Share this page
motarsa ba har ta shige cikin gidan A hankali ya dan dafe gabn goshinsa cike da tunanin abubuwa da yawa da suka shafi rayuwarsa a yau din nan Ajiyar zuciya sanyayiya ya sauke sannan ya tayar da motarsa ya nufi gidansu, zuciyarsa cike da tunanin wanka ne ya dace da shi da kuma nutsatsen hutu, ama wani abu a cen kasan zuciyarsa na fada masa cewa eh lalle wanka da hutu mai sunnan hutu ne suka dace da shi, a yau shima Taufeek bayan dogon jira da dogon daukan rayuwa irin ta gwauraye ya zama ango, ya zama magidanci...........tabas wannan rana ya dace ya yi hakuri da duk wani abin da zai iya taba masa zuciya ya fuskanci sabuwar rayuwar dake gabansa Bai samu isa gidansu da wuri ba, sai da ya yi yan biye biyensa ya samo guzuri irin na cikaken ango sannan ya karasa A cikin motar ya bar komai ya fice ya nufi bangaren mahaifiyarsa dake cikin zuciyarsa Mutanen dake falo baba basu fi a irga ba, dan kowa gajiya ta kai shi ya nemi waje ya tsugunar da hakarkarinsa dan samun hutu Sama ya haura ya karasa kofar dakin mahaifiyarsa A nutse ya bubuga sannan ya yi salama ya kuma saurara Jin muryarta tan amsa salamar ya saka shi bude kofar ya shiga yana sake dan dubawa har ya dawo da dubansa kanta yana dubanta Murmushin ya saki shima, kamar yadda fuskar mahaifiyarsa ta fitar da sansanyan murmushi mai tafe da sakwani kala daban daban A hankali ya karasa ya zauna daf da ita ya harde kafafuwansa ya ce" Barka da warhaka Umana" Murmushin ta yi itama tana sake dubansa ta ce" Daga ina kake haka? Ko guduwa ka yi irin na Fulani?" Yar dariya ya yi yana girgiza kai ya ce" Su Khausar na mayar gida ai" Itama ta yi dariyar , sannan ta sauke ajiyar zuciya a sanyaye ta zubawa fuskarsa ido Bata da bakin magana a yau face ta godewa Allahu sarkin samai da kasai, wanda ya halici bawa ya kuma saka masa jarabawa kala daban daban a tsanin rayuwarsa Ita dai jarabawarta abokanan zamanta ne a kan d'anta, a da zamansu sunna yi ne komai shawara guda, ita bata bin malaman tsubu ko bokaye bale ace a cen ta jiyo abinda ya tsotatata da su, yau da gobe ne d babu abinda ta bari ya saka ta wayi gari ta ringa tsintar abubuwan da suke yi a bayan fage wa'inda suka girgiza tunaninta suka tsotatata har suka saka ta dauki wannan dabi'a ta kadaice kanta ya zamto idan ka ji muryarta a falo mijinsu ya bukaci haka ko d'anta ya bukaci haka, sai ko idan baki ta yi , yawancin lokuta ta fi tarewa bangaren Hajia dan ta fi sakewa , ita din mutun ce mai gudun munafurci, idan ta zauna da kai da zuciya daya ka ringa munafuntarta lokaci daya zaka nemi wace ka sani ka rasa, sam zaka kasa gane kanta, tana iya shafeka a babin bil'adaman da idannuwanta suke da hurumin gani a gabanta, dalilin da yasa tsakaninta da matan baban Taufeek mutunci gaisawa bayan wannan kowa ya rike abinda yake hurumi a gareshi A sanyaye ainun ta ce" *MAGIDANCI* " Idannuwansa ya dago daga kunce agogon hannunsa ya dan zunawa fuskarta ido jin ta ambaci sunnan da hajia ke kiransa da shi A hankali ta ci gaba da fadin " Yanzu na raka Hajia, a yau lakabin da take maka cewa MAGIDANCI ya cika Autana" Dan tsai ya yi dan alamu da yake gani na tana son yin kuka Kansa ya cire kasa kasa sosai ya ce" Bafa gidan miji za'a kaini ba fa ake son rikitani ina zaman zamana, Matar babana kuka za'a yi?" Daria ta saki ta miko hannunta tana dungure kansa ta ce" kai ba zaka barni irin dan kukanma na taba ba?, Haba Baban yara" Shima yana dariar ya rike hannayenta duka biyu yana dubanta ya ce" Da izinin Allah, in ina raye, kuma ina kusa, kuka sai dai idan ya shamaceni ya samu fuskar mahaifiyata" "Allah ya yi maka albarka, tabas na yarda cewa daya tak gari ne, kuma mai albarka ake nema ba wai tarawar ba a tara mararsa albarka, Taufeek ina matukar alfahari da kai, ina kuma gannin kokarinka, kaine ASIBITIN KA, kaine KASUWAR MAHAIFINKA, kaine hidima wa al'umarka, ina matukar alfahari da kai, ina fatan Allah ya dafa maka duniya da kiyama........, Ka ga yau burina ya cika, a da idan na dan dubeka sai na ga shekaru fa ja suke, shekarunka tafiya suke yi, ama maganar aure shiru kake ji , ashe kamar yadda Hajia ta fada ne lokaci ne mu naka dama gashi yau Allah ya yi, Allah ya sa iyalinka ta zamto cikon farin cikinka duniya da kiyama" Maman Taufeek ta fada a sanyaye ainun tana mai dan jimke haannunsa dake karra tabatar masa maganar daga zuciyarta take fitowa A hankali ya sada dubansa, sannan a hankali ya amsa da amen ya Allah, sai kuma ya sake dagowa yana dubanta a lokacin da ta ci gaba da fadin" Taufeek du shekarunka, da iliminka, wajibunmu ne idan muna raye mu ringa tunatar da kai da kuma yi maka nuni a kan abinda ya dace da rayuwarka dan samun rabauta a wajen ubangijinka, ka ga aure baa abin wasa bane, a yanzu wani nauyi mai girman gaske ya rataya a wuyanka, wanda ba wai iya ka ciyar kaa shayar ka tufatar bane kawai, harta maganar baki idan har domin Allah zaka zauna da iyalinka ya dace ka ringa tauna harshe kafin furucinka a gareta, kuma ka kiyayi shiga hakinta ko wani iri, ka yi kokari kaa koyar da ita yadda kake so ta kasance cikin salama ba da wulakanci cin zarafi ba, domin ka ga mace , makarantar da ka sakata a zamanta da kai karatun zatai maka bita har ku koma ga ubangijinku, ina nufin idan ka gyara kanka ka gyarawa, idan kuwa ka bata kanka ka batawa ka ji Taufeek?" Kai ya gyada, a hankali yana sauke ajiyar zuciya, sosai yake daukan karatun mahaifiyarsa a ko yaushe, ya kasance mai matukar ba hudubarta mahimmanci, bata taba budar bakinta idan sun yi zama irin wannan ta koyar da shi mugun abu ba, shi yasa yake girmama dukkan furuci nata koda kuwa cikin wasa da dariya zata yi masa "Shin yaushe ne aikin nan da kake yi zai kare?, Shekara nawa kennan bana?" Ta fada a nutse tana dubansa da kula Yar ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya ce" In sha Allah inaga dole sai na karra wasu yan watani a makarantar , domin an samu wasu ba'a samu wasu ba, " Mahaifiyarsa ta ce" Ama yaya zaka yi da sanninka da aka yi da sunnanka da kuma yannayinka?, Taufeek aikin nan wani lokacin ni tsoronsa ke kamani kar aje a bincikeka a san wanene kai, yanzu haka ina gannin mamakin manyan makarantar ace basu ganeka ba?" Da kula sosai ya ce" Mama, ai basu san da zamana a makarantar ba, abindama ya sa na zabi hakan kennan, dan yawancin lokuta mutun kan hangi matsalarsa a nesa ne bayan tana daf da hancinsa, ba zasu taba sakawa ransu cewa ni zan iya shigarsu a haka, sai dai ya zame min wajibi na yi domin nima sheda ne an kawo min daidaikun daliban da suka ringa rikita min patin wa'inda makarantar ta yaye, abinda ya fi dan sakani dakatawa a tafiyar nan shine rikita rikitar da nake ciki na amsoshina barkatai, shin laifin na wanene a ciki? Daliban ne, ko malaman, ko kuwa masu rike da makarantar? Idan aka yi duba da wasu daliban cikin makarantar nan za'a sha mamakin tarin baiwar da Allah ya masu, kin ga ai Khausar na daya daga ciki, na san wacece ita a fannin karatunta, a yanzu haka na tsame takardarta zan turata ne hospital baba ta je ta idasa gogewa a aikinta, hakn na nunin idanma akoy maganar malaman kansu akoy masu wasa to fa akoy jajirtatu dan dalibi ba zai koyar da kansa abinda yake bako da girma irin na asibiti kai tsaye ba, ina dai cikinsu yanzun matsayin malami ne zan dauka dan har an gama gyara komai" Cike da kula itama Maman ta ce" Allah ya tsare, Allah ya sa a samu abinda ake nema, kuma Allah ya bada ladan taimako" A saman lebensa yake amsawa da amen, ya dan karra jimawa a wajen Maman sannan ya mike ya tafi, Mama kuwa ta bishi da addu'a a zuciyarta tana ji inama ace ya ajiye aikin nan? Sai dai ta san abu ne da ba zai yiwu ba dan ta san yaronta da tsayuwa kan abinda ya saka a gaba, bale wannan din aiki ne na samun lada dan kuwa idan har ba'a gano ina matsalar take ba tsaf za'a yi ta kashe al'uma dan son zuciya da dan kudin da bai taka karra ya karya ba, ta san bama zai yarda a masa maganar bari ba, ai yama jima a ciki kai tsaye ba zai janye kansa ba, abinda ka ga mai Kwanoni ya hakura ya bar Taufeek a ciki ka san mai mahimmanci ne Gidan ya sake daukan tsitttt, ba motsin kowa ba na komai Wayarsa ke kange a kunnensa yana amsa kiran mahaifinsa sunna dan zantawa, duba da yannayin daren da ya tsala ga kuma yau din ba mahaifiyarsa ce da aiki ba ya sa ya yi kiran mahaifin nasa wanda shima ya takaita firar tasu yana mai sanar masa zasu hadu da safe idan Allah ya nufa Da wannan ya karasa kofar nasa bangaren Bangaren da aka saka iyalinsa, bangaren da aka yiwa gyara na musaman, waje mai nisa da wajen iyayensa sai dai duka a cikin gida guda ne A sanyaye ta yi salama bayan ta daga kiransa Dan lumshe idannuwansa ya yi a hankali ya ce" Shin amaryana ta yi barci ne?" Yumnah dake zaune da kawayenta biyu, sai wasu daga cikin familly dinsu da suke tare da ita zasu yi mata kwanakin da ake yiwa amarya a al'adance ta dan shagwabe fuska tana sake kallon agogo har karfe daya ta gota fa, tun kwaliyarta na walwali har ta disashe bai karaso ba, bayan ance idan aka kawo amarya wani angon a dakin yake salatar isha tare da amaryar dan zumudi da farin cikin kasantuwarta a tare da shi a darensu na farko a tarihi ta ce" Aa bamu yi barci ba" Dan tsai ya yi jin basu yi ba, maimakun bata yi ba, ya zata zuwa yanzu yan rakiyar nata sun yi barci shi yasa yake son lekawa ya ga lafiyarta da yar tsarabar da ya riko mata, ama kuma tunda ya riga ya zo ai ba zancen juyawa "Ina kofar falo" ya fada a nutse sannan ya kama kofar ya murda da sallama a bakinsa kasa kasa sosai kamar yadda ya saba Du juyowa suka yi sunna amsa salamarsa Da sauri cousint sister dinta ta rufa mata mayafinta a kanta tana fadin" Ke yaya zaki bude bayan zaman jiran ya sayi baki muke? Oyoyo angonmu ama gaskiya ka san dole ka sayi bakin nan da tsada dan ka jima a waje" Da dan mamaki ta dago tana kallon Basira, ya salam, tana cewa basu jima da ta gama kwatanta masu kar su masa irin wasan nan ba, in kudin ne su bari zata amsa masu? Ama basira har wani zakalkalewa take yi jiki na rawa tana ta zuba? Mamaki bai gama kasheta ba sai da ta ga Basirar ta amso abubuwan hannunsa, a nan ta so budar baki dan yin magana , harufan bakinsa cikin kamala da kula da tsare hakoki irin na adininsa suka dakatar da ita a lokacin da ya yi maganar cikin dan murmushi sannan ya shige ciki bayan ya nemi afuwa da fadin lalle ba maganar neman ragi ko nawa yar uwarsu ta yanka ya siya in di baki ne Yana shigewa ta juyo a dan hasale tana duban su Basira su dukansu, domin ido suka ringa zarowa kowace na tofa albarkacin bakinta a kan Taufeek din, maganganunsu irin lalle ta dauko zazafa, ashe a kusa da kusa da shi ya fi cika ido, ga halin girma dan kyauta na sakawa a ga tsayin Wada, a cikinsu kawarta daya ce tak bata ce komai ba, ita kuwa kamar barci ne ke kwasarta ko me? Takaicin hakan ya sakata girgiza kai ta nufi cikin a ranta tana ayana da ace dare bai yi ba tsaf zata nemi hanyar rabuwa da su, itafa bata haka a kan Taufeek, Ledojin da ta shigo da su ya dan bi da kallo a lokacin da ta shigo dakin ta so nufar wajen table dan ta ajiye *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣6️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Ajiyewar ta yi sannan ta juyo saman kujerar da yake zaune ta zuba masa ido Murmushi ta saki a bayane ta rufe fuskarta da hannayenta biyu, domin idon da ya zuba mata sai da ta ji har kasan zuciyarta wani irin zirrrr mai kama da tashin tsigar jiki da kuma wani irin nauyin idannuwansa a fuskarta Murmushi ya yi a hankali ya dan miko hannunsa kasa kasa ya ce" Zo " Kamar jira take yi ta daga kafarta da sauri ta karasa ta fada jikinsa tana sake rufe fuskarta a kirjinsa ta saki ajiyar zuciya bayananiya A hankali ya mayar da dayan hannunsa ya rungumeta a jikinsa shima nasa idannuwan a lumshe Kasa kasa sosai ya ce" Na fa yi dati zaki gogi dati a kwaliyarki mai kyau" Idannuwanta ta sake lumshewa a hankali ta ja numfashi kadan tana jin kanshin turaran jikinsa mai sanyin kanshi na shiga hancinta kasa kasa ta ce" Bana jin wani dati, Ya Taufeek i'm so happy today " Hannunsa ya saka ya dago fuskarta ya zuba mata ido Ya yi murmushi a hankali ya kai lalausan lebensa saman goshinta ya mana mata kisss din da ya sakata sake lumshe ido Kasa kasa ya ce" Ina maki barka da shigowa rayuwana Yumnah, Allah ya bamu zaman lafiya" "Amen ya rab" ta amsa ita dinma, sannan ta sake zubawa sajensa ido kamar ta sake rukunkume shi haka take ji A nutse ya ce" Bara na koma" Ido ta bude da sauri tarr ta dora saman fuskarsa Ya koma? Ina? Kasa hakuri ta yi gannin da gaske yake ta ce" Ama ina zaka je ne da daren nan Yah Taufeek?" Da kula sosai ya ce" Ba zan kwana a nan ba sai an gama bukukuwa irin na al'adun nan, you see da kunya na ringa tsalake mutane ina shigowa kuma ina fita" Wani irin makoko da dana sannin barin wadincen rubda rubdan rubabun banzan kwanar mata a yau ya sake shake mata wuya, innalilahi tafia zai yi ? Du irin wankin kwakwaluwar da ta sha na irin kulawar da zata bashi daga yau har karshen rayuwarta dan kar ya dubi kowace irin mace haka zasu wani wargaza mata niya? Wace ta yi mata gyara ta yi mata wankin ido mai matukar girma domin mahaifiyarta ta nemi hakan, an sakarwa matar kudi na mamaki da ya saka ta zage dantse ta yi mata dala dala cewar sai ta ki jikinra ta sakar masa jiki ta yadda babu wata banza da zata shiga zuciyarsa sama da ita, har fada mata ta yi kar ta saki dan tana budurwa tace zata masa raki, komai wahalar da zata sha ta jure ta mike kamar ba ita ba, kuma ta yiwa kanta alkawarin jurewar sai kawai yace zai kwana ba a nan ba? Tana ji tana gani, mijinta ya yi mata salama bayan ya dauko ledojin da ta ajiye ya damka mata cewar na baki ne sannan ya fice ya nufi bangarensa cikin nutsuwa Nan ta zubar da ledojin ta karasa saman shinfidarta da aka yane da farin abin shinfida mai tsada aka baza turaran girma da kannanun flowers masu kanshi sai daukan ido suke ta hau ta kwonta tana rintse idannuwanta hawaye suka shiga bin gefen kuncinta cike da bacin rai ta kasa koda komawa inda suke bale har ta wani kai masu abin ledar cen, hasalima itama yinwar take ji, ama wannan abu da ta shaka ya sa ta ji ta hakura da jin yinwar, ama da bakin naci sai da Basira ta tardota har nan tana faman tsokanarta cewa angon ya fice ya masu sai da safe ita kuma ta makale ko zumar soyaya aka lasa mata? Ta fito mana, Cike da rashin walwala ta nuna mata cewar ta gaji ne barci take son tabawa ga sakon nan ta je masu da shi inji shi, ita ta kwonta sai da safe Da wannan ta yi kwonciyarta ta barsu da surutu tsakaninsu da baje bajajar suka auna a tumbinsu sannan suka kama wajen kwonciya dan hutawa A nutse ya karasa bangarensa Kamar yadda yake jin har wani mintsininsa datin jikinsa ke yi direct bayi ua wuce da babaan tawul dinsa a kafadarsa bayan ya cire rigar jikinsa Ya dauki lokaci a ciki sosai kafin ya fito a nutse ya karasa wajen wrdrn dinsa ya ciro jalabiya ya saka sannan ya saka gajeran wando ya karasa wajen salaya dan gabatar da shaf'i da wuturi Yana gamawa falo ya koma da laptop dinsa, da kuma wayarsa baba sai dan abin rufa da ya janyo domin niyarsa a cen zai yi barcinsa, dan dole sai ya duba laptop din ya yi yan aiyuka masu mahimmanci sannan ya kwonta A lokacin da ya zo dan cin abinci kamar wayarsa ta fado cikin ransa Tsam ya yi yana tunanin inda ya sakata, domin gaba daya ya manta da ita a cikin kwakwaluwarsa Rigarsa da ya cire har ya ajiye saman mashine din wanki ya koma ya lalube, sai dai babu A hankali hoton wayar a hannun KHausar ya shiga dawo masa idannuwansa Idannuwansa ya lumshe ya koma falon sannan ya dauki wayarsa baba ya saka numbar sekatarinsa ya yi kiransa A nutse ya sanar masa cewa kar a tura sakon komai a karamar wayarsa ta fice a hannunsa Sakatarin ya sanar masa cewa ba'a rigai aka tura wani baban sako ba, wanda aka tura na marar lafiyar nan da aka dauko daga kauye ne kawai, ana iya nunin an bacewa lamba idan yana so? Dan shiru ya yi, kafin ua girgiza kai yana fadin kar a ce komai, sannan ya kashe wayar ya karasa wajen cin abincinsa ua zauna dan cika kulunsa ______________________________________ Washe gari da wuri wuri Khausar ta shirya ta fice a gidansu bayan babanta ya bata dari biyuntata nufi cen wajen da ake kafa sunnayen wa'inda zasu iya zuwa su amshi takardunsu da wajen da zasu amsar Sai dai tunda ta je din hankalinta ya nemi rikicewa sakamakon rashin gannin sunnan TAUFEEK a layin wa'inda aka tabatar cewa sun samu din bayan ga sunnan du wani wanda ta ji ance ya samu ciki harfa ita Takardar nan ta mata karantawa ta fi a irga har sai da ta fara shanye sunnayen dake laye ta hakura ta juyo gida ido sai zubar da ruwa yake tana tafe tamkar zata tashi sama, uwa uba yau din hijab din Mama nema ta saka du irin kwaliyar da aka sha jiya kamar ba a fuskarta ba fuska tana neman sinkime mata dan shiga rudani da tunanin me kennan? Tana shigowa a lokacin har karfe goma na safe ta gota ta nemi waje ta shiga rusawa Mama kuka kan ai Besty fa da alama bai samu ba, dan bata ga sunnansa ba Itama Maman hankalinta ya tashi gaskiya, dan harma ta rasa to me kennan? Aisha ce ta ringa kwatanta masu to ko dai an mance ne, ana samun irin haka fa kar su yi hahawar rikicewa, ama ina Khausar kaffafuwa baje a tsakar gida kukanta take kashirban da kyarma ta iya cin maka yar murden da Aisha ta silala tana faman bin Aishar kan ta zo ga dari biyunta nan ta siyo kati a kireshi Mama ne ta hanna hakan, cewarta jiya fa yake ango, kar su kireshi bata so A dole Khausar ta hakura da maganar kiran, sai dai nata sunna da ta gani gaba daya zumudinta da farin cikinta suke neman bacewa bat, abinda ya fi damunta in har bai samu ba fa yaya zai ji? Yaya zasu yi? Sam ta manta fushin da take yi da shi, burinta ta ganshi su je su sake dubawa su ga ta inda zasu bilowa al'amarin Kusan karfe biyar na yama sunna zaune su uki a tsakar gidan ya shigo bakinsa dauke da salama Mama ce ta fara amsawa fiskarta wadace da fara'a tana sake rufe jikinta da hijab dinta sosai tana masa maraba da zuwa Dukawa yayi kamar yadda ya saba ya gaishe da Mama sannan ya yi zamansa saman tabarmar da Aisha ta sake kabewa ba wani kyankyami ko wani dari dari yana duban kwanon dake gaban Kausar tana dibar awara ta kudinta na safe ya mika hannu ya ja gabansa shima ya shiga ci hankali kwonce a lokacin da Mama kuwa ta mike ta yi ciki dan bata cika zama idan sunna nan ba, ba dan komai ba sai dan akoy yan matan, a

Chapter 11 of 47