da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Da dan Mamaki Khausar ta juyo dan gannin ko dai bata jita bane?, Sai ta ga aikinta take yi bata kuma bi ta kanta ba
Da wani mamakin ta dan sake dubanta, sai ta dan koma baya ta sake yin salama wannan karron da dan karfi
Sai dai abin mamaki bata ajiye maganarta ba ta ga Yumnah ta yi wani ecpression da fuskarta sannan ta dan ja tsakin da sarai ta ji shi ta saki abin zuba abincin dake hannunta ta juyo tana cire safar hannun nata ta dangwarar a nan da wani yannayi irin na wulakancin nan dake bayane ba a boye ba ta ce" Na ji ki, ban san inda yake bane"
Daga haka ta juya da saurin tafiya ta koma kicin
Baki da hanci ke bude Khausar ta rakata da kallo har bata ji takun saukowarsa ba sai muryarsa da ta ji ya ambaci sunnanta yana idasa saukowa da mamakin ganninta dashe a nan baki bude
A dan tsorace ta juyo da madaukakakin mamakin da bai barta ba ta zuba masa ido, sai kuma ta dauke dubanta a kansa na tsarewa da kallo, domin farar riga ce a jikinsa ama botiranta a bale sai ash color din snglt a ciki mai siraran hannu , hakan ya dan bayana wasu sashe na sirrin jikinsa wanda bata taba ganni haka kai tsaye ba
Hannunta na dama ta saka tana dan murza goshinta cike da shiga rudu da kuma yar kunyar yannayinsa ta dan juya ta ce" Am, barka da yanzu, dama ina kiranka ne baka daga ba sai na zo , Mujaheed ne ke cen kofa nake so idan ba damuwa a shigo da shi ko a fada masu na leka ......???"
Ta idasa maganar tana dan ajiye zancen da dan sake duban hanyar kicin din nan
"Ok" kadai ta iya ji daga bakinsa, sai kuma ta ji yana magana da waya cewar a bar bako ya shigo a nan kofar gidan
A hankali ta dan juyo dan yi masa salama, sai ta ga ya bala boturan, hakan ya sa ta samu sakewa ta dan dube shi ta bi wayar dake hannunsa da kallo, wace ta tabata itace mai dauke da numbar da ta yi ta kira tun dazun bai daga ba, ta so kwari yi masa korafin hakan, sai dai wani abu da ya dan tsaye mata a kahin zuci na yannayin da matarsa ta yi yanzun ya dauke hankalinta, a hankali ta juya ta ce" Thank you" sannan ta yi waje
Kansa ya mayar a zaunen da yake jikin kujerar ya lumshe idnanuwansa
Shin ta ina zai bi ya raba wannan alaka? Barin wannan alaka dan ta ji dadi anya daidai ne?
Idan ya yi duba da tarin abinda ya sani shi a kan manemin auren aminiyarsa kuma kanwarsa in ya yi shiru ya yi mata adalci daga ita har iyayenta kuwa? Shi dai ba abikin yin Mujaheed bane, abinda ke iya sab hanyarsa da tasa daya ce tak idan shagonsu na son sari a kampani, bayan wannan babu ta inda wani abu zai iya hada su, da ya dan kwatanta ganninsa sun zanta a kan lamarin......, A gaskiya baya tunanin in har zai iya yin hakuri ya zuba ido KHAUSAR ta auri mutun irin wannan bayan du irin wahalar da ta sha ta rayuwa a kan wannan subjet na mijin aure ba
Kwata kwata shi din ba mijin mace irinta bane
Ba dan aljihunsa ba ko yannayinsa ba, sai dan Halayarsa da suke boye wajen yan mata ama suke bayane wajen wa'inda suke iya sani
"Honey, na kawo abincin nan ne?" Yumnah ta katse tunaninsa da sanyayar muryarta da yannayi irin na macen dake gabar son birge abin birgewarta
Idannuwansa ya lumshe a kanta , sai kuma ya mike yana dubanta ya ce" Ina zuwa Yumnah"
Daga haka ya nufi hanyar fita a falon
Da ido ta bi shi, kirjinta na dokawa da tunanin ta yiwu wancen abar zai bi?
A hankali ta silale saman kujera ta dafe gaban goshinta da hannayenta bibiyu tana tunani, tunani take yi anya kuwa tana cikin hanyyar da zata kubuta daga wannan mugun abin dake faruwa a aurenta? Duka duka yaushe aka yi auren ama ita ta hadu da kalubalan zaman auren fiye da tunanin mai karatu, babu lokaci idan wannan mata ta nemi layin mijinta yana iya amsawa, babu lokaci idan ka ganshi kana iya ganninsu tare, ba dangin iya ba na Aba an kwaso katuwar mace an kawo gidan da mijinta yake da ta dan nuna sai ya nuna tamkar yar uwarsa yake kallonta? Anya ba zata yi tashi irin na kirki dan gannin ta samarwa kanta mafita daga wannan abin ba? .....da wannan bacin ran ta yi zamanta a nan tana neman mafita da tunaninta
Fitar da ya yi shi kuwa bangaren iyayensa ya nufa , domin tunda ya zo bai shiga ba, ashe rabon ya tarda abinda yake faruwa ne, rikici tsakanin iyayen nasu , Hajia na zaune tana ta kashe wuta tana fada domin mahaifinsa baya nan
A hankali ya fice a falon, ba dan komai ba sai dan gannin halin da suke ciki, ya tabata in dai yace zai zauna to yana iya haduwa da bacin ran da zai saka ya kasa hakuri
Sometimes, yakan ji kamar ya dauki mahaifiyarsa ya kaita nesa da wannan rayuwa, ama idan sun kadaice sai ta ringa kwatanta masa cewa wannan din ba damuwarsa bane tsakaninta ne da matan mahaifinsa, ya barta zata iya kwatar kanta tunda ita ba yarinya bace, kuma zaman aure take yi dole zatana haduwa da kalubale na yau da gobe, shi dai ya ci gaba da addu'a ya kuma kiyaye huldarsa ta yai da gobe da kowama
A bangaren Khausar
Tunda ta shiga motar bayan ya nuna mata cewa in bata shigo ba a ina zasu zanta? Duba da bata kawo masa kujera ba kuma bai ga wajen zama ba, kanta ke kasa tana sauraron irin tarin mitar dake bakinsa da kuma rikicin dake cikin bakinsa
Gaba daya rigimarsa idan ya jema ya dawo a kan TAUFEEK take sauka, hakan sai yake bata mamaki, ama ta nutsar da tunanintaa tunawa da wasu kalaman da ta ringa haduwa da su cewa dole fa zata iya haduwa da haka, ba kowaki namiji bane zai yi hakuri da mu'amala irin wannan dan haka a sanyaye yau ta budi baki bayan ta dago ta masa duba kamar sau biyu ta ce" Na san ba zaka taba yarda cewa mu'amalata da TAUFEEK zumunci ne kawai ba Elhaji, ka sani zumuncina da shi ya hada zumunci da iyayenmu, ko yanzu da ka ganni a gidansu Hajia ce ta zo da ni, a bangarenta nake kwana ina tashi, bayan wannan Elhaji maganar mu'amalata da TAUFEEK a yanzu da nake budurwa take da karfi, idan na yi aure du abinda mijina ya shinfida min ai dole zan yi biyaya in dai hakan bai sabawa adinina ba, dan Allah ka yi hakuri ka cire wannan magana daga ranka kwata kwata"
Har ga Allah, bai taba jin salama a maganarsu kan TAUFEEK ba irin nna furucinta na yau, ko dan ya kasance mutun mai son a girmama shi? A yanzu yana jin zai iya tunakarar wannan masifafiyar matar da ya kakabowa kansa take neman hanna masa rawar gaban hantsi, mace sai fitina, mace sai neman fitina, yanzu abinda ya fi jin tsoro maganar nan, da ya kwatanta ashariyar da ta dura a kan yarsa sai da cikinsa ya juya, ama abu daya ya sani ita din mayar kudi ce, zai kwatanta lasa mata zuma ya san da wahala ta iya kin amincewa da maganar auren nan, shi fa har mafarkin Khausar yake gashi ga ita matsayin matar aure, kuma ya tabata da wahala matarsa ta fi karfin Khausar dan kuwa in me take takama a jikinta Khausar ta damata ta shanye
"Mun yi magana da Aba, Aba ya nunan bacin ransa dan na je jiya da jus, yace baya son haka kar na kuma, sannan ya min maganar na fito idan da gaske nake" Ya fada yana dubanta
Khausar ta dan dago ta dubeshi sau daya ta sake dauke dubanta a kansa, a ranta tana tunanin yauwa ga abinda ya hasala Aba, dan ya masa magana ba sau daya ba, ba sau biyu ba, ama shi kamar baya jin me ake nufi da kar ya yi
Ya dan sake muzgutawa irin rikakun mazan nan da suka isa da gidansu ya ce" in sha Allah karshen watan nan za'a kawo sadakina, shikenan zaki zama tawa ko Khausar?"
Khausar ta sake sada kanta, tana jin wani abu na dan ratsa zuciyarta mai shige da salama
A hankali ta ringa jin kamar wani abu mai kama da kwonciyar hankali da nutsuwa na game zuciyarta, har dan murmushi ya wanzu a saman fuskarta ta yi gagawar rufe fuskar cike da jin kunya
Hakan ya sa ya sakota a gaba da zolaya dan ya riga ya sani Khausar akoy kunya kamar me
Da wannan ta masa salama ta koma ciki, shi kuwa ya juya ya tafi daga gidan yana sake kallon gidan da gyada kai, shi da kansa ya san nan ana magana ne ta babansa ba wai yayansa bama a dukiyar, zai yi gagawar dauke matar nan ko dan ya ringa fada a cikin maza cewa ya yiwa ELHAJ TAUFEEK kwacen mace.....
Da Khausar ta koma bangaren Hajia ta tarda ita zaune saman kujera da waya a kange a kunnenta
Zama ta yi bayan ta cire hijabin na Hajiar a kasa daf da Kafar Hajiar ta dan kamo kafar tata ta shiga matsa mata a hankali a hankali
Jim kadan Hajia ta gama wayar ta dubeta da murmushi tana amsa gaisuwarta kafin ta ce" Kin zo bana nan, da na dawo kuma sai wancen yar tace kin yi bako, wanene ne ?"
Khausar ta sada kanta tana dan murmushi ta ce" Hajia, wanda yake zuwa wajena ne "
Hajia ta dan yi shiru tana kallonta, a hankali ta ce" A ina yake, menene sana'arsa? Saurayi ne ko magidanci?"
Khausar ta dan sauke numfashi a ranta ta ayana' To Fa Allah ya sa kar a koreni dan haushina'
A nutse ta sanarwa Hajia amsar Tambayoyinta
Hajia ta dan tabe baki tana fadin" Ni fa ban cika son namiji mai kai kawo ba kamar mace, to me yake jira da bai fito ba? In fa baya yi karma ya nemi bata maki lokaci a banza a wofi, gwara ya gusa wani ya shigo!"
Khausar dai kasa cewa komai ta yi, Hajia ta janye kafarta da kula ta ce" Tashi ki je bangaren iyayenki, in kin samu wani a falo ki gaishe shi ki haye sama wajen Mamanku tana kiranki"
Mikewa Khausar ta yi ta dauki hijabin ta saka sannan ta tafi
Da kallo Hajia ta rakata kafin ta dauke dubanta ta dan sake lumshe idannuwanta tana ci gaba da jan carbinta
Sai dai a kasam zuciyyarta wani abu ke damunta ainun dangane da matan yaron nata, akoy wasu furuci da ta tsinta a yau din da suka tsaye mata a kahon zuka, sun mata bake bake har sunna son hannata wani abin cikin walwala,
Ita dai yar hausa ce bata cika daukan magana a shantakai ba, magana kuwa irin ta gannin baya bata cika sonta ba, shi yasa ta shiga a hali na tunanin shin zafin kishi ke damun matar ko harda matsala wata daban?......
(Wannan kennan)
Khausar jiki ba laka ta karasa dakin Maman TAUFEEK , sakamakon irin amsa gaisuwarta da mutanen nan suka yi a lokacin da ta shigo da yar fara'arta
Ta samu Maman TAUFEEK din saman salaya ama kuma ba sallah take yi ba, tana dai jan carbi ne
Da fara'a sosai a saman fuskarta take amsa gaisuwarta sannnan ta mata nuni da wajen zama ta karasa adu'arta ta shafa ta juyo fuskarta a sake ainun ta ce" Khausar yaya bakunta ya fama da kakar taki?"
Khausar ta yi yar dariya ta ce" Alhamdulilah Mama"
Mama ta mike tana nufar wajen wrdrb dinta ta bude tana fitar da wasu manya manyan ledoji masu dauke da sunnan wani rantsatsan kampani da ake yayi a garin masu kawo lesuka da atampa da shada da kuma abayoyi ne su mayafai dai da sauransu
Ajiye su ta yi nan bakin gado d taimakon Khausar sannan ta shuga fitar da su da kula ta ce" Na cewa aminin naki gobe ba zaki je asibiti ba dan ina so mu fita, ya so ma ya kiya dai na fada masa ba fa zaki je ba ya sanar masu dan zamu je wajen mai dinki da kuma shagon Hajia FUSAM mai turaren wuta"
Maganar cewa ya sanar ba zata je ba ta so ta dan sakata a tunani, sai dai maganar sako sunnan FUSAM ya cire mata tunanin da dan mamaki tana bin rantsatsun atampopi da lesukan da Maman ke fitarwa da kallo ta ce" Lah Mama kin san Fusam kennan?"
Mama ta yi murmushi ta ce" na san Fusam Daughter ai wajenta nake siyan turarukana, yaya kika ga lesukan nan sun birgeki kuwa?"
Nan fa ta ringa shafawa tana fadin cewa babu na yarwa baki daya sun tafi da ita tun daga yannayinsu da color dinsu a kalla sun kai goma ko fi dan ba irgawa ta yi ba ama kuma sun rikitata
Itama Maman ta ji dadin haka, dan haka ta umarceta kan ta je da su bangaren Hajiar gobe sai su kai dinki in sha Allah, harda dorawa da fadin a ciki abinda bai mata ba sai a cenzo mata dan a online ne ne ta yi siyayar
Mamaki, tsoro, rasa abin cewa ya saka Khausar sake tambayar Mama wai tana nufin nata ne?
Mama ta gyada kai tana mayar da su ciki harda mayafan yan yololuwai da su domin shara shara ne ama rantsatsu irin na yan gayun nan yan mata
Gaba daya sai Khausar ta rasa abun cewa, ta rasa me zata ce, ta rasa ta inda zata yiwa Mama godiya, ta gaza zaune ta gaza tsaye har sai da Maman ta nuna mata bafa ta son haka ta yi addu'a kawai ta yi shiru ita yarta ce dan ta mata alkhairi ba wani abu bane
Da zumudin wannan ta koma bangaren Hajia, nan fa Hajia ta saku daga yannayin da take ta ringa shiwa Mama albarka kamar irin an yiwa bakuwarta alkhairin nan, sosai ta ringa sakawa Mama albarka bama da ta ji cewa zasu je wajen dinki da sauransu a goben, da wannan farin cikin suka kwonta barci
Washe gari kusan karfe tara na safe tana tsakar gida ta dora tukunya saman murhu tana tukawa Hajia tuwo na masara da tace tana sha'awa ta ajiye karamar kujera ta yi zama irin na tuka tuwon domin ko hijab bata da shi , haka kuma ta nanade zanin jikinta ya dan yi sama kadan ta yi zaman nan na gantsarewa kadan tana dirkar tukin tuwon mai aikin Hajia na gefe tana mamakin Khausar din domin bata san cewa ta iya tuka tuwo haka ba
Salamar Hajiar wace ta fita tun da sasafe ita da Magidanci ne ya saka Khausar dan dagowa tana amsawa hadi da fadin" Hajia har kun dawo?......"
Sai kuma ta yi shiru sanadiyar gannin TAUFEEK ya shigo da waya a kunnensa shi sarkin amsa waya sai ky a hannunsa yana dan yiwa hajia Alamun ta tsaya dan juyawa zai yi kasuwa
Ido hudun da suka yi da ita da shi ya saka shi binta da kallo sakamakon hayakin da yake ganni na tashi a gabanta, nan idannuwansa suka yi arba da irin zaman da yarinyar nan ta yi rabi da rabin cinyoyinta du sun sauka daga marainiyar kujerar nan ta nade hannun riga ta wani yada zama kamar an mata gorin haka tana tuka tuwon da bai san wa ya sakata aikinsa ba
Cire kansa ya yi ya maida kan Hajia zai yi magana, sai ya ga Hajia tana wani rinrintse ido tana wani tabo baki tamkar ba daga wajen rasuwa ta fito yanzun ba tana rus kuka har ana bata hakuri kamar jikanta ne ya rasu wato shi
Ido ya kifta a sanyaye yana kallon yannayin Hajiar, dan a gaskiya in dai Hajia wani abin ta saka a ranta yau zai fito mata a mutun ya mata nasiha
Kasa kasa hajiar ta matso har tana dan dage ta ce"
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 2️⃣4️⃣
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Kasa kasa Hajiar ta matso har tana dan dage ta ce" Ka ga mata, wannan sunne mata, irin matan da na so ace ka wanko ka kawo min, wa'inda na san du gajiyar da ka kwaso to fa kana da wajen saukewa, magidanci irin matan nan ina iya rantse maka idan suka rike namiji an gama, ama sai ka je ka dauko mace gatacen sai shegen shafa pankeke, yo in yar nan ta yarda ta koyi shafa pankeke ai an kade, ina mana bakin cikin rasata Allah ma kuwa!"
Gata dai fuska du ta fara nuna alamun daf take da zagwonyewa dan tsufa, ama bakinta ko amon muryarta bai cenza ba, shi a yau in ba dan mai kwanoni ba da matar nan sai ya saka an zo an ririketa an sauke mata aljannun kanta, ama ba komai zai kyaleta ne har su tafi haji shi ya san yaya zai yi da ita
Banza ya mata ya juya zai bar gidan, Hajia ta daga murya ta ce" Au na bata maka rai Hala dan nace wancen abar kamar muciya? Na fada in ranka ya kiya ka kawo mace mai dima dima mana ka gani in an zageka dilla malan"
A hankali Khausar dake rage wutar nan ta dan dago ta kalli Hajia, an yi katari itama ta kallota sai ta karaso tana sakin murmushi ta ce" Yar nan tuki ake? Sannu ke kuwa tashi ki yi wanka ku tafi mana tace karfe goma zaku tafi fa, tashi maza dan watsa ki dan sha na sha kin ga na karbo maki wani na farin jinnin yanzunnan wajen malan, je ki yi wanka kafin ki fito na saka maki a nono sai ki sha "
Khausar ta amsa hajia da to, domin bata da amsar da ta wuce wannan ta mike ta je dan shiryawar ta barawa mai aikin Hajiar sauran aikin,
Tana gama shiryawa ta dauki wayarta da nufin kiran TAUFEEK, dan ta ji yaya maganar wajen aiki ne yau? Kamar yadda Mama tace shin yana da hanyar da zai sanar masu ba tare da an mata fadan rashin zuwan ba, sai kuma ta dakata da wayar a hannunta tana tuna abinda ya faru jiya, ko yau ba wani gaisuwar da suka saba suka yi ba dan sai take jin wani iri a cen kasan zuciyarta da tarin tunanin me hakan ke nufi, sun dai gaisa da murmushi ama bata wani tsaya ta ji daga gareshi ko ta masa tambayar iyali ba
Salama ta yiwa Hajia ta wuce bangaren su Maman bayan hajiar ta shaida mata ta bar kayan za'a mika mota
Yau dinma sai da aka bata damar shiga kafin ta shiga baban falon
Mutanen dake falon ta fara bi da kallo kafin ta gaishe su, sai dai a cikinsu yar budurwa matashiya daya ta amsata itama a dan fizge ta dauke kanta
Ido ta zubawa Yumnah gannin sai da ta dubeta ta watsar
Tana shirin hawa saman sai ga Maman na saukowa da yar karamar jakkar hannu
Yumnah ce ta fara mikewa tana dan sosa gaban goshinta alamu na dan jin kunyar surukar nan ta shiga gaisar da Mama
Da dan sauri Maman ta amsa ta karasa saukowa ta dan dube su baki daya ta ce " Barkarku da hutawa, zamu dan fita ne da Khausar sai mun dawo"
Hajia Nuwairah ta yi kamar bata jita ba sai yarinyar wajenta da take riko wato hamdiya ce ta karasa da dan sauri tana sake gaisar da Maman
Jakar hannunta da Hamdiya ta so karba Maman ta dan rike da kula sosai tana mata murmushi ta ce" Na gode yata yi zamanki ai ba wani nauyi Allah ya maki albarka"
Hamdiya ta amsa tana dan sinne kai irin girmamawar nan tana kuma.jin dadin adu'ar Maman a ranta, a cen kasan zuciyarta kuwa ba abunda ke faranta mata a yanzu irin ta faranta ran yayansu ta hanyar yin abinda Yayansu ke so
Mama kuwa daga haka ta fice tare da KHAUSAR suka yi tafiyarsu
Cike da isa irin tata Hajia Nuwairah ta dan sake kallon yannayin Yumnah, sai kuma ta saki dan murmushi tana dauke dubanta cikin basarwa ta ce" Ya haka Yumnah na zata tare ne zaku fita da srakuwar taki?"
Yumnah ta juyo da dan sauri, dan kamarma wace ta afka tunani ta kalli Hajia Nuwairah, sai ta ga hankalinta ba a kanta yake gana daya ba, tana dan yi nata firar ne kuma tana maida hankali kan Hamdiya
Dan numfashi ta fitar, sai kuma ta juya tana fadin" Bara na koma Hajia dama gaishe da ku na leko"
Daga haka ta yi gaba
Tan fita Hajia Nuwairah ta mike ta kama kunnen Hamdiya ta ja da karfi ta yi wajen kicin dinta da ita danma kar a fito a sameta da ita a haka
Rai bace tana rike da kunnenta ta ce" Ke na tambayeki, Hajia fatima kanwar uwarki ce?"
Da sauri Hamdiya ke girgiza kai tana ji kamar Hajiar zata tsinke mata kunne ne
Murya a kausashe ta ce" To ki kula, bana son rainin hankali da shishigin tsiya, ba abinda
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 47