je ta haɗa masa ruwan wanka nai dan ɗumi.
Tashi ya yi ya nufi bathroom ɗin sa. Zama ya yi a bakin gado tana tsaye ta ce.
"Ko na taya ka rage kayan jininka ne?'
"Ki bar shi na gode.'
Ba haka ta so ba sai dai ba yadda za ta yi."
"Ki koma falo idan na fito zan zo na same ki ."
Tura baki ta yi don ita ba ya ga ranar da burin ta zai cika akan Hilal ba, amma da sannu akuya take shiga gidan kura har ta ci ta da yaƙi.
Fita ta yi daga cikin ɗakin ta bashi wuri kamar yadda ya ce.
Kayan jikinta ya rage sannan ya shiga wanka.
Ya kwashe kusan mintuna talatin yana yin wanka kafin ya fito sanye da bathrobe a jikinsa.
Sury kam tana falo tana jiran fitowarsa.
Loka-lokaci take sakin murmushi ita kaɗai. Har ya fito sanye da ƙananan kaya a jikinsa. Ƙaramar riga da kuma wando Three quarter.
Kitchen ya shiga ya fito dauke da wani biscuit da lemu. Zama ya yi kusa da ita ya fara ci. Ita ma ta saka hannu kasancewar biscuit ɗin babba ne a cikin gwangwani a tare suka ci biscuit ɗin suka sha lemun.
Da misalin karfe goma na dare ya goma na dare ya gama shirin kwanciya don yau baya jin zai iya wani aiki kafin ya kwanta .
Sury ce ta shigo ɗakin da sallama ya amsa mata, wani irin turare t shafa a jikinta wanda tun ya ji kamshin sa dai da ta haifar masa da kasala.
Lumshe udanu ya yi tare da sakin ajiyar zuciya sakamakon kamshin ya masa daɗi, dama shi mutum ne mai son jin ƙamshi shi ya sa kullum yana cikin ƙamshi.
Zama ta yi bakin gadon tana sakar masa murmushi, yana kishingide yana kallonta .
Da hannu ya mata alama, gane me yake nufi ya saka ta haurawa saman gadon ta faɗa jikinsa.
Wani remote ya danna hasken ɗalin ya ɗauke, cikin farin ciki ta ƙanƙame Hilal tana addu'a Allah ya sa kada ya yi mata abun da ya saba yi wa sauran mata da ta ji suna faɗa. Sai ya kai su ƙololuwar bukatar kasancewa da shi sai ya tashi ya bar su ba tare da ya biya masu bukata ba.
Hakan ya saka ta sa aka kawo mata wannan turaren akan cewa ina dai har ya shaki kamshin turaren dole sai ya yi sex da ita duk taurin kansa kuwa. Sai ta tsinci kanta cikin farin ciki don ta ji yadda turaren ya ji rasiri akan sa har yana sakin ajiyar zuciya.
Dama babu riga a jikinsa wando ne Three quarter ya sake sa wani. Janyo ta ya yi cikin bargon
Yamutse fuska ya tare da yi mata alama da ta cire rigar jikinta. Cikin azama ta cire rigar dama ba ta saka bra ba, pant ɗin ma ta cire shi.
Bakinsu ya haɗe waje guda suna sumbatar juna.
Kamar dai kullum yau ma haka ne, sai da ya gama sarrafa ta son ransa ya taba duk in da yake so ya shafa duk in da yake so amma bai yi gigin yin sex da ita ba kuma bai da niyya.
Ganin take-takensa kuma an fada mata in dai ya shaƙi kamshin turaren nan duk abinda take so shi zai mata ne ya saka ta kai hannu zuwa wandonsa da niyyar cire wa.
Tsawar da ya daka mata ne ya saka ta firgita tare da ƙanƙame shi.
Kamar za ta yi kuka ta fara magana.
Babu wani wajen da ba ka sani a jikina ko ka taɓa ba, to akan me kai ba za'a ga jikinka ko a taba kamar yadda kake yi wa matayen da kake mu'amala da su?"
Haka tsarina yake kuma kowace macen da ta sanni a haka ta san ɗabi'ata, babu macen da zan iya sex da ita sai dai idan na tabbatar da cewa akwai igiyar aurenta a kaina, lalacewar ta wa bai kai da zan iya shiga gonar da ba ta wa ba na yi ban ruwa, amma matukar gona ta ce zan shiga na yi ban ruwa har na samar da yabanya mai kyau. Ba ke kaɗai ba ce kuna da yawa kuma kin san wasu da nake harka da su za ki iya tambaya ko akwai wacce na taɓa yin amfani da ita. "
"To ai idan za ka sha giya ka sha ta dubu, tun fa ka iya romancing ɗin mace ka iya kissing Higgins da mace shi halal ka aikata da kake tsoron zina su Meye kake yi?"
"Ke tashi ki fita kafin na sauya maki kamanni!"
Ya faɗa a zafafe ba shiri ta mayar da kayan jikinta ta fice daga ɗakin.
Sai ƙarfe tara na dare sannan Hajiya Bilkisu da yaranta suka shirya don komawa gida. Don tare suka yi girki da Ummi Khalil kuwa tare da Sadik da Mahmud suka tafi masallaci.
Da za su tafi Khalil ya so keɓewa da Zahrah bai samu damar hakan ba, don haka ya ɗauki wayar da ya gani akan kujerar wanda ya ke da tabbacin na Zahrah ne, dubawa ya yi ba password take ya saka lambar wayarsa ya kira. Sai da ya ji kiran ya shigo wayarsa ya ajiye.
Ganin kowa ya zuba masa idanu ne ya faske tare da cewa.
"Akwai maganin da zan kawo mata ne shi ya sa na ɗauki lambar idan zan kawo sai na sanar da ita"
"Yes Doctor."
Amal ta yi maganar tana sara masa.
Dariya Sadik da Mahmud suka yi don su kadai ne a wajen Ummi da ƙanwarta suna cikin ɗaki suna magana.
A tare suka fito daga cikin ɗakin tana sauri ganin kiran mijinta na shigowa wayar.
Har parking space suka taka su sai da suka ga wucewarsu suka koma ciki.
_Sulaiman_
Yana magana da Dad wayarsa ta yi ruri. Ganin Asadullah ne ya saka bai ɗaga a gaban Dad ba. Magana suke yi akan Asad don Dad ya damu da rashin sanin halin da yake ciki, ga ramar da ya ys yi . Dad yana cikin damuwa sosai sai dai yanayin da ya ga Sulaiman a ciki ya saka shi cikin wani tunanin.
A baya idan ya ga Sulaiman yana hango tsantsan damuwa da tashin hankali, sabanin yanzu da yake ganin kamar bai damu da rashin uban gidan na sa ba. Dole akwai wani abu a ƙasa.
Bayan ya sallama Sulaiman ne ya koma ciki yayin da Sulaiman ɗin ya fito daga falon Dad ɗin.
A can bakin gate kuwa hayaniya ce ta kaure a tsakanin Isah Yayan Jidderh da security. Ya zo ne saboda ya sake jin ko an samu labarin ta, security suka hana shi shigowa shi kuma ya dage sai ya shigo.
Sulaiman na sauri don zuwa gidan Asadullah kenan ya ji hayaniya.
A can bakin gate kuwa Isah ne yake yi wa security magiya akan su bar shi ya shiga ciki karo na karshe kenan.
"Don Allah daga yau ba zan sake dawowa ban nan ba, zan so na yi magana da..."
"Kai wallahi ba zan bari ka shiga ba, wani irin bakin naci ne da kai, idan mutum ya ɓata ai police station za ka je ko gidan rediyo ba nan ba."
Dole isah ya hakura ya goge ƙwallar da ta cika masa idanu ya juya zuwa wajen babur ɗin da ya kawo shi. Wato abokinsa tun safe suna ta yawon nemanta.
Yana hawa babur ɗin daidai lokacin Sulaiman ya fito hannunsa rike da waya ya kara a kunnensa, suka haɗa idanu da Isah daidai lokacin da babur ɗin ke shirin barin wajen.
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
[11/2, 7:57 PM] My Uwar Ɗaki: *GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan ce)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
Page5️⃣4️⃣
Yana hawa babur daidai lokacin Sulaiman ya fito hannunsa rike da waya ya kara a kunnensa, suka haɗa idanu da Isah daidai lokacin da babur ɗin ke shirin barin wajen.
Kallon ɗaya daga cikin security ɗin ya yi sannan ya ce.
"Hayaniyar ne nake ji?"
"Wasu mahaukata ne suke neman kawo mana shirme a nan, idan mutum ya fadi a police station amma sun damu mutane da hayaniya anan."
"Wani ne ya ɓata?"
Cewar Sulaiman yana tsare securityn da idanu.
"Wai wata ce da take aiki a gidan nan suka nema suka rasa?"
A kiɗime Sulaiman ya tambaya security ɗin.
"Wai tun ranar da aka yi gobarar nan aka..."
Kafin security ya karasa fada masa tuni Sulaiman ya bi hanyar da ya ga sun bi da babur ɗin a guje.
Security da suke waje suka saki baki suna kallonsa cike da mamaki.
Ganin ba alamar su ya saka ya dawo da sauri yana cewa security su bude masa kofar gate ɗin da sauri.
Da gudu ya nufi parking space ya shiga daya daga cikin motocin da ke wajan ya saka makullin ya yi mata key ya fige ta.
Zuwa lokacin har an wangale masu gate a guje ya bar wajen suka mamakin rikicewar da ya yi lokaci ɗaya .
_Washegari_
Jirginsu na sauka a filin jirgin sama, tun daga nesa suka hango kakan na su da direban na sa, fuskarsa dauke da murmushi yayin da shi ma murmushin take sakar masa. Ita ma murmushin take yi.
Kowa na rike da madaidaicin jakarsu.
Direban Kakan na su ne ya karbi jakarsu ya saka a bayan motar .
Rungume tattijon Ammar ta yi ita ma Humaira ta rungume shi ta baya.
Farin ciki ne ya daka idanun Dattijon ciki da ƙealla, cike da son jikokin na sa ya ke saka masu albarka. Don Allah ya sani yana son kusanci da iyalinsa, sai dai ɗan na sa wato mahaifin su Ammar ya nisanta kansa da gida. Sai shekara yake zuwa da iyalansa. Sai dai wani lokaci ya kan ga Ammar ya zo shi ma dalilin abotarsu da Hilal ne idan ya kawo masa ziyara. Saboda Hilal yakan shigo ko na lokacin ziyara da suka saba zuwa .
ba.
Yanzu kuma dalilin zuwan na su saboda Zahrah ce, tun da aka fada masa ba ta da lafiya ta kwanta asibiti shi kenan hanakilinsa ya tashi ya ce dai ya zo ya ga halin da take ciki.
Lokacin da ya kira wayar da niyyar ya haɗa Zahrah da ƙanwarsa Humaira don su gaisa ne dai Dada ta ɗauka take sanar da shi rashin da Zahrah ke fama da shi .
"Ba shi kaɗai ya shiga tashin hankalin ba Humaira da yake tare da ita a lokacin ta shiga damuwa sosai ba kaɗan ba. Don haka da ya ce zai zo da ta ce za ta biyo shi, iyayen sun ɗauka cewa za su zo saboda kakanninsu ne amma su kam sun san dalilin zuwansu ba don ziyara ga kakanninsu suka zo ba.
Shi ma Baba Alhaji wato Kakansu ya ɗauka sun zo don su sada zumunta ne, shi ya sa har ƙwallar farin ciki ya yi .
Mota suka shiga Direban ya ja don kai su gida.
Ko da suka isa gidan Kakansu mace wato Hajiya Mama ta yi farin cikin ganin jikokin na ta.
Farin ciki sosai ya cika gidan. Sail da suka yi wanka suka ci abinci ne sai suka ce za su fita
Mutanen gidan sun yi mamakin jin cewa za su fita, sai ya sanar da su gidan Aninin na sa zai je. Ba su da wani zaɓi suka bar su.
Ɗaya daga cikin motocin ya ɗauki key ɗin, sannan ya basu tsarabar su bayan ya ce wa Humaira ta kai na Zahrah mota.
Bayan ya ji wa motar key ne ya danna horn maigadi ya wangale masu gate ɗin suka bar gidan.
Suna ta fira duk yana bata labari akan Zaheah har suka karasa gidan.
A parking space ya yi parking ba tare da ya fito ba. Kallonsa Humaira ta yi tare da cewa.
"Lafiya kuwa Yaya?"
"Ina tunanin yadda zan shiga gidan ne da sunan wajen Zahrah na zo, ai ba baki labarin irin zaman da suke yi a cikin gidan nan. Ta ya ya xan kalli iyayen abokina bayan na san ba jituwa a tsakanin su da su Zahrah. Wancan zuwan na ga kallon da suke yi wa Zahrah."
Taɓe baki ta yi sannan ta ce.
"Kada ka damu Yaya ka share su ka yi abinda da ya kawo ka."
Wayarsa ya ɗauka sannan ta lalubo lambar Zahrah, tana ganin kiransa da ɗauka da sauri ganin lambarsa ta Nigeria ce
"Assalamu alaikum Ya Ammar ka zo ne?"
Mumrmushi ya yi sannan ya ce.
"Ina mota har da ƙanwata ki fito ki same mu a parking space."
"Okay"
Ta fada ta kashe wayar sannan ta kalli Dada dake kallonta. Don su biyu ne a falon Dada .
"Wai Yaa Ammar ne ya zo da ƙanwarsa suna parking space wai na je."
"To jeki amma ki tabbatar iyakar ki wajen kada ki fita daga cikin gidan nan."
"In sha Allahu."
Ta saka hijabinta har ƙasa sannan ta saka flat shoe ɗinta ta fita .
Mutanen gidan kuwa suna fakon gidan suna fira, don gabaɗaya sun hallara idan aka cire ƴan part ɗin su Zahrah. Maza da mata iyaye da yara, har da iyayen maza suna cikinsu sau fira suke yi cike da nishaɗi.
Zahrah ta zo ta wuce su ta nufi hanyar fita.
Tun daga nesa suke hango ta tana karasawa in da suke cikin takunta na nutsuwa.
"Wow"
Humaira ta furta tana murmushi.
"Gaskiya Yaya Zahrah hadaddiya ce, wannan tsantsar kyau haka?"
Mumrmushi kawai yake yi idanunsa na ga Zahrah.
"Ba iya kyau kawai take da shi ba, tana da kyawun zuciya da halayya masu kyau, Zahrah nagartacciyar mace ce wacce ko wane namijin da ya san kansa zai yi kokari mallakar ta a matsayin mahadin rayuwarsa uwar ƴaƴansa."
Gakskiya ka yi sauri ka aure ta kada ka tsaya kallon ruwa kwaɗo ya yi maka kafa. Ba namijin da zai ganta ya kaida kai."
Haka ne, shi ya sa kullum take sanya niƙab ko Facemask idan za ta fita waje."
Daidai lokacin ta karaso bakinta ɗauke da sallama cikin zazzaƙar muryarta.
Amsa mata suka yi s tare suka fito daga motar.
"Yaa Ammar sannu da zuwa ."
"Yauwa Sanni sarauniyar mata, kin warke ma ko?"
Ya faɗa yana mata murmushi.
"Tare da ita kuka zo tun daga London ne?"
"Eh wai za ta zo ta duba jininki."
"Sannu da zuwa ƴar uwa, ya hanya?"
Ta faɗa tana murmushi, rike hannun juna suka yi suka shiga daga cikin gidan.
A falon gidan suka yi sallama dukkansu, gabaɗaya suka juyo suna kallonsu. Humaira ta sunkuya cikin girmamawa ta gaida mutanen gidan. Ganin ta da Zahrah ya saka ba wanda ya amsa, sai dai Mommy da Aunty Laila suna mata kallon sani, sai dai sun rasa ina suka san ta.
Jan hannunta Zahrah ta yi suka nufi part ɗin Dada, da sallama Dada ta amsa masu cike da fara'a.
Nan Humaira ta gaishe ta ta amsa mata cikin sakin fuska da walwala.
Sallamarsa ne ya saka suka amsa suna kallonsa.
"Yaa Ammar."
Da mamaki kowa ke kallonsa, ganin cewa bai taba zuwa idan Hilal baya nan ba, duk zuwansa sai Hilal na ƙasar yake zuwa.
"Ammar saukar yaushe a ƙasar?"
"Yau na zo."
Da fara'a kowa ya tarbe shi ya zauna suka gaisa da kowa.
"Ga shi abokin na ka baya ƙasar."
Cewar Mummy.
"Eh wajen Zahrah na zo."
"Wajen Zahrah?"
Suka haɗa baki kusan dukkansu wajen furta kalmar."
"Eh na ji labarin ba ta da lafiya shi ne muka zo ni da ƙanwata don duba lafiyarta."
"Wai wannan yarinyar da suka shigo da Zahrah ita ce Humaira ?"
Cewar Mummy cike da takaici.
",Eh ita ce dama ba ki gane ta ba ne?"
Tsabar takaici kasa magana ta yi, kowa dake wajen ba wanda ya yi farin ciki da jin jin zancen Ammar.
Tashi ya yi yana cewa .
"Bari na gaida Dada "
Bayan tafiyarsa Aunty Laila ta ce
"Sai na bi duk hanyar da zan bai don ganin na hana Ammar auren wannan yarinyar, matukar ina numfashi a duniyar nan ba zan taba bari na wani ya zo neman aurenta ban lalata maganar ba."
Jinjina kai Mummy ta yi tare da cewa
"Ina bayanki ɗari bisa ɗari. Ba za ta taɓa yin rayuwar farin ciki ba daga ita har Iyayenta mu zuba mu gani."
Jinjina kai Umma ta yi tana murmushi tare da masu alamar Jinjina.
A ɓangaren Dada suke a falonta, Dada, Ammar, Zahrah, da Humaira.
Fira suke yi cikin annashuwa da farin ciki,, duk da cewar Zahrah ba ta saki jiki ba saboda Ammar na wajen kunyarsa take ji
An cika masu gaba da kayan ciye-ciye da na sha.
Bayan sun kammala ne Suka tashi suka nufi part ɗin Abbi. Su uku ne Zahrah da Humaira na rike da hannun juna sai Ammar dake bayansu.
Har lokacin jama'ar gidan na falo.suna ganinsu bakin cikinsu ya kafa ninkuwa.
Don sun san in dai Ammar ya auri Zahrah ta huta. Za ta samu duk wani abun da take buƙata na more rayuwa. Su kuma ba haka suke so ba, so suke yi su ga rayuwarta ta tagayyara.
Da sallama suka shiga part ɗin Ummi tana zaune da alƙur'arni mai girma tana karantawa .
Tana kai aya ta ajiye ta tarbe su da fara'a duk da ba ta yi mamakin ganin Ammar ɗin ba.
"Bisimillah."
Suka zauna bayan sun gaishe ta, ta amsa cikin farin ciki da walwala.
Abbi ya fito daga ɗakinsa ya ya karaso falon.
Suka gaishe shi kasancewar weekend ne kowa na gida, Yaa Mahmud da Yaa Sadik ma duk sun fito an gaisa.
Nan ma Ummi ta kawo masu abun sha duk da sun ce sun cika ciki a bangaren Dada.
_Asadullah_
Wayar Sulaiman yake kira baya daga wa. Jikinsa ne ya bashi akwai wata matsala dake faruwa .
Sake kira ya sake yi a daidai lokacin da yake driving yana ƙoƙarin barin layin Asadullah mansion, ɗagawa ya yi tare da kara wayar a kunnensa.
"Yallaɓai zan kira ka ina ƙoƙarin bin bayan wadanda suka zo neman Jidderh ne, da alama Yayanta.
Yana faɗin haka ya katse kiran wayar da alama sauri yake yi sosai.
Asadullah bai san sanda ya saki murmushi ba, saboda ya ji dadin wannan labarin da ba ya ji. Ya kuma yi addu'ar Allah ya bayyana ta.
Kiran waya ne ya shigo wayarsa dubawa ya yi ya ga sunan da ya bayyana akan fuskar wayar.
Inspector Bashir. Shi ne sunan da ya bayyana akan fuskar wayarsa.
Ɗaga wa ya yi tare da yin sallama.bayan ya amsa sallamar daga can ɓangaren ne Asadullah ya ce.
"Ya aiki?"
"Alhamdulillah." Inspector ya amsa sannan ya ce.
"Shi wannan sagir ɗin da ya yi ƙoƙarin kashe ka a baya tare da ɗan uwanka mun gano in da yake."
Da sauri Asadullah ya mike tsaye yana cewa.
"A ina yake yanzu?"
"Bayan mun yi bincike mun gano cewa yau satin sa ɗaya kenan da ya dawo ƙasar, kuma yana garin Lagos ne a yanzu haka."
"Da kyau."
"Mun gano cewa akwai yarinyar da yake nema a garin ne, ta hanyar ta za mu fara bi, ita ce tsanin da za mu bi ta kai mu zuwa gare shi.
Don yanzu yana taka tsan-tsan da mutane ba zai saki jiki yadda zai kamu cikin sauki ba."
"Okay"
"Yanzu ka jira za ka ji daga gare ni, don akwai abubuwan da nake bukatar ji daga gare ka."
"In sha Allah."
"Kada ka damu zai shiga hannu kamar yadda Kamal ya shiga hannu yana prison, wata kila ma yana da saka hannu a abinda aka yi maka na rufe ka tsawon lokaci. Bisa la'akari da ya zauna a cikin mansion ɗin tsawon lokaci ya san komai na ciki."
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
[11/2, 7:57 PM] My Uwar Ɗaki: *GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan ce)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
Page5️⃣5️⃣
Kada ka damu zai shiga hannu kamar yadda Kamal ya shiga hannu yana prison,watakila ma yana da saka hannu kan abin da aka maka na rufe ka tsawon lokaci. Bisa la'akari da ya zauna a cikin mansion ɗin tsawon lokaci ya san komai na ciki."
Ɗan jim Asad ya yi kafin ya ce.
"Ta iya kasance wa haka ne, amma abun da hankalina ya fi karkata wani ne daban ba Sagir ba."
Ta iya yiwuwa haka ne, ta iya yiwuwa ba haka ba ne, amma bincike zai tabbatar mana da ko waye ya aikata wannan laifin. Ku shi ne ko kuma wani ne daban daga gefe".
"To shi kenan inspector Bashir Na gode sosai."
Daga haka suka yi sallama ya kashe kiran wayarsa.
_Zahrah_
Wunin ranar yin shi ta yi tare da Ammar da kuma ƙanwarsa. Ta yi shi ne cikin farin ciki da jin dad'i. Don Ammar ya shiga ranta duk da idan ta tuna da zantukan mahifiyarta jininta yana sanyi sosai. Don ta ga alamar cewa su Mummy ba za su bari Ammar ya aure ta ba. Ko da ba su san waye iyayen Ammar ba za su yi iyakar kokarinta ganin sun ɓata komai. Ballantana akwai mutunci da zumunci a tsakanin Mahaifiyar Ammar da mahaifiyar Hilal ɗin
Sai kusan magrib Ammar ya ce wa Humaira ta tashi su koma gida.
Don lokacin sun bar part ɗin Ummi sun koma na Dada. Wata shaƙuwa ce ta shiga tsakanin Humaira da Zaharah a cikin yini guda . Tamkar Wadanda suka shekara da sanin juna
Dama sun yi wa su Ummi sallama don haka suka yi wa Dada sallama a lokacin da za su tafi.
Ko da suka karaso main falon gidan ba kowa. Da alama kowa ya koma part ɗin sa kenan.
Kallon Humaira Ammar ya yi kafin ya ce.
"Ya kamata na shiga na gaida Mummyn Hilal, idan na tafi ban shiga ban kyauta ba."
"To ka shiga ka dawo mana."
"A'a tare da ke za mu je."
Da mamaki take kallonsa.
"Ni kuma wallahi Yaya bana son zuwa na ga take-taken mutanen gidan nan ba su da mutumci. "
"Eh ba da da shi amma dole sai mun je mun gaida mahaifiyar Hilal."
Tura baki ta yi kafin ta kalli Zahrah ta ce.
", Sister mu je ki raka ni."
Da sauri ta girgiza kai, don ta san matuƙa ta ke part ɗin Mummy sai ta gwammace dama ba ta shiga ba.
Don haka ta ƙaƙalo murmushi ta ta ce.
"Ku dai je ku dawo."
Zata sake wata magana dai Ammar ya ja hannunta suka nufi part ɗin Mummy, ba tare da ya ba ta damar sake magana ba .
Da idanu Zahra ta taka su tana murmushi.
Da sallama suka shiga kofar part ɗin.
Daddy, Mummy, Faisal, Maryam duk suna falon, amsa masu sallamar suka yi yayin da suka karaso ciki.
Cikin girmamawa suka gaida Dad da Mom. Suka amsa masu ba yabo ba fallasa. Faisal da Maryam ma suka gaishe su
"Dama har yanzu kuna gidan nan ne?"
"Eh Mummy wannan karon kun ga ban zo lokacin da Hilal kenan ba ko, wannan karon zuwan na Zahrah ne."
Amma tun wancan zuwa Laila ta baka shawarar cewa ka fita harkar Zahrah domin ƴar iska ce bin maza take yi ko?"
Shiru ya yi kafin ta cigaba da cewa.
"An fada maka bar cikin shege ta yi ta zubar shi ne ba za ka nemi yar mutunci ka aura ba sai ita ko? Idan ma ya zama dole a cikin wannan family na Tafarki kake neman aure ga ƴan mata nan muna da su da yawa sai wacce ka zaɓa, why not ka zaɓi ɗaya ka mance da Zahrah."
Ɗago idanu ya yi ya kalle ta kokarin ita ma shi take kallo ya ce.
"Mummy wallahi zuciyata Zahrah take so, bayan ita ban ga wata ƴa mace da ta kwanta Mani a rai ba, Mummy ana zuwa gidan ƙaruwai a auri mace jihadi ne domin an tairatar da ita daga halaka. Wallahi duk yadda Zahrah ta kai ga lalacewa ina son ta a haka , kuma in sha Allah kafin na bar garin nan zan tura a nema mani aurenta."
Sakin baki suka yi suna kallonsa, yayin da ya ce wa Humaira.
"Tashi mu tafi."
A tare da ita suka mike suna masu sallama ba wanda ya amsa sai Maryam.
Mamaki da al'ajabi ya hana Humaira da Ammar magana har suka karaso in da Zahrah take.
Ƙoƙarin daidaita kansu suka yi don kafa ta fahimci komai. Sai ma murmushi da suka yi mata lokaci guda.
"Kun fito?"
Ammar ya ce
"Eh mun fito, jibi xan dawo ni kadai don yau wannan yarinyar ta takura Mani, ba ta bari mun samu isasshen lokacin da za mu yi zance ba, ta cika ku da surutu."
Humaira ta yi saurin cewa
"Ai ko za ka dawo ba biyo ka zan yi ba, na zo na ga Zahrah, dama ai ni ka kawo na ganta . Idan ka sake dawowa Sai ku ci soyayyarku."
Umarnin ɗauko sakon da suka zo da ji ya ba Humaira. Ta karbi key ɗin motar ta fita don dauko sakon.
Manyan kedoji ne guda biyu shaƙe da kaya, ta ajiye tare da cewa
"Ga su."
Kallon Zahrah ya yi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 29 Chapter of 39