yi kennan kafin ya fice daga gidan dan zuwa samun liman ya karra amso aduo'i kamar yadda ya saba
A cikin dakin kuwa rarashinta suke yi har sai da ta daina kukan ta dawo sauke ajiyar zuciya
A tausashe tamkar sunne yayun suka ringa nuna mata cewar kowani bawa ai da irin kadararsa, jarabawa ce ta ubangiji kuma alhamdulilah Allah ya basu iyaye masu tausasawa a dukkan rikita rikitar dake iya samunsu yau da gobe a cikin gidansu
Cikin ikon Allah suka samu ta saki jikinta sosai sai ajiyar zuciyar da take ta saukewa kafin A'isha ta dauki wayarta ta buga numbar TAUFEEK bayan tace bara a mata kiran TAUFEEK din ta bashi hakuri tunda da kanta ta gane itace da laifi tace ta masa rashin kunya
Kira na farko bai daga ba, sai a na biyu ne ya daga kuma ya yi shiru ya ki ya yi magana hakan ya sa Aisha yin murmushi dan ta san TAUFEEK ba dai zuciya ba ta ce" Yayanmu barka da warhaka, dama bamu jika ba muka ce bara mu tabo mu gaisar da kai"
Amsata ya yi jin A'isha ce sai kuma ta ba Kausar wayar tana fadin" Amshi aunty ga yayanmu nan"
Wayar ta amsa tana kallonsu sunna dariya suka fice dan yadda ta zaro ido irin kuma sai ki bani?
Shiru ya mata kamarma ya ajiye wayar, sai dai ita ta san bai ajiye din ba dan baya mata haka du fadan da zasu yi kuwa
Hanci ta ja wani hawayen ya bale mata a sanyaye ta ce"Ka yi hakuri dan Allah"
Wani irin tsinkewa gabansa ya yi ya fadi har sai da ya dakatar da rubuta code din bankinsa da yake yin transfer ya saurara yana sake tabatar da kamar kuka take yi kamar kuma mura take, sai dai to me zai sakata kuka ita ? KAUSAR fa mutun ce mai mugun hakuri da kuma juriya, har ga Allah shi yana girmama hakurinta da kawar da kanta a kan abubuwa da dama, kuma ya san dai fadansu ba shine zai saka ta yi kuka ba, shi yasa ya ce" Mura kike yi ne?"
KAUSAR ta dan yi jim, Sa kawai ta fashe masa da kuka har tana shasheka ta ce" TAUFEEK...... TAUFEEK ka gani ko?????"
Idannuwansa ya rintse a hankali ya idasa saka code din ya tura ya rufe computer sannan ya mike ya kashe kiran ya fito daga office din nasa yana lalubar aljihunsa dan jin inda ky dinsa yake ya nufi wajen dankareriyar jeep dinsa dake ajiye ya bude ya shiga yana dan lalubar gashinsa ya kunna sannan ya harbata kan titi
Silalewarya ta yi tana hawayenta, bayan ta yi tunanin gaba yake mata shima ta rintse ido tana tunanin to mema ta masa ai du laifinsa ne ta yi zuru zuru ta jiyo muryar Abansu yana fadin" Shiga mana TAUFEEK, ke Rukaya shinfida masa tabarma , nima ba zama zan ba zan koma nan na dawo"
Firgigit ta mike daga kwonciyar ta bi Rukaya da ido da ta fitar da tabarmar ta shinfidawa TAUFEEK wanda ya cire takalminsa ya zauna yana kunce agogonsa ya ajiye gefe kafin ya dago kansa ya zuba mata ido
Abinda da mai manyan idannuwa masha Allah idon yai mata zuru zuru ya yi ja , haka abin kwalin du ya zubo sai wani wiki wikitu take da idon tana kikiftawa shi kuwa yana sake kallonta har ta karaso tana kallon A'isha ta janyo masa ruwa a rijiya a zuba a tsaftatacen kwanon silba an ajiye masa
Habarta ta ringa sosawa a hankali murya shake ta ce" Da kana anguwar?"
Hannunta ya bi da kallo dake dauke da kunshi ja ya dan tabe baki ya ce" Ke kukan me kike, ke da waye?"
Kasa kasa ta yarda harara ta ce"
ππππβ€βπ©Ήβ€βπ©Ήππππ
*DA CIWO A ZUCIYATA*
ππππβ€βπ©Ήβ€βπ©Ήππππ
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 7οΈβ£
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicΓ©
Lait de nuit
Parfums dΓ©sodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*WaΙannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwaraiππ
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuΙi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mataπππππ
Kasa kasa ta yarda harara ta ce" Kukan me zan yi ni kuwa, ba kukan da nake yi"
Da haushi haushi ya ce" Kin ga ya isheki haka, zaki fada min kukan me kike yi ko ba zaki fada ba?"
Ido ta zarro tana kallonsa ta ce" Besty dukana zaka yi?"
Shima ya kare mata kallon da haushi ya ce" Idan ta kama a dake kin ai option ne, meye wannan a fuskarki du ya maki baki ? "
Sai a lokacin ta shafo sai kuma ta tuna ashe fa kwali ta saka itama a ido
Daria ta saka kasa kasa tana sake gogewa da kyau ta ce" Malan ya ka ga mata? Kwali na saka kuma na je na yi kitso harda kunshi....."
Ta karashe tana wani basarwa ta wani hade fuska irin ta kankaro wulakancin nan
Murmushi yake yiwa dariyar su Rukaya dake mata tsokanar wa ya ga ba saban ba
A tausashe ya ce" Rukaya kukan me take yi wannan matar? "
Rukaya ta kalli auntynsu, ta kalle shi sai ta samu kanta da kasa sanar masa, tunda bata san ko auntynsu zata so hakan ba
Itama da basarwa ta ce" Ba fa abinda nake yiwa kuka, ra'ayi ne ai shi kuma kuka kamawa ne"
Shiru ya mata dan ya kula banda tashin balagar rashin kunya harda neman fitina a wajen yar nan yau
Hira suka shiga yi tsakanin su hudun, duda su Aisha hirarsu ta fi karfi, su hirarsu a kan abinda ya shafi karatun fa ta kirta ba dadi a kai ne da kuma hira irin ta gidansu haka wace dai yawanci abokanai ke yi idan sun hade ne kawai suke yi, yan matan na aikinsu su kuwa sunna zaune har dai hirar ta yi nisa sosai sannan ya tunna abinda yake son fada mata da kula ya sanar mata abinda Abansa ya yanke kan maganar aurensa da YUMNAH wace ta san da zancen dama kuma ta san da an yi zaman ba'a dai yanke bane
Farin cikin da ya wanzu a fuskarta sai da ya saka A'isha wace jikinta haka kawai ya yi sanyi tana kallonta dakatawa ta zuba mata ido sosai tana kallonta a lokacin da KAUSAR ke ta murna tana ainahin fitar da murnarta kafin ta ce" Allah na gode maka zan aurar da besty, tsayama wai kennan kwana nawa ya rage? Bai fi arba'in da uku ba fa, gaskiya aiki ja a gabana, kuma tun yanzu zan fitarwa da yan mata da samari anko, ta yan mata daban ta samarin daban du wanda bai min ba ya cira bata nuna ba, ka ga fa azumin da za'a fara jibi da sati saya zamu shiga aji mu yi jarabawar ai ni komai ya zo min daidai ba tunanin jarabawa bale na kasa kwaso shoki dan kuwa sai na kwaso shoki"
Ido ya zarro ya ce" KAUSAR shoki? Dama kina rawa?"
KAUSAR ta yi dariya tana sakar masa harara ta ce" Komai ai da mafari, a aurenka rawa zan har kafafuwana su yi ciwo, me kake tunani?"
Daria ya yi yana girgiza kai dama ya san farin cikin da zata nuna idan ta ji mai yawa ne, gashi ko YUMNAH dinma bai hadu da ita ba bata san maganar ba , domin da ta sani ya tabata da Yumnah ta neme shi ta fada masa
Haka dai ya cika dare domin sai bayan magariba ya tafi har Mama ta zo nan fa ta sanarwa Mama maganar auren sai murna take inda mahaifiyarta itama ta tayasu murna har tana fadin" Lalle daga yau ganninki sai an shirya , watau kirjin biki ba dama, kema Allah ya nuna mana naki KAUSAR na tabata har TAUFEEK sai ya gayato mutanen da ba yan gari ba"
Daria suka yi gaba dayansu, suka sake cika dare sunna hira kowa ya je ya kwonta
A daren ne Aba ya zauna da mamansu ya sanar matta abinda ya yanke, ya fada mata ba zai tayarwa da Kausar hankali ba, zai ci gaba da addu'a, ama yan uwanta a ba manema aurensu damar su turo dan ba za'a ce sai ta samu ba tukunnan a hade
Karshe dai da tsokana suka kwonta domin ya shigo da wani katon asusu ya bata kudade yana fadin a zuba a adana masa shi yanzu kuma a dole ya kule ciki ko ya yiwa yan mata gado da gara............
Daga wannan ranar KAUSAR ta daina gannin magana makamanciyar haka,
Sai dai tana gannin yan shirye shirye na auren kannenta
Haka kuma gefe guda Aisha da Rukaya sun sakota a gaba ga karatu ga jarabawar karshen shekara su a dole sai ta ringa kwaliya tana gyagyarawa irin nasu bayan ita ta san ba zata taba yin irin nasu ba, za dai ta kamanta
Wannan jarabawar kaf dinta da TAUFEEK aka yi har karshe, kuma cikin ikon Allah idan aka shiga aka fito suka zauna sunna dudubawa ba laifi ya amsa tambayoyi masu yawa harma ya bata mamaki domin bata yake ta rike ya ringa fada mata amsoshin da ya bayar itama sai ta ga hakan ne ta bayar hakan na nufin ya leka karatun ya duba sosai, sai ta ji nutsuwa a zuciyarta harma ana gama jarabawar da sati daya ta je ita da su Rukaya suka fitar da anko ta maza shada ruwan sararin samaniya , ta mata atampa mai tsada mai kyan gaske mai sirkin ruwan sararin samaniyar da baki baki wace ke iya yiwa kowace fata kyau
Daga kasuwar direct gidansu TAUFEEK suka wuce domin sun sanar da Mama cewar idan sun cire zasu kaima mamansa dan sun yi waya tace tana jira idan KAUSAR din ta ciro anko din ta kawo mata kalar da sunnan shagon da aka fitar dan a sayo na jama'ar gidan
Kasancewar Azumi ne basu samu matan gidan a falo ba, kuma yau girkin Maman ne sai kawai suka samu Maman suka nuna mata ta yaba sosai sannan ta nemi da su zauna su sha ruwa kafin su tafi, ama suka nuna sun baro Mama da aiki a gida, a dole ta salamesu da kyauta kamar yadda ta saba duda sai da ta kusan kaiwa Kausar rankwashi a kan ta nuna na zasu amshi kudi ba ga wata leda mai dauke da kaya nauyi jikit wai ankon safensu ne, atampar da suka fitar ta rana ce , da jin ledar ta yi nauyi ba iya ankon kadai bane
Haka suka fito sunna ta godiya ISHRAT na biye da su tana labari suka nufi bangaren Hajia, domin ko giyar wake ta sha ba zata shigo ta fita bata je ta gaisar da hajiar ba
Hajia na zaune saman kafet tana kallon gabas sai musmus take da baki ga dukan alamu carbi take ja dan kuwa tana ta ja tana motsa bakinta ne, dakinta dauke da kanshin turaran wuta ya game ko'ina sai dai yau ba hayakin nan bane mai yawa babuma hayakin kamar yannayin dakin ne da ya saba da kama turare idan bako ya shigo zai ji kanshin ama ita dake ciki ba lale bane kanshin ta ji shi
Da murmushi take amsa gaisuwar KAUSAR har KAUSAR ta gama gaisheta a duke sannan ta mike ta zauna kusa da ita kadan tana ciro ankon da hannu biyu ta mika mata ta ce" Hajia, dama daga ciro ankon muke, kin ganshi nan, wannan ne na mata ga kuma na maza nan"
Hajia ta saki murmurshi ta karbi atampar, tana daf da yin magana aka daga labulen kuryarta aka leko kadan , hakan ya sa ta dago ta zuba idannuwanta tana kallo hadi da kankance dubanta
Baki ta tabe ta cire kai kasa kasa ta ce" Munafurci dai ba abun yi bane, aikin mata du sai kaura yake yi yana sarkafar maza, in ba tsohon munafurci ba ai da na tsaya ina maka magana shiru ka min irin ka yi barci, ama yanzu kana jin maganar ita wannan ka wani leko, uhum zamani mai abin mamaki ku duka bakwa jin tsoron Allah, ace wai iyayenku na kallo ita wannan din itace kawarka kai kuma abokinta, a gaban mai kwanonima sai a zanta, ai tunda yanzu na yarda eh kawancen ne abu daya nake jira na ga na mika ka dakin Yamaniya ita kuma itama dakin miji in ga iya shege, ai nasara ba kowa ya samu galaba a kansa ba, na tabata in kai ka fi karfin Yamaniya ita wannan mijin da za'a aura mata zai fi karfinta, ni abinda na kasa ganewa wai me kike jira har yanzu ba'ai maki aure ba?"
A'isha ta turo baki tana ji uwa ta mike ta bar auntynta a dakin nan ta yi tafiyarta, itafa dama tsoron tsohuwar nan take yi sosai, babu wanda ta bari, da ta ji maganar kawancen auntynsu da jikanta shigarta gidan ya fi a irga, har cewa take yi a dai ringa saka ido kar a ringa barinsu su kadai lau a haifo masu dan besty
Da kyar ta hakura da zumuncinsu sannu a hankali har take kaunar Kausar, ama hakan baya hana ta ringa yanko zance marar tsari haka kawai
Fuska ya daure ya fito gaba dayansa ya kai zaune yan duban Kausar ya ce" Daga ina kike ke?"
Hajia ta sake zuba masa ido tana kankancewa ta ce" Daga inda ka aiketa ubanta!"
KAUSAR ta zarro ido sai kuma ta dauke kanta tana murmushi ta nuna masa atampar dake hannun hajia ta ce" Ankon muka ciro ka manta ne na fada maka jiya cewa yau zamu je kasuwar? Biyu na raba na hannun nan na wajen Hajiya naka ne ka gwadawa abokananka ni kuwa jibi in sha Allah zan fara gwadawa sauran freinds"
Ankon ya dan kalla sai kuma ya yi diffg bai ce masu komai ba, Hajia kuwa har yi take kamar zata bude masu baki ta kalli wannan ta kalli wancen, cen dai ajinta ya tsimkota ta ce" Ni ko a kauye, zamanin da nake ta balarabe, kafin kawata ta kwacen shi karya ne ace a kawancenmu ni in ringa yiwa kawa surutu ta kyale ni, wannan Ζawance naku lalle akoy alamar tambaya, ace kina surutu ya wani kyale ki? In nice in na kumaa kulaka in zama tsintsiyar sharar kurma!"
Aisha ta mike tsagal tana tatara komatsansu tana fan murmushi ta ce" To bara na tare mana taxi Aunty ""
KAUSAR kam dariyarta take ci, ita fa walahi lamarin hajia baya wani damunta, baya taba bata mata rai, kuma tsufan HAJIA tsufa ne mai kyau, domin koda yaushe tana rike da carbinta tana ja, wannan zamanin da ya zama abin tashin hankali wani tsufan dake zuwa a gigice? Rikicinta kuwa tafe yake da rashin munafurci da bata iya ba, wasu bama tsofin bane a gaban idannuwanka zasu nuna maka so a bayan idannuwanka kuwa tamkar su soka maka wuka su daina ganninka a cikin duniyar kwata kwata
Fitowar da ya sake yi da ky a hannunsa ya ce" Tashi mu je" ya saka HAJIA sakin murmushi tana kallonsa ta ce" Ba dai rai na bata maka ba ko? Ai ka ga ciwon kai kake yau kuma kace tare zamu sha ruwan ko? KAUSAR tayani gani kamar ya kumbura fuska?"
KAUSAR ta girgiza kai tana murmushi ta ce" Hajia yama yarda ya maki fushi haba dai, bai yi fushi ba ko besty?"
Gannin ba dai zata tashin ba ya saka shi yin gaba , hakan ya sa ta mike da sauri, hajiarma ta mike tana fadin" Bara in dubo maki yar tsaraba Y'ar nan, yadda kika san me bana iya na ganki ban dan miko maki wani abin na tsaya tsaya ai na zai tafi ya barki ba"
KAUSAR na faman Hajia dan Allah ki barshi na gode Allah ya saka da alkhairi ama sai da ta fito da bak'ar leda tana murmushi ta ce" ke kuwa, sakon Babanki ne duda yau bai aikon da goron ba, ki ce ina gaishe su kin ji? Allah ya maki albarka"
Amsa ta yi bayan ta rage tsayinta sannan ta ringa godiyar itama ta fice ta fito tana ta waige dan gannin inda zata ganshi
Da sauri ta karasa wajen motar yar sumulmula fara dake parker ta bude gabam ta shiga ta rufo tana fadin" Ka ga fa da bari ka yi muka shiga taxi kai dake ciwon kai?, Wai ciwon kan menene haka?"
Hanci ya dan ja kadan yana tashin motar ya fara tafia da su a hankali ya ce" inaga rashin isashen barci ne, shi yasa yau ban fita ba na huta"
Kai ta gyada ta ce" Banama kana jan tafsir ne?"
Kai ya gyada kawai bai bata dogon amsa a wannan tambayar ba, sai kuma ya ce" A wani shago kika fitar da ankon nan?"
Dan murmushi ta yi ta ce" a shagon Elhaji Habu ne, ana mutumen nan bashi da kirki kawai sharin mutane ne, mu dai ya mana mutunci sosai"
Baki kawai ya tabe har suka karasa gidan bai kuma cewa komai ba sai tatausan karatun dake tashi a hankali a cikin motar
A kofar gidan suka tsaya Aisha ta ringa sauke kayansu murna fal zuciyarta tana kaiwa ciki sannan ta dawo ta dan rage tsayi tana yi masa godiya ina ya zabga mata harara ya ce" Malama mike ki bace min da gani ni"
Da daria ta mike din ta yi ciki
KAUSAR da kula ta kalle shi ta ce" Kamar ranka a bace ko ciwon kan ne?"
"Na gaji ne" ya bata amsa , sai kuma ya kalli agogo ya kalleta zai yi magana ta sake fadin" Ko na fadawa Mama ta maka kunun ayar nan? Na ga kamar kana sonshi?"
Ido ya zarro da sauri ya girgiza kansa, wanda hakan har ya so dan bata mamaki, sai kuma ya cire mata mamakin ta hanyar fadin yau ba zai fito ba zai je makaranta ne, a zuciyarsa kuwa yana ambaton ina shi ina kunnun nan? Abu dadi a baki yana sha kamar kar ya kare ashe ashe yana shirya masa tashin hankali ne? Saboda kunnun ayar nan da ya sha jiya a gida ya gaza barci har kusan biyu na dare yana fama da ciwon ciki, ga tarin gajiyar kasuwa da ta huldodinsa na gida da waje, a haka a dadafe ya kai kiran sallar fari , an yi kira kuwa ai ba barci dole ya sake fitowa ya sha madara mai dumin gaske har yana zufa, shi dai ya rainawa kunnun aya wayo kuma ya yi tirrr da shi dan bai kyauta masa ba
Gannin yau kamar yan shiru shirun sun fi komai yawa ya sakata yi masa salama ta yi shigewarta gida tana cire hijab dinta tana shafa cikinta da yake ta sabewa saboda abin azumi a jikin nata shi kadai ke raguwa sosai sanadiyar azumi ama ba wai shafewar dindindin ba, dama da azumi haka yake mata yakan ragu sosai, har bayan azuminma yana iya daukan kusan wata biyu bai koma yadda yake ba, sai fatar jikinta dake dan karra gyaruwa daga yannayin haskenta kadan ta karra yin luwaiwai, ko dan zaman gida ne da hutu ba hanyar school?, Itafa ba fa fara bace aa, fatar mahaifiyarta ce mai haske haka, irin bakin nan mai haske mai kyau, to haka yannayin fatar jikinta take
"KAUSAR, wannan kaya haka jama'a mutanen nan su basa gajiya da dawainiya ne Fisabililahi?, Shin auren yaron nan ni me zan yi na kyautatawa ga ahalin nan?"
RUKAYA dake ta farin cikin itama domin sun zagaye kayan sunna ta dadagawa ne ta ce" Mamanmu, sai dai a je tunda safe idanma da hali a kwana a cen ko kwana biyuma , in ba wannan ba ina muka ga abin basu?"
Mama ta yi murmushi ta ce" Gaskiya ne daurin aure har amsar amarya da mu za'a yi shi, ama kuma du yawan arzikin mai arziki yana jin dadi idan ya ga an masa kara an kula, in sha Allah komai kankantar bajintarmu zaki ga mahaifiyarsa da shi kansa sun ji dadinta, duba fa ki gani, idan ta tashi ware mana abu harta ni sai an ware nawa , lalle zumuncin mace da namiji akoy jin wani iri, ama idan har da kare dokokin Allah sai nace na Kausar da TAUFEEK alkhairinsa muke gani, idan an yi aure kowane ya kama gabansa kuma shikenan sai zumuncin mu iyaye in mun rike"
KAUSAR ta yi murmushi tana kaiwa zaune hadi da neman wajen kwonciya ta ce" Mama, yinwa nake ji"
Mama ta dungure mata kai ta ce" Zaki fara ko?, Ke kam ki yi kokari ki daina yiwa ciki bauta, wannan lamari naki da cikinki abin haushi, ace mace kadan ta ji yinwa ta kama raki kennan?, Azumi dai baya son haka, tashi maza yau ke zami tuka tuwon sahur kin ga na shinkafa za'a tuka kuma kin fimu iyashi"
Baki ta zumburo ta ringa kyakyafta ido tana jin gaba daya kasala da juwa sai yanzu suke lulubeta, ama a haka dole ta mike ta kama aikinta dan kuwa kowa da aikinsa basa barin Maman ta yi komai har a sha ruwa sai iya aikin Baba wanda har yau suke mamakin irin yadda Mamansu bata sakar masu aikin mahaifin nasu, lokuta da dama idan sun yi nacin hakan sai tace to ita kuma a ina zata samu ladan ? Kowa ya yi inda yake da lada kawai su barta da aikin mijinta (wannan din wata hikima ce da hanyar da zaka iya ba yayanka tarbiyyar sanni da kuma sake rike girman miji a bayyane da kuma badini, domin a rayuwa yaya babu abinda ya kai iyayensu girma da daraja, sukan dauki dukkan abinda iyayensu suka dauka da daraja suma da daraja ne, idan har uba na so ya'yansa su raina shi ko su ringa yi masa biyayar dole to ya ringa wulakanta mahaifiyarsu a gabansu , a cikin iyayen kuwa wace ta fi gagawar saka zuciyar Ζ΄aΖ΄anta biyaya da daukan launin abinda take so itace uwa, uwa idan ta so za'a gyaru, in ta ki za'a lalace kuma a kan turbar da ta dora ne, Muna karbe du wani motsi na iyayenmu muna hanna su yi dan ba zamu iya muna zaune su motsa su yi wani abin ba bayan gamu a zaune, hanyar da suke bi ta nuna mana na mahaifinmu bamu da hurumi a ciki na matukar shiga zuciyarmu har muma muna gina tamu rayuwar a haka, idan har a gidan aure irin haka ta samu kuwa inaga da izinin mai sama jin dadin zaman auren zai samu domin akoy gannin kima da biyayar wanda ya ajiyeka...., Allah ya dafa mana)
A lokacin da Baba ya zo aka sha ruwa aka wuce masalaci sai kusan goma suka dawo suka zauna fan cin abinci, a kuma lokacin ne Aisha da zumudinta ta kawowa Baba kayan
ππππβ€βπ©Ήβ€βπ©Ήππππ
*DA CIWO A ZUCIYATA*
ππππβ€βπ©Ήβ€βπ©Ήππππ
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 8οΈβ£
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 47