar, amma sai ta ji ta a gam alamar ya yi lucking ɗin motar ta juyo ta lalle shi da niyyar yi masa magana ya bude mata sai ta kasa sakamakon zuba mata Mayun idanunsa da ya yi masu masu matukar kwarjini da ya yi. Sai ta sunkuyar da kanta tana Wasa da yatsun hannunta da suka sha jan lalle. Tsabar kwarjinin da ya yi mata ne ta kasa yi masa magana .
"Tambaya ta ƙarshe zan yi maki kada ki ce mani baki sani ba. Waye ya yi maki ciki.?"
Tura baki ta yi tare da cewa
"Wai kai kana ta Mani maganar ciki ya za'ayi ma ace wai ina fa ci..."
Kafin ta kai aya ta ji saukar yatsunsa biyar a gefen fuskarta wanda sai da ta ji wani shuu a kunnen nata, ga wani duhu da take ganin ya gifta, jin ta da ganin ta sau da suka ɗauke na wucen gadi, ba ta gama farfaɗo wa da azabtar marin da ya yi mata ba ta ji ya kai mata duka a baki, nan ma wani azaba ta ji wanda ya saka ta sakin ƙarar azabtar da ta sha har ta rintse Idanunta.
Wani gishiri ta ji a cikin bakin nata, alamar jini ne bakinta ya fashe.
"Get out in my car ƴar iska mai fuska biyu. Zan yi maganin ki ne."
Tana buɗe kofar ta ji ya buɗu. Hakan ya saka ta fita a guje tana kuka.
Lumshe idanu ya yi ransa na masa zafi. A hankali ya fito daga cikin motar cikin sanyin jiki kamar an jefi kaza da gishiri.
Ba kowa a main falo, kai tsaye ta nufi part ɗin na su. Tana zuwa ta ga gabaɗaya suna falon. Abbi Ummi, Yaa Mahmud da Yaa Sadik.
Cikin tashin hankali suke tambayar ta daga ina take suna ta kiran wayar ba ta shiga, sannan kuma wannan fuskar da ta kumbura da ga baki ya fashe.
Ƙasa ba su amsa ta yi sai faɗa wa jikin Ummi ta yi tana sakin kuka mai cike da raɗaɗin zuciya da ƙunci.
"Abbi me y saka ƴan uwanka suka tsane mu, me ka saka ba sa ƙaunar su ga nuna farin ciki da walwala. Dangin Ummi kawai suke ƙaunarmu ba sa son ganin kukan mu, amma danginka ba sa son su ga nuna farin ciki."
Ummi ce ta ce .
"Ya na ga fuskar ki a kumbura ga baki shi ma ya kumbura ya fashe, daga ina kika mun dawo ba ku nan ga wayarki a gida. Ballantana a kira .
"Mom kin san lokacin period ɗina ne yanzu ko?"
"Eh na sani me ya faru?"
"Daga cikinsu da marata na ciwo na kwanta kin san wani lokacin ina zubar da jini sosai daga gani shi ne su Sunyi Laila da Mummy suka ce wai ciki ne da Ni na zubar..'
Dukkansu salati duka hau yi.
"Kada ki damu Allah yana tare da ke."
Cewar Abbi yana mata kallon tausaya wa.
"Me ya saka naga kamar kin sha duka ga fuska ta kumbura ga baki ya fashe?"
"Yaa Hilal ne ya mare ni ya kuma duke ni a baki wai sai na fada masa wanda ya Mani ciki ."
A fusace Yaa Sadik ya mike don zuwa ya samu Hilal.
Yaa Mahmud ne ya rike shi tare da cewa.
"Ka kiyaye Yaa Hilal domin ba Mansur ba ne ko Faisal da ka saba faɗa da su. Wannan Hilal ne karo da shi ba za ka ci riba ba, kai ma ka san waye shi ba sai na baka labari ba."
Dawowa ya yi don shi ma ya san ba zai iya ja da shi ba.
" A gaskiya wannan rayuwar cikin waɗan nan mutanen ba dad'i, gara mu bar masu gidan gabaɗaya mu koma wani wajen.,"
Sadik ta yi maganar cikin ɓacn rai, Ummi ne ya ce.
Sai dai ku yi hakuri domin kuwa domin Kakanku haka ya tsara cewa ba wanda zai bar gidan nan."
Hannun Zahrah Ummu ta kama suka shiga ciki n ɗakinta ganin yadda bakin ma ya kumbura. Wanka ta saka ga yi da ruwan ɗumi sannan ta fito ta sauya kaya ta sanya pad a jikin panta ta shafa miski a ƙasan wajen ta shirya cikin doguwar riga.
Tea Ummi ta haɗa mata sannan ta ɗauko mata magani ta kawo mata.
Amsa ta yi ta kafa kai bayan ta yi bisimillah ta sha, maganin ma ta sha sannan ta kwanta.
_Hilal_
Yana shigo wa kai tsaye ya nufi upstairs. Jin Muryar Mummy ya yi tana cewa.
"Yanzu da ka kai ta asibitin ka yarda ciki ne da ita ba sharri aka yi mata ba ko? Wai ina ruwanka ne ma da ka kai ta asibiti?"
Na yi abinda zan yi wa kowa ne ko da a hanya na ga mutum haka zan taimaka masa ba wai don ita na yi ba ."
"To Meye na ka na shiga damuwa ?'
Daniwata ita ce yadda za ta zubar da kimar ahalinmu ta ɓata mana sunan family yadda aka san wannan family ya ji suna idan mutane suka ji daya daya cikin familyn ga abinda take aikatawa ai ta ɓata mana suna don. Sai ya shafi kowa da ke cikin gidan nan. Bayan haka Meye damuwata ita ta ne can ga ƙararta."
Ya ji maganar yana haurawa upstair.
*Kuyi hakuri na ji na shiru ina da uzuri ne don ba na ma gari na yi tafiya ne. Am very busy almost all the time*
*Maman ihsan ce*✍️
09065357995
[11/2, 7:57 PM] My Uwar Ɗaki: Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan ce)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
Page3️⃣3️⃣
"Damuwa ta ita ce yadda za ta zubar da kimar ahalinmu ta ɓata mana sunan family yadda aka san wannan family ya yi suna, idan mutane suka ji daya daga cikin familyn ga abinda take aikatawa ai ta ɓata masa suna don ya shafi kowa dake cikin nan. Bayan haka ta je can ta ƙarara."
Ya yi maganar yana haurawa upstair .
Ummi na fitowa daga cikin ɗakin Fatima Zahrah bayan ya ba ta magani ta yi barci ne sai ta nufi ɗakin Abbi.
Zaune ta same shi akan gadonsa da alama tuninin yake yi.
"Hannunsa ta rike a cikin nasa wanda hakan ya saka ya juyo ya kalle ta yana mata murmushin yaƙe .
"Ya jikin Zahra?"
"Ta yi barci."
",Allah ya sauwake."
"Abban Mahmud."
Juyowa ya yi ya kalle ta da alama yadda ta kira sunan maganar na da mahimmanci.
"Yanzu haka za mu cigaba da rayuwa a cikin wannan gidan. Na gaji. Kusan shekaru talatin muna abu ɗaya. Na sha yi maka maganar mu tashi mu bar wannan gidan, ka ce Papa ya hana bayan ƙiyayyar da ake yi maka ya shafi matarka da ƴaƴanka, idan muka yi wasa sai ya shafi jikokinnu. To ba zan bari hakan ya faru ba, akan me za su saka mu a gaba. Musamman Fatima Zahrah tsanar da suke yi mata ya fi na kowa yawa a cikin gidan nan. Zan je na samu Papa idan har kai ba za ka bar gidan nan ba to ni zan bar gidan nan ni da yarana."
Tana shirin tashi ta ji ya rike hannunta.
"Kin ga don Allah ki sake hakuri in sha Allah wata rana komai zai dawo daidai. "
Mumrmushin takaici ta yi tare da cewa.
"Haƙuri na nawa kuma ai tun da ba yi haƙirin kusan shekaru talatin to wani hakuri ya rage kuma?"
Da kike maganar tashi a cikin gidan nan kin san cewa ba na da in da yafi nan ko? Saboda nan gidan ubana ne kuma ya mallaka Mani wannan ɓangaren halak malak, ba wanda ya isa ya tashe ni a nan, kamar yadda suma suke takama gidan ubansu ne to haka ni ma, kamar yadda ya mallaka masu ɓangarorin da suke zaune haka ni ma ya mallaka mani na wa. Kuma sanin kanki ne cewa ya haramtawa ƴaƴansa barin gidan nan dole kowa ya zauna a cikinsa. So kike na saɓa umarnin mahaifina ne?"
Tun da ya fara magana ba ta katse shi ba sai da ya kai aya ta ce .
"Ba so nake ka tsallake umarnin mahaifin ka ba, ka zauna amma gaskiya ni da ƴaƴana abun ya ishe mu haka. Sun saka mu gaba musamman Zahra kullum cikin matsalarsu take. Har ya kai ga an yi mata ƙazafin ciki. Ba'a bar ta hakan ba sai da aka haɗa mata da suka akan laifin da ba ta aikata ba. Wallahi, summa tallahi ba zan bar maganar nan ba sai na sanar da Papa wannan zancen idan bai ɗauki mataki ba ni na san matakin da zan ɗauka akan hakan."
Tana gama fadar haka ta nufi kofar fita duk yadda Abbi ke kiranta ba ta saurare shi ba ta fice abun ta, don ranta ya gama ɓaci akan zancen."
_Asadullah_
Yana zaune a wata kujerar roba dake ɗakin da aka ajiye shi . Har lokacin hannunsa da ƙafarsa ɗaure suke da wani sarƙa. Sai dai wannan karon da alama yana cikin hayyacinsa.
Wani mutum ne ya turo ƙofar ya shigo cikin ɗakin, sannan ya mayar da ƙofar ya rufe. Yana sanye da ƙananan kaya, sai dai ba za'a iya shaida kakanninsa ba, sakamakon ya sanya P. Cap 🧢 a kansa sannan ya sanya face mask 😷 a fuskarsa ga bakin gilashi a idanunsa.
A hankali ya ƙara so gaban Asadullah ya janyo wata kujera ya zauna suna fuskantar juna.
"Asad ya kake?"
Kallo ɗaya Asad ya masa ya kauda kansa gefe .
Dariya mai sauti mutumin ya yi sannan ya ce.
Bari na baka wani labarin abun da ba ka sani ba, ko kuka na yi maka fashin baki akan a abinda ya shige maka duhu."
Ajiyar zuciya ya sauke yana cewa na san ba za ka mance ranar 27 ga watan Oktoba ba na shekarar na shekarar dubu biya da sha huɗu. Ranar da ka kawo abokinka cikin mansion ɗin nan."
A hankali Asadullah ya fara tuno abinda ya faru a wancan ranar.
Tafiya suke yi cikin motocinsu yayin da motoci biyar ne suka suke a jere sai dai ta tsakiyar tafi kyau da tsaruwa. Don da alama ita ce wacce uban gidan na su ke ciki. Biyun da ke gabansa da biyun dake bayansa .
Sanye take cikin Suit fara ta cikinsa ma fara sai bakin necktie da ya ɗaura a wuyansa . Takaliminsa ma baki sai sheƙi suke yi agogon hannunsa ya duba tare da kan gajeren tsuki. Daidai lokacin ya kalli gefensa idanunsa ya sauks akan abokinsa Sagir wanda suka yi secondry school tare.
Alamar tsayar da motar ya yi wa Direba. Take duka motocin suka tsaya, ya yi wa ɗaya daga cikin guard ɗin alamar ya kira masa wancan mutumin.
Take kuwa suka dawo tare ya yi masa alama da ya shigo cikin motar, kasancewar a ƙasa yake tafiya. Sam bai gane Asad ba.
Guard ɗin ya ce masa
"ka shiga daga ciki."
"Na shiga ina a wannan zamanin na rashin tsaro na san ina za ku kai ni?"
Mumrmushi Asad ya yi tare da cewa.
"Sagir Ibrahim Sahabi."
Wato idanu ya yi tare da cewa
"Asadullah Ahmad Abubakar?"
Jinjina masa kai ya yi tare da sake wani murmushi.
Da sauri ya shiga ya zauna gefensa yana dariya.
Suka cigaba da tafiya.
"Sagir ya na ganka haka?"
"Ai dole ka ganni haka domin mahaifiyata da mahaifina sun rasu, ga bashin da ake bin mahaifina da aka biya jama'a bashi har da na banki haka ban tsira da komai ba, hatta gidan da nake ciki sai da aka siyar da shi yanzu haka ɗakin wani abokina nake kwana shi da ƙaninsa yanzu haka a takure nake a cikin ɗakin.
Jinjina kai Asad ya yi tare da yi masa addu'ar Allah ya ya jikin iyayen nashi. Ya amsa da Amin.
"Ya zancen aiki fa ana zuwa aiki ne?"
"Har yanzu ban samu aiki ba ka san yanayin ƙasar aiki sai mai hanya."
"Kada ka damu lokacin samun aikinka ya yi, yanzu ka koma can in da kake ka ɗebo duk wani abun da ka san kana bukata ka zo zan baka wajan zama da aikin yi."
Zaro ido Sagir ya yi tare da cewa.
"Da gaske kake yi abokina?"
Jinjina masa kai kawai ya yi alamar gamsarwa. Tasanar murna da farin ciki bai san lokacin da ya rungume Asadullah ba.
Kai tsaye suka nufi *ASADULLAH GLOBAL RESOURCES*
sai a lokacin Sagir ya lalle shi ya ce.
"Dama kai ne kake da ASADULLAH GLOBAL RESOURCES da kuma ASADULLAH INVESTMENT NIGERIA LIMITED? kai ne me wannan hamshaƙin ɗan kasuwa da ake faɗa?"
Murmushi ya sakar masa ba tare da ya ce komai ba. Kallon Sulaiman amintaccen bodyguard ɗinsa da ke gefen direba ya yi ya sanar da shi cewa ya sa ɗaya daga cikin direbobin su ya kai Sagir gidan da zai je ya kwaso kayansa.
Haka kuwa aka yi Direban ya kai shi ya kwaso kayansa ya yi wa masu ɗakin sallama ya shiga mota suka bar layin
Asadullahi na zuwa kamfanin bai wani jima ba ya bar komai a hannun ƙaninsa Kamal, yayin da ya koma gida tare da muƙarrabansa.
Wani part ya bawa Sagir a cikin Asadullah mansion ya zauna a ciki.
Sannan ya kira Jidderh ya saka y don ta gyara part ɗin. Bayan haka ya masa alƙawarin bashi aiki a kamfanin bayan ya karbi takardunsa.
Haka kuwa aka yi washegari Asad ya ba shi gurbin aiki a kamfaninsa. Ya yi matukar farin ciki da wannan aiki. Wajen ɗaya suke da Kamal don shi ne mataimakin Kamal ɗin.
Bayan wata ɗaya da faruwar haka sai kuɗaɗen suka dinga ɓacewa a cikin kamfanin. Dan miliyoyin kuɗaɗen ne ake sacewa.
Lokacin da abun ya ishe shi bayan ya gano cewa ta hanyar Kamal da Sagir kudaden ke fita, don haka ya kira Abokin nasa Sagir da ƙanin nasa Kamal ya yi ya nuna ɓacin ransa akan abun da suke yi na almundahana da ku kudaden kamfani. Sannan ya yi masu maganar cewa idan albashi da ake biyansu ya masu kadan ne ko suna bukatar kudi su tambaye shi mana, zai iya kara masu ko ya basu. A lokacin sun bashi hakuri ne, sannan a wannan watannin kuɗaɗen suka ƙara ɓata kimanin Naira Miliyan Hamsin. A lokacin bai masu magana ba ya ƙale su bayan kwana biyu aka sake sanar da shi cewa miliyan ɗari aka rasa kuma an tabbatar ta hannunsu kai dai ne kudaden kamfani za su iya fita. Daga nan ya dakatar da su daga aiki har sai ya gama bincike.
A binciken da ya yi ne ya gano ba iya kudaden da suka ɓata ba kenan, ransa ya ɓaci ƙarshe ya ce su rubuta takardar barin aiki su kawo masa.
Kallomsu ɗaya bayan ɗaya ya yi tare da cewa.
"Ƙanina da abokina sune suka yi Mani wannan aiki. Da ace wasu ne suka yi Mani ba zan yi mamaki ba, amma a ce ku makusanta na da na yarda da ku ne kuke Mani wannan ta'asar."
Kallon Kamal ya yi da cewa.
"Ina za ka kai waɗan nan kuɗaɗen haka, me za k yi da su, idan kana bukatar abu ka tambaye ni ba zan iya yi maka ba ne? Kana jinina ne ka yi mani wannan abun me ya saka ba za ka tambaye ni ba."
Sunkuyar da kai ƙasa ya yi tare da cewa.
"Yaya dan Allah ka yi haƙuri."
Hakuri kam ya ƙare don dole za ku bar aiki a nan don ba zan sake yarda da ku ba, kun ci amanata yayin da na ɗauki yarda ba baku. Na baku damar canzawa ba ku canza ba yanzu kam bakin alkalami ya riga ya bushe."
Zufa ce ta karyo masu suka fita jiki ba ƙwari.
*Bayan awanni uku*
Yana zaune a office ɗin sa ya sanya system a gaba yana duba wasu bayanai.
Wayarsa ce ta yi ruri yana dubawa ya ga Sagir ne yake kiransa. Ya ɗaga take ya mike a firgice. Katse kiran wayar ya yi tare da fice wa a guje ko ta kan wayarsa bai yi ba ya fice.
Yana fita ya samu Sagir a tsaye, cikin tashin hankali yake cewa .
"Ina Ƙanina yake?!"
"Mu je abokina, wallahi ƙaninka yana cikin mawuyacin hali."
Ya faɗa yana bude masa murfin motarsa wanda Asad ya siya masa lokacin da ya bashi aiki."
Shigewa ya yi bodyguard ɗin sa na kokarin yin magana Sagir ya ce.
"Ku jira mu yanzu za mu dawo "
Ya faɗa sannan ya figi motar a guje ya bar kamfanin. Slaiman ne ya bawa sauran bodyguard ɗin umarnin su bi bayansu.
Take suka shiga motocinsu suka bi bayansu. Sai dai cikin rashin sa'a suka kasa gane in da motar Sagir ta bi.
Don haka sai suka bi haryar da ta sha bamban da wanda suka bi.
Gudu Sagir yake yi kamar zai tashi sama. Asadullah na tambayarsa wani asibiti Kamal yake ya ce masa bayan gari. Da mamaki yake kallonsa tare da tambayarsa.
"Kamar ya bayan gari ba asibiti ne sai bayan gari?"
"Abokina yanzu ba lokacin tambaya ba ne mu je kawai ka gan shi."
Asadullah bai sake cewa komai ba fatansa Allah ya kai su ya ga ɗan uwansa.
Sai da suka kai wajen da ba kowa sun sauka akan hanya tun daga nesa ya hangi Kamal a kwance. Suna karasawa ko parking din kirki bai bari Sagir ya yi ba ya fita ya nufa in da Kamal ke kwance. Ya
"Ƙanina lafiya me ya same ka?"
Kamal da idanunsa ke rufe ne ya buɗe idanunsa tare da watsawa Asad wani banzan kallo.
"Meke damunka tashi mu je asibi..."
Kafin ya ƙarasa magana Kamal ya fito da wuƙa daga ƙasansa ya soka wa Asadullah a ciki."
Tsabar azabar da ya ji ne ya saka ya saki wani sautin azaba, bai gama dawowa daga duniyar azabar da ya ji ba ne ya ji an sake suka mashi wukar ta bayansa.
Ya juyo don ganin wanda ya soke shi ta baya, amma bai samu ganin ko waye ba sakamakon duniyar da ya ji tana juya masa take ya zube a wajen jini na fita daga jikinsa.
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
[11/2, 7:57 PM] My Uwar Ɗaki: Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan ce)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
Page 3️⃣4️⃣
Yana juyawa dan ganin wanda ya soke shi ta baya, amma bai samu ganin ko waye ba sakamakon duniyar da ya ji tana juya masa take ya zube a wajen jini na zuba a jikinsa.
Sagir ne ya saki wata dariya yana kallon Kamal tare da yi masa jinjina da hannu, shi ma alamar jinjinnar ya yi masa. Ya mike.
"Ina fatan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 39