shigo gidan, ta window Umma ta leka, ganin Mahmud da Sadik ta ce.
"Ga su nan sun zo gaida uwarsu."
Kallo ɗaya suka yi wa Mahmud suka gane yana cikin tashin hankali. Sunyi Laila ta saki uwar dariya tana sawa Nabeela albarka.
Sadik ne ba za ka iya karantar yanayinsa ba tashin hankali ko akasin haka, don cikin farin ciki yake ganin halin da ɗan uwansa yake ciki ya gurguntar da farin cikin da ya tsinci kansa a ciki.
"Zan je na duba Nadeeya don ga tashin hankali a tattare da wanna mai taurin kai da zuciyar ba."
Part ɗin Dada suka je suka gaishe da Papa da Dada, in da suke kara masu nasiha da sanya albarka sannan suka nufi part ɗin Umminsu.
Hankalin ta ya tashi ganin Mahmud a firgice, ya sa Ummi ƙwalla ya cika idanunta, sai ta dauke da sauri. Don ta san halin Mahmud da Sadik ne ba za ta damu ba. Albarka ta sanya masu suka shiga sauka gaida Abbi suka tafi.
_Zahrah_
Tun bayan da Hilal ya ja mata bargo ya ya tafi yake kuka. Duk da ba ta san dalilin da ya saka ya bar ta yana mata kallon mamaki ba, ta lura jikinsa ya yi sanyi ya yi mata kallon da bai taɓa yi mata ba a rayuwarsa.
Lallaɓawa ta yi tana bin bango ta rufe kofar ta da sakata. Tana kukan abubuwa da ya yi mata. Goge bakinta ta yi tuna yadda ya dinga tsotsan bakin ta kamar ya samu sweet.
Bathroom ta shiga da jin bango ta dauki brush da toothpaste ta dinga wanke bakib tana tofar da miyau cike da ƙyankyami.
*Saura page ɗaya na kammala book 1 wacce ta shirya siyen Book 2 zata tura kuɗinta ta wannan account number 2242538358 Zainab Abdullahi UBA bank sai a tura shaidar biya ta wannan lambar 09065327995*
[11/2, 7:57 PM] My Uwar Ɗaki: Follow the TASKAR MAMAN IHSAN channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaiufWb3LdQYnzC2vH0z
*GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan ce)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
Page7️⃣0️⃣
*LAST FREE PAGE*
Bathroom ta shiga da bin bango, ta ɗauki ta ɗauki brush da toothpaste ta dinga wanke ta dinga wanke baki tana tofar da miyau cike da ƙyanƙyami.
Sau uku tana saka toothpaste tana wanke baki kamar za ta canza haƙoranta da harshe take ji.
Wanka ta yi da ruwa mai ɗumi sannan ta fito ɗaure da towel, wankan da ta yi sai ta ji jikinta ya ɗan yi mata ƙarfi. Sai dai har lokacin yunwa na ɗawainiya da ita jin ta take yi tamkar fanko.
Riga da wando na barci ta saka farare, wandon da kadan ya wuce guiwarta, ji ta yi ba za ta iya yin barci ba yadda yake jin yunwa don duk yai sau daya ta ɗan sha ruwan tea kaɗan, ga yanzu dare ya yi bata san ya za ta yi ba.
Hawaye ne ke bin fuskarta ta Kudundune ta cire wuri ɗaya hannayenta a cikinta wanda take ji har ciwo yake yi mata.
_Hilal_
Sai faman Safa da marwa yake yi a cikin ɗakinsa. Ransa a ɓaci idanunsa sun sauya launi zuwa ja kamar zai su fitar wuta.
Yana tuna yadda mahaifiyar sa da ƙanwar mahaifinsa ke ta aibata Zahrah da zancen lalata da cikin da aka ce tana zubarwa. Ƙarin abunda ya saka ya yarda da cewa maganarsu gaskiya ce ranar da ya ganta kwance cikin jini ya kai ta asibiti likita ya sanar masa da zubar da ciki ta yi. Ga shi kuma Family Doctor na su ne wanda suka yarda suka saba da shi tsawon lokaci. Sannan ga shi ya tabbatar da cewa yarinyar cikakkiyar budurwa ce. Shin me ya saka suka yi mata haka sun saka ya tuna Abba, Ummi, Mahmud, Sadik, Zahrah. Yadda ake nuna masu wariya a cikin gidan, kullum sai nufar su da sharri ake yi wanda su kuma har yau bai ga wani aibu ko mugun balin da aka ƙakaba masu ba. Cikin ƙaraji ya ce.
"Meye dalilin da za ku yi wa ƴar mutane shaidar zina? Mummy, Aunty Laila da Doctor dole za ku amsa mani tambayoyin da zan yi maku, tabbas ba na jin zan iya saurara wa kowa. Musamman yadda na cutar da ƴar mutane ba tare da hakkinta ba."
Ya tuna ranar da ya kai ta asibiti aka ce ciki ta zubar ya tuna maruka da dukan da ya yi mata akan laifin da ba ta aikata ba. Da sauran abubuwan da ya yi mata cikin takaicin halin ta yana mata kallon kura lulluɓe da fatar akuya."
Ƙofar fita ya nufa don ya ga halin da take ciki
Zuwan lokacin karfe biyun dare ya yi. Tana nan tana tausayin sabuwar rayuwar da ta tsinci kanta sai ta ji ƙamshin turarensa.
Cikin faduwar gaba da firgici ta kalli ƙofar sakamakon jin ƙamshin turarensa.
Tsaye yake jikin bango yana sanye da wando 3-quater da farin singileti ƙirarsa na ƙaƙƙarfan namiji ne bayyane a jikinsa saboda yawan motsa jikin da yake yi. Hannunsa ɗaya a cikin aljihunsa ɗayan kuma yana rike da handle ɗin kofar. Ya zuba mata rikitattun idanunsa.
Gabanta ne ya faɗi ta kara matsawa can ƙarshen ta ƙara Kudundune jikinta, gani take yi kamar zai yi mata wani abun.
A hankali ya ƙaraso bakin gadon, fuskarsa babu walwala.
"Are you okay?"
Banza ta yi masa kamar ba ta ji shi ba, kallo mata ya yi na mintuna biyu kafin ta ɗauke idanunsa ya ce.
"Meke damunki."
"Ni wajen Ummina za ka mayar da ni, ba na son auren."
"Auren ne ba ki so ko kuma ni ne ba ki so?"
Shiru ta yi ba ta ce komai ba.
"Talk to me, ni ne ba ki so auren ne baki so?"
"Ba na son ka."
Shiru ya yi tare da cije lips ɗin sa na ƙasa. Kafin ya yi wata magana ne ya ji tana cewa.
"Don Allah ka sake ni ba zan iya zama da kai ba."
Bai yi mamaki don ta ce ba ta son sa ba, saboda shi ya gina mata tsanarsa a cikin zuciyarta, sai dai bai taba tunananin za ta bijire wa auren ba.
"To yanzu wa kike so."
Ba tare de jin shakkar sa ba ta ce "Yaa Ammar."
Sai da rintse ido ya buɗe sannan ya ce.
"Okay ki daina kuka."
"Don Allah ka taimaka ka sake ni, wallahi yanzu ni kadai na san me nake ji a cikin zuciyata, matukar na ci gaba da zama da kai tabbas sai an ɗauki gawata a cikin gidan nan."
"Me za ki ce wa su Papa dangane da mutuwar auren idan kika koma gidan.?"
"Zan fada masu ni ce na nemi ka sauwake Mani."
Yana tunani ta ina zai fara sai ya ji tana cewa.
"Ka yi Mani alkawarin za ka sake ni."
Kai kawai ya jinjina ya fita daga ɗakin. Ba jimawa sai ga shi ya dawo da cup ɗin tea da biscuit a hannunsa.
Mika mata tea ɗin ya yi Wanda ya haɗa mata shi da kauri.
Kauda kanta ta yi don ko kallonsa ba ta son yi, tsuke fuska ya yi cikin dakiya ya ce.
"Za ki karba ko sai na baki da kaina?"
Kallonsa ta yi ta ga ya koma mata asalin Hilal ɗin da ta sani. Kamar ba yanzu shi ne yake yi mata magana cikin taushi ba.
Ganin kallon da ya yi mata ne ya saka ta ɗauke idanunta da sauri ta karɓa tana maganar zuci."
'Mai hali ba zai taɓa canzawa ba, duk macen da ta zauna da shi za ta sha wahala, a haka Aunty Bilkisu ke cewa sai yadda na yi da shi?'
A hankali take tauna biscuit ɗin tana shan ruwan tea ɗin. Kallonta yake yi har lokacin fuskarsa a tsuke, ta ci rabin biscuit ɗin ta shanye ruwan shayin ta ce masa ta ƙoshi.
Karba ya yi ya fita daga cikin ɗakin da cup ɗin a hannunsa.
Sai a lokacin ta ji yunwar da take ji ta ragu da kashi hamsin ta fara jin daidai. Hamdala ta yi tana mamakin yadda ya hado mata tea ya kawo duk jin kai da isar sa.
Dawowa ya yi ya kalle ta ya ce.
"Akwai abinda kike bukata ne kuma yanzu?"
"Takardar sakin da na roke ka nake so zuwa safiya sai na tafi."
Shiru ya yi yana kallon ta kafin ya ce.
"Zan baki tun da haka kike bukata ki bani nan fa zuwa jibi idan na kammala abinda na saka a gaba."
"Ton na gode."
Bai ce komai ba ya ja mata kofar bayan ya kashe switch ɗin ɗakin.
_Asadullah_
Zaune yake a falo shi da Jidderh da Mallamin dake mata addu'o'i. Ruwan zamzam da ya tafa addu'a a ciki take sha .
Tun da aka fara yi mata magani ba ta da abun yi sai barci. Kowane lokaci cikin barci take, da Asad ya yi wa Mallamin complain na yawan baecin ya ce ya ba damuwa alamar nasara ce. Anisa na zaune a gefen kallinsu kawai take yi, ganin yadda Asad ke bata magani da kansa tun da Mallamin ya zo shi je yi mata komai. Wankan ne kawai yake bari Anisa ke yi mata shi ma sai ya tabbatar an yi mata da sabulun da Mallam ya bayar.
Mallam ya tashi tafiya Asad ya mike zai raka shi zuwa wajen mashin ɗin sa dake waje. Da
Bayan ya raka shi ne Isa wajan mashin ɗin sa ya hau mashin ɗin ya tafi. Har lokacin Facemask ne a fuskar Asad wanda idan ba ka yi masa farin sani ba to ba za ka gane shi ne ba
Tashin mashin ɗin kenan yana barin wajen Asad ya juya da niyyar komawa cikin gidan. Da sauri ya durƙusa don kare kansa.
Ta jikin gate ɗin gidan ya kalli wanda ke bayan da rike da wani karfe zai buga masa a kai.
Sake yunkurin buga masa ya yi a karo na biyu, nan ma ya kauce daga nan suka fara kokawa da shi, sosai suke kokawa da juna.
Cikin ikon Allah Asad ya kayar da mutumin ƙasa yana ƙoƙarin cire cire masa abinda ya rufe fuska da shi indanusa kawai ake gani.
Suna tsaka da kokowa sai motar Sulaiman ta karaso wajen, a lokacin mutumin ya samu wani karfi har ya iya ƙwayar kansa daga hannun Asad ya ruga a guje kafin Sulaiman ya karaso wajen.
Bin bayansa ya yi suna gudu kafin ya cin masa ya ga ya hau bayan wani mai mashin da alama jirsnsa yake yi.
A guje suka bar wajen Sulaiman ya dumƙule hannu ya naushi iska.
Dawowa ya yi ya samu uban gidansa tsaye kamar wanda aka dasa a wajen.
"Sir."
Sai a lokacin ya ɗago ya kalli Sulaiman ba tare da ya ce komai ba.
"Are you okay?"
Kai kawai ya jinjina sannan ya yi magana cikin kamilalliyar muryarsa mai cike da nutsuwa ya ce.
"Am okay"
Cikin gidan suka shiga in da suka yada zango a falo. Jidderh ce kawai ke barci a falon kan kujerar mai zaman mutum uku.
Asad ya zauna har lokacin ya sa magana a abubuwa sun yi masa. Indanusa sun yi ja ya dafe kansa da hannayensa biyu.
"Me ya faru ne har hakan ta faru?"
"Mallam dake wa Jidderh magani ne ya zo sai na raka shi iya ka ta bakin gate ɗin.
Yana hawa mashin na juyo zan dawo sai na hangi mutum ta jikin glass ɗin, da ba don Allah ne ya kare ni ba dan Allah ya kare ni wannan karfe bai daki kai na ba da yanzu sai dai wani labarin ake yi."
"Sir, shi ya na ce ka yi tunani cikin mutane ukun da suka san inda kake tabbas ko ma waye yana daya daga cikin masu son ganin bayanka. Amma kai ka yarda da kowa, kuka a wannan yanayin da ake ciki bai kamata a ce kana saurin yarda da kowa ba, domin wani lokacin wanda ka yarda shi ko ba ka yi zato ba sai a wayi gari ya cuce ka
Tashi ya yi ya nufi upstairs Yana cewa.
"Ka tafi ina son kadaici z ka iya dawowa gobe."
Yana fadar haka ya haura sama.
_Hilal_
Fitowar sa daga wanka kenan yana goge jikinsa wayarsa ta yi ruri, yana dubawa ya ga Jamilu ne mijin Sumayyaa da suka sauka a gidansa shi da Zahrah.
Ɗagawa ya yi suka gaisa da shi.
"Ina Amarya ne wallahi ga Sumayya sai farin ciki take yi tun da na sanar da ita aurenka da Zahrah."
Bai ce komai ba in da Jamilu ya cigaba da cewa.
"Gaskiya na taya ka murna ka yi sa'ar mace tagari, ai ina ga yadda ta dame ni zuwa next week za mu shigo mu ga Amarya. Kafin nan tana son ta yi magana da ita."
"Ban sani ba ko ta tashi yanzu."
"Kamar ya kai kana ina?"
"Ina ɗakina."
"Ita kuma tana ina?"
"Tana ɗakinta."
"Man idan za ka ajiye girman kai da izzar da kake da shi ka ajiye, mata duniya ne."
"Ba sai kun yi wahalar zuwa ba."
"Saboda me?"
"Saboda ta ce na sake ta ba ta sona, idan ba haka ba za'a wayi gari a ga gawar ta."
"Subhanallah, kai yanzu za ka iya sakinta?"
"Why not?"
"Kada ka biye mata na san idan ka cigaba da lallaɓa ta da kyautata mata za ta so ka, domin ita zuciya an halicce ta na bisa ga son wanda ya kyautata mata da kuma kin wanda ya munana mata."
"Akwai wani abokina Ammar na san ka san shi, to ya fara nemanta suna soyayya ta ce Mani shi take so, ta nemi na sake ta."
"To yanzu sakinta za ka yi?"
Murmushin gefen baki ya saki kafin ya ce.
"To ya zan yi?"
Ganin ɗayar wayarsa na ruri ya saka ya yi wa Jamil Sallama ya katse kiran wayar.
_Aunty Laila_
Bayan sun gama magana da Umma akan za ta je gidan Sadik ta binciko gaskiyar magana ko Sadik ya yi mu'amalar aure da ita kamar yadda Nabeela ta faɗa. Mummy da Ummar sun goyi bayanta idan har da gaske ne to Aunty Laila ta yi mata dukan tsiya, sannan ta tabbatar tare da ita ta bar gidan Sadik, ba za su kawo ta nan ba, sai dai za su kai ta gidan ƙanwar Umma."
Direba ta saka ya kai ta gidan Sadik ɗin, kai tsaye ya dauki hanyar zuwa gidan, horn ya yi maigadi ya bude yana masu sannu da zuwa.
Tambayar sa ta yi ko Sadik na gidan, ya ce mata baya nan ya fita.
Ta ce wa Direban ya ajiye motar a waje yanzu za ta dawo.
Tana shiga falon ko sallama babu.
"Nadeeya dake waya da Sadik tana ta zuba masa shagwaɓa wai har yanzu ba ta warke bai tsaya jinyar ta ba ya wuce ya bar ta. Tana wayar cike da shagwaɓa, tana jin dadin yadda yake kula da ita yana biye wa shagwaɓa da take masa abun da ba ta yi tuninin samun kansa cikin sauki ba, amma saboda samunta ya dace ta kawo masa mutumcin ta gidan sa ya saka yake ganin wani ƙimarta a idanusa.
Ba ƙaramin firgici Nadeeya ta yi ba na ganin Aunty Laila, ta san ba alkhairi ya kawo ta ba.
"Aunty kece da safen nan?"
Sadik da ya ji Muryar ta cikin firgici ya saka ya katse kiran wayar, ƙara taka motar ya yi sakamakon ya san Sunyi Laila ce ta je gidan. Kuma da gangan ya yi maganar a gaban Nabeela saboda ta isar da sakon ga iyayenta. Don ya san komai
Hakuri yake bata akan cewa tana ransa ga shi nan dawowa.
Don a lokacin Driving yake yi suke waya.
Ganin Aunty Laila ta shigo cikin mamaki ta ce "Aunty kece?"
"Wato ke dake yar banzar yarinya ce duk maganar da muka yi maki ya shiga ya fita daga kunnenki ne ko?"
"Aunty me na yi?"
"Ba komai je ki kawo Mani ruwa na sha."
"Lah ga ruwa a nan ai yanzu na dauko ban sha ba."
Ta yi maganar tana ɗaukar bottle watar mai sanyi za ta zuba wa Aunty Laila.
"Ba lemu a gidan ne?"
Sanin halin Sunyi Laila da bin ƙwakkwafi idan ta tashi zarta gane wani abunne ya faru tsakanin ta da Sadik, tunda yanayin tafiyarta ya canza.
"Aunty ba lemu ruwa ne kawai a gidan, tun da jiya muka tare sai yau zai kawo."
Jinjina kai Aunty Laila ta yi tare da cewa.
"Okay wannan ruwan ya mani sanyi ina mura, je ki kawo mara sanyi."
Jikinta ne ya yi sanyi, amma ba wata hanyar dole sai ta tashi.
A hankali ta mike ta fara tafiya cikin kokarin daidaita tafiyar yadda Aunty Laila ba za ta fahimci komai ba.
Shigar ta kitchen ba jimawa sai ga ta ɗauke da faranti da ruwa har da lemu.
Tana zuwa ta zauna bayan ya ajiye mata a gaban ta saman Centre table.
"Ina fatan dai kin dauki zantukan da muka yi maki, kina gasa masa aya a hannu."
"Sosai kuwa."
Finciko ta ta yi tare da cewa .
"Munafuka zo na dubu ki ban yarda da ke ba sai ba duba ki, kwanta na gani Allah sai na dub ko na tabbatar bai taba ki ba."
Ta yiagamar yana nuna wa Nadeeya doguwar kujerar wai ta kwanta.
Kuka Nadeeya ta saka tana cewa ba abinda ya faru tsakanin ta da Sadik.
"Za ki tsaya na duba ki ko sai na ci mutuncin ki a wajan nan?"
A hankali ta durkusa tana kuka.
"Kum yanzu za ki bar gidan nan, ba za ki kwanta na duba ki ba sai na Maki dukan tsiya.
"Tana kuka za ta kwanta kenan sai ga Sadik ya turo kofar y shigo."
"Akan me za ki duba ta saboda ta aikata zunubi?"
"Kai mara kunya ka iya bakinka ko uwar ka A'isha ba ta isa..."
Kafin ta yi wata magana sai ya finciki hannunta y yi waje da ita, a harabar gidan sannan ya sake hannunta.
Alama ya yi wa Maigadi, wanda a guje ya tashi ya nufi ɗakin karnuka.
A bude karnukan suka yi kan Aunty Laila, a guje suna haushi.
Ihu ta ƙwala ta nufi hanyar gate ɗin. Takaliminta ma faduwa suka yi, sai da ta fadi ta fasa baki kafin ta tashi da ƙyar ta cigaba da gudun. Mayafinta ma faduwa ya yi, tana fita ta fada mota ba tare da ta jira direban ya bude ba.
Sai haki take yi tana tsinewa Sadik albarka.
"Hajiya lafiya ?"
"Dalla mu je ina ruwanka."
Bakinta da ya fashe jini ke fita ta goge tana cewa.
"Allah ya tsinewa Sadik albarka A'isha ta haifo mana masifa da bala'i a cikin zuriya."
Tsinewa Sadik take yi har suka isa gidan.
_Hilal_
Fita y yi daga cikin gidan bayan ya yi order abinci ya ajiye wa Zahrah.
Driving yake yi ransa a ɓace , sai magan yake yi shi kadai a cikin motar.
"Mummi, Aunty Laila, Doctor why? MD ya saka kuka aikata haka? Tabbas zan aikata abinda ba yi maku dadi ba, Doctor yau zan hadu da ko kuma za ka girbi abunda ka shuka. Ba abinda zan wanke Zahrah da shi kamar na sex da ita a cikin gidan tafarki, na kira Sunyi Laila da Mummy zan ce su taimaka mata, a lokacin za ku amsa Mani tambayoyin da zan yi maku tambayoyi dole ku amsa Mani tambayoyin da zan yi maku."
_Asadullah_
Yana zaune bakin swimming pool ya yi nisa cikin tunani,
Wata mace sanye da bakin kaya har da niƙab a fuskarta. Hannunta rike da wauka, tana zuwa bayansa ta soka masa wuƙar ta bayansa .
Daidai lokazin Jidderh ta farka ta daki wani ihu mai ƙarfi, tana cewa.
"Yallaɓai.!?"
Ihu ta yi fa kati sakamakon mafarkin an soka wa Asadullah wuka ta rikice.
" Guje ta fito daga dakin ta hadu da kuku, kallonta yake yi yana mamakin jin tana magana. Son shi bai taɓa jin ta yi magana.
"Ina yallaɓai yake yake?"
Mamaki yake yana farin ciki da alama ta samu lafiya.
Fita ta yi zuwa harabar gidanz, zare idanu ta yi tana kallon wajen, kafin ta ruga zuwa wajen guje.
*Alhamdulillah na kammala book 1 ga mai son karanta book 2 sai tura ₦500 ta wannan account number. 2242538358 Zainab Abdullahi UBA bank sai a tura shaidar biya ta wannan lambar waya.09065327995*
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 39 Chapter of 39