ba ni da ja ki tafi sai kin dawo ,Yesu Almasihu ya albarkace ki a tafiyar da za ki ki je ki dawo lafiya",sai da fuskar Jadeeda ta faɗa ta rungume ta gami da cewa,"That's My Sweat Mom na Gode da samun ki da nai a ciki rayuwata".
"Nima na Gode ma Jesus da ya sanya ki ka kasance ɗaya daga cikin tsatsona,amma dakata ba zaki kai 4pm a waje ba ko".
Sai da Jadeeda ta yi jim kafin ta ce"Ehhhhh to ba lalle ba,domin case ɗin na wata ƙaramar yarinya da ke fama da ciwon zuciya to muna son foundation ɗin mu yaɗauki nauyin aikin da za ai mata ne, da zaran mun yi solving ɗin sa zan dawo buy the grace of God".
"Okay ki kula ki kira ni ki sanar da ni komi ke faruwa kin ji,in ma da buƙatar mu sa hannu a cikin lamarin sai ki sanar da ni","Wai da na ce ina Martin ya ke ko shine sai mu tafi tare ban san tafiyar ni kaɗai",ta ƙare maganar zuciyar ta na bugawa da ƙarfi da addu'ar Allah ya sa baya Gidan,"Sun fita shi da Papa ɗin ku,ita kuma Nora Unexpected test ce ta taso ma ta tafi school sai dai ko kusa Driver ya kai ki","A indai haka ne Gara in tafi ni kaɗai ,na yi driving ɗin da kaina amma kafinnan in wuce zan shiga Church ɗin Our Lady Queen of Nigeria Pro‑Cathedral","Kina ganin ba zaki sanya su ta jiran ki ba","A'a Bazan jima ba zan wuce,ina so in ɗan yi addu'o'in ne kafinnan","okay ba matsala ina maki fatan alkairi sai kin dawo".
Da wannan damar ta samu ta haɗa duk abinda zata buƙata tasa a cikin troly ta saɓa ta fitowa ta ci karo da Ester wanda har sai da gabanta ya faɗi,"Aunty ina za ki haka na ga kin fito da sauri irin haka?",sai da Jadeeda ta haɗiye yawun da ya tarar mata a baki kafin ta ce da ita,"Wanki zan bada na","Wanki kuma Aunty ba akwai Machine ba?",Cigaba da tafiya tai kafin ta ce da ita,"Bana da buƙatar shi ",idanu Ester ta zaro waje ta na mai cewa a cikin Zuciyar ta,"Anya kuwa lafiya,Aunty Jadeeda ba haka ta ke ba,ba ta magana da mutun a irin wannan yanayin kuma na ga kamar unguwa za ta ,Uhmmmm ba ruwana",ta ƙare zancen ta na mai tafiyarta abinta.
Kai tsaye Church ɗin ta nufa acan ta kwashe tsawon lokaci acan sai da taga gabatowar 4pm sannan ta baro cikin Church ɗin ta samu wani ɗaya daga cikin masu aikin Cleaning a cikin Church ɗin ta kira shi gefe guda ta ce da shi,"Ina son za ka yi min wani aiki zan biya anan take shin kana da interest akan shi?,zan biya ka 50k anan take just delevering ɗin saƙo za kai min zuwa wani address da zan baka",zaro idanu waje yai alamun zuciyar shi na son kuɗin kafin ya ce,"Anya ba akwai wani abu a cikin wannan aikin da ki ke son sanya Ni acikin da ba,ma'ana akwai lauje cikin naɗi akan shi ba","Ba wata manufa a bayan haka,tafiya ce ta gaggawa ta ka mani zan baka keyn Mota ta ka kai min ita,zuwa Gidan mu,da takarda da zaka ba su in ka isa, simple shine kawai,na faɗa maka haka da iya gaskiyata ba zan cutar da kai ba,nan guri mai tsarki mu ke,ba zan faɗa maka akasin gaskiya".
"To shikenan na yarda da ke","Amma ina so sai nan da 6pm za ka kai sauƙin",da to kawai ya amsa mata ta je farking space ta nuna masa Motar tafidda trolynta ta ba shi keyn sannan ta tafi ta tari tacxi ta nufi Airport kai tsaye.
Bayan awannin biyu da tafiyar Jadeeda a kai sallama a bakin gare ɗin Gare Akan ɗin Gidan ya leƙa ya ga wani Magidanci tsaye da takarda a hannunsa ga kuma Motar Jadeeda tare da shi,"Lafiya Malam na gan ka anan ko wani ka ke nema ne?",Gate Man ɗin ya tambaya.
"Eh wani daga cikin Halin Gidan na ke nema domin in isar da saƙon da na zo da shi","Kamarya wani daga cikin Gidan kana da alaƙa da su ne","A'a kawai dai an bani saƙo ne,wanda zan fi son in ba wani ahali na Gidan",Shiru Gate Man ɗin yayi kafin kuma ya ce da shi,"A'a ka dai fara sanar da ni abinda ke tafe da kai sai in ji daɗin sanar da mutanen Gidan abinda ya kawo ka ba hakanan in tunkare su da labarin da ba ni da wata masaniya akan sa ba","Zan dai fi son ka kiramin wani a Gidan sai a yi komi a gaban ja domin Ni ban zo da wata cuta ba".....Isowar Nora wurin ya dakatar da musayar yawun da suke ,ta dakatar da gami da tambayar Gate Man ɗin da cewa,"Baba Joshua lafiya na ga Motar Aunty Jeeyyyy a waje ?","Nima yanzu na fito na iske ta anan da alama dai wannan mutumin ne ya zo da ita",da sauri Nora ta maida hankalin ta akan mutumin da aka nuna da sunan shine ya zo da Motar,"Ina ka sami wannan Motar,Ina mai Motar ta ke,meye haɗin ka da ita", wannan sune jerin tambayoyin da Nora tai mi shi a ƙagauce da son jin amsar su.
"Kwantar da hankalin ki me motar da kanta ta bani ita gami da bani address ɗin wannan Gidan ta ce in kawo ,in sanar maku tafiyar gaggawa ce ta risketa,ga wannan takardar da ta bani don ku tabbatar da abinda na ce da gaske na ke",ya kai zancen ya na mai miƙa mata ,tana amsa ya juya yai tafiyarsa ba tare da ya tsaya ba.
Ita kuwa Nora a hargitse ta shiga cikin Gidan kamar wacce aka biyo,tun kafin ta shiga ta ke kwalama Momy kira,"Lafiya Nora me yake damun ki za ki shigo Gida a cikin irin wannan yanayin,sai kace makauniya".
"Momy ina Aunty Jadeeda,ina ta tafi?","Nima abinda na ke tambaya kenan ki ka shigo",cewar Papa da ke zaune a kan dinning suna cin abinci".
"Ohhh,ta tafi duba wata Yarinya mai ciwon zuciya ƙarƙashin Foundation ɗin su, Shikenan ko sai ki samu wuri ki zauna kin shigo kina ƙoƙarin tada ma mutanen Gida hankali".....,"Kin kirata ko kuma ita ta Kirani tun bayan tafiyar ta?",Papa ya tambaya.
"A'a na yi ta trying number na ta amma a kashe ba ta tafiya wani lokacin ma sai ace min not reacherble".
"To ga Motar can wani ya kawo ya ce,wai a gaya maku tafiyar gaggawa ce ta kamata,da kuma wannan takardar",ta kai zancen ta na mai miƙa masu Papertun kafin wani ya motsa Papa yace,“Ina ita Jadeedar? Me yasa wani ya kawo Mota da wannan takardar?!” Papa ya buge da tambaya, yana ƙoƙarin ɗaukar takardar.
Gidan kowa ya firgita, Zuciyoyinsu sai faman kai komo take da son sani ne takardar ta ƙunsa Granny tana zaune dafe da ƙirjinta, Papa har ya fara fitar da ɗigon zufa . Momyn Jadeeda kuwa ba ta iya ɗaga kai ba.
Papa ya buɗe takardar cikin sauri, zuciyarsa na dukan bugun tashin hankali. Granny ta daga hannu tana karanto addu’a a cikin ranta, kamar zata faɗi,Papa ya fara karantawa kamar haka
“Ina roƙon gafararku…
Ba don na tsane ku ba ne na tafi, sai don na rasa inda zan nufa,Zuciyar ta kasa iya ɗaukar abinda ya tunkaro ni.
Kowane numfashi a cikinsa akwai ruɗani, tsoro da ɓacin rai. Idan ni ce kuskure, sai na zauna kuma na rayu da shi
Ban san inda nake nufa ba, amma ba zan iya komawa inda ku ke ba.
Ina mai tabbatar maku da zan dawo amma sai Sheɗanin da ya ƙawata Zukatan Ƴan'uwana kuma makusanta na ya bar gangar jikinsu,to a sannan zan dawo,ina kewan dukkanin kulawa da soyayyar da ku ke nuna min,zan yi rayuwa a inda na ke cike da kewar ku.
Uncle Miey har yanzu matsayin ka yanan a cikin raina bai sauya ba,haka kaima Bro Edwin,Nora da Martin zan yi kewar ku,ku kula min da Mommy da kuma Papa har zuwa sanda zan dawo.”
Jadeeda
Uncle Miey ya dafe bango, yana kallon Edwin,“Mun cuce ta...!” Granny ta faɗi da hawaye.
"Kai ne dai ka cuceta,kaine mabuɗi kuma sular faruwar komi,kai ne ka cuceta", Uncle Richal ya faɗa cikin hargowa yana nuna Edwin da ya yatsa
Papa ya jefar da takardar, ya nufi inda Madam Gloria ta zube ƙasa tana kuka mai cike da raɗaɗi ba kuka irin na ɓacin rai kawai ba, amma kuka mai tambayar "me ya faru da ƴata Jadee?,ina take a halin yanzu wacce irin rayuwa za ta riska a duk inda ta ke,shin sake jefa kanta cikin wata rayuwar mai cike da hatsari tai ko ko hanyar mafita ta samar kanta a sanadin barin Gida"
Amma tabbas barin Jadeeda ya bar ƙura, damuwa, da abin da babu mai iya warwarewa,face sai lokaci domin shine alƙalin da baya ƙaryata,kuma baya cuta ko kaɗan.
na farin cikin sanar da ku cewa an buɗe Paid Group na Littafin JADEEDA domin masu sha’awar ci gaba da karanta wannan labari mai cike da sirri, ƙauna da ruɗani.
Farashi: ₦300 kacal.
Za ku samu damar karanta Jadeeda har zuwa ƙarshe cikin sirri da tsari.
Account Number: 8102641528
Bank: Opay
Sunan Sumayya Usman
Kai tsaye za ku iya tuntuɓar ta ta wannan Lambar waya 08102641528
Bayan biyan kuɗi, ku tuntuɓe ni kai tsaye domin a saka ku cikin group ɗin.
Mun gode da ƙauna da goyon bayanku kullum. 💕
Cwt~Sumiey ✍️
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 30 Chapter of 30