jinya"
Mahaifiyar Yumnah cike da gannin rainin hankalin TAUFEEK ta ce" Basa bari ko baka bari, ko kana tunanin har yanzu bamu san wanene kai da matsayinka ba? Bama wannan ba, Taufeek bani da muradin a kula da ita a wajen da ake neman ranta, ko shekara bata rufa ba an dankara mata uwar mata, wa ya san me zai sameta idan na tafi na barta, a bani y'ata kawai a tafi da ita gida mu yi jinyarta a cen!" Ta karashe tana fitar da huci, daci take ji a ranta sosai na wannan lamarin, babu irin tarewar da basu yiwa wannan abin ba ama a karshe sai da wannan anobar ta zama mata a wajensa? Lalle da take kwabar Yumnah cewar ta daina tunanin akoy wata mu'amala da ta wuce soyaya da abotakantaka tsakaninsa da wancen guzumar yanzun itama ta fara tunanin ta yiwu wata jarabar ta bulo aka yi wannan auren rufa rufar dan kar a ji!
Murmushi mahaifiyar TAUFEEK ta yi tana girgiza kanta
Shi kuwa cikin nutsuwa ya saukewa vigil din dake tsaitsaye duba, kafin kace me sun yi gaba sun bar wajen
Hajia baba ta girgiza kai cike da tarin takaici ta ce" Kai, fito mata da y'ar ta tafi da Itan mana sai me, wato ke ana baki kina roko kema nan uwar y'a kike ko? To bari ki ji da bakina ina waje a raye babu mai dagawa magidanci hankali, aikin banza wannan har matar huce haushi ce? In ba rashin daukan shawara Bama , ai macen farko rusasa ake dauka gidan hakuri gidan huce haushi idan ya so daga baya sai a bi dadi duniya yan idan Kanada shi ake iya zama da kai in baka da shi ba'a iya zama da kai!, Aikin banza ke kuwa kina tsaye ana neman zagar maki d'a sai dai ki yi murmushi , shin zafin nakuda aka fi ki sani ko amfanuwa yarta ta fi d'anki? Idanma zafin fitar kai ne ai na magidanci zai fi azaba, ke dai Allah ya shiryeki!"
TAUFEEK ya idasa sauke dubansa a kan Hajia , ikon Allah yake kallo, Hajia da hijab kamar zai tadeta ta fadi ama banda neman rigima ba komai a cikinta,
Kai ya girgiza ya juya zai bar masu wajen mahaifiyar Yumnah da take ji inama inama idan ta bude baki ta durawa uban kowa zagi babu abinda za'a yi, ama tana tsoron wannan dakewa ta TAUFEEK da kuma sharewar da mamansa ta yi, bata san me hakan ke nufi ba, ta sake dubansa ta ce" Yaya zaka tafi bayan na fada maka ina so a fito min da ita mu tafi gida?"
TAUFEEK ya dakata da tafiyar da yake yi ya juyo, a hankali ya washe fuskarsa daga yannayin hadewa ya dan saki murmushi ya ce" Cewa na yi kowa ya koma gida, zan kawo ta idan na ga zata iya jurewa hakan"
Daga haka ya yi tafiyarsa
Mahaifiyarsa ta yi murmushi ta dauki ledar goron Hajia da ta yar tana masifa ta ce" Hajia mu je a maida mu gida"
Hajia da ta gama summa a tsaye gannin badalar da Magidanci ya aikata ta ja numfashi ta ce" Eh kaini gidan dai na ga mai Kwanoni, kin ga kuma yannayin magidanci ya bani tsoro gaba dayanmu ya hade ya kora, Ni uwar mai kwanoni harda Ni? Mu je mu je"
Da sauri Akilah ta fice itama a wajen ta bi bayan su Mama, har Mama ta shiga Mota ta dakata gannin ta karaso
Tsayinta ta rage sosai ta ce" Mama dan Allah ku yi hakuri da abinda ya faru, in sha Allah idan mun je gida komai zai daidaita"
Mama ta sakar mata murmushi cike da gannin girmanta, sosai yarinyar ta birgeta, da kula sosai ta ce" Kar ki damu auntynsu, ba wani abu kin ji? Allah ya bata lafiya, a kuma yi hakuri abin ne ya zo a haka, kin san aure da haihuwa ke da komaima na rayuwa lokaci ne, Allah ya yi haka zata kasance, kwarai ba'a kyauta mata ba, kuma Ni mace ce na san me muka dauki kishi, ama ina mai bata hakuri kuma in sha Allah Elhaji karami zai yi adalci a tsakaninsu"
Daga haka suka yi mata salama direban da TAUFEEK ya sa ya kai su gida ya ja motar
Sai da suka yi nisa Hajia ta ce" Uhum, wani lokacin sai ki yi halaya na munafukai sak , yo me kika masu da zaki basu hakuri? Aure fa an daura sai dai a ci da haka, Ni abinda nake son sani wani shege ne ya yi kiran uwar yarinyar nan ya sanar mata kai tsaye har take son zagina?"
Mama ta ce" Aa Hajia ba zata yarda ta zageki ba, kawai rai ne ya bace, ama komai zai wuce , ita Allah ya bata lafiya, wanda ya hadasa haka kuma Allah ya bashi ribar da ta dace da shi"
Sunna tattaunawar nan har suka isa gida
A asibiti kuwa hajia nawarah basu tashi bada hakuri mai kama da zigi ba sai da aka watse aka barsu da Maman Yumnah
Hajia Fatahiya ta saba yarta a kafada tana fadin" Zamu tafi Hajia, kin san mijin Yumnar bai cika lalaba abu ba, du girmanmu da matsayinmu na matan mahaifinsa in ya dawo ya same mu a nan yana iya zazaginmu , kin san abu da baban gida , Allah dai ya sanyaya ama ai abin ba tausayi sam, yarinya karama a hada da wannan ina zata saka ranta, yaya zata iya kishi da wannan mace, ai kawai in nice Elhajin zan nemi gani a duba lamarin nan , gaskiya a zaba y'ata ko wancen kaska rabi mai jinni jikar"
Hajia nawarah ta cafke da fadin" Uhum, Ni dama na san a irin kwadayin yarinyar nan da iyayenta komaima zai faru, Allah dai ya sa a barwa Yumnah cikinta kar aje a kaita wajen bokaye a rabata da cikinma dan kuwa na tabata kai sake Elhaji ba zai aurawa Magidanci wannan guzumar ba, menene abin mora a mota mai hayaki? Wahala ce kawai, Allah dai ya kyauta mun tafi kar ya dawo ya wulakantamu , kin san bashi da sauki ko kadan!"
Sosai abin ya sake rikita mata lisafi, suka fice suka barta zaune ta zubawa waje daya ido har Akilah ta dawo ta zauna gefenta kanta a kasa ta kasa cewa komai ama tana sauraron wayar mahaifiyar Tata domin ta yi kiran babansu ta sanar masa abinda yake faruwa ya kuma ce zai kirayeta yanzu yanzu su koma gida zai dawo shima yanzun ya sameta
Huci ta sauke tana share hawayen fuskarta ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, kar dai idonmu ya rufe mun biyewa Yumnah da son da take yiwa yaron nan mun aura mata marar mutuncin dan kasuwa? Ki duba ki ga kaf dinmu ya kora ba jin nauyina yace zai kawo min y'ata kennan yana iya sakinta ba damuwarsa bace ko?, Kin kuwa ji me iyayensa ke fadi? Wai bari su yi su koma kar ya dawo ya same su ya wulakantasu, wai ya saba, to ya wulakanta su su, Ni wacece da ba zai min ba? Uwa uba y'ata? Innalilahi Wa ina ilaihi raj'une kar dai mun shigo rigimar da ta fi karfinmu, d'an baba da so ne ubansa ya masa aure ko shekara y'ata bata rufa ba a gidansa ba shawara ba komai kuma kakarsa ta zageni tasss? Ba zai yiwu ba, Allah ba zan iya yarda ba, sai an saki yarinyar nan ba za'a hadata kishi da Yumnah ba, ko ni uwarta ba'a min kishiya ba bale ita!"
Ita dai Akilah kanta a kasa, har ta gama kira ya shigo wayarta mahaifinsu bai tsaya sauraronta ba ya bata umarnin kasancewa a gida yanzu yanzu yana jiranta
Da kyar ta yarda suka tafi tare gidan suka bar Yumnar a asibitin, a gaban idonsu Nurse ta shiga da kayan kula da ita da komai , itace mai jinyarta kuma likitocin sai lekowa suke ana fadin matar docter ce ba lafiya, ita ya san za'a kula da Yumnar fiye da du inda zasu kaita, fatanta mahaifinta ya ci karfin wannan fitinar dan babu inda zata kai su sai dana sani
Sosai ya samu hutun shima a asibitin a ranar, barcin da bai samu ba jiya ya samu ya dan rama sannan ya sauka ya koma dakin Yumnah ya dubata sosai da karin ruwan da aka jona mata da abinda aka rubuta za'a ringa mata har ta warware sannan ya yiwa nurse din dake tare da ita salama ya nufi gida
Ko da ya isa gidan part dinsa ya wuce ya shige wanka, Yana gamawa ya je wajen mahaifiyarsa ya zauna suka dan taba fira sannan ya je wajen mahaifinsa, daga nan ya yi tafiyarsa bangarensa ya kwonta dan zai je aiki ne goben da wuri dole
Washe gari karfe takwas da yan mintina
Sauri take yi tamkar zata zura da gudu sakamakon yan mintinan da ta dora a yadda ta saba zuwa asibitin, a cen kasan zuciyarta kuwa fada take yi kamar zata ari baki na irin tsayar da Itan da direban ya yi da irin yadda Mama da kanta ta sakata saka wannan suturar ta jikinta kuma ta rufeta da fadan wai ta saka turare da yawa bayan yanzu matar aure take, ita abinma ya so bata dariya, ama kuma da ta duba tsantsareren kunshin hannayenta sai ta ji wani dadi dan kunshin ba karya ya zanu Allah ma kuwa
Da dan gudu kadan cike da tsoron kar sabon takalmin nata ya kayar da ita ta saka hannunta ta hanna lft din rufewa sannan ta shige da sauri tana dan haki a hankali tana duban mutanen ciki ta furta" Barka da safia"
Docter Aliyu , da sister Bahija ne suka amsa, Sister Bahijar na rike da wata yar akwati baka a hannunta tana duban Khausar sunna dan jiran ta danna wajen da zata sauka dan ya rufe su tafi ta ce" Dubiya kika zo ne? A wani etage zaki sauka ne? Yi ki danna muna tare da Sir muma bangaren dubiyar muka nufa"
A hankali ta ji gabanta na neman yankewa ya yi faduwar da bata taɓa ji ba, sakamakon mutumen dake tsaye ya bada baya ya dan juyo , ashe waya ce yake amsawa , fuskar nan tasa cike da kamilalan saje, bakinsa dan ciwat da shi, idannuwansa dauke da farin tabarau, rigar jikinsa baka ce sidik sai abin wuyansa ruwan kasa mai duhu, ama rigar da wani tsabar sabon salo da rashin jin magana boturanta uku reras a bude suke, da hannunsa daya yana dan alamun balawa yake yi, watau ya fito ya ratso doguwar tafiyar nan bai Bala ba sai a nan, hannun dake rike da wayar kuwa agogo ce shekekiya dai Wali take irin na rashin mutuncin nan Wada ke nuna wanke hannunka ka taba ne ya wani kafeta da duban da ta tabata shima bai zaci ganninta ba da bai dubeta ba dan abin kunyar da aka launa masu su , wai su din nan
Da karfi KHausar ta juya bayan ta zarro ido jikinta na rawa ta saka kafa ta fita daga lft din da gudun balaki ta saki yar wayar salular Tata a nan da rigarta ta Nurse ta karasa bakin matatakalar hawa ta zauna tana haki zuciyarta tamkar zata buga da tashin hankali
A hankali ya lumshe idannuwansa, ya dan girgiza kansa da idannuwansa ya yiwa docter alamun ya rufe su tafi, sannan ba nuna kyankyami ko wani abin ya duba ya dauki wayar nan da rigar daidai abin ya tsaya ya fice gaba sunna biye da shi ya yiwa sister Bahija shiru a lokacin da take tambayarsa ya bata kayan ta rike, dama kayansa ne a hannunta, ama ya yi kamar kurma yake ya bude dakin da Yumnah take ya shige
A bangaren Khausar kuwa hannaye ta saka ta talabe tana jin tsararen kukan dake neman zuwar mata
Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, yanzu itace take tsoron kallon besty? Ita da ta zo da kudirin su hadu ta sanar masa su fa samawa kansu mafita tun wuri? Shin yaya zata fara masa zancen nan ne? Ta tabata shima abin ya wuce tunaninsa, ina ita ina shi? Me zata ce masa ne? Kai bari ta mike ta je ta yi jiransa kofar office dinsa su zanta, ya bata takardarta ta koma ta kaima Aba, wannan magana ta Aba cewar a zauna da wahala Bama zata iya zaunawar ba gaskiya
Tana mikewa ta ji ana fadin".......
☹️☹️☹️☹️🙃🙃🙃🙃🙃🙃🙃
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 4️⃣5️⃣
*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*
1: Duk karyar kada
2: Yar mahaukaciya
3: Neman na kaina
4: Bani da zabi
5: Bak'a ce
6: Kutkale
7: Makauniya ce
8: Mage
9: Duk nisan jifa
10: Idan ka raina inda kake
11: Dutse
12: Alkalamin kadarata
13: Bani da zabi
14: Dakika Biyar
15:Wata kokowar
16: Aure yakin mata
17: Ni zan ladabi
18: Daga tafia daukar soja
*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Ta ce" Khausar Muktar? Alhamdulilah, zo maza kama wannan ki hau cen dakunan VIP ki jona mata wannan allurar, yi gagawa zan kai hoton cikin da akai mata ne waje Docter tana jirana, kar sai na je na jona mata ruwan kuma ran sir ya bace"
Magana take yi da dan gagawa da alamun azalzala , sai kuma ta dan dakata tana kallon KHausar din
Da dan mamaki ta ce" Ke wai lafiya? Ina rigarki da takalmin ki na aiki? Ko dubiya kika zo yau?"
Da sauri Khausar ta girgiza kanta tana kama kanta ta ce" Aa aunty kayan na bari a adaidaita sahu shine nake jira a kawo min"
Kai ta dafe, sai kuma da dan sauri ta cire Tata farar rigar tana mika mata ta ce" Saka bani abayar nan ki je ki yi aikin nan Ni inada wata a office dina in an kawo maki taki kya kawo min"
Tana fada ne tana taya Khausar cire abayar jikinta, da sauri Khausar ta dora rigar auntyn tasu ta tare kwanon silbar mai dauke da maganin ta sakarwa auntynsu abayar da ta ɗora saman riga da sket dinta sababi masu masifar kyau wa'inda suka kama jikinta dasss da su
Juyawa ta yi ta koma lft din tana adu'ar Allah ya sa har ta gama ta koma kar su hadu da shi, ta fi ganewa ta tarda shi da kanta
Lft din na tsayawa ta fito a nutse ta nufi VIP na dakunan ma'aikatan asibitin a ranta tana tunanin waye ba lafiya a cikin ma'aikatan asibitin, dan kuwa waje ne da ake saka manyansu ko ahalin manyansu
Tana daf da karasawa dakin ta dubi madubin dake ajiye sai walwali yake
Gabanta sai da ya yanke ya fadi, a dan rikice take kallon kanta tun daga sama har kasa,
Watau dama aunty ba wani tsayi ne da ita ba, kuma tana da jiki hakan ya sa rigar Tata ta shigi Khausar, sai dai ta je cen daidai da dima diman cinyoyinta ta wani hau take budewa idan tana tafiya
A raunane Khausar ta hadiye yawu mai wahala tana jin nauyin shigar Tata, da dan sauri ta karasa kofar dakin ta ayana magana kamar haka' zan shiga in yiwa marar lafiyan allurar sai in koma gida, idan na je sai in dauki wayar Baba in kirashi mu yi magana kawai, sai ya zo mu daidaita ya bani takardar kawai'
A nutse ta bude dakin bayan ta dan buga kadan sannan ta yi salama kasa kasa sosai, dan wannan din shine dabi'arta, koda tana likita tana kiyaye hakin mutane, bata cika irin shigowar nan kai tsaye fuska daure ba ta wasu likitocin, takan dan buga ta dan yi jim, sannan ta bude ta shiga da sallama a hankali duda ta san nurse zata tarar sai marar lafiyar dan kuwa yanzun ba lokacin shigowa gannin mararsa lafiya bane, sai an jima kusan sha biyu na rana ake budewa a bada damar ziyara, karfe uku kuma a rufe sai shigar sasafe karfe shida zuwa takwas rufe
A hankali ta ja ta tsaya idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa da kuma wace ke kwonce tamkar babu rai a jikinta, ga dukkan alamu barci ne take yi mai nauyin gaske
A hankali Khausar ta lumshe idannuwanta gannin shi bashi da niyar kautar da nasa duban a kanta, kamar yadda ya saba a da cen, a kanta yakan dan jima yana kallonta , sai dai a da din bata dauki haka a bakin komai ba, yanzu kuwa sai take gannin hakan bai dace ba
A hankali ya dan yi gyaran murya ya mike daga saman kujerar da hannunsa ya mata alamun ta yi aikinta sannan ya koma bayanta sosai ya tsaya ya dauke kansa a kanta dan ya san wacece ita, bale sabon yannayin da ya ga ta ara tsaf take iya juyawa ba tare da ta yi aikin da ya kawota ba
Jiki ba karfi ta ajiye kwanon, sannan ta duka ta tsayar da gudun karin ruwan, ta daidaita allurar da ruwanta ta bude wajen da aka jona karin ruwan a hankali ta rike tsintsiyar hannun Yumnar ta shiga zuba mata ruwan allurar a hankali a hankali tana dan duba yannayinta domin allura ce mai zafi ba'a zugata zuuuuuuu ta tafi, kuma tana iya taba numfashin mutun ko ta saka shi amai ko muguwar juwa shi yasa ake yi a hankali ana hankalce da motsin mutun
Sai da ta gama saka mata ruwan allurar sannan ta maida mata karin ruwan
A hankali ta juya tana dan duba dakin dan gannin abin auna bugun zuciya
Dayan nan dai na wuyansa shine, ita kuma nata yana cikin rigarta da ta yar a cikin lft
Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta karfafawa kanta gwuiwa cewar Besty ne fa, TAUFEEK ne fa, dilla menene a ciki
Ba tare da ta sake saka tsoro ba ta nufe shi tana aro jarumta tana yafawa kanta ta ce" Shin me yake damun Yumnah ne? Ban san bata da lafiya ba, dan bani abin nan na ga bugun zuciyarta"
Maimakun ya bata abinda take nuna masan sai kawai ya kama hannunta kiiiii ya fice da ita daga dakin
Jefa kafa take yi gabanta na faduwa domin bata san ina suka nufa ba, kuma irin yadda fuskarsa ta dauki ja alamun ransa a bace ko menene sai ta sake tsorata ainun har suka shiga lft suka sake hawa sama cen wajen office dinsa
Ko da lft din ya tsaya hannun nata ya cika ya yi gaba yana kunce abinda ke daure a jikin rigarsa na wuyansa dan ji yake yi tamkar zai tsaida masa numfashinsa ya dadana code din kofar office dinsa ya shige lokaci daya ya dauki commande din camarar bangarensu ya sakata a halin duhu sannan ya kurawa kofar ido yana jiran shigowar ta
KHAUSAR da ta gama summa a tsaye da kyar ta cira kafarta ta karasa office din
Rana shigowa ta ajiye farar rigar aikin domin itama du a rikice cire rigar ta yi ta tunkaro kusa da table din da yake tsaye kanta tsaye tana dubansa idannuwanta na cikowa da kwallah ta ce" Kana tunanin laifina ne?, TAUFEEK kana tunanin nice na saka su Aba aikata aikin nan?, Walahi walahi ban sani ba, nima na san ai na wani hadi, in kana tune ka min alkawarin kasancewa da Ni har a Daura aurena da .........."
"Khausar Please cn U be quiet?!" TAUFEEK ya fada a kasashen da ya saka Khausar zuba masa ido tana jin tamkar zata kifa a tsayen da take , shin yaya zata kwatanta masa cewar ba fa ita tace a daura mata aure da shi ba?
A nutse yana binta da kallo ya ce" sai yaushe zaki fara jin maganana ne? Menene wannan shigar? Ina hijab dinki? Me yasa kike son daukan dabi'ar da zata ringa bata min rai? Babu ruwanki a gaban kowa sai ki arta a guje ? Kina kallo muna tare da docter kika wani fita da gudu menene haka ne?"
Da mamaki take kallonsa, sai kuma ta kalli jikinta
A hankali ta shiga juyawa a gaban nasa har sai da ta juyo tana fuskantarsa a sanyaye ta ce" Menene laifin shigata? Me yasa kake son min fadan shigata ne bayan na san cewa harda ita a tsaikon samun mijina yanzu na kare da ......"
Ta yi shiru sakamakon zuba mata jajayen idannuwansa da ya yi yana sauraronta
Gannin ta yi shiru a hankali ya ce" Kika kare da me?"
Khausar ta dafe gaban goshinta, a hankali ta ja kujera ta zauna sannan ta mika hannunta ta kama bayan hannunsa dake jimke saman table din a tausashe dayan hannun nata kuwa ta bude abinda ke ajiye ta ciro tisu fari ta nufi gaban goshinta da shi a hankali tana share zufar da ta karyo mata kasa kasa ta ce" Dan Allah ka zauna, ka san ba son rikici nake ba, kuma baka san abinda ya faru ba ga dukkan alamu, ka zauna dan ina tsoron in na fada maka yanzu ka fadi, Taufeek its vry srius , ka zauna Please"
Hannunsa ya janye daga jikin nata, domin tunda ta dora din tana magana ne tana dan shafa bayan hannun nasa da sigar rarashi ba da wata manufa ba, wace sshi kuwa hakan ba daidai da yannayin da yake iya dauka bane
Da ƙafarsa ya dan tura kujerar baya ya zauna yana kallonta , a hankalin da sam bata so yana mata magana ya ce" Kika kare da me? Tl me"
"Na kare da auren aminina, abokina, freind dina, TAUFEEK basu fada maka aurena da aka daura da kai bane ko menene na ga ba maganar kake min yanzu ba?, TAUFEEK ka san cewa wai ashe Ni aka aura maka.....?" Ta fada tana watsa hannayenta hadi da dan zarro idannuwanta alamun ta fada masa tashin hankalin nan
Bakinsa ya dan tabe yana kauda dubansa ya ce" Eh haka na ji"
Khausar ta girgiza kai ta ce" Ka ji? Kennan ka ji? Ya Allah, da ka san irin yadda na yi ɓaci a kwana biyun nan da ka sha mamaki, TAUFEEK aminina?"
TAUFEEK ya zuba mata ido, ya dora hannayensa duka biyu yana dubanta ya ce" Eh, sai aka yi yaya?"
"ka kuwa ji me nace ne?" Khausar ta fada tana dubansa
TAUFEEK ya dan dantse lebensa da dan jin yana daf da kowa a wannan dogon maganar da tarin raini ke jagoranta tsakaninsa da Khausar ya ce" Eh na ji me kika ce, an daura maki aure da Ni, Ni amininki, nace eh sai mene kuma?"
Baki da ido da hanci ta bude tana kallonsa har ya mike ya nufi wajen frij din office din nasa ya ciro faro ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 30 Chapter of 47