KAUSAR?"
Magangannunsa ba da tashin hankali yake fadarsu ba, hasalima a sanyaye harufansa suka fi fita sunna shiga cikin kunnayenta, sai dai mamaki mai karfin gaske da ya kamata shine dama yanada iyali? Fuskarsa kamar bata nuna ya kwana biyu ba, bama wannan ba irin lokutan da ya ware yake kiranta bata taba sannin cewa shi din mai iyali bane da bata ringa amsawa a lokuta irin wadannan ba, domin yana kiranta kafin a yi sahur fa, haka kuma bayan an fito daga sallar asham yana kiranta su dauki lokaci mai tsayi sunna magana, magidanci? A irin wannan lokacin ai ko yayane yana tare da iyalinsa, in ta yi duba da lokutan da Abanta yake gida kennan, sunna tare baki dayansu a gida fa? Ina laifin ya ware lokacin da yake kasuwa ? Sai ta ji wani iri, ama kuma maganar wai ko dan yanada iyali zata iya kasa amsa masa ko daya, to mem ake tunani ne? Ita dama abinda take tunani kennan da rayuwarta cewa lalle ba zata taba aurwn saurayi ba, to ita a haka din nan ta auri saurayi ta ce me ta yi kennan? Tap ai da kunyama wani abin , ita aurensa da ya'yansa saima tace adu'arta ALLAH ya amsa sai ta je su yi zamansu
MUJAHEED ya dan sake muzgutawa ya ce" Hajia KAUSAR kar dai a saka na sare an min shiru?"
KAUSAR ta sake sinne kanta ta boye fuskarta cike da nauyi da jin kunya ta ce" In sha Allah zan sanarwa su Mama, abinda suka yanke sai na sanar maka"
Murmushi ya yi yana gyada kansa ya ce" Masha Allah, haka ake so, ya zamto ana tambayar amanar iyaye , to ama ke yaya kika ganni na maki ko?"
Ta kofar hijab din take dan kallon nasa, yadda ya wani kanne ido sai ta ji kamar ta kwala kiran Mama dan ta zo ta tayata gannin wani makararan rashin da'a, ama kuma sai ta kwabi kanta ta sake sade kai har dai ya gaji da surutunsa shi kadai ya gaza samun yadda yake so ya hakura ya mike cike da mamakinta, kwarai ya yi mamakinta, domin halayarta sai suka so bambanta da wasu yanmatan da yake kulawa , yan matan da kamar jira suke a taya su? In ka je inda suke kuwa sai in Allah ne ya tsare maka amaninka, in ba haka ba tsaf za'a iya lalata da y'a a gidan iyayenta, ama ita tabarmar da ya zaunama bata hau ba kuma kanta da ta sada har ya mike ya ajiye alherin da ya ajiye wanda sam bata kula ba bata dago ba sai da ta ji yana yiwa su Mama salama ne sannan ta dan ciciba ta mike murya a fan sanyaye ta ce" A gaida gida da Y'ayana Elhaji, Allah ya hutar da gajiya"
Yar dariya ya yi yana amsawa sannan ya sa kai bayan ya tabatar mata zai kireta fa kar ta kashe waya, ita kuma ta gama yanke hukuncin in sha Allah ba dai zata kuma amsa wayarsa a lokatan da take kyautata zaton magidanci na tare da iyalinsa, dan a yadda ta dafe din nan ta sha ruwan gidansu har ta batse ba zata so in ta zama matar aure a ringa yada mata mugwayen manufofi irin wadannan ba
Fitarsa da amsa kiran TAUFEEK ta tabata ko mota bai karasa ba, ya sanar mata ta turo Aisha ta amshi sakon zasu fice,
Da dan sauri ta ce" Aa, to bamu gaisa da ita ba zaka wuce ne? Bara na fito"
Tana fada ne ta katse sannan ta karasa ta sanarwa Mama da dan sauri ta fita ta tsalaka ta karasa kusan motar gefen da yake dan dayan gefen da take bakin hanya ne ta mika hannunta suka gaisa tana fadin" Amaryarmu, kin kusa zama tamu dai yar uwa nan da yan kwanaki"
Murmushi YUMNAH ta sakar mata tana fadin" Aunty Kausar har kin saka na ji kunya"
Dan murmushin ya yi shima ya juya a zaunen da yake ya ce" Kin ga sakonki baya ni fa ba zan shiga gida ba dan so nake na kaita na wuce akoy aikin dake gabana mai yawa"
KAUSAR ta je bayan ta bude motar tana fadin" Ba'a gama rikicin gidan bane TAUFEEK?, Ba zaka barwa HAJIA maganar ba"
Da dan haushi kadan ya ce" Haka fa, HAJIA HAJIA tsohuwar nan ni da ita ne, ai ta gama siye ฦดaฦดanta tsaf sun ce sai dai na yi hakuri har ta amince min zaman gidana daban, KAUSAR ki je ki mata nasiha ta ringa jin tsoron Allah "
KAUSAR ta kyakyace da dariya tana rike da marfin motar bata taba katon bokicin dake shake da tuyar da aka kawo masa ya sa Mamansa ta debar mata ba ta ce" Ni? Ai in na hadu da HAJIA ka tabata idasa ajiye maganar zamanka a gefenta zamu yi , TAUFEEK so kake dan shirin d amuke ya bare?"
YUMNAH da zuciyarta ta cika da tambayoyi game da mutumen da ya fito daga gidan wanda sarai ta sanshi , sai kuma maganar da ake kamar ana nufin a cikin gidan nan za'a zaunar da ita ko menene? Ko dai itace bata fahimta daidai ba? Sai kawai ta ji wani abin TAUFEEK na fadin ta sauke bokicin mana ya sanar mata fa sauri yake yi? Hakan ya sa da sauri ta kalle shi ta kuma kalli baya tana zubawa bokicin ido cike da mamaki da wani tsoro tsoro dan bokicin ta tabata na gidansu ne daya daga cikin bokitan da aka yiwa TAUFEEK din ne na kwarya kwaryar sallah aka kai gidansu ai ?
Da kyar ta sauke shi tana fadin" Menene a ciki?"
TAUFEEK ya miko mata katuwar ambulop din katinta ya ce" KAUSAR daga wannan aikar kar ki kuma sakani wata kin fahimta?"
Murmushi ta yi ta ce" An gama Yalabai, ama maganar dinkunnanka na wajen abashe ya yi kirana jiya baka leka ba ashe, sai kuma maganar wunin da muka yi da kai da kuma wankan ango da Mama tace a gidan su Uncle Abdallah za'a yi?"
Yana yiwa motar ky ya kunna ya ce" Zamu yi waya idan na koma gida ki gaishe min da Mamanaa please "
Hannu ta daga tana masu byby ta ce" YUMNAH na san sai ranar ko na kuma ganninki, sai mun je daukoki"
YUMNAH dake hadiye wani makuku mai taurin tsiya da daci a wuyanta cike da takaici ta dan saki murmushin yake tana sake bin kofar gidan su Kausar din da kallo wanda a ranta take ayana ita ko kasheta za'a yi ba zata iya zaman minti daya a gidan nan ba , ama a cikinsa aka haifi rundumemiyar yarinyar nan da take neman hanna mata sukuni da kwonciyar hankali? Subahanalah wannan wace irin masifa ce?
Sun koro da tafia cikin yannayi da dabara irin tamu ta mata ta ce" Sir, masha Allah gidan su Aunty Kausar ana samun baki, wanda ya fito ta yiwu uncle dinsu ne ko?"
Yana tukinsa normal, a fuskarsa ba wani yannayi haka a yannayin motsin gabansa bayan ya tsayawa danja ya ce" Aa ba uncle dinta bane, Saurayinta ne Baki gane shi ba?"
Cike da mamakin furucinsa da yannayinsa ta ce" Saurayi? Dama tanada saurayi?"
Da dan mamakin yannayin tambayarta ya dubeta, sai kuma ya tayyar da motar ya bi ayarin motocin da suka yi gaba bayan danjar ta saki suka dauki hanyar gidansu dake kusa da wajen danjar
Bai jima ba ya karasa kofar ya tsayar da motar a nutse ya kasheta sannan ya dan juyo ya zuba mata ido ฦadan
Da kula sosai ya ce" YUMNAH na gode da ziyara"
Murmushi ta yi tana dan sake kallon tsararen sajen fuskarsa da yannayin askin kansa mai fitar da fasalin fuska da tsarinta, sai kalar shadar jikinsa mai ruwan Ash color mai haske da ta dauki zare ashe mai duhu dinkin dan kadan ba wani da yawa ba
A hankali ya dora da fadin" But daga yau, bana so kina fita, ko ina ne kin fahimta?"
YUMNAH ta dan tsatsare fuskarsa da kallo, a hankali ta ce" Dama ba inda zan je Sir, sai wajen gyaran jiki kawai"
Dan kureta ya yi da duban da ya sakata jin ta dan tsargu, sai kuma ya dauke kansa yana kallon gefe a hankali ya ce" ita mai gyaran ta zo gidan ta maki YUMNAH"
YUMNAH ta dan zarro ido ta ce" idan gida ne fa akoy mugun tsada ne "
Da mamaki ya dan mata kallon kai? Tsada? Shi zata kawowa maganar tsada? Tsada ta kai maganar mutuncinta da yake son fara karewa daga yau har karshen rayuwarsa? Tsadar me da zata kamo shi nashi kwonciyar hankalin? Baya tunanin in har zai iya hakuri shi TAUFEEK iyalinsa a waje da shigar da ba ita ba kowani shara na kallo da sunna ta tafi gyaran jiki
A hankali ya ce" Kina iya fita"
Fuskarsa ta tsatsare da ido, da dan sauri ta ce" Zan fa yi a gidan, ba zan tafi wajen gyaran ba"
Motar ya kunna yana dan dage kafadunsa kadan , hakan ya sa ta kama marfin motar ta ce" Zamu yi waya da dare ne?"
A hankali ya dan duba agogon hannunsa, ya tabata idan ya fito dare ya yi sosai, sai kawai ya dubeta da kula ya ce" Aa, ki yi kwonciyarki, zan kirayeki da safe in sha Allah"
A hankali ta sake kureshi da duba, a zuciyarta kuwa tana ayyana ' Kennan ni ba zaka kirayeni ba dan zaka kirayeta?, Me sunnata ne wannan mata a duniyata ko nace a rayuwata?'
Budewar ta yi ta fice ta shige cikin gidansu
Tana nufar falonsu mesage na shigowa wayarta, sai ta ki dagawa tana sake kasa kunne dan gaskata idan har muryar yayarta ne
๐๐๐๐โคโ๐ฉนโคโ๐ฉน๐๐๐๐
*DA CIWO A ZUCIYATA*
๐๐๐๐โคโ๐ฉนโคโ๐ฉน๐๐๐๐
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* ๐
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicรฉ
Lait de nuit
Parfums dรฉsodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waษannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐๐
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐๐๐๐๐
Da sauri ta daga kafarta ta idasa shiga tana bude sakon bankinta dake sanar mata shigowar makudan kudi na mamaki da ta tabata daga angonta ne, kuma kudin ba na komai bane sai na gyara Wa'inda in har gyaran zata yi ko amare ashirin ne ya ishe su tsaf harda suturun wunin biki da komai komai tsadar abin kuwa bale ita daya, sai dai maimakun ya mata dadi sai ta ji sam bata jin wani dadi ko zumudin abin har ta karasa ta zauna gefen yayarta dake wake ga amarya yar dangi ga amarya YUMNAH tana tafi da murmushi na farin ciki
Yannayin YUMNAH ya sakata rage zumudinta tana kallonta sai kuma ta kalli mai aiki dake ajiye masu ruwa ta salameta ta ce" Ke lafiyarki kuwa ? Yannayinki ya nuna kina cikin wani bacin rai?"
YUMNAH ta zubawa fuskar yayarta ido, a hankali hawayen dake makale mata suka samu damar zubowa , sai kuma ta fashe da kuka ta mike ta karasa ta fada jikin yayar tata , tana kukan sosai ta ce" Aunty, kun zo?, Sannunki da zuwa....."
Hankalin yayarta a tashe ta dagota daga jikinta tana jan hijabin dake jikinta ta ce" Subahanalah ke kuka kuma? Menene? Subahanalah lafia? Me ya faru a gidan sirikan naki? Mama tace kin je masu barka da sallah har ina cewa me yasa kika fita yanzun fa kuma ba maganar fita in ba dole ba?"
Tana kukan tana kallon auntyn nata, duda ta san yawancin lokuta yayar tasu ta kasance daban a yannayin halaya, domin wani lokacin harta da mamansu kwasa suke yi, bama a kan maganar saka hijab da sauransu in dai ta zo gari to fa sai an kwasa da ita kamar ba wace ke rayuwar turai ba haka zata ringa fadan a suturce jiki da sauransu dai abubuwa dai irin na tsauri
Tana hawayen wani na korar wani ta ce" Aunty, TAUFEEK ne, Aunty lamarinsa ya fara damuna, abubuwan da nake gani sun fara tsoratar da ni, tun yanzu ina tsoron nan gaba ya zamo irin mazan nan masu kara aure, watau ya kasa hakuri da ni daya kwal a matsayin matar aurensa!"
Kallonta take yi, bata katseta ba, tana kuma jira ta ji baban abinda ya sa kanwar tata ke kuka haka, dan kuwa ta tabata ba wannan kawai bane....domin in har wannan ne bata san me zata kirayi YUMNAH da shi ba,
Sai dai ga mamakinta YUMNAH ta ja ta tsayar da maganarta tana ta shashekar kuka
Fauziya ta ce" Ki daina kukan haka mana ki fada min menene wai damuwar? Dan na san ai ba zaki kasance mace mai irin ra'ayin nan ba, ko nace mai son sakawa kanta ciwo a banza da wofi ba, ina nufin yau mace komai kankantar shekarunta in dai ta fara amsa bayanan soyaya daga namiji in tana da hankali ai Auta ta san cewa ba'a halitoshi dominta ita kadai ba, bale kasancewarta musulma kuma y'ar hausa? Koda a gidanku ba'a yi ba kin gani a makota, menene zai dameki da irin tunanin nan tun yanzu salon ki kasa kula da kanki da maganar aurenki tun da jan sawunki a kan shirme? Ko kuwa maganarki da shi dama shi baya sonki kece ke sonsa zaki kai kanki inda za'a gaza hakuri da yarintarki a ringa maki uzuri? Ke Auta Allah na tuba ke da kika dauko dan kasuwa ai kin san ba dai a kan maganar mace zaki kawowa kanki damuwa ba ko????"
Kukanta ba wani dainawa ta yi ba, saima ji da ta yi kamar damuwar ta karru a kan da
Tana kallon yayarta ta ce" Aunty ba fa dan kasuwa kawai bane ba fa likita ne, kuma kin ga wata mata ce mai sunna KAUSAR wai take kawarsa ko me?, Aunty ya fi a irga zai amsa bukatun KAUSAR ni ya kawo nawa a matsayin na biyu, in karkare maki harta iyayensa sun santa kuma sunna zumunci da ita, bama kakarsa du masifar matar nan tana son KAUSAR din nan dan ni ganau ce ba jiyau ba , Aunty abin damuna yake yi fiye da tunaninki, ni da ace budurwarsa ce na rantse maki da na san yadda na yi da ita dan kuwa na fi karfin jagaliyancin ฦดaฦดan garin nan, damuwata kawai ita ba maganar soyayya tsakaninsu dan ai abin bama wani tsari in kin ganta ta yi hudunmu fa ni da ke, sa'arsa, kawai abinda yake damuna haushi take bani irin yadda mijin da zan aura yake bata lokaci fiyema da ni kaina, Aunty harfa kaya ake mana iri daya fa, ko kishiyata ce ai sai haka!"
Kwarai, auntynta ta ji wani iri a bayanin kanwar tata, sai dai ko menene zata fi so a bishi a hankali, dan haka da kula ta ce" YUMNAH, mijinki yana sonki?"
YUMNAH cike da bada tabaci ta ce" Kwarai kuwa yana so na"
Auntynta ta ce" Shin a dan tsanin nan akoy wani abu da ya tauyeki da shi irin wanda aka saba tsakanin budurwa da saurayin da aka saka masu rana saboda ita? Ko kuwa akoy lokacin da kika fahimci ya so maki wata kyauta ta hanna?, Ina son sani ne dan na gane wani abin"
YUMNAH ta yi gagawar girgiza kai ta ce" Aunty maganar kyauta ai ba za'a nunawa TAUFEEK ba, yana min harda ta mamaki dan kin ga allert din gyaran da ya sako min yanzu haka dan wai baya so na ringa zuwa wajen gyara, kuma gaskiya ban dai tsaya na gane ba a kanta dan ina iya cewa wani lokacin yakan kawon abu yace KAUSAR ce tace zai min kyau suka siyo min dai da sauransu...."
Auntynta ta yi tsai tana hangen mamansu dake tsaye tana kallonsu ta baya ta harde hannayenta
Dan murmushi ta yi ta ce" To shikenan, abinda nake so da ke Auta ki kula, kin ga a furucinki kan iyayensa kina sakin harshenki ya fadi abinda kika ga dama, ki kula Auta ki girmam masa dangi koda autar gidansu ne a haka shima zai girmama naki dangin, sai kuma maganar Kausar , ina so ki fadawa Allah, idan kin tashi fada ki barawa Allah zabi, ki sanarwa Allah in har damuwa ce a rayuwar aurenku ita din Allah ya maku tsari da ita, in kuwa alkhairi ce Allah ya haska zuciyarki a kanta ku yi mu'amala ta alkhairi, kin ga mijinki namiji ne tsayaye da yake da mutane a karkashinsa tun yanzu, baki fa isa ki hanna shi ire iren mu'amalar nan, bama kamar yanzu da zamani ya zo haka, wasun matan abokanan lalacewarsu nema, ba tsoron Allah ba tsoron ciwo ko kunyar ya'ya, kuma gasu ana zaune da su kalau har sun isa da gidansu, ki kula ki bi komai a hankali, yanzu ne zaki fara, kar ki yarda ki fara da garaje da shirme Auta, inama abin kukan da daga muryar da tayar da hankali a nan?, Kefa macece cikin salama sai ki yakicetaba ransa ta hanya mai kyau ba ta hanyar muzguna mata ba in har kin kula cewa alakarsu fa bayan zumuncin da wani abu a kasa, kin ga namiji kowa da halinsa, abinda suka yi taraya a kai daya ne lamarin mata, Auta in har kin yarda cewa ba ta wani waje kika gaza ba yannayi ne haka Allah ya halicesu sai ki ba kanki lafiya ki rayu lafiya a gidanki da walwalarki, in kuwa har baki yarda da haka ba ina tabatar maki wahala zaki sh........."
"Ke, Auta bani wayarki " mahaifiyarsu da takaicin y'arta baba ya gama kamata ta karaso tana katse maganar da take yiwa kallon shirme ta amshi wayar y'ar tata ta duba adadin kudin da aka saka din na gyaran sannan ta mika mata ta ce" Tashi maza ki je dakinki ki yi wanka ki sha magani ki kwonta dan na san wannan kukan sai ya hadasa maki ciwon kai"
Mikewa ta yi tana daukan hijabinta dake ajiye gefe ta juya ta shiga haurawa, dan har ga Allah itama maganar yayar tata ba wani birgeta take yi ba, maimakun ta tayata samo mafitar da za'a iya raba TAUFEEK da wannan karfen kafar sai ta wani shiga magangannu wasu iri, ai walahi bama zai yiwu ba, du yar shegiyar da zata duban mata miji sai inda karfinta ya kare, ba maganar boka ko malan magana ce ta kai da kai!
Zama mamansu ta yi tana dauke kai hadi da hade fuska a lokacin da Fauziya murya a tausashe ta ce" Haba Mama, haba Mama, yanzu haka zaki nunawa YUMNAH bayan kin san maganar da nake fada mata gaskiyar kennan?"
Rai bace mahaifiyarsu ta ce" Kim ga Fauziya dazu kika iso, bana son damuwa please, ba kuma na son mu fara raba hali, ke sai ki mance ni na haifeki ki ce zaki sakani a hanya , ki je kawai ki huta ki yiwa Mubaraka wanka na yiwa su Mahfuz, maganar nan kar ki saka kanki a ciki, ki barmin kawai na san yadda zan bilowa lamarin lokaci nake jira dan ba zai yiwu ba, mu da muke garin mu muka san wannan mu'amalar kuma muka hango ilarta, ko ciki daya suka fito gaskiya ba zamu iya yarda da kusancin nan ba tsar zamu raba bale wai kawa kawancen namiji da mace, irinsu ne ke hanna maka zaman auren kana ji kana gani , domin ko me mijinka zai kareka da shi sai sun amince"
Ajiyar zuciya ta sauke, ba dan komai ba sai dan gannin maganar da alamu baba ce, kuma ba za'a barta ta shiga ba dan ra'ayi na iya bambanta, sai dai ta so su bata dama ta yi hanni irin na addinin musulunci ta kuma yi tuni da abinda aka sani, dan a ganninta yau macen da ta san ciwon kanta take kuma neman lahirarta zata yi domin Allah da kuma gyaran kanta, bayan wannan yaushe zaka saka damuwa a kan wanda aka halartawa irin hakan? Yau koda su biyu zai aura rana daya tanada abin fada ne? Wannan din kamar wata hanya ce da ta dauko wace ba zata bileta ko'ina ba, domin in har ta saka damuwar nan a ranta tabas ba zata rayu yadda take so ba, hakan na iya zama wata tawaya koma dalilin da zai ringa hadasa mata fitina da mijinta, bayan cewa namiji a waje da kuke saurayi da budurwa ne kake da damar ya tsaya ka tsaya in ta yiwu fine in ta bace kowa ya kama gabansa, daga bakin da ka zama malakinsa matarsa zaman zai cenza salo ne daga ka isa da shi zuwa ya isa da kai, watau rayuwa yar shawara yar samun matsaya mai kyau tare da yi masa biyaya, kai inma abinda ya shafi mata ne bama duka maza suke baka fuskar ka kawo masu maganar ba, tsaf za'a nuna maka ba huruminka bane kuma ka hakura kuwa ka zauna, domin wannan din ba cikakiyar hujar da zaka zo gidanku bane a kasarmu ta hausa
Mikewa ta yi bayan ta yi fatan Allah ya sanyaya ta yi gaba kamar yadda Mamanta ta umarta
Mahaifiyarsu kuwa ta dan girgiza kai cike da takaicin Y'ar tata ta fari, ita har mamaki take idan Fauziya na wani abin, kamar ba nononta ta sha ba , salo salo irin na ubanta, to ta je cen ta yi kanta ake ji ita dake zumunci kamar a hada kai da kishiya ita ta gano, na zata sakawa autarta sakaran ra'ayi tana zaune kalau ba
A gidan su KAUSAR kuwa a lokacin da ta koma ta samu mahaifiyarta rike da kudin nan a zaune ta balbaleta da fadan a kan me zata bari ya bata makudan kudi har haka? To kuwa za'a mayar dan ba zata ja mata rigima da babansu ba, da kyar Maman nata ta yarda cewa bata san ya ajiye ba da bata yarda ba, haka suka yi jigum jigum har abansu ya dawo ya tarar da abinda ya faru, nan ya sake yin nasa fadan shima yace aaba za'a karba ba dan haka ta sanar masa idan ya dawo a bashi, baya cikin amsar kyautar mazan zamani ba'a san me gobe zata yi ba in Allah bai yi su din ne mazan ya'yan ba a zo ana rikicin kudin da bashi da su bashi da inda zai hako su, dama shi haka ya hori ya'yansa, bai cika son irin kaye kayen kyautar samarin nan ba, in ba an san da maganarka har ta yi karfi ba a fara amsar irin abu dan jefi jefi kyauta irin ta sallah da sauransu ba, to kuwa koda sun amsa ba da sanninsa ko na mamansu bane, Mahaifin nata ne ya ajiye da kansa da nufin in ya dawo a mayar masa da abinsa
Washe gari kusan karfe goma da zai fita ya fitar da kudi masu yawa har kusan dubu talatin a cikin ajiyarsa ya ba
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 47