Maganar ka gaskiya ne wanda hakan ne yasa shi asalin mamallakin Companyn ya aiko da wad`annan mutanen wasu likitoci ne guda biyu daga can Abuja suke kawai don su dubasa su bashi kulawar da ta kamata in ta kama a kai ga a fidda shi zuwa k`asar waje ne sai a fidda shi".
"Kai Bayin Allah, Allah ya saka maku da alkairi, mun gode mun gode,ku Isar da sak`on godiyar mu ga shi Ogan na ku,ni ban ma San da wanne baki ya kamata in nuna muku jin dad`in wannan abun da kuka zo mana da shi ba,Allah ne kad`ai zai iya biyan ku,ya saka maki da alkairi yai maku tukwuici da Gidan Aljannah", Cewar Baba K`arami Wanda hatta a muryasa zaka gane yana cikin farin cikin game da abinda ya saurara.
"Kar ka damu wannan duk can-cantar da shi Abbakar d`in yayi ne,ba sai ka yi wani Godiya ba, suna son a samu wani yayi masu cikakakken bayanin abinda ya ke faruwa da shi,da kuma irin matakin da ya ke akai a yanzu".
Nasir ne yai masu cikakakken bayanin asalin da yanda abun ya faru," Ya samu buguwa ne akan shi sakamakon accident d`in da ya gamu da shi Wanda a turance muna kiran wannan cutar da suna Neurological disorder the Conditions affecting the brain, spinal cord, and nervous system (e.g., epilepsy, multiple sclerosis).
Also Neuro developmental disorder Conditions affecting brain development (such as ADHD, autism spectrum disorder),a ta haka in ka kalle shi zaka iya cewa barci yake ba dan wannan oxygen d`in da aka sanya mashi ba ,wannan shine matsalar da take damun shi".
"Ammmmm but amma in dai condition d`insa a wannan matakin ya ke bai kamata ace kun na jinyarsa a cikin Gida ba,zai fi samun Good treatment da samun ingantattun magungu ba da kuma nagartattun kayan aiki ya akai haka Doctor Nasir ?".d`aya daga cikin Doctors d`in ya tambaya.
"Eh haka ne nasan da hakan amma kasan irin wannan problem d`in yana da matuk`ar hatsari da don bin taka tsan-tsan gami da lura dalilin ba d`aya ne da ya sa Na dawo da shi,da zaran wurin da yake,yanzu zai fara shebaring yana shirin fad`owa,yanzu da ace zamu kaure da surutu a cikin wannan d`akin duk da kasancewar sa baya iya ko motsa d`an yatsan shi to da haka ce zata kasance".
" Okay na fahimci inda matsalar take yanzu za muyi mashi `yan wasu gwaje-gwaje da zamu je muyi amfanin da su,Amma na so ace zamu iya admitting nasa a Hospital yanda zai samu kulawa da shi 24/7,amma hakan ma ba damuwa zan turo Nurses guda biyu da zasu rik`a taimakawa Madam wajen kula da shi, har zuwa sanda zamu kammala namu binciken".
Godiya Sosai Mama Hadiza,Baba K`arami, Nasir da kuna Ummie Maryam suka rink`a yi ba, don ita Hibba ba bakin magana sai faman zubar da hawayen farin ciki ta ke, a tare su duka suka tafi raka su bayan sun gama duk abinda za suyi har sun kusa fita daga Gidan Abbas Acounter ya dakata yana nai cewa da su yana zuwa yayi mantuwa,"Madam zan iya shigowa ?",Yace da Hibba bayan yayi sallama ta amsa.
Tsaye take akan Abbakar tana mai motsa mishi wasu daga cikin sashen jikin saboda gudun kar su mutu su daina amfanin,"Am kana neman wani abu ne ko kuwa ka yi mantuwa ne ?",Hibba ta ce da shi.
"Madam ba mantuwar da nayi,Na zo ne na Isar da sak`on da aka bayar in baki tun kafin yanzu".
" Sak`o kuma wanne irin sak`o ne wannan haka ?",Hibba ta tambaye shi,bai bata amsa ba sai zura hannunsa yai a cikin aljihunsa ya fiddo wani Embolof daga aljihunsa ya mik`a mata yana mai cewa,"Wannan shine sak`on da yalla`bai ya bani akan sai bayan ya dawo bikin k`anwar shi,in ya tafi seminar d`in da yake shirin tafiya sai in kawo maki,to kafin hakan ta faru wannan tsautsayin ya fad`a akan sa,shine na yanke shawarar in kawo maki ko da abun ciki ba zai amfani ba,ni dai na sauke alk`awarin da na d`auka ".
Amsa Hibba tai idanuwanta na fara k`ok`arin zubda hawaye, ta amsa tana mai yi mashi Godiya.
Jikin Hibba na rawa ta fara bud`e Embolof d`in abinda ta gani ne yasa numfashi da kuma jikinta tsayawa cak,sai da ta d`auki wani dogon lokaci kafin ta dawo cikin hayyacinta,hannunsa guda ta kama ta rik`e kam tana mai d`ora kanta a saman gadon da yake kwance tare da fashewa da kuka cikin mad`aukakiyar murya tana mai cewa "Me idanuwana ke gani,wacce irin cutarwa ce na aikata ma kaina,Na cutar da kai na zama silar salwantar mana da `ya d`aya tilo da muke da ita kai kuma ga ka kwance cikin halin mutuwa da rayuwa,duk don saboda tsananin fushi da son kaina da ban hassala ka ba da idanuwanka basu rufe daga ganin motar da ta tunkarowa mu ba,da yanzu ina tare da kai da kuma ƴata ɗaya tilo da na ke da itanikam wacce irin Mata na zama,wacce irin uwa ce ni mai salwantar ta ran `yarta da kuma ta Mijin ta,bayan kai ka kasance mutum mafi adalci kyautatawa a gare ni,kullum buri da fatan ka ka ga na zama abar kwatance,Na cika buri da duk wani fata da nake da shi,da wacce irin fuska zan kalle ka aduk ranar da ka warke ka tambaye ni ina Jadeeda ta ke, da wanne baki zan iya gode maka irin tarin alkairan da ka yi min a iya d`an zaman da muka yi tare da kai?"......
Da sauri Ummie Maryam ya k`arasa iso kusa da ita tana mai tambayar," Lafiya me kuma ya k`ara faruwa ?".kasa iya cewa komi tai sai nuna mata Peppers guda biyu da ke zube a k`asa ,d`auka tayi ta fara dubawa,d`aya admission na shiga jami'a ne a matsayin d`alibar jinya,sai na biyun kuma dogon bayanin ne akan yanda yake sonta da kuma murnar samun admission da yake taya ta,daga k`arshe ya ke cema ta ta kula da kanta da kuma Jadeeda har zuwa ran da zai dawo.
"Mene ne abin tashin hankali a cikin wannan lamarin naga kamar takardar cigaba da karatu a university ce waye ya samo ta?"," Shine ya samo min tun kafin faruwar wannan a'lamarin ya bari ne yai surprised d`ina sai kuma hakan ta faru ".
Sai da Ummie Maryam ta samu guri ta zauna tana fuskantar Hibba sosai da sosai kana ta fara cewa da ita,"Hibba ki natsu wannan babban dama ce kika samu, bai kamata ki yi wasa da ita ba,a da idan kin d`auki wannan karatun a matsayin buri ko fatan ki,to a yanzu ki canza ki d`auka Cewar za ki yi karatu dan Mijin ki,za ki rayu dan shi ki yi karatu dan shi,ki manta da komi da ya faru,ki farfad`o da rayuwar ki da tashi a lokaci guda,kar ki wasa da wannan damar".
Shiru Hibba tayi na wani lokaci kafin ta bud`e baki tace,"Ummie na yi miki alk`awari zan yi amfani da wannan damar da kuma shawarar da ki ka bani,zan yi karatu ko dan Mijina,zan zama Malamar jinya ko dan shi ya cigaba da rayuwa ya samu kulawa ta, zan yi iya yi na don ganin haka ta faru".
Sosai Ummie Maryam ta ji dad`in wannan lafazin na Hibba har sai da ta kai ga ta rungumeta.
Wannan kenan
After 5yrs
A guje ta fito tana mai kwalama Ummie Maryam kira ta na mai d`oki da murna,"Mun samu damar ganin Likitan kwakwalwa a can U.s.a,Ummie muna cikin alkairan Allah ".
Cikin zumud`i Ummie Maryam ta ce," Kai Alhmdllh Masha Allah gaskiya muna cikin alkairi yanzu bayan Schoolarship d`in da ki ka samu ,kuma sai ga wannan babban alkairin ya zo ?".
"Ke dai bari Ummie ga Mama can ta tafi ta sanar da Baba Malam ,nasan shima zai yi farin ciki, har Baba K`arami da kuma Yayah Nasir na Kira a waya na sanar da su, yanzu haka na san Baba K`arami ya kusa isowa domi mu fara tsara yarda zamu yi tafiyar,kin San fa tare da Yarona zamu tafi", ta kai zancen tana mai fad`ad`a fuskarta da murmushi.
" To ai dama nasan da haka Jaheed ai d`anki ne in ki ka tafi ki ka bar ni da shi, ai ba zan iya ji da rigimar shi ba,dan haka addu'a ce tsakani na da ku,yanda kuka sanya mashi rai a wannan tafiyar ai in baku tafi da shi ba ba zaman Lafiya kaf Gidannan don haka Allah ya ba Abbakar lafiya ya sa wannan shine k`arshe wahalarsa,ku kuma Allah ya sa albarka a cikin karatun da za ku yi".
Haka dai suka cigaba da murnar su har sanda su,Baba Malam, Baba K`arami da kuma Yayah Nasir su ka zo,suka cigaba da tsara yanda komi zai tafi game da da tafiyar su Hibba, lokacin da mutanen Gidan suka samu labarin wasu sun yi murna wasu kuma a fili suka rik`a bayyanar da hassadar su a fili,amma a cikin su ba wanda ya kula su,sai ma k`ara k`aimi da suka yi game da shirin su.
*JADEEDAH*
STORY & WRITTEN BY :
(*Cwt~Sumiey*)
Marubuciyar littafin
MENE NE ABIN YI ?
KARAGAR MULKI
And now.....*JADEEDAH*
BOOK 1
*YOTA*
PAGE 17❤🔥
Gudu ta ke tsalawa na fitar shari'a akan saman titin Tafawa `Balewa Area 8 ,yanayin yanda take tsala gudun kad`ai ya Isa ya tabbatar maka da ba a cikin natsuwarta take ba,gab da zata hau titin da zai sadata har zuwa babban gate d`in Garki Hospital Abuja ,ta buga ma motar dake gabanta,runtse idanunta kam tai tana ambaton suna Jesus da neman agajin gaggawa a wurinsa.
K`arfin bugun ne yasa motar da ta daka kaucewa daga Saman kan titin har sai da ta kai ga bugar wata bishiya dake gefan su,kafin ta tsaya cak kamar an rik`eta cikin gaggawa da hanzari Dr. Imam Muh'd Jaheed shi da Driver d`in da ya d`auko shi suka fito daga cikin Motar da har ta fara fidda hayak`i.
Kasa cikakakken motsin kirki Jedeeda ta yi har na wani d`an lokaci,ganin yanda Driver d`in ya nufo ta a fusace ya sa tai hanzarin fitowa daga cikin tata motar tana mai fuskantar shi da jiran me zai fara fitowa daga bakin sa.
"Are you out of your sense, ta ya za ki rik`a yin wannan mahaukacin gudun a saman titi,sai ka ce dan ke kad`ai aka yi titin ko kuma na Gidan ku ne titin?".Saurayin Driven ya ce da ita cikin tsawa da d`aga murya.
"Hey...hey hold on how dare you are da zaka rik`a yi min magana cikin tsawa,Call the mechanic I will pay the bill".....," Me ne? Maganar kud`I ki ke a irin wannan k`adamin magana fa ake ta tsakanin mutuwa da rayuwa, wace ce ke me ki ke tak`ama da shi da har ki ke wannan kurin ?".
"Hmmmmmm bana da Lokacin `batawa da kai ina cikin uziri just name the price or you can call your mechanic I will pay the bill,ka fahimce ni?, ina cikin wani uziri mai muhimmancin gaske".duk wannan abun da ke faruwaDr. Imam Jaheed ya na gefe nad`e da hannayensa a k`irji yana kallon abinda yake faruwa a tsakanin su.
"Okay tunda haka ki ka ce let me call the Police ko ba kome za su `bata maki lokacin da ki ke ikirarin baki son `batawa kin ga inya so sai ki biya bill ta hannunsa".
" Oh Jesus Christ ",Jedeeda ta fad`a can k`asa tana mai dafe kanta da hannunta na dama," Ka ga zan baka kud`i iya adadin da kake so but don't waste my time, so please accept the money instead of my apology ".
Sakin baki Drivern yayi yana kallonta da tunanin ina wannan rashin kunyar ta ta zata kai ta,ji yai ba zai iya kyaleta ba har sai ya kai ga yin reporting d`in ta ko ba komi zai samu sauk`in rashin kunyar da ta yi masa.
Ganin da gaske kiran Police d`in zai yi yasa ta saurin dakatar da shi ta hanyar cewa," Ammm......I'm sorry kar ka kira su cause I can not stay,this's my my card you can call me anytime in ya so sai mu kai k`arshen batun ",ta kai zancen ta na mai d`ora masa card d`in nata a saman wayarsa da yake k`ok`arin kiran number Police ta ko ta `baci.
" To hell with your card, har ke wace ce,me ki ka d`auki kan ki da har ki ke iya fad`ar duk abinda ya zo maki a bakin ki ba tare da Kin yi duba da irin asarar da ki ka janyo min ba,dubi fa ki ka ga yanda motata ta koma duk a saboda ke ,ita fa ce hanyar da nake ci da ahalina da ita,ke kawai hankalin ki na kan lokacin da za ki `bata,mai yasa ba za ki tsaya ayi ficzing d`in matsalar da ke ki kayi causing d`inta ba, Don haka na rantse mi ki sai Na yi reporting d`in ki ko ke yar wace ce kuma ko da hakan na nufin ba za a biya ni hak`ik`i na ba,ko ba komi zan `bata maki lokacin da ki ka nuna kin fi martaba shi fiye da komi"......
"A'a let her be kyaleta ta tafi,ni zan biya duk abinda ya kamata ayi,ko ba komi kai Namiji ne kuma sama da ita ka ke,ka fita nisan hankali da kuma sani abinda ya kamata,just one thing da na ke so daga gare ka ka samar mani da wata tacxi d`in da zan idasa inda za ni cikin sauri",Cewar Muh'd Jaheed da ya iso inda su ke.
Da hanzari Jedeeda ta d`ago kanta ta na mai sauke idanunta akan shi,eh tun d`azu ta san ba iya Driver d`in ne kawai a cikin motar ba, amma hankalin ta bai sake komawa a kan shi ba,rasa me ma za ta ce da shi tai,sai juyawa tai ta nufi inda ta ta motar ta ke domin barin wurin.
Cikin d`acin rai da zafin abinda ta aikata Drivern ya bita da kallo ji yake inama wata kyakykyawar isaka zata taso ta yi gaba da ita ,da ya ji dad`in hakan, hakan ya d`ar su a ransa ne sakamakon yanayin k`irar halitta da ta ke da ita,kwata-kwata bata da k`iba shi is slim girl,ta Na da matsakaicin tsawo,wacce ba zaka iya kiranta gajera ko kuma wacce ta cika tsawo ba,irin medium d`in nan haka take,plazon wando ne a jikinta sai kuma wata `yar riga `yar k`arama da iya gabanta kawai ta rufe mata daga baya kamar belt ne ya rik`e ta kawai,ta tara gashin kanta wuri guda sai faman reto yake.
"Kaga kira Mechanic d`in da zai iya gyara maka motar ka,domin ina son in bar wurinnan da wuri"..... K`arar da wayarsa ta fara ne ya dakatar da shi, picking call d`in yai muryarsa d`auke da sallama.
" Jaheed lafiya dai ko?,ka ce min ka kusa isowa tun d`azu amma har yanzu na ji shiru,Matarnan fa tana cikin critical condition ne fa?".
"Uncle Nass mun samu accident ne",....." Subahanallahi kana lafiya dai ko ba abinda ya same ka ko ?".
"Ina lafiya ba abinda ya same ni har ma da driver d`in da mu ke tare motarce kawai ta samu Matsala".
"OK Masha Allah I will be here right now ka jira ni,tura min location d`in inda ka ke ganinan zuwa", Uncle Nass ya fad`a ya Na mai barin duk abinda ya ke.
Kamar wacce aka hankad`o ko kuma wacce aka biyo haka ta shigo cikin room d`in da Mahaifiyarta ta ke kwance ba tare da ta san inda hankalin ta ya ke ba.
" Nora ya jikin Momy a wanne mataki ta ke a yanzu ?",shine abinda ya fara fitowa daga bakin ta.
Da d`an gudun wacce a ka Kira da Nora ta k`araso kusa da ita idanuwanta na fara zubda ruwa,"Anty she is still in unconscious situation, tun jiya a haka muka kawota",..."What tun jiya a cikin wannan halin take kuma kuka zauna a cikin Hospital d`in,where is Papa ina ya tafi ?","Ammmm Asibitin suna iya bakin k`ok`arin su yanzu haka Ana jiran zuwan wani Special Doctor ne,Wanda yake kula da `ban garen masu lalura irinta Momy,to jin shirun yayi yawa ne ya sa Papa ya tafi ya dubo ko lafiya har yanzu bai iso ba".
Jadeeda rasa me ma za tai tayi sai kai da kawo ta cigaba da yi a cikin d`akin Asibitin.
Sheshshekar kukan Norah ne ya dakatar da ita tayi kanta da sauri,"Norah lafiya ki ke,me ya same ki,ko kema ba ki da lafiya ne,why are you crying ?",duk ta jero mata wad`anban tarin tambayoyin a hargitse.
Cikin muryar kuka ta bata amsa da cewa,"I'm so afraid, ina jin tsoro kar wani abu ya samu Momynah, ina jin tsoran haka,wannan wanne irin ciwon kai ne haka mai tsanani da azaba Wanda har ya ke d`aukewa mutum ji da ganinsa ,Momy fa har fita tai daga cikin hayyacinta tai bata San mun iso wannan Asibitin ba fa".
"Kin ga Nora ki kwantar da hankalin ki ba abinda zai faru da ita da sunan Yesu Almasihu, cuta ba mutuwa ba ce,Allah ya na aiko ma bawanda da ita ne don ya jarrabe shi,ya ga zai iya cinye wannan jarabawar ko ba zai iya ba,ko kin manta ISAIAH Chapter 43 Verses 19 yana cewa "Do not lose hope in time of trouble, for God is working in the unseen.His hand is steady, and his timing is perfect in bringing good out of difficulty", haka ma a cikin MATTHEW Chapter 7 Verses 7 yana cewa," Ask and it will be given to you, seek and you will finds,knock and it will be opened", don haka bai kamata ki sa damuwa a ranki ba kin ji ko".
Wata sassanyar ajiyar Zuciya Nora ta saki Wanda hakan ke nuni da ta samu sassaucin abinda ta ke jin tsoran game da ciwon Mahaifiyar ta ta,bayanin `yar'uwarta Jedeeda ya kore mata shakku da kuma jin tsoran da ta ke cikinsa a baya,hannu Jeddeda ta sa ta janyo ta kusa da ita tana mai kwantar da murya ta duk dan ta samu ta kwantar mata da hankali,"Let's prayer for her, in Jesus name za ta samu sauk`i kin ji",a tare su ka nufi inda take kwance akan gado,a tare suka kai gwuiwowin su a k`asa gami da runtse idanunsu tare da kama hannun Mahaifiyarsa da ke mafi kusa da su suka rik`e tare da cewa,"Heavenly Father, I seek your healing touch
We come before You with hearts full of hope,Our sweet mother lies here, weak and silent.But we know, O Lord, that You are the Great Healer.Please touch her body with Your healing power.Restore her strength, renew her spirit.Let Your peace cover her like a blanket.We still need her, Lord. Please don’t take her from us yet.
We trust in You, Lord.
Your ways are higher than ours.
Even in pain, we will praise You.
Heal our mom, dear God, if it be Your will.
And help us be strong while we wait.
Amen"
Bayan sun gama addu'ar ne sai ga shigowar Papa da hanzari Jedeeda ta matsa kusa da shi ta na tambayarsa da cewa,"Ya ake ciki Doctor d`in ya k`araso ko?","Ki kwantar da hankalin ki my Daughter bai iso ba motar shi ta samu matsala amma ga Doctor Nass can ya tafi ya taho tare da shi da zaran ya zo Mahaifiyar ku za ta samu sauk`i".
"Oh har hankalina ya kwanta tunda komi zai yi sauk`i da zaran ya zo"," By the grace of God ".
A can `bangaren Jaheed hankalin shi kacokan Na kan duba file d`in patient d`in da zai duba tun bayan had`uwar su Dr Nass," Uncle Nass hankalina ya tashi Matarnan she is in critical condition, wannan wanne irin ciwon kai ne mai matuk`ar rikitarwa haka ?","Kai dai bari ni kaina ranar farko da aka fara kawota na ga halin da take ci,shiyasa ma na ce ka zo ko zaka taimaka mata".
"To Allah ya taimaka mana,ya kuma bamu ikon aikata alkairi muga abinda za mu iya akan hakan", da haka dai suka cigaba da tafiya har suka isa,ba tare da `bata lokaci ba suka fara shirin zuwa su ga patient ta su.
Esther ce ta shigo hannunta rik`e da baskets na abinci Momy Rebecca na biye da ita a bayanta,wan da suma sai yanzu da safe su ka sami labarin rashin lafiyar .
Kanta Momy Rebecca tayi tana mai cewa," Oh My Daughter Gloria me ya same ki,wannan wanne irin ciwo ne haka,Yarinya ace ba a wani dogon lokaci da ita sai ace gata can kwance ba ta san inda kanta yake ba"......,"Mom ki yi hak`uri za ta samu lafiya in the name of Jesus Christ, kar ki damu kan ki kin ji".
"Haba Revered Anderson ta ya za ka ce kar in damu kana kallon halin da ta ke a ciki kuwa,ko ko..motsi ba ta yi ba ta ma fa san na zo nan ba",
" Akwai Doctor yananan zuwa zai dubata,idan har ya dubata naga ba wani improvement sai in fidda ta wata k`asarnan kawai".
"Hakan shi ya fi Papa,ni kaina hankalina bai kwanta da wannan Hospital d`in ba", Cewar Nora,shigowar wani Doctor da kuma Nusses guda biyu janye da gadon d`aukar marasa lafiya," Mr Anderson Doctor d`in da zai dubata ya iso yanzu haka an umarce mu da shigar da ita Emergency, Sanan ku kuma a canza maku d`auki kafin a fito da ita"Cewar d`aya daga cikin su.
"Okay ba matsala nan ", Nusses d`in su ka wuce da ita Emergency shi kuma ya tafi ya nuna masu sabon d`akin da aka ce ya kai su.
After some hours," Congratulations Revered Anderson mun samu mun shawo kan matsalar da ke damunta yanzu haka muna saran farkawarta ta nan da wani d`an lokaci ",shine furcin da Dr Nass ya fara yi bayan fitowar su daga Emergency d`in.
" Praise be to Allah,the one who control everything around the world,blessed be to the God Father of our Lord Jesus Christ, wannan shine abinda tun d`azu muke dako da kuma fatan ji daga gare ku",Nan fa kowa dake cikin d`akin su ka fara nuna jin dad`i da kuma godiyar su,don Jedeeda kuwa runtse idanunta tai tana mai had`e hannayenta wuri guda, ita kad`ai ta San me take cewa a cikin Zuciyarta,daga bisa ni ta kai hannunta saman goshi da kuma gefe da gefan kafad`unta.
Bayan sun d`an natsa Dr Nass ya ce da shi, "Am Doctorn da ya dubata yana buk`atar ganin ka a office d`in sa","Okay ba damuwa ma iya tafiya yanzu ?"," Yes uppcourse yana can ya na jiranka".
Har sun kusa fita Jedeeda ta dakatar da su da cewa,"Papa in biyo ka mu tafi tare ?","A'a ki zauna I will be back soon kin ji my Daughter ".jiki a sanyaye ta koma ta zauna domin Maganar gaskiya ta so ta ji musabbabin wannan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 30