da taimakon junna ne, zamansu kuwa bayan Adu'ar gamawa da duniya lafiya sai fatan a je a samu baban rabo gobe kiyama.......
Shi dai Abansu bashi da kiba ko kadan, domin lange lange yake kamar zai rabe biyu, mamansu ce mai jiki sosai, dan ifan har jerawa zasu yi ba zaka taba hango abansu ba in ta yi tsaye......a haka tafiyarsu take tafe cikin aminci da tsarin addinin islama, inda Allah ya azurtasu da ya'ya hudu , mata uku dai auta namiji
Da salama ya shige dakin ya karasa ya shiga fitar da kwalayan turarukansa yana ajiyewa gefe , ga dakin Mamansu ta kunna dan turaran haki ya gama dakin da kanshi masha Allah
Shafa fatihar ta yi sannan ta ciciba ta mike ta karasa wajen kayan da ya zo da su jiya ta dauko ledar da bai mata bayaninta ba ta kawo ta ajiye sannan ta duka tana gaishe shi kamar yadda al'adun malan bahaushe mai nagarta yake
Da kula yake amsata da yi mata yan tambayoyin gidan da yaren, itama ta amsa shi sannan ta ce" Aban KAUSAR ledar nan baka min bayani a kanta ba"
Ledar ya dan ƙalla yana cirewa yaren turarukan daidaya masu kyau da tsada ya ce" Au na manta, na KAUSAR ne"
Dan murmushi ta yi tana kuncewa ta ce" Bara mu ga me yar gatan Abanta ta samu ne?"
Shima murmushin ya yi ya dan dakata da aikin da yake yi yana kallonta yana kuma jiyo kiciyar ya'yan nasa a tsakar gida ya san abin kari suke shiryawa da kuma shirin school ya ce" Kayan kwaliya ne jiya a shagin elhaji na ga wata mata na siyawa y'arta, y'ar yadda kika ga Kausar dina ana ta siya mata su nima nace a bani abinda aka basu kin ga takalmin nan mai dan tsayi kuwa? Zai yiwa KAUSAR kyau , harda wata shada nacewa Elhaji a yanka min yafi goma sha takwas karshen wata zan kai kufin mu ci sallah da ita in sha Allah"
Mama fuskarta bata gushe da murmurshi kawace a kai ba tana ta dagawa duda abinda take sakawa daban a zuciyarta shine addu'a da fatan gannin wata rana KHAUSARma ta fara gabatar da rayuwa irin ta yan mata, irin yadda mahaifinta ke kokarin nan yana son lalle lalle shima babar yarsa sai ta zamo kamar yan uwantan nan ta san burinsa daya ne Allah ya nuna masa ta samu miji ya aurar da ita ko ya fuskanci kannenta da suke da manema tuntuntuni...., A yanzu dai a kasar hausa shekara ashirin da hudu zuwa da shida ai an kai a shiga dakin miji, sai dai halin rayuwa da kadarar bawa idan har Allah ya yi mijin bai samu ba dole a yi hakuri a yi ta addu'a
Tana murmushin ta ce" Allah ya karra budi, ya karra rufa asiri, to ina na yan matana kayan kwaliyar ?"
Murmushin ya yi shima ya ce" yan matanki rasawa suke, inace ba'afi sati biyu da suka ce hodarsu ta kare ba har nace da Aisha ni indo hodar nan ko barci za'a shiga fai badata ake yi kau?"
Mama na daria ta ce" Kai, ai ƴaƴan nan sunna son kwaliya nu har mamakinsu nake yi, koda yake kwaliyar ai da ranarta gashi du sun samu manema , ama ita hajiar ba ga kwaliyar ba , ba ga dandasa gayun ba, ita dai barta da takarda da byro abinta"
Murmushi kawai ya yi , hakan ya sa ta sake tausasar da muryarta, domin abinda ta kwana da shi har ya saka ta kwana tana juyi kennan, maganar ya'yan nasu
A tausashe sosai ta ce" Abansu ina so mu tatauna wata magana ni kam"
Ajiyewa ya yi ya fuskanceta ya ce" Ai tunda na ga an ki fita a kamawa yayana aiki an bar min yan muleka da shara da wanke wanken asubahi na san da magana, yi bayaninki kai tsaye mamansu"
Murmushi ta yi , harshenta na yi mata nauyi kan maganar, a sanyaye ainun ta ce" Baban Muhamadu, kan maganar ya'yan nan ne yan mata...., Abansu dan Allah ina so ka dan duba lamarin nan mu samu mafita, ka ga Aisha da Rukaya sunna da masu so dan manemin auren Aisha yace idanma da hali yana so bayan babar sallah a yi bikinsu dan ya gama ginninsa...., Haka Rukaya a yadfa KAUSAR ta dabar min itama manemin aurenta ya shirya dama yake jira....."
Ta dan tsagaita tana sake sada kanta ta ce" Abansu na san menene damuwarka, ama idan har haka Allah ya yi gwara mu fuskanci lamarin a aurar da Wa'inda suka samu malamuncin nasu, kar a tsaya jiran har sai KAUSAR ta samu miji a hade aje Allah ya kiyaye suma su zo ana kame kame...., Ka fa san menene rayuwar y'a mace, gashi KAUSAR bata yin wani kokarin da zai nuna tana son ta samu itama mijin nan ta je ta kilace kanta, yanzu dogon karatun nan na likita dai bana an ga karshensa in sha Allah koda sakamako bai yi kyau ba ba za'a kuma zaman bence ba sai dai a yi jiran wata jarabawar....., Ka ga sai ta zo mu girka sana'a ginaniya mu yi dan karra talafa maka a cikin gidan"
Da kyar ta iya kai karshen zancen, domin ta sani ne abinda ke daga masa hankali Kennan a rayuwa irin maganar nan
Ya jima yana kallonta , shiru yana tunani
Cen ya iya budar bakinsa ya ce" In sha Allah, itama zata samu malamuncinta....., Lamarin rayuwa kowa da irin tsarin da Allah ya yiwa rayuwarsa......, Maganar ta kama sana'a aa ban lamunta ba, tunda dai da sauran karfina kuma ina yin daidai gwargwado bi izinillah zan ci gaba , ba zaku ringa fita sana'a ba, ta cikin gidanama da kike yi dan kar na hanna a ga na so kaina da yawa ne Mamansu, maganar shekarunta kuwa ni baya gabana , ko dan ni na haifa? Lalle yana damuna ama ba shi yake nufin yana gabana ba, abinda yake gabana bara ki ji , dama jira nake yi ta gama, in sha Allah dukkan hanyar da zata dan daidaita rayuwarta zan sake nema na rike, zan kaita a dan kokoya mata dan gyara irin na yan mata, ni bana yiwa y'ata kwadayin auren wane sai dan mutunci ko wanene komai tsufansa, kar ki manta a lokacin da na ganki bakida ko digon kwali a idannuwanki, ina yiwa y'ata fatan miji na gari baki dayansu, dan Allah mamansu ki daina yin magana da sarewa a ciki kin ji? Na san abu ne mai matukar hanna zuciya sukuni, ama idan har ke kika fara haka zaki yi gagawar cin mini kin ji?......, Yaran nan kuwa zan duba maganar auren Allah ya doramu a kan hanya madaidaiciya"
Ajiyar zuciya ta sauke tana amsawa da amen sannan ta ciciba ta tashi dan ya ci gana da aikinsa haka kuma yannayinsa baya mata dadi dan walwalar tasa ta ragu, ama ba zata saka damuwar haka a ranta ba, fatanta ya gane ya kuma rike wannan dama, dan idan har suka rayu da jiran babar yarsu in Allah bai yi zata samu da wurin ba sai a zauna a tauye kowa da kowa?, Su Aisha kansu yanzun sun fara gandamewa ai
Da wannan ya'yan du suka shirya, ita zata fara fita bayan ta gaisar da Abanta tana ta doka murmushin tambayoyin da yake yi mata tana bashi amsa sannan ya salameta yau har dari uku ya wanka mata hakan ya sa ta fito kanta a sama kamar sarauniya ta zo ta duka ta yiwa Mamanta salama sannan ta mikowa Maman nata watsetsiyar wayar TAUFEEK wace ta saka su Aisha zaro ido sunna kallon wayar domin su sun san cewa ba karamar waya bace, ita dai ce da ba komai ya dameta ba ba wani sannin kudin wayar ta yi bama bale har ta ji tsoron rikewa ta ce" Mama wannan wayar adanawa TAUFEEK ita kar aje ta fashe ina hadeta da kaya a jakar nan"
Maman nata ta amsa tana kallonta ta ce" KAUSAR me yasa kika amshi wayarsa har ki je ki yar bakya tsoro? Da gani wayar nan ba karama bace ba fa?"
Aisha da ta rafka tagumi ta ce" Mama, wayar nan ai sai ta sayi aunty Kausar tsaf harma a nemi kari, Aunty Kausar da wayar nan kika kwana a gidan nan a san tana nan a shigo a yi kidmashin dinmu?"
Rukaya ta yi dariya tana dungure kan Aisha ta ce" Ke haba dai wayar zata wani sayi mutun, ama fa Mama wayar nan ba karamin kudi ne da ita ba gaskiya, koda yake su a gidansu yar autarsuma mai shekara goma sha uku iphone ce a hannunta ranar da muka je din nan amsar books din aunty kamar na kifa kallonsu kawai nake yi, Mamansu wata yar gayu da ita bakinta turanci ya amshe hausar"
KAUSAR ta girgiza kai ta ce" Ku dai kula sani, Mama wayar yau kwananta biyu a wajena, ba kin ga irin fadan da na masa da wayar Aba kan karatu ba? To Mama za'a shiga aji na amshe wayar dan karma ya zauna yana dane dane, har an shiga aji kawai ya tashi ya tafi har yau dai da ban ganshi ba, gatanan wayar a hannunki idan ya ga dama ya zo ya amsa, ni ba ni ba shi ko a hanya ya ganni ba zan nuna na sanshi ba, tunda haka ya zabarwa kansa sai ya yi"
Ta gama fada da takaici ta mike ta tafi tana fadin ta tafi
Aisha a a sake tafa hannu tana rakata da ido kafin ta dawo dubanta kan mamansu ta ce" Iko sai Allah, ni wani lokacin sai su rikitani da tunani, wani lokacin kuma sai kawai in ga kawancen ne kawai, ama yanzun kamar wata budurwarsa????"
Rukaya ta ja numfashi ta ce" Ke da ke kadai ce sai a maki maganin haka, ama kuma idan har kika yi duba da yannayin abin nan bayan zumuncin babu komai, aunty fa babu wannan maganar tsakaninta da shi, shima haka, inaga fa shekara hudu ce kawai ya batama, kuma bayan wannan yarinyar da zai aura fa in fada maki komai a hannun Aunty yake, kawai haɗuwar jinni ce mai wuyar fasara, ni abinda ke bani dariya da Aunty idan suka yi fadansu ta ringa rantse rantsen ba ita ba shi, ita dole sai ta sa ya mayar da hankali kan karatun da ya je ko bai je ba takardunsa tuni a hannunsa, kuma ya yi ko bai yi ba sunnansa mai kudi, ama haka ta yi ta fushi shima ya biye mata"
Mamansu dai da ta kai wayar ta boye dan ita tsoroma wayar ke bata ta dawo tana fadin" kai maza ku tashi ku yi da jiki ku kama hanyar makaranta ba sai kun yi lati ba ku ce sai an baku na sahu!"
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 3️⃣
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Haka suka mike kowace ta shirya suka fice makaranta, Aisha na ajin karshe a secondary domin ita akoy wasa da karatu, Rukaya kuwa tana karantar malamar makaranta
Kwonci tashi har suka gama jarabawa kwana bakwai cif suka shiga hutun sati daya , hakan ya sa hankalinta ta tarkato shi ta mayar hanyar islamiya sai yan shige da fice kasuwa lokaci zuwa lokaci na shorye shiryen auren y'ar makociyarsu da kusan komai ke hannun mahaifiyarsu domin akoy zumunci sosai sannan sun sani ne Mama akoy amana, in dai ka sakata a lamarinka da izinin Allah ba zaka ga ha'inci ba, ƴaƴanta yan mata suka zamto kawayen amarya , ama KAUSAR bata wani yawan shigewa cikinsu, domin haka kawai take jin kanta ba yadda take so a cikinsu ba, hankalinta baya taba kwonciya waje daya idan tana cikinsu, sai ta ga duniyarsu ba daya bane, hangensu ba daya ba, kai komaima sai ta ga ba daya bane da ita da su, hala suma irin lokaci zuwa lokaci da zaka ga sun hade da itan basu da wata sakewar a zo a gani, idanma tana wajen du wani abu na yan mata basa sakata, dan tun daga yannayin jikinta har kafarta bai nuna tana da muradin hakan ba, sai ana gobe daurin auren nema ta yi kunshi a gida, shima Mama ce ta kunsa mata kunshi na hausa hannayenta da kaffaguwanta ta kwana da shi, ya zamto tunda ta tashi sallar asubah ta wanke ta daura alwallah ta shige dakinsu, yau ita daya ne domin kannenta sunna gidan su amaryar cen suka kwana , hakan ya sa da jiki tana gama sallar ta saka doguwar riga kawai ta saka hula ta fito ta shiga aiki ka'in da na'in dan tsaftace gidan domin nan amaryar zata wuni da kawayenta
Tana tsakiya da wanke balbalin gidan suka yi salama suka shigo da amaryar da babarsu yayar mahaifinta sai kannenta aka rako amaryar, hakan ya sa ta dakata tana gaishe su da murmushi shinfide a saman fuskarta ta masu jagora har dakinsu inda ta shinfida katifar mamansu ta shinfida zannin gado sabo mai kyau dakin sai kanshin turaren haki yake haka kuma kasan an shinfida tabarma biyu an malale ko'ina, tsaftsaf dai ba dati
Tunda ta dage labulen babarsu amaryar ta kama baki tana kare mata kallo, har ta gama ta janyo hijabinta zumbulele ta maka tana sake gaishe su da fada masu su shige ta ci gaba da aikinta har matar ta gama ta fito ta tafi gidan bikin zuciyarta fal mamaki ne ke neman kasheta
Lalle Allah ke halita, lalle ta yi mamakin wannan sankacecen sanwon dake bayan Kausar mai sunna duwawu
Ashe yarinyar nan hijabin da take sakawa abinda take boyewa a karkashin sa kennan? A kulun sai a rinha cewa KAUSAR balaluwa mai hijab, Kausar bata son kwaliya, bata son meye meye ta ki kama jiki ina zata samu mijin aure wannan zamani na yanzu da mazan suka zamto kyale kyalim shine abinda suke so, gashi Allah ya yankota mai baban jiki sai nuku nuku da hijab kamar zai makata da kasa, ashe ashe rufin asiri ne saka hijab din nan? To da ace Kausar bata lulube jikinta lalle da an ga kudan zumu a tare da ita, domin mazan fa zasu zo ne ko ana ha maza ha mata, tabas da dubu sun mayar da ita doki koda kuwa bata so, kai ita a yau sai ta ga gaskiya gwara da yarinyar ke rufewar, sai dai rufewar ba damuwa bane, damuwar KAUSAR bata damu da gyaran ba, ba wai wari take yi ko wani abin ba, ama a shekarunta bai dace ace tana fita haka ba kwata kwata, yan mashinshinan nan ko na anguwa sun gagara?
Da kyar ta kade tunanin a ranta ta shiga harkokin kaye kaye na shagalin biki
A ranar an wuni shagulgulan biki, domin anguwarsu anguwa ce ta talakawa ama fa akoy kara, dan ina ana sabga zaka ga kwansu da kwarkwatarsu an hadu ana ta murnar abin, ba wai zaka raba su da tsegumce tsegumcen anguwa ba, ama kuma hakan bai fi karfin zumuncinsu ba, dan kuwa koda irin hakan ya faru akoy Hajia datijuwa wace ta kasance mai tsawatarwa yaren matan , kuma sunna jin maganarta sosai da sosai
Kowace budurwa ta sha kwaliyarta ana shan hotuna ama KAUSAR tana fama da rabe raben abinci da sauransu, harta Ankonta bata wani saka ba tana ta kai kawo ne bata zauna ba har yama ta yi aka raka amarya gidansu dan shiryata kafin dare a yi mata rakiya
Bayan sallar magariba Mamansu ta shigo tana dan sauri ta shige ciki tana kiran sunnan Kausar
Fitowa ta yi tana amsawa hijab dinta a hannunta domin bata jima da gama sallah ba zaune dai take tana karatu
Mamansu ta miko mata jakarta ta ce" Ke ba zaki je rakiyar amaryar bane?"
KAUSAR ta girgiza kanta tana murmushi ta ce" Mama to wa zai tsare gidan? Yau auta kansa ba dama ba'a ko ganninsa yana cen wajen su Kabir"
Mamansu ta yi murmushin itama ta cenza hijab dinta ta fesa dan turare ta ce" Ai kam, to bara na je kin ga sai mun kaita dakinta, ga wayar nan ta wajen Taufik fa kar na fita na barta haka a daki duniya ta rikice ni kuwa su Aisha sun tsoratar da ni da tsadar wayar"
Wayar ta dalawa harara tana jin wani takaici nasa ya taso mata ta amsa ta kai ta ajiye dakinsu tana tsaye har mamanta ta tafi sannan ta koma ta ci gaba da karatunta hankali kwonce
Bayan sallar isha'i da kamar minti talatin da daya ta fito tana rufe gifan dan zuwa ta kamo Auta, domin ya cika dare haka a waje dan kawai ana taron nan ne da ba haka ba da tuni yana gida sallah kawai yake fita , gashi mamansa bata nan , hakama Babansa gwara ta kamo shi ya dawo gida ya ci abinci ya kwonta ko dan islamiyar safe
Dakatawa ta yi ta zubawa galeliyar motar dake parker gaban gidan kadan ido
Gane mai motar ya sakata sake bude gidan ta shige, shi kuwa daga zaunen da yake sake zubawa kofar ido ya yi a hankali ya shiga dan lumshe idannuwansa dan maganar sai ta so zame masa biyu a cikin kwonyarsa dan kuwa budurwarsa na magana ne ta wayar da ta yi kiransa da kuma tunanin me nufin komawar aminiyarsa cikin gida bayan ya tabbata ta san motar nan?
Jim kadan ta fito tana sake kulle gidan ta karaso hankali kwonce ta bude gaban motar gefen da ba kowa ta shiga ta zauna ta mika hannunta ta dan matso kofar dan a bakin hanya ne ga anguwarsa da yan acaba
......ba komai ya saka ta shiga motarsa ba sai dan ta fada masa abinda ta kulo a zuciyarta!
Tarin abinda zata juye masa ne a zuciyarta!
Kuma ta rantse sai ta fadawa Taufik duka kaf abinda ta shaka
Kasa kasa sosai Taufik dake kallon wayarsa da ta ajiye gaban motar ya ce" Zan yi kiranki *YUMNAH*"
YUMNAH dake son sannin wai yaushe zai karaso gidansu ta ce" To shikenan, ama baka fada min karfe nawa zaka karaso ba?"
Agogon ya dan kalla, sai kuma kasa kasa ya ce" Zan dai taboki"
Wannan karron bai tsaya ta bashi amsa ba ya katse kiran sannan ya juyo yana dan sake rage girman idannuwansa dan ya ga ta gyara zama ta cika fuska tamkar zata fashe ya bata hankalinsa
A takaice dai kamar yadda ta saba ne idan ta kwaso masifa sai ta zo juyewa ta rasa ta inda zata fara da kowama hakan ne yanzuma yake neman samunta
Da kyar, da kyar ta iya sake cije lebenta sannan ta saka hannunta zata bude motar ta fice
Da sauri ya ce" KAUSAR "
Dakatawa ta yi ta juyo da wani tuwon takaicin mai hadasa ciwon kai ta sake zuba masa idannuwanta tana sauraronsa
Kai ya dan sinne kasa kasa ya ce" Sorry besty "
Rai bace ta ce" Taufik, ka rike sorry dinka, nace ka rike Sorry dinka Taufik, bari ka ji in dai ni yar halak ce an haifeni a hanyar halaci ba zan kuma........................."
Idon da ya tsura mata da wani irin kallo mai kama da kashedi ya saka ta shiga wani inda inda kamar tana gaban Aba, har sai da ta tuna irin haushin da ya shaka mata sannan ta jure ta yi watsi da wani wasi wasin tunani ta ce" Ba zan kuma yi maka magana a kan harkar karatun nan naka ba, ai da ake fada min nice nale rintse ido dan tunanina na isa ko ina iya gyarawa ne? Ban san cewa nice nake lalube kai karatu ya maka rana ko kar ya yi kansa ne, sai dai na kasa gane a kan me ka zabi zama likita bayan ka san shine aiki mafi hatsari a duniya, domin da allura daya kana iya kashe bawa, na san kana da ilimi, hakan ba yana nufin kai aljani bane, likitanci ba'a cenkarsa sai dai a karanta du ilimin mutun!, Ka ki ka gane ko ka ki ka mayar da hankali zan ce? Duka wannan yanzun kam babu ruwana ka yi yadda kake so Taufik, ka ga tafiata"
Watau da ake cewa babu abinda ya fi ciwo a duniya irin ka shako fadanka ka rikoshi da hannu bibiyu irin na rashin mutuncin nan, ka zo dan ka juye shi a kan mai rabo ama ka yi ka yi a maka shiru hakane, watau a ki biye maka hakane, yau ta karra yarda da maganar
Du wannan babatun da ta yiwa Taufik, duka kaf wannan fadan da ta saukewa TAUFEEK ita TAUFEEK ya karewa kallo ya mata banza tamkar wata shashasha wace bata san ciwon kanta ba? Ita TAUFEEK ya kyale ta ringa hayaniya kamar zata ari baki? Lallema!
Da bacin rai ta maki masa marfin motar , tana juyowa ta ga Auta a tsaye yana bangalar baki shi da abokinsa har yana dage ya ce" Auntynmu, yayanmu ne a motar?"
Wani takaici ya kuleta, wai ƴaƴansu, to yau du wani mai kiran TAUFEEK yaya dan yana dan uwanta ta soke!, Da bacin rai ta janyo shi ta ingiza keyarshi gaba bata bashi amsa ba suka karasa kofar gidan ta saka dan makulin ta bude suka shige ko gaishe da Malan Barau bata yi ba domin ya wani kura mata ido har lekawa yake yi motar da ta fito, ta tabata yau sai an dora dandalinta a anguwar
Ajiyar zuciya ya sauke ya sake duban wayarsa dake haskawa
Bai daga ba kawai ya tayar da motar ya juya ya nufi gidansu, dan ba zai je wajen abokanan nasa ba, haka kawai yake ji idan ya je yana iya sauke fushin da ba nasu ba a kansu
Mikewa malam Barau ya yi yana lekawa kafin ua juyo yana kama haba ya gyada kai ya ce" Ikon Allah, ni ban taba gannin gida irin na bawan Allahn cen ba, ka ga fa malan Saidu sai ya je ya dawo daga kasuwa da ledoji na kayan kwalam da makulashe ya shige ciki ya sake tirke kartin yan matan cen ya ciyar ya yi barci harda minshari safiya na yi ka ganshi kalau abinsa....., To ni Allah na tuba ko daya na girke irin ya'yansa ai ba ni ba rintsa ido kalau kamar wanda bani da damuwa a duniya, ba zan taba iya rintsa idannuwana ba dan ya'ya mata ai fitina ne, ka ga du sun kamo shi a tsayi biyu jikaka biyu mudil mudil ama baya ko yar suman nan ta badi? A gaban idannuwansa a shiga a fita ana rawar nanaye wai yan mata ne? Ka ga yanzun itama wace ake cewa bakin aljani ne ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 47