ce dole sai kun bayar da yaranku ba sai dai za mu baku adireshin wajen da za'a gudanar da karatun sai ku kawo su akan lokaci."
Takarda mai ɗauke da adireshin wajen ya ɗauko ya bawa Hilal sannan ya sanar da shi jibi da misalin karfe tara na safe za'a gudanar da karatun don haka idan son samu ne sai a kawo ta zuwa karfe takwas da rabi."
Amsar adireshin ya yi tare da yi masa sallama ya mike ya fice.
Da sauri Zahra ta bi bayansa yayin da Mallam Usman ya bi ta bayanta don yana son magana da ita.
Ko da ta ƙarasa har ya shiga motar yana jiran fitowarta. Har ta kai hannu za ta bude murfin motar sai ga Mallam Usman ya zo yana kiranta, hakan ya saka ta karaso wajensa tana jiran me zai ce.
"Mallama Zahrah bai dace na kebe ina magana dake a titi ba, amma zan zo neman izini wajen iyayenki, akan amincewar su na zo ko Allah zai sa mu fahimci juna don ina ƙaunarki fisabilillah."
Hilal ganin ta tsaya tana magana da wani yana zaune a mota yana jiranta, sai ya bawa direban damar ya tayar da motar su wuce su barta wajen.
Hakan ya saka direban ya figi motar suka bar wajen, don dama Hilal ya ga yadda Mallam Usman ke yi wa Zahrah kallon ƙurilla.
Ganin sun tafi ya saka hankalinta ya tashi.
"Ya Salam Ya tafi ya bar ni."
"Na ɗauka Yayanki ne."
"Eh Yayana ne."
"Me ya saka zai tafi ya barki?"
"Ban sani ba Akaramukallah."
"To yanzu ki yi gaggawa ki koma kada na jawo maki wata matsala, tun da kin ga ya yi fushi ya tafi, dama ba wata dogon magana ba ce zan nemi izinin ki ne kawai . Amma ko za ki shiga motata na kai ki gidan.?"
"Ka bari kawai zan samu abun hawa."
Sanin hakan zai iya janyo mata matsala duba da yadda Yayanta ya tafi ya barta ne ya saka shi ƙyale ta.
Karasawa ta yi zuwa bakin titin don neman abin hawa.
Tana tsaye a bakin titi wata mota ta tsaya a gaban ta, mamallakin motar ya fito yana mata magana ko kallonsa ba ta yi ba , har ya gaji ya tafi. Wani m ya tsaya shima bai samu fuska ba ya tafi. Ganin yadda ake kallonta ne ya saka ta yi nadamar fitowarta ba niƙab, don ko a school ma sai ta saka hijabi da niƙab.
Tana tsaya ne don ba ta san ma yadda za ta tsayar da abun hawa ba. Wata motar ce ta tsaya kallon motar ta yi sosai ta tabbatar motar Mansur ne cos mate ɗin ta ne da suka karatu a University tare, wanda ya suka zo suka kai ta asibiti shi da A'isha.
Yana zuge Glass din motar suka hada idanu, sanyayyar murmushinsa ya sakar mata,ita ma murmushi ta yi tare da karasawa wajan motar, murfin motar ta bude ta shiga.
"Aminiya ya na ganki akan titi ke ɗaya ina motarki take?"
"Hmm ba komai Aminin ƙwarai."
Kasancewar su uku haka suke kiran junansu, daga Zahra har A'isha Aminiya yake kiransu su ma suna kiransa da Amini."
Haka ya dinga jan ta da fira ita dai ba ta iya amswa masa ba, daga uhm dai um um.
A ƙofar katafaren gidan na su ya yi parking daidai lokacin da Hilal ke fitowa daga gidan waya na kare a kunnensa.
Cire wayar ya yi daga kunnensa tare da ƙarasawa wurin motar kasancewar glas ɗin motar bakin Glass ne na waje baya hangen na ciki.
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
[11/2, 7:56 PM] My Uwar Ɗaki: Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.NT
(Maman Ihsan)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
*Eid Mubarak to you my fans, Allah ya maimaita mana da alkhairi*
Page1️⃣6️⃣
Cire wayar ya yi daga kunnensa tare da ƙarasawa wurin motar, kasancewar glass ɗin motar baƙin glass ne na waje baya hangen na ciki.
Knocking ɗin glass ɗin motar ya yi. A hankali Zahra ta kalle shi tare da cewa.
"Amini bari na fita ka bar wajen nan da sauri."
Kallon ta ya yi tare da cewa.
" To laifin me na yi da zan bar wajen da sauri?"
A hankali ya zuge glass ɗin motar tare da kallon Hilal. Wani banzan kallo Hulal ya yi masa sannan ya maida kallonsa kan Fatima Zahrah wacce ta sunkuyar da kai. Ɗagowa ta yi ta kalle shi sai da gabanta ya faɗi, ganin irin kallon da yake jifanta da shi. Ya tabbata ba wancan malamin da ya bar su tare ba ne, wannan kuma daban ne, wato ita kowa take kulawa kenan.
"Ke fito ki shiga gida!"
Jinkinta na rawa ta fito daga motar ta tsaya tana kallon Amini.
"Kai ja motarka ka tafi kada na sake ganinka a ƙofar gidan nan."
Wani kallo Amini ya masa yana don ya tanka masa sai Zahra ta yi magana a hankali yadda Amini ne kawai zai ji.
"Don Allah ka tafi mutumin nan fa ɗan yawa ne zai iya tarfa ka a wajen nan"
Ta yi maganar cikin sigar rarrashi. Don haka ya ja motar ya bar Wajen.
"Zo nan!"
Ya faɗa ransa a ɓace yana kallon Zahrah, sanin abinda da abun da zai biyo baya ba zai masa dad'i ba ya sa ta ruga cikin gidan a guje.
Rufa mata baya ya yi shi ma ya koma ciki.
Kamar daga sama suka ha an jeho ta. Gabaɗaya suna zaune a falon iyaye da ƴaƴansu.
Gabaɗaya suka juyo suna kallonta, sallama ta yi masu ba wanda ya amsa a cikinsu, sai Abba da Dady su ma ciki-ciki suka amsa mata sallamar.
Jin yadda ya banko ƙofar ya shigo ne ya saka ta juyawa da sauri ta nufi part ɗin su.
Rufa mata baya yayi da sauri abu ga dogon mutum tana ƙoƙarin rufe ƙofar ya banko ƙofar da ƙarfi wanda hakan ya saka ta yi baya ta faɗi.
Wuyan hijabinta ya cakumo ta miƙar da ita tsaye. A fusace ya fara magana cikin kakkausar murya.
"Gabaɗaya ke ce kika fita zakka a cikin gidan nan, na tsani macen da ke kuka kowane kare da jaki, kin taɓa ganin wani namiji ya zo ajiye wata a cikin gidan nan? Wato sai ke ko? To bari ki ji ba wai na damu da ke ba ne ko ina da matsala da ke ba, babu ruwana dake matsalata ɗaya shi ne zubar da kimar ahalinmu.Don da zaran kin aikata wani abun da zai zubar da Mutuncin zuri'armu. Dama Abin da Aunty Laila take faɗa aka ki gaskiya ne yau na gani da idona. Sai dai zan maki gargaɗi duk sakaran da kika gayyato zuwa gidan nan ni na san abin da zan masa. Duk shashancin da za ku yi ku yi shi a waje amma ba gidan nan ba. Idan kuma ba haka ba ko?"
Kwafa ya yi tare da barin ɗakin bayan ya sakar mata wuyan hijabi. Yana komawa falo ya same su zaune kamar yadda ya bar su. Aunty Laila ce kawai a tsaye, tana ganinsa ta ce.
"Son meye haɗinka da wanan yarinyar ne?"
Ciwon kai ya fara ji saboda dogon maganar da ya yi saboda shi baya so ya yi magana mai tsayi. Don haka bai ce mata komai ba ya nufi upstairs.
Jin mahaifinsa na magana yana sake tambayarsa ne ya sa ya ce.
"Dama na ga da muka tafi can lokacin da za mu dawo ta tsaya da wani saurayi. Na taho na bar su a wajen. Yanzu kuma wani daban ne ya kawo ta ba wancan ba."
"Dama na fada maka yarinyar nan bin maza take yi, ai yau ka gane wa idanunka ai, yarinyar nan har cikin shege ta yi ita da munafukar uwarta suka zubar."
Umma mahaifiyarsa ce ta faɗi haka, Cikin takaici ya ce.
"Dole na ɗauki mataki akanta kafin ta zubar mana ƙimar gidan nan, don koma mene ne sai dai a ce ɗaya daga cikin familyn Muhammad Tafarki."
Yana gama fadar haka ya haura sama har yana tsallake steps.
Ɓangaren Zahra kuwa tun da ya shaƙe wuyar hijabin dake jikinta ta fara jin numfashinta na barazanar ɗauke wa. Haka ta fara komawa da mumfanin nata wanda yake jin ba ta da wata hanyar shaƙar iska. Ko da ya gama faɗarsa ya fice duk ciwon nata ya fara tashi.
Madadin ta tashi ta nemi maganinta sai ta zauna tana ta riskar kuka duk da yadda take numfashi daƙyar. Don kalaman sa sun yi mata ciwo. Tana tunanin me Aunty Laila ta fada masa akanta ne ya har yake cewa gaskiya Sunyi Laila take faɗa.
Yana haurawa sama direct ɗakinsa ya nufa, yana shiga ya fara cire rigarsa, ya saura daga shi sai singileti da dogon wandon dake jikinsa .
Wayarsa ta soma ruri ya duba ya gani Papa ya sa ya ɗaga tare da yi masa sallama. Muryar tsohon ya ji yana cewa ya sanar da Zahrah sammako za su yi sannan ya kira wayar Zahrah ya ji kamar ciwonta ya tashi.
Bayan ya katse wayar gajeren tsaki ya yi cike da takaicin yarinyar ya sauko ƙasa.
_Asadullah_
Kwance yake a saman katifar dake ɗakin, tun yana kan kafa har ya fado ƙasa, dafe kansa da yake jin kamar zai fashe. Wani sauti yake fitarwa mai kama da gurnani.
Doctor dake tsaye a kansa ne ya ciro wayarsa a Aljihu tare da lalubo wata lamba. Kira ya dannawa lambar nan da nan aka ɗaga.
Cikin wace irin murya mai kama da rauni ya fara magana.
"Na gama maku aikinku don Allah ku sake mani ƴaƴanta."
Ta cikin wayar ya ji Muryarta tana cewa .
"Gaggawar ne kake yi ai aikinka bai ƙare ba."
"B haka muka yi da ke ba kun saka ni aiki kuma na yi maku me kuke buƙata kuma, amma kin san ba haka muka yi da ku ba?....Wallahi ba za ku ga annabin rahama ba, mutumin da ya yarda da ni yake kyautata mani iyalai na, har yanzu wannan aikin da nake yi ina cin alfarmarsa, wanda bai cancanci haka daga gare ni ba, amma saboda son zuciya da kwaɗayin abun duniya kuna neman kashe shi. Sai dai shi idan ba ku sani ba kainuwa dashen Allah ne shi ba na mutum ba. Don da wani ne yadda kika dinga sakawa ana yi masa waɗan nan alluran da tuni ya bar duniya amma shi har yanzu yana a raye."
Tsawar da ya ji wani ya daka masa ta cikin wayar ya saka shi yin shiru.
"Za ka yi aikin da aka saka ne ko kuma sauratan banza? Kar ka manta ƴaƴanka suna hannunmu ba za mu sake su ba har sai ka kammala mana aikin mu. Idan kuma ka ɗauki lokaci mai tsayi to za mu tiro maka da gawar ɗaya daga cikinsu. Ya rage saura ɗaya wannan gargaɗi ne."
Muryar macen ya ji tana cewa.
"Kada ka bamu matsala fa ba wai mun ɗauke ka aiki ba ne saboda matsala, mun ɗauke ka ne saboda muna neman mafita. Don kai kaɗai ne likitan iyalin dake cikin Asadullah Mantson. Idan aka wani yana shige da fice waɗan nan security za su tsaurara bincike ne, amma kau ba wanda zai damu saboda sun san kai ne mai duba marasa lafiyar, za su yi zaton rashin lafiyar ɗaya daga cikin ahalin ne ya saka kake zuwa. Don haka ka iya takunka."
Ana faɗin haka aka katse kira wayar, kallon Asadullah ya yi cikin rauni ya ce.
"Ka gafarce ni yallaɓai, ƴaƴana guda biyu da Allah ya bani suka kama, saboda sun san cewa suke rauni na. Ba yadda zan yi ina son ƴaƴana."
Yana gama faɗar haka ya harhaɗa kayansa ya fito daga ɓangaren idanunsa cike da ƙwalla.
Kiciɓis suka ji da amintaccen bodyguard ɗin Asadullah wato Sulaiman, kallon Dr ɗin ya yi ganin daga in da ya fito ga shi yana zubar da ƙwalla.
"Hey Doctor daga ina, me kake yi a wancan ɓangaren?"
_Hilal_
Yana saukowa downstairs suka zuba masa idanu daga shi sai farar singileti da dogon wando baƙi. Singileti ya fitar da surar jikinsa na ƙaƙƙarfan namiji jarumi. Kallo ɗaya za ka masa ka san cewa yana yawan motsa jiki bisa la'akari da yadda ƙwanjinsa suka bayyana a fili.
Kausar ta saki murmushi tare da maganar zuci .
'Allah ya nuna mani ranar da za ka zama mallakina ni ma na zama taka.'
Nabeela kam cewa ta yi a zuciyarta
' Yaya Hilal har yanzu ba ka amince da bukatata ba, ko ba ka aure ni ba so nake mu ɗumin juna.'
Kai tsaye part ɗin su Zahra ya nufa, bakinsa ɗauke da sallama.
Gabaɗaya ahalin dake falon suka bishi da kallon mamaki ganin in da ya koma.
Dady da Abba ne suka mara masa baya sannan su Aunty Laila da Mummy da Umma suka bi bayansu. Haka yaran ma suka tashi maza da mata.
Yana shiga ɗakin ya tarar da tana kokawa da numfashinta.
Kai tsaye ya nufi in da ya ɗauki maganin ranar da ya saka ta punishment ciwonta ya tashi.
Yana duba wa ba komai a ciki haka ya hau duba maganin ko ina ya birkice ɗakin bai ga magungunan ta ba.
Cikin kufula Umma ta ce.
"Me kake ƙoƙarin yi ne?"
"Maganinta nake nema baya nan."
"Wai me ya sa duk cikin ƴaƴan da na haifa kai kaɗai ne ban isa da kai ba, ina ruwanka da maganinta ko halin da take cikin, shin kana da alaƙa da yarinyar nan ne ?"
"Umma ba wata alaƙa ko wani abu a tsakanina da yarinyar nan, hasalima na tsane ta, wannan ƙoƙarin ceton rai ne. Wanda ko da ba ita ba ko wani ne na hadu da shi a hanya yana cikin halin da take ciki sai na taimaka masa ko da ban san shi ba zan ceci rayuwarsa wanann shi ne."
Cikin takaici Aunty Laila ta kalli Abba ta ce.
"Kana ganin yaronka na shirin ba mu matsala ko, ka faɗa masa ya fita daga harkar yarinyar nan idan ba haka wallahi sai ga abinda zai biyo baya."
"Aunty ba na shiga harkarta yanzu ma Papa ya turo ni wajenta akan ciwonta ya tashi kuma na fada maki ba don ita ba ko maƙiyina ba na masa fatan ya tsinci kansa a cikin mawuyacin hali, aikin ceton rayuwaka da dukiyarsu nake yi rashin imanin nawa ba kai da zan iya ganin ɗan Adam w cikin mawuyacin hali na ciwo na yi fatali da shi ba saboda wata aƙida, ku saka wa ranku ba ita na ce ta ba rai na ceta ko na waye kuwa ."
Abban ya ce.
"Hilal mu ne marasa imani kake nufi ko meye?"
"Ban faɗa ba Abba ka yi hakuri ba nufina kenan ba, ku saka a ranku ban ceci yarinyar nan ba rayuwa na ceta wacce ko a ina ne ko ban san mutum ba haka zan yi."
Cikin ɓacin rai Umma ta ce.
"Hilal ka fita ka bar ɗakin nan yanzun nan."
"Zan fita Ummana amma sai na kammala abun da ya kawo ni, matukar na sa gaba a bi ba na dakata wa har sai na kai ga ci."
Bai saurare su ba ya cigaba da neman maganin ba su yi mamaki ba don sun san halinsa in dai akan gaskiyarsa ne ba zai taɓa sauraren kowa."
Kausar ce ta yi magana ƙasa-ƙasa tana cewa.
"Ka gama wahalarka ba na kwashe magungunan na fita da su, kafin ka kai ta asibiti Allah ya sa ta mutu."
Ba wanda ya ji ta sai shi a fusace ya kalle ta nada sai da hanjin cikinta ya ƙaɗa. Ya nufe ta tare da cewa.
"Ki yi sauri ki kawo mani su duk in da kika kai su."
"Yaa Hilal me zan baka ni fa ban san komai ba."
Ganin za ta raina masa hankali ya sa shi cewa
"Kada ki bari na sake maki tambaya a karo na biyu, ina suke na ce."
Ganin ta masa banza ya saka ya shaƙo wuyarta tare da cewa .
"Za ki fada ko sai na kashe ki kafin ita ta mutu ki riga ta mutuwa?"
Idanunta suka firfito nan da na Yaa Mansur da Yaa Faisal suka fara ƙoƙarin kwatarta, amma ina sun kasa cire hannunsa daga wuyanta . Aunty Laila sai kuka take yi tana cewa zai kashe mata yarinya.
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
[11/2, 7:56 PM] My Uwar Ɗaki: Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
Page1️⃣7️⃣
Idanuwanta suka firfito nan da nan Yaa Mansur da Yaa Faisal suka fara ƙoƙarin kwatarta, amma ina sun kasa cire hannunsa daga wuyanta. Aunty Laila sai kuka take yi tana cewa zai kashe mata yarinya.
Nan da nan Abba ya ƙarasa yana kiran sunansa shi da Abba, su ma sun kasa cire hannunsa daga wuyanta.
"Za ki faɗa ko ba za ki fada ba kin fi son mutuwa.?"
Dukansa Aunty Laila take yi tana kuka amma kamar dutse take duka.
Kausar jin ta kusa mutuwa ne kuka ba ta ga alamar zai sake ta ba ne ya sa ta ɗaga masa kai da muryarta da baya fita ta ce.
"Zan faɗa"
Jin haka ya sa ya sake ta tare da fuszar da iska mai zafi ta bakinsa.
Aunty Laila ta rungume ta tana kuka yayin da Kausar ɗin ma ta kasa kuka. Don tashin hankali idan ya yi yawa ma ba ka samun damar yin kuka.
Sai wuyar ta da ta rike take tari.
"Ina suke!?"
Ya faɗa a fusace yana kallonta.
"Yana ɗakinmu a ƙarƙashin gado."
Kallon Nabeela ya yi tare da cewa.
"Ki yi sauri ki kawo Mani."
Ba ta da wani zaɓi dole ta tafi duk da ba da son ranta ba ne, amma tun da tana son shige masa dole sai ta bi yadda yake so.
Ba jimawa sai ga ta ta dawo da jakkar magungunan. Miƙa masa ta yi ya karba tare da juye su kan gadon.
Kallon Zahra ya yi dake kwance kamar gawa, sannan ya mai da dubansa kan magungunan, sanin cewa alluran zai fi mata aiki a yanzu ne ya saka ya ɗauki alluran da sirinjin. Dubawa ya yi ya karanta sannan ya yi mata alluran.
Bayan ruwan alluran sun bi jijiyoyin jikinta ne ta ja numfashi da karfi . A hankali ta buɗe Idanunta tare da sauke su akan fuskarsa dake ɗaure tamau.
Sai ta fara bin su ɗaya bayan ɗaya da kallo, tana mamakin yadda gabaɗaya ilahirin gidan suka cika mata ɗaki. Ta dai san alkhairi ba zai kawo su wajenta ba. Tun da ba ƙaunarta suke yi ba. Hatta idanunsu duk ya nuna hakan bisa la'akari da irin kallon tsanar da suke jifanta da shi.
Abba ne ya fara fita sai Dady, daga nan Umma da Mummy suka fita. Daga nan sai Yaa Mansur da Yaa Faisal, Nadiya da Maryam ma suka fita, ya saura sai Aunty Laila da yaranta.
Aunty Laila kwafa ta yi tare da hannun Kausar suka fice. Nabeela ta rage ta tsaya ganin abinda zai tura wa buzu naɗi.
Zuciyoyin kowa na gidan cike da takaicin Hilal, sai dai ba yadda suka iya da shi. Sun so a ce baya nan hakan ta kasance don damar da suka faɗe suna jira kenan. So suke ta bar duniyar gabaɗaya, don sun san hakan zai dasa baƙin ciki a zuciyar Salis da Matarsa. So suke ya ɗandani bakin cikin fiye da wanda ya yi sanadiyyar saka su a baya. Wanda tun tasowar ɗan uwan nasu ba su taba ganin ya kwashi bakin ciki ba a rayuwarsa sai farin ciki. Amma idan ya ji labarin mutuwar ƴarsa mace tilo da suka fi ƙauna shi da matarsa da iyayensu dole duk za su kwashi bakin ciki.
A falo suka hadu dukkansu cikin takaici Aunty Laila ta ce.
"Kan waccan banzar yarinyar ne yake kokarin kashe Mani ƴa ko?"
Abba ya kalle ta tare da cewa.
Kuyi hakuri Laila."
"Haba Yaya wani haƙuri kawai abin da zai fi dauki ka yi gaggawar cewa ya koma can U.S a bakin aikinsa. Don wani sati mahajjata za su dawo, idan iyayen yarinyar nan fa su Papa suka dawo ba halin shirin mu ya tabbata."
Umma ta cikin takaici ta ce.
"Ba abinda ke ɓata mani rai da Hilal kamar taurin kansa sam baya tanƙwasuwa, idan ya kafe ya kafe kenan ba mai saka shi ba mai hana shi. Ina ga idan ya ƙure ni akan waɗan nan mutanen dai na gifta kalmar tsinuwa sannan zai dawo cikin hankalinsa."
"Kul!"
Abba ya dafa yana kallonta.
"Abban Hilal ba ka ganin yadda muna hana shi abu baya hanuwa?"
"Yana hanuwa mana, duk muka bashi umarni baya taba tsallake wa, sai dai na lura da shi in dai akan gaskiyarsa ne baya mana biyayya, matuƙar ya san cewa shi ne mai gaskiya to fa baya sauraren kowa."
Cikin takaici Umma ta sake cewa
"To zan nuna masa mu ne muka haife shi ba shi ya haife mu ba."
Aunty Laila ta ce.
"Ina ga ayi masa aure kawai shi ne mafita, ya ɗauki matarsa su tafi can U.S sai idan sun zo mana ziyara. Don haka ha ƴan uwansa nan ya zabi daya daga ciki, idan bai zaba na mu za mu zaba masa da kanmu."
Jinjina kai Abba ya yi cike da gamsuwa. Dady ya ɗaura da cewa.
"Ƙwarai kuwa a cikin Nadiya, Kausar da Nabeela cikin su uku ba zai rasa wacce yake so ba."
Aunty Laila ba ta so ya hada da ƴarsa Nadiya a ciki ba, taso cikin ƴaƴanta biyu don haka ta ce.
"Ai Kausar da Nabeela suna son sa ne ita Nadiya ta ce tana sonsa ne?"
Kowa ya kalle ta dake ba kunya ce da ita ba ta ce.
"To wace mace ne za ta kalli cikakken namiji irin ya Hilal ta ce ba ta so, wallahi ina son sa ."
Maryam sai taka ƙafarta take don ta yi shiru amma ko a jinkinta .
Abban Hilal ya ce .
"Shi kenan, za mu bashi zaɓi cikin su uku , idan ya ki haƙiƙa za mu sura masa duk wacce muka ga dama."
Daga haka suka watse kowa ya yi part ɗin ta sai Aunty Laila da ta zauna zaman jiran fitowar Hilal.
A can cikin ɗakin kuwa bayan ta dawo daidai ne ta yunƙura da niyyar tashi amma ta kasa.koma ta yi ƙasa ta kwanta.
Sanin sanyin tile zai iya kawo barazana ga lafiyarta ya saka shi ɗaukar ta cak ya ɗaura a saman gadon. Sannan ya kalli Nabeela ya ce.
"Ke kuma fa akwai abinda kike jira ne?"
Taɓe baki ta yi tare da cewa.
Magana nake so mu yi da kai."
Kallonta ya yi na sakan sakan uku ya ce.
"Ina jin ki."
"Sirri ne."
Jin haka ya sa ya juya dan ficewa daga ɗakin. Cikin sanyin murya irin nata ta ce.
"Na gode da ceton rayuwata da ka yi, Allah ya saka maka da gidan Aljanna."
Bai amsa ba sai ce mara ya yi
"Ki shirya ƙarfe bakwai na safe za mu tafi.
Da mamaki Nabeela ta lalle shi tana cewa.
"Ina za ku je tare?"
Fita daga ɗakin ya yi ba tare da ya ce mata komai ba.
Haka ta dinga binsa a baya har ya haura upstairs, ya shiga falonsa ta bishi, yana ƙoƙarin shiga bedroom tana ƙoƙarin binsa.
Dakata wa ya yi ba tare da ya juyo ba ya ce.
"Lafiya?"
"Magana da nake so mu yi da kai."
"Ina jinki."
"Ina za ku tafi da waccan yarinyar ne?"
"Wata yarinya?"
Sai da ta yamutse fuska sannan ta ce.
"Zahrah "
"Kaduna"
Ya bata amsa sannan ya saka hannu a handle ɗin ƙofar zai shiga.
"Yaa Hilal me za ku je yi da ita?"
Bai ba ta amsa ba ya yi shigewarsa ciki, kai tsaye ita ma ta kutsa kai ta shiga bedroom ɗin nasa.
Singileti dake jikinsa yake ƙoƙarin cirewa ganinta ya saka shi dakata wa tare da ɗauke fuska tamau.
"Ke meye kuma?"
"Maganar da zan maka ne ai ban yi ba ka shigo ɗaki."
"Ina jinki."
Juya baya ta yi yadda ba za ta kalli idanunsa ba ta ce .
"Ya Hilal ina son ka don Allah ka aure ni, na maka alkawarin kasancewa duk yadda kake so."
Ransa a ɓace ya juyo yana kallonta.
"Ke!"
Sai da ta firgita da ganin yanayinsa.
"Sa'anki ne ni?"
Sunkuyar da kai ta yi ta kasa hada idanun da shi, saboda tsoron da idanusa suka bata. Cikin ɓacin rai ya sake cewa.
"Duk san da kika dake tara ta wannan maganar sai na karairaya ki."
Ƙofar fita ya nuna mata da fice a guje tana kuka.
Washegari tun da Fatima Zahra ta yi sallar asuba ta yi azkar da karatun Alqur'ani, ta gyara gyara ko ina a ɗakin duk in da ya dace sannan ta yi wanka.
Riga da siket ta saka na leshi, kalar purple an yi masa ado da kalar zare pich colar ɗinkin sun ɗan kama ta amma
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 39