ya shafi rigarki?"
Daidai lokacin ya shigo fuksar nan kamar kullun a murtuƙe.
Kallonsa suka yi Aunty Laila ta taso da sauri tana duba gabar rigarsa in da shape ɗin laɓɓan Zahrah ya fito a rigarsa sakamakon fadawa jikinsa da ta yi da karfi lokacin da ya janyo ta . Maiƙon ne ya fito a a rigarsa kamar an zana.
Zahrah tuni ta nufi part ɗin Umminta. Wani kallo Mummy ke yi masa.
Aunty Laila ta ce
"Son daga ina kake yanzu ?"
"Sabon gidana da na kammala."
Wani kallo suka masa kafin ta ce .
"Waccen yarinyar Zaharah fa ina ka haɗu da ita?"
"Tare muke tafi "
Cikin yanayin rashin damuwa da yanayin da suke kallonsa ya nufi upstairs Yana cewa .
"Bari na yi wanka."
Daskarewa suka yi suna kallonsa.Yana shiga falonsa ya ɗauke idanunsa akan TV Wanda ya yi jirwayen fari-fari saboda kumafa. Haka duk abinda suka goge suka yi Centre table ma haka duk jirwayen. Ga tiles ma dake me duhu ne duk ya yi ya jirwayen wani wajen kuma ga ruwa nan kwance.
Ransa ne ya yi mugun ɓaci ya taka zuwa bedroom. Ya ga sanin gadon an ɗan yafa ne har da bargon ga pillow duk a karkace. Toilet ya shiga nan ma ya sake ganin wani ɓacin ran.Turarrukansa ma da alama sun yi masa wasa da su
Zuciyarsa har tafarfasa take yi ya nufi downstairs.
Daidai lokacin da Faisal ke dawowa kallo ɗaya ya yi wa Yayan nasa a zuciyarsa ya ce .
'Tau fa waye ya taɓo wannan birkitaccen?'
"Ka kira mani yaran nan dukkansu!."
Ya faɗa yana zuba idanunsa da suka canza launi zuwa ja.
"Yaa Hilal wasu yaran?"
Hararar da ya jefa masa ne ya saka ya nufi part ɗin ƴan matan gidan don kiransu, a zuciyarsa kuma yana tausaya masu.
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
[11/2, 7:57 PM] My Uwar Ɗaki: Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan ce)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
❤️YAR GIDAN TAFEEDAH Beauty world ❤️ Kayan Matta Pure and Natural with Zero Side Effect
*YAR GIDAN TAFIDA KAYAN MATA PURE AND NATURAL WITH ZERO SIDE EFFECT*
*Matan gidan nan mace seda gyara , Ina masu fama da rashin sha'awa to matsalar ku ta kau in sha Allah,muna da abinda za ki sha ya canza miki yanayin jikinki ki fara jin kema macece.*
Kina fama da matsalar rashin gamsuwa ko gamsar da me gida ? To ga solution🥰🥰.
Ina macen da takeson ko yaushe ta jita ajiqe muna da abinda zamu ba ki ,kisha ya saukar miki da ni'ima💃💃💃.
Mata masu son su gyara fatar su ,su dinga sheki da ƙyalli da haske me kyau bana bleaching ba ki zama kalar hutu🧖
Kuma akwai naku .🤩🤩
1. Gumban kwakwa da madara
2. Original tsumin Tabani ka ji ruwa
3. Original tabaje
4. Sweetener powder
5. Sweetener milk
6. Dilka soap
7. Snow whitening soap
8. Morroccan whitening soap
9. Pure sha butter
10. Special yaji and more
Ina matan da suke son su zama na musamman agun oga,in nace ta musamman ina nufin karshen_ karshen ta musamman ajin farko ..... To ku matso nan kuji Yar gidan Tafida ta kawo muku ingantattun kayan mata 100% pure ba side effects in nace muku pure to pure Wanda akayi su da itatuwa masu kara lafiyar dan Adam 💃💃💃💯💯.
*YAR GIDAN TAFIDA*
Tana da alaidi
Akwai pure man kadai
Akwai gumba ta madara da kwakwa
Akwai kuma hakki,akwai tsumi da original tabaje, sai kin gwada za ki gane sirrin 😜😍.
*Duk products dinmu are 100% natural baby chemical,with zero side effects.
Zaku iya tuntubata ta wannan layin 09032036606 Yar gidan Tafida 💯💯
Page4️⃣5️⃣
Hararar da ya jefa masa ne ya nufi part ɗin ƴan matan gidan don kiransu, a zuciyarsa kuma ya tausaya masu.
_Sulaiman_
Ko da ya koma Asadullah mansion ba kowa a wajen da abun ya faru, da alama kowa ya koma ɓangarensa.
Kai tsaye ɓangaren su Mom ya nufa.
Tana zaune a falo ita da Fauziyya. Wacce ke kallon Mom cikin damuwa take cewa.
"Yanzu Mom waye zai aikata irin wannan aika-aikar?"
"Sulaiman nake jira ya zo mu tabbatar da ko waye."
Knocking aka yi suka bayar da izinin shigowa, Sulaiman ne ya gaida Mom. Ta amsa tana bashi izinin shiga part ɗin Asadullah ya bincika.
Kasancewar Sulaiman amintaccen bodyguard ɗin Asadullah ne, ko lokacin da Asadullah kenan yana shiga part ɗin kai tsaye har cikin bedroom ɗinsa.
Bayan ya shiga don tabbatar da wanda ya haddasa wannan gobarar ne ya janyo computer a gabansa bayan ya zauna kan kujerar dake gaban computer ɗin.
Binciken abinda ya faru juya ya soma yi har zuwa yau .
Ya girgiza matuƙa lokacin da ya ga Jidder ta nufi wata hanyar da abu a cikin hijabinta sai waige-waige take yi alamar ba ta da gaskiya.
Sai dai bayan ta nufi bayan part ɗin ba ya iya hango ta, Don ba'a dasa cctv Camera ta bayan ba
Sai dai ɓacewarta ba jimawa ya ga ta bar wajen a guje yayin da wuta da hayaƙi ke tashi daga can baya.
Bayan Jama'a sun taru ga motar kashe gobara ta ƙaraso ne ta koma wancan hanyar a guje.
Sai ta dawo tare da wani ya rufe rabin fuskarsa da hula sannan ga Facemask. Yana biye da ita.
Duk da ba ganin fuskarsa ya yi ba amma ya tafiyarsa ya kalla da kyau ya gane cewa ubangidansa ne.
Abin da ya girgiza shi kenan yana mamakin abun da idanunsa suka gani.
Danne-danne yake yi yana sarrafa computer cikin ƙwarewa.
Sallamar Mom ce ya ji ta shigo bayan ya amsa.
"Sulaiman akwai abinda ka gani ka ga ko waye ya haddasa mana wannan ta'asar ko? Don a gakskiya ba za mu taɓa barin ko waye ba, duk da ba wani daga waje ba ne don akwai matakan tsaro a nan ba wanda zai shigo daga waje dole na ciki ne."
"Mom a gaskiya tsawon kwanaki bakwai kenan da CCTV Camera ɗin nan ta daina aiki.
"Abinda ya faru daga kwanaki bakwai zuwa yau duk ba sa cikin nan."
Ya faɗa yana zuba mata idanu.
"To ta ya hakan za ta faru?"
Nan ya yi mata danne-danne yana nuna mata yana tabbatar mata da ba komai.
Shiru ta yi kafin ta ce.
"To ba hanyar da za'a gane ko waye?"
"Gakskiya yanzu babu komai a nan, amma ina da hanyoyi da yawa da zan iya gane abinda ta faru ki bani kwana biyu."
Jinjina masa kai ta yi cikin sanyin jiki tana cewa.
"Allah ya ya sa."
Da amin ya amsa sannan ya mata sallama ya fice.
Zuciyarsa cike da tarin tambayoyi, me hakan ke nufi, dama kenan ta tabbata Asad na cikin gidan nan kamar yadda ya dage bai ga fitarsa daga cikin gidan ba a gidan ba har Uncle Adam na ganin laifinsa.
Tsawon wannan lokaci ne hakan ke nufi kuma ya aka yi Jidderh ta san da zaman Asadullah a wajen. Sannan me ya sa Asad ya hana a sanar wa da Mom da Dad?
Wadannan tarin tambayoyi sune fal a zuciyarsa ba shi da mai amsa masa waɗan nan tambayoyi dole sai shi uban gidansa.
_Zahrah_
Tana shiga part ɗin Umminsu ta tarar ba kowa a falon, bedroom ɗin ta ta nufa cikin matsanancin sauri don ta ga numfashinta ya fara fita sama-sama.
Side drawer ta buɗe. Inhelar ta ɗauko ta yi saurin kai shi bakinta har hannunta na rawa.
Bayan ta shaƙa ne ta fara jin numfashinta ya na daidaita a hankali.
Kwanciya ta yi tare da lumshe. Daidai lokacin Ummi ta shigo tare da Sallama.
Ganin yamma ce kuma Zahrah in dai lafiya take ba ta kwanciya ta yi barci da yamma. Sanin haka ya saka ta ƙarasa gaban gadon da sauri.
"Auta me ya same ki ne, ko ciwon ki ne ya tashi?"
Gyaɗa mata kai kawai ta yi alamar eh, kafin ta sake lumshe Idanunta.
Mayafin abayar dake kanta ya zame Ummi ta shafa gashin kanta tana mata sannu. Ya kamata a ce duk in da za ki je kuna tare da Inhelar kullum sai na fada maki."
Ganin kamar Ummin ta shiga damuwa ya saka ta yi kokarin kawar da yanayin da take ciki, mumrmushi ta sakarwa Ummin sannan ta tashi tana cewa.
"Bari na tashi Annabi ya hane mu da barcin yamma."
Ta fada tana murmushi yayin da Ummin ma murmushin take sakar mata cikin so da ƙauna hadi da tausayin ƴarta.
_Faisal_
Ko da ya shiga part ɗin ƴan matan gidan a nan ya same su a falonsu. Duk da kasancewar ba su cika kwana a part ɗin ba sun fi kwana part ɗin iyayensu. Amma idan ba dare ba ne nan suka zauna su yi fira.
Sallama ya masu suka amsa suna masa sannu da dawowa har da tambayarsa tsarabar me ya kawo masu yau.
Mumrmushi ya yi sannan ya ce
"Tsarabarku na wajen Yaa Hilal."
Gabansu ne ya faɗi suka kalli juna. A tare suka hada baki wajen cewa.
"Ya dawo ne?"
Kai ya jinjina masu sannan ya ce
"Hope dai ba wata matsala."
"To ai kiransa wallahi ba alkhairi ba ne."
Maryam ta faɗa kamar za ta yi kuka.
"Ba ku sani ba sai kun ke kun tambaye shi za ku san dalili."
"Yaa Faisal me ya saka yau ba ka tsaya ka gyara masa part ɗin sa ba ne?"
Nadiya ta yi maganar kamar za ta yi kuka ita ma.
"Yau da wuri na wuce kasuwa customers na jira na, shi kuma bay tashi barci da wuri da na ga bai tashi ba na tafi bayan na tura masa text message a waya ."
Kausar ta ce.
"Allah ya sa mun masa daidai tsoro nake ji ya ce mu gyara masa part ɗin sa. Mu kuma ba iyawa muka yi ba tun da ba mu ke yi ba masu aiki ke mana, haka nan muka ƙoƙarta muka yi masa."
Sai a lokacin Faisal ya gane dalilin ɓacin rai da ya gani akan fuskarsa. Dariya ce ta taso masa amma sai ya shanye ya ce su je yana jiransu kada su ƙara wa kansu laifi.
Nabeela ce ta fara tashi ta ce su tashi su je su gani.
Suna zuwa babban falon gidan suka ga Mummy da Umma sai Aunty Laila.
Ganin yanayinsu Umma ta ce.
"Lafiya kuwa kuke?"
"Wai Yaa Hilal ne yake kiran mu."
"Okay to ku je ku same shi ku ji."
"Wallahi tsoro nake ji"
Nabeela ta yi maganar tana kallon mahaifiyarta Aunty Laila.
Ganin haka ya saka Sunyi Laila ta ce.
"Ke ba na son rashin hankali daga kira sai ku fata tsoro wata kila akwai abinda za ku yi masa ne?"
"Mu tafi don Allah kada mu yi laifi."
Cewar Maryam ta na yin gaba zuwa hanyar matattakalar stage ɗin.
Mara mata baya suka yi har zuwa falonsa layi suka jera kamar an ce su jeru.
Sallama suka yi suka shiga ƙofar falon ya amsa can ƙasan maƙoshinsa.
Kansa a ƙasa yana kallon ƙasan tile ɗin kamar me karantar wani abu a ƙasan Ɗago kai ya yi ya kalle su, yatsarsa manuniya ya saka ya shafi dogon karan hancinsa wanda ya dace da kyakkyawar fuskarsa.
Ganin yanayin da suka same shi sun tabbatar ransa ya yi ƙololuwar tashi.
Zuba masu rikitattun idanunsa ya yi ɗaya bayan ɗaya yake kare masu kallo kafin ya ce.
"Me na saka ku kafin na bar gidan nan?"
"Gyaran part ɗin ka?"
"Me kuka yi yanzu?"
Nan suka hau bashi hakuri suna cewa wallahi ba su iya ba ne. Cikin mamaki da takaici ya kalle su ya ce
"Shut up!"
Ya daka masu tsawa wanda ya saka suka zube a gabansa saman guiwoyinsu.
"Ko kunya ba ku ji ba, kuna ƴaƴa mata ace ba ku san yadda za ku kula da muhalli ba? Tur da wanan rayuwar ta ku."
Ji ya yi kansa ba masa ciwo ba zai iya dogon magana ba.
"Na baku mintinan ashirin na ga komai yadda ya dace. Idan ba haka ba."
Ya faɗa yana cije laɓɓansa na ƙasa.
Ficewa ya yi ta ƙofar baya da ke cikin part ɗin na su.
Cikin tsoro kowaccensu ta kasa magana sai aiki suke yi ta ko ina.
*Washegari*
_Asadullah_
Yana zaune kan sofa ya jingina bayansa idanusa alumshe kamar mai barci.
Sallamar Dr Isma'il ne ya dawo da shi cikin duniyar da ya lula. A hankali ya bude idanunsa ƙawayan idanunsa da suka kasance blue ya sake su a kan Jidderh.
Jallabiya ce a jikinsa fara duk wanda ya san shi kallo ɗaya za ka masa ka san ya rame.
"Dr ya jikin na ta ina fatan dai ba wata matsala ko?"
Asadullah ya tambaya cikin tausaya wa
Zama Doctor Isma'il ya yi ba tare da ya ce komai ba.
"Ka yi magana mana akwai matsala ne?"
Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya kalli Jidderh sannan ya mai da dubansa ga Asad.
"Yallaɓai a gaskiya duk binciken da aka yi ba wata matsala a tattare da ita. Ƙwaƙwalwarta lafiya lau take ba wata matsala.
"Ban gane ba wata matsala ba yarinyar nan ba haka take ba accident muka samu "
"Ban yi maka musun cewa ba accident kuka samu ba, ina mai tabbatar maka da cewa ƙwaƙwalwa yarinyar nan lafiya lau take babu wata damuwa s tattare da ƙwaƙwalwarta. Ko bugawa ba mu gani ba ƙalau take."
"Ba ƙalau take ba!"
Ya faɗa rai a ɓace.
Duk yadda Doctor Isma'il ya so fahimtar da shi ƙi ya yi daga karshe dai hakura ya yi ya masa sallama akan gobe zai dawo.
Kallonta ya yi ta zauna kan kujera ta dubawa TV.
Sulaiman ne ya yi sallama ya shigo. Bayan ya gaida uban gidansa cikin girmamawa ne ya mika masa ledar hannunsa.
Wata kwali ne y ciro daga cikin ledar, waya ce ya fito da ita daga cikin kwalinta.
Har da sim card an yi register an yi komai.
Saka sim card a cikin wayar ya yi ya saita komai.
Har lokacin fuskarsa ba walwala. Sulaiman ne ya ce.
"Sir zancen CCTV Camera na yi yadda ka ce yanzu ba wata matsala in sha Allah."
Ya yi maganar yana kallon Jidderh wacce ba ta san me ke faruwa ba.
"Gud job."
Ya faɗa idanunsa akan wayar dake hannunsa.
"Za'a kai yarinyar nan wani asibiti a ninki matsalar ta."
"Sir me Doctor Isma'il ya faɗa?"
"Wai laflya lau ƙwaƙwalwarta take."
Da mamaki Sulaiman ke kallonta don tabbas ba haka ya san yarinyar.
"To yallaɓai ya kake so ayi yanzu?"
Shiru Asad ya yi kamar ba zai yi magana ba kafin ya ce.
"A canza mata wani asibitin don gano matsalar amma ban gamsu da zancen cewa ƙalau take ban yarda ba."
Jinjina kai Sulaiman ya yi kafin ya ce.
"Ba damuwa zan kai ta asibiti maikyau ƙwararrun likitoci za su duba ta."
Jinjina kai ya yi kafin ya tashi ya haura upstairs.
Kai tsaye bedroom ɗin sa ja shiga. Ya wani na'ura ya danna dake manne jikin bango, take dai ga wata dorowa ta bayyana wanda ba za ka taɓa cewa akwai ta wajen ba. Kuɗaɗe ne a ciki jere daga kan Dollar har zuwa Naira.
Ɗiba ya yi ya zuba a wata ƙaramar jaka kafin ya fita zuwa falo in da ya samu Sulaiman.
Zama ya yi a in da ya tashi kafin ya ce.
"Ya kamata ka nemo mata abun da za ta ci kafin ku tafi zuwa wani asibitn."
Jinjina kai Sulaiman ya yi sannan ya mike tsaye ya nufi ƙofar fita ya fice.
_Hilal_
Tsawon mintuna talatin ya ɗauka a wajen garden ɗin kafin ya bi ƙofar baya ya koma part ɗin sa.
Ko da ya shiga tsaye ya same su dukkansu kowacce a tsorace take .
Falon ya fara dubawa ya ga ba abinda suka gyara da alama iya iyawarsu kenan ba su iya komai ba.
Idanunsa ne suka sauka akan home theater da ruwa ke ɗiga daga sama na shi zuwa ƙasa. T.V ma haka, Centre table ma haka.
Bedroom ya koma ya ga sun gyara shimfidar zanin gadon amma lillubashi suka yi filon ma a karkace.
Cikin ɓacin rai ya karasa in da suke yana zuwa kan Maryam dake ita ce farko ya ɗauke mata wani lafiyayen marin da sai da ta ji ji da ganinta ya ɗauke. Kafin ta ankare ya saka ƙafa ya harɗe mata ƙafa tare da zubar da ita ta fadi ƙasa wanwar.
Haka ya yi masu dukkansu sai da suka zube suna ihu.
Daga nan ya saka su tsallen kwaɗo suna yi suna kuka.
Har sun gaji amma sun kasa tsayawa wa, sai da ta tabbatar sun gaji kafin ya dakatar da su.
Kuka da majina suke yi iya jigatuwa sun yi. Kafin ya ce.
"Kodayake ba laifin ku ba ne, saboda an sabgarta ku ba'a koya maku ba kasancewar ku mata waɗanda za su je gidan wani. Ko wane namiji ne zai yarda a ce yar aiki ke masa aikin gida?"
Shiru ya yi kafin ya ce.
"Ku tashi ku fice mani daga nan."
Sun kasa tashi da rarrafe suka fice. Sai dai zuwa wajen matattakalar ya saka kuka don ba za su iya taka ƙafar ba.
A zaune suna jan mazaunai suka sauko har lokacin kuka suke.
Mummy, Umma, Aunty Laila da suke falon suka taso cikin tashin hankali jin kukan yaran na su.
Cikin tashin hankali suka taso suke tambayar abinda ke faruwa. Ba su iya amsa masu ba, shi kuma Hilal ya hangi ɗaya daga cikin ma'aikatan gidan ta fito bangaren Aunty Laila.
Kiranta ya yi ya sanar da ita cewa ta kira masa duk ma'ikatan gidan, ta wuce jikinta na rawa .
Cikin ƙufula Mummy ke kallon su Kausar kafin ta ce.
"Me suka yi maka ne haka kana neman illata su?"
Kafin ya yi magana masu aikin gidan suka karaso wajen . Kallonsu ya yi kafin ya ce .
"Su waye ke gyara masu part ɗin su?"
Ya yi maganar yana nuna su Nabeela dake jigace.
Wasu ƴan mata masu suna Saude da Lami suka ce su ne. Jinjina kai ya yi kafin ya ce
"Daga yau ba ƴanta ku daga yi masu aiki, kuma idan na ji labarin cewa kun gyara masu part kai ko tsinke idan kuka kawar sai kun bar gidan nan."
Da sauri suka bashi hakuri suna cewa za su kiyaye.
Mai da dubansa ga wata dattijuwar mata ya yi wacce suke kira da Baaba ya ce.
"Mama duk sanda za ki yi girki a cikin gidan nan ki tabbatar yaran nan suna cikin kitchen kina koyar da su girki. Idan gari ya waye za ki shiga kitchen ki aika a kira su haka da rana ko yamma sai dai idan sun je school wannan ba matsala. A cikin sati biyu da koyon nake son su fara gwada wa. Idan wata ta yi maki rashin kunya ko cin mutunci ki sanar da ni."
Jinjina kai Baaba ta yi sannan ta ce .
"In sha Allah za'ayi yadda ka ce."
Sallamar su ya yi suka fice, har lokacin su Maryam na kuka .
A ƙufule Mummy ta sake magana .
"Akan me za ka yanke irin wannan hukuncin sai ka ce ba na gaba da kai. Akan me za ka ce su za su dinga aiki sai kace Kai?"
"Sunyi Laila ta ce.
"Hilal me kake yi haka ne?"
Daidai lokacin da Papa da Dada suka shigo bayan direba ya dauko su.
Cikin damuwa suka karasa wajen in da Dada ke cewa
"Meke faruwa haka me ya same su?"
"Dada ki bar su tarbiyyar da aka kasa ba su ne nake ƙoƙarin ba su shi a matsayin wa tun da iyaye sun gaza ba su gatar da ake bawa kowace ƴa mace."
Jin haka ya saka suka fahimci komai Papa ya ce wa Hilal ya rabu da shi haka, kafin ya nufi part ɗin su Dada na biye da shi a baya.
Mummy ta sake ɓata rai ganin tana mahaifiyarsa bai saurare ta ba.
"Ba da kai nake magana ba Hilal mu kake cewa ba mu ba wa yaran nan tarbiyyar ba sai kai ne za ka basu? To ka fita daga idanunna ba wanda ya isa ya saka yaran nan aikin da ka ce su yi tun da ba jakai ba ne, akan me me za ka wahalar da shi Allah ya hutar da su to wannan karon dole na taka maka birki."
Mumrmushin takaici ya yi, Aunty Laila ta ce
"Akan me za ka mayar da yara kamar marasa gata har da aikace-aikace ba za su yi ba."
"Shikenan ku kuma mu zuba ni da ku wanda ya fasa."
Cikin rawar murya suka hada baki wajen cewa za mu yi aiki.
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
[11/2, 7:57 PM] My Uwar Ɗaki: Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan ce)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
❤️YAR GIDAN TAFEEDAH Beauty world ❤️ Kayan Matta Pure and Natural with Zero Side Effect
*YAR GIDAN TAFIDA KAYAN MATA PURE AND NATURAL WITH ZERO SIDE EFFECT*
*Matan gidan nan mace seda gyara , Ina masu fama da rashin sha'awa to matsalar ku ta kau in sha Allah,muna da abinda za ki sha ya canza miki yanayin jikinki ki fara jin kema macece.*
Kina fama da matsalar rashin gamsuwa ko gamsar da me gida ? To ga solution🥰🥰.
Ina macen da takeson ko yaushe ta jita ajiqe muna da abinda zamu ba ki ,kisha ya saukar miki da ni'ima💃💃💃.
Mata masu son su gyara fatar su ,su dinga sheki da ƙyalli da haske me kyau bana bleaching ba ki zama kalar hutu🧖
Kuma akwai naku .🤩🤩
1. Gumban kwakwa da madara
2. Original tsumin Tabani ka ji ruwa
3. Original tabaje
4. Sweetener powder
5. Sweetener milk
6. Dilka soap
7. Snow whitening soap
8. Morroccan whitening soap
9. Pure sha butter
10. Special yaji and more
Ina matan da suke son su zama na musamman agun oga,in nace ta musamman ina nufin karshen_ karshen ta musamman ajin farko ..... To ku matso nan kuji Yar gidan Tafida ta kawo muku ingantattun kayan mata 100% pure ba side effects in nace muku pure to pure Wanda akayi su da itatuwa masu kara lafiyar dan Adam 💃💃💃💯💯.
*YAR GIDAN TAFIDA*
Tana da alaidi
Akwai pure man kadai
Akwai gumba ta madara da kwakwa
Akwai kuma hakki,akwai tsumi da original tabaje, sai kin gwada za ki gane sirrin 😜😍.
*Duk products dinmu are 100% natural baby chemical,with zero side effects.
Zaku iya tuntubata ta wannan layin 09032036606 Yar gidan Tafida 💯💯
Page4️⃣6️⃣
Cikin rawar murya suka haɗa baki wajen cewa za mu yi aiki.
"Gud"
Ya faɗa yana amsa kiran wayar da ake masa ya fice daga falon.
Nan suka saka masu aikin suka taiamaka wa su Kausar zuwa part ɗin su.
Zahrah bayan ta samu yi nutsuwa ne ta na zaune tana karatun Alkur'ani da kanta kasancewar ta haddace ta .
Suratul Maryan take ƙarantawa cikin muryarta mai zaƙin sauraro.
Kitchen ta nufa da niyyar taya Umminta aiki, sai Ummin ta fito take sanar da ita yau abincin gidan za su ci su ma, ta je ta yaya Dada girkin.
Fita ta yi ta nufi part Dadar da sallama a bakinta. Suka amsa kafin Dada ta cigaba da cewa.
"Ban ga laifin Hilal ba daidai kenan, iyayensu ba son gaskiya suke yi ba."
Sannu da dawowa Zahrah ta yi masu kafin ta ce.
"Dada me za ki girka ne, ko na gidan gabaɗaya za ki ci?"
"Eh saboda yau na gaji ba zan iya girki nan ba, amma tun da kin zo shiga ki sama mana abu mai sauƙi."
Kitchen ɗin ta nufa Daidai lokacin da Sunyi Laila ta shigo da sallama.
Amsa mata suka yi ta shigo ta zauna tana cewa .
"Barka da warhaka Papa. Dada ina wuni?"
Ba wanda ya amsa mata, ita ma sai ta tsuke fuska.
Tabbas ba sa jin daɗin abinda Aunty Laila da su Mom suke yi. Sai dai Aunty Laila ce suka haifa ita ce ƴarsu. Su Mummy da Umma surukai ne hakan ya saka ba su cika matsa masu ba sai Aunty Laila.
Papa ne ya yi gyara murya ya ce.
"Laila."
"Na'am."
Ta amsa bayan ta daga kai ta kalle shi.
"Ba na sanar da ke cewa ki kwashi su Nabeela da Kausar ki mayar da su gidan ubansu ba?"
Kara ɓata rai ta yi tana cewa.
"Mutumin nan fa ya sake ni ya dauki matarsa sun bar ƙasar nan. Zan taho gidan ubana ne bar su wajen waye tun da bai damu da yaran ba. Kuma nan gidan Kakansu ne ai gidan Mahaifina ne. Ba na da inda zan kai su bayan nan Papa ka duba lamarin nan."
Shiru ya yi kafin ya ce
"Duk in da za ki kai su bai fi a ce suna gidan mahaifinsu ba ai da uba ake ado ba uwa ba."
"Amma a baya lokcin da mahaifiyar Zahrah ta ce za ta tafi gida ta gaji ai cewa kuka yi ba za ta tafi da Zahrah ba don ba ta da in da ya fi nan. To ita kun yarda za ku rike ta ballantana
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 24 Chapter of 39