LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Sosai Baba ya rasa bakin magana, sai dadagawa yake yi ,
Shi dai namiji ne bai san tsadar kayan mata a ido ba, in ba zuwa siya ya yi ba yakan hanki masu irin nauyi a idon nan haka a cen bangaren manyan kaya, bangaren abinda ya haura dari du kwaya daya, a yanzu haka wannan na hannunsa ya tabata kudi ne na mamaki, hakan ya sa ya dubi iyalinsa ya ce" Mamansu, kayan nan basu yi yawa ba kuwa?, Kayan nan da gani zasu yi tsada"
Murmushi ta yi tana dan sake ziga masa kunnun dake hannunta ta ce" Ai kama Abansu kayan nan zasu yi tsada sosaima, kuma ka ga na wajen mutuniyarka? Har cewa ta yi yau ko dan goron baka aika mata ba, dama jira nake yi idan ka zo ka gani abinda kace sai a yi in sha Allah " (not, kar ki ringa nunawa namiji a cikin gidansa a irin girma da daraja da Allah ya masa cewa bai isa da wasu manyan decision na cikin gidansa ba kece kika isa..., Tsakaninmu mu mun sam cewa muna da baban iko da rayuwarsu fiye da tunanin bawa, domin muna da damar tankwasa su a lokacin da su da kansu basu gane ba....., Yarda da hikima irin tamu ta siya mana haka ba nuna isa da takama ba, to wai wace isarma Allah na tuba ke da akace ki zo ki yi biyaya dan neman aljannarki? Ba gazawa bane dan kin bashi damarsa a matsayinsa na mai nemo gero da hatsi yana daukan decision din abinda ya shafe ku a cikin gidansa.......hakan ba yana nufin ki kasa juya abinki cikin hikima ba, cikin hikimar kina iya samun abinda kike so shima yake so ba tare da daya ya ga an tauye daya ba......, Allah ya karra hada kawunnanmu da Mai hause🥹😍)
Murmushi Aba ya yi yana girgiza kai ya ce" Hajia hajiar shagali, ai zan je da kaina na kai mata goronta , ama kuma ba za'a mayar da kayan nan ba, a tsakaninmu da mutanen nan inaga idan muka yi haka bamu kyauta ba, sai dai kin ga kudin shadar da na ba Elhaji? Zan koma na ce zasu je su zabo maku takalma da kudin, idan ya so kudaden takalman da wasu tanadin sai na karra mu fara shirin gudunmuwa, har sai na shiga tunanin nawa zan tanada ta gudunmuwa ?"
Mama ta miko masa kunnun da dan dumi ama kuma ba sosai ba tana murmushi ta ce" Abinda Allah ya hore maka, yadda ba zaka takura ba ba kuma zaka yi kauro ba, kai da kake da bikin a gabanka kaima?"
Ai kam ta saka shi dariyar, domin katon asusu ne ya bude yake jefa tanadi kulun ta Allah, da safe da kuma yama , tanadin da suke sakawa a tare domin itama in cenjin kayan miya aka yi sai ta kai ta zuba, a zaunen da take yan saide saidenta su lalle da salatif da dai dan abinda ba za'a rasa ba ta kayade riba na hawa tana zubawa, danma ya ki sana'ar a fita ne ai da samun ya fi haka.....haka dai suka cika darensu kafin suke kwonci dan murnar yau ta hanna masu kwonci da wuri
Kwana biyu tsakani Khausar ta shiga rabon anko ita da yan uwanta
Kusan abinda ke ba Kausar mamaki har ya bata dariya shine du wace ta kaima sai ta jefo mata tambaya fuska cike da mamakin wai dan Allah dama irin yadda zumuncinta yake da TAUFEEK ba saurayinta bane?, Har sai da ta gaji da bada amsar a tsare sai kawai ta katse amsar ta badata a hade dan maganar ta wuce, takan yi dariyar wannan kwabin da wani tunanin wasu mutanen, kai du wanda yake irin wannan tunanim ta yi waje ta ajiye shi a matsayin mutun mafi rashin fahimtar rayuwa gaskiya
In ba rashin fahimta ba ina mahadi? Ina hadi? , Eh lalle TAUFEEK ba wai ta girmeshi bane, haka kuma a yannayin jikinsa TAUFEEK ya fita tsayi kuma jikinsa kakauran jiki ne ba lange lange ba, ama sam bata gannin wata mahada ko kamanin dale iya sakawa mutane wannan banzan tunanin, ba wai da tana y'ar talakawa ba yana ɗan masu kudi ba, ko daya, ita bata taba raina asalinta da samun mahainfinta ba, kuma ta san masu kudin na auren talakawan su kilace cikin hukuncin mai sama, abinda ta gama sani ne ko giya take sha TAUFEEK ba abokin soyayarta bane, ba kuma abokin kalamai ire iren wadinnan bane, kai mtssss haka kawai ana nema a hade mata tunani? Tana zamanta ana hade mata lisafi? A gaskiya abin sai ya fara bata haushi da tarin dumbin uban mamaki..... karshe ta kawo na mujiya ta zubawa du mai mata kallon, in har a ganta da ankonsa ba zai cire tambayar nan ba a ran mutun to dan Allah ya rike tambayarsa a ransa abinsa
Yawan zuwa shagon Elhaji amsar atampopin masu hada mata kudadensu wata halaka ta kulu a tsakaninta da baban yaron Elhajin watau Mujaheed
Alaka ce irin ta shanshakai ta siyaya da farko farko, a hankali ta ringa karantar wasu sababin hulda a tare da shi da suka so bata tsoro, domin sai take tunanin cewa ta zo ne zata yi lokaci kalilan a shagonsu zai kula alakar dan ya tozartata ko dan ya mayar da ita costoma a wajensu ta yadda ko zuwa gaba bata da wajen cire anko sai shagonsu
A hankali kiran dake shiga tsakaninsu ya dan fara yawa, ya zamto ya fara sakata boyewa idan har zata amsa kira a cikin gidansu domin kamar jira ake yi yar rakani masai dinta ta kwashi tsuwa du sai a ratabo mata ido ba ga Maman ba , ba ga ya'yan maman ba, uwa uba ana daf da shan ruwan kwana na goma sha takwas da azumi a ranar Aba ya dawo da wuri wayar nan ta dauki tsuwar da ta saka yayan hanjinta yamutsewa dama ga abin yinwa na sakata juwa domin a irin lokacin nan du wani kayan buda baki a gabanta suke jira kawai take yi a yi gyaram murya a masalaci ko na tsokana ne ta daga ta maka sai kawai kiran nan ya shigo ya zamana Aba dake zaune saman darduma yana jan carbi sunna dan taba hira da Mama dake zaune daga kusan dakinta Auta a saman kan cinyarta ya yi matashi yau azumi yake kamar an summar da shi , su Aisha kuwa sunna gama wanke wanke dan su kam da sauki sosai sunna da juriyar azumi sosai da sosai kowa ya juyo inda wayar ke ajiye tana kuka irin na kashe kunnan nan tamkar mai son saka kurma ya ji tana ringin daf da yasashen hannun Kausar dake yashe ya sake du ya fice a hayacinsa
Da sauri ta dauke kanta, har zuciyarta bugawa take yi, wani takaici na neman kunnota gannin sunnan dake kai watau ATAMPA sai ta ji kamar tana dagawa ta kirta masa Alllah ya isa da masa tsakani da ita, to in ba yana neman sakata a halin ha'u'i ba a gaban Aba? Sai dai kashhh, a dole hawaye suka tsinke mata a lokacin da Aba cike da wani yannayi na son ta daga wayar ya ce" KAUSAR ba kiranki ake yi ba?"
Kai ta girgiza da sauri tana share hawayen dake sake zubo mata murya a kurya ta ce" Ba kira bane Aba"
Aba ya kafeta da duba kadan yana fadin" Aa, kamarya ba kira bane, daga mana wannan na uku ne fa, kukan meyema kike ni ba an kusa shan ruwan ba? Ko yau juwar da karfi ne?"
Kai ta sake gyadawa , ta dauki wayar ta mike da kyar ta shige ciki ta je cen bayan katifar Mama ta duka ta labe sosai murya a shake ta amsa wayar tana cicijewa da son sannin wani bakon munafurci ne wai wannan kiran nata ba lokaci?
Murmushi Mujaheed ya yi , da yannayinsa na sanyi sosai ya ce" Wai kina jin kishirwar nan ta yau kuwa Kausar?"
KAUSAR sai ta so ta ce da shi Ina ruwanka da kishirwata? Ni fa bana son neman fitina ban iya fada ba gaskiya, sai dai jin yana dan murmushi ya sake cewa" To ko dai aikin mamana kike ne na dameki?" Ya sakata jin ba zata iya fada masa hakan ba, hasalima sanyin da muryarsa ke yi in zai mata magana na damunta lokuta da dama, sai ta ji kamar ta dauke shi ta goya ta bashi hakuri kar ya yi kuka, kamar wani maraya gaba da baya, koda yake Mujaheed ai bashi da alamun karfima bawan Allah, jiki ne da shi sosai kuma bashi da tsayi, ga yannayi irin na yayan madara dai tare da shi dan ko a shagonsu a zaune yake abinsa yana yan ciye ciyensa yana kai karshen yayan banki, watau shi ke amsa ya ja gaban table ya zuba ya dadana abin irge ya watsa , su kuwa yaran shago na zubawa a leda da kuma kaima mutun waje, sai dai ba zata yi karya ba a dan tsanin zuwa da dawowa sun kula shegen kyauta ne da shi sosai, bayan ribarsu ta atampa da ake ware masu a shagon du wanda ya je siya wace aka basu damar dorawa, sai kuma ya karra masu da na adaidaita sahu du idan sun je , ita tana kyautata zatonma Aisha ko Rukaya yake so, ai kuwa zata fada masa gaskiya ya yi hakuri an masu miji dan har an zauna da manema aurensu an basu su har an saka lokacin biki da babar sallah ne in sha Allah
Dan gyaran murya ta yi ta ce" Ina yini Elhaji?"
Murmushi ya sake yi ya ce" Lafiya Hajia , yaya gajiya?"
Yanzun kam bata amsa ba sai dan uhum kawai da ta ce tana dan murja yan yatsunta, haka kuma wayar na dan tsut tsut tsut alamun wani kiran na shigo mata ne
A hankali ta ce" Dama , dama babu mai son atampa fa"
Dan tsai ya yi ya ce " Wace atampa fa HAJIA?"
KAUSAR ta yatsine gaban goshinta ta ce" Na zata dan ka ji ko na tara kudaden masu son atampa ne?"
Har ga Allah abin sai ya bashi dariya, ama sai ya ki nuna mata dan kar ta ji ba dadi, a sanyayensa shima ya ce" Aa, ba wannan bane, dama ji na yi ina matukar son jin muryarki da kuma jin ko kina lafiya? Bale yau kin ga ana rana sosai ga zafi ina jin kishirwa sai na damu da son jin kar aje kema haka kike ji?"
KAUSAR ta yi tsuru tsuru, wannan wani irin bakon balagagen tashin hankali ne? Tana zaman zamanta yace wani dan ya ji ko tana lafiya ne? To ita ina hadinta ina shi dan Allah? Mema ta masa da zafi?
Da sauri ta samu kanta da kashe wayar tana ta zazaro ido cike da tsoro da fargaba, sai kuma ta ji alamun motsi hakan ya sa ta juyo da sauri
Ido hudu suka yi da A'isha, wace tun shigowarta take tsaye tana kallonta da sauraronta
Cikin dabara Aisha ta wayance ta ce" Aunty, baki ji kiran sallah bane? Aba yace ace maki an sha ruwa"
Sai a lokacin kunnayenta suka ringa jiyo mata alamun dake nuni da an sha ruwa
Jiki ba karfi ta mike ta fito ta samu waje ta rakube ta dauki kayan shan ruwanta ta shiga sha tana sauke ajiyar zuciya, baki daya ahalinta sai suka yi tamkar basu ga komai ba suka ci gaba da shan ruwansu suka tayar da sallar magariba
Da dare bayan an dawo daga masalaci yau yan matan kaf dinsu sunna daki, tunda yayarsu ta shige ta labe suka tatara abincinsu suka bita, hakan ya sa Abansu dan damuwa yana tambayar wai ina suke ne?
Murmushi kawai Mamansu ta yi tana sada kanta, domin har ga Allah ita din da kanta sai ta ji tana iya jin kunyar maganar nan da Abansu, KAUSAR fa itace yarsu ta fari, sai ta ji tana iya jin nauyin maganar sosai da sosai
Daria Aba ya yi, har cikin zuciyarsa wani farin cikin na sake ratsa shi, a hankali ya daga hannayensa ya ce " Allah kai ke badawa, kai ke hannawa, ko waye yake son shiga rayuwar y'ata idan da alkhairi ya zo ya ubangijina ka tabatar mana, in ba alkhairi ya zo ba ka rabata da shi cikin aminci, domin irin wahalar zaman da ta sha ina fata idan ta shiga gidan aure ta yi zama na farin ciki"
Mama ta amsa da amen a hankali, a zuciyarta kuwa tana tunanin lalle lalle sai ta bada gudunmuwarta itama a matsayinta na uwa, domin ƴaƴanta ita ta haifa babu wace bata san halinta ba, a cikinsu tsaf zata iya zana halayar kowace, ta sani ne bakon lamari ne wannan din a duniyar yarinyarta, idan aka yi wasa tana iya kabe shi ta kore dan tana tsoro, a dole za'a jata a jiki cikin dabara a ringa kwatanta mata har ta gane ta kuma dauka da hannayenta bibiyu ta rike, dole za'a tayata idan ya so in har abin ya tabata gaba sai ta kwaci kanta, sam sam KAUSAR bata da wayon iya zancema bale wai har a kai ga fahimtar junna ita da namiji, zata iya cewa maza biyun nan kwarara sunne suke da mu'amala ta fahimta a tsakaninsu da halayan KAUSAR, daga Abanta sai amininta
Da wannan farin cikin suka yi zama a ranar
Yan matan kuwa a ciki kowace dariya ke neman halakata
Kiri kiri auntynsu ta kashe waya ta nemi mutsukets tana ta hada rai, ta ki kowama ya kawo mata wata maganar ta raini ta hade ta tsare tana ta basarwa, abincin kansa yau ba damka ta sako da sako akai masa ba, sai da aka raba shi biyu sannan aka samu ya shiga a hankali, daga karshema ta yi kwonciyarta da wuri wuri bayan ta kawo dalilinta na kwonciyar da wuri cewa tana so idan Alllah ya wayi gari lafiya su fita da wuri dan kaiwa mace daya da ta rage, tana kuma yarda da maganar Rukaya da tace da ita ya dace su malaki wayar android koda daya tak ce, domin da da ita da ta wayar zasu raba ankon ba tare da sun sha wannan uban yawon ba, abinda ya fi bata takaici da shi kiri kiri ya ki ya rabawa abokanansa maza, sai da ta ga ba fa zai yi ba ta kaiwa amininsa daya da suke jin maganar junna ta bashi ta yi tafiyarta, ta tabata shi kam ya raraba, TAUFEEK kuwa dole ya shafa mata lafiya domin biki sai ta warwasa yadda ake yi a ko'ina ehe!
Tsakanin wannan lokacin zuwa karshen wata mai albarka, watau watan azumi a hankali shakuwarsu ta fito fili har ya zamto babu wanda bai san cewa Kausar itama ta samu masoyi ba, ciki kuwa Harda TAUFEEK
A hankali yan uwanta suka fi karfinta suka saka mata ra'ayin amsa kiran da kuma ra'ayin kulashi har ya zamto ita da kanta tana jin dadin hakan har ta iya rike lokutan da yakan kirayeta su zanta, sannan ta sanar masa ya yi hakuri nacin yana son zuwa gidansu ya bari a salace baki ya bude sai ta sanar a gida , a lokacin kuwa tuni Mamansu ta sani itacema ta ce sai baki ya bude dan a yanzu cikin ibada ake ba ji ba gani du wani mai neman duniya da kiyama zai maida hankali in dai yana da hankali kuma yana da rabo
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 9️⃣
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Sanu sanu azumi ya zo karshe, aka wayi garin sallah, sallar musulmai, baki daya musulmai kwonsu da kwarkwatarsu a wannan rana sunna cikin yannayi na farin cikin gannin sun samu gabatar da ibadarsu har Allah ya nuna masu ranar sallah
Hakan ya sa a ranar da yawa sunna gida wasu kuwa sun fita ziyara...., Ranaku a kalla sun kai biyar da ake gabatar da bikin sallah kennan a kasarmu ta hausawa, ziyara ne gidajen yan uwa da aminan arziki, zuwa wajen wasan sallah ne da sauransu har kwanakin kaiwa samari kwarya kwaryar sallah ta zo, ya kama daidai da ranar da KAUSAR zata amshi nata bakon, watau goma ga watan sallah
Ita dai du gannin abun take yi wani iri, bama da ta ga mahaifinta ya shigo da kankana da yan kayan hadin da ya saka Mama ta zana masa ya ba su Aisha kan su yiwa bakon ruwan tarba wanda hakan ya matukar sakata sake jin kunya da nauyin mahaifanta harma ta kashe wayar ta boye a daki ta wuni cikin tunanin ta inama zata fara ? Yaya zata dubi abin? Ta ina zata bi da abin? Haka dai ta har magariba ta kawo kai Mama ta shigo ta tasheta tana fadan me take haka bata kimtsa ba bayan ta san tanada bako?
Aisha ce ke dan murmushi tana kallonsu Maman na tsaye kofar bayi tana fadin maza ta yi wankan nan da kyau ta fito Rukaya kuwa ta idasa kimtsa kayan tarbar bakon ta saka a dakin Mama ta kilace bayan sun fitar da na gidan
Shirin ya zo mata wani iri, riga da sket dinta sai hijab wanda da kadan ya zarce gwuiwarta aka bata kan su zata saka domin tarban bakon
Ta saka sket da rigar ama ta kasa saka hijab din har Rukaya ta sanar da ita cewa bakonta fa na waje kusan minti ashirin kennan
Jiki ba karfi ta mike ta dauko wani hijab din sabo wanda suka saka ranar sallah ta zumbula abinta sannan ta dauki carbi kamar wace zata he bayar ta wa'azi ta fito tana rakubewa wayarta a kunnenta tana amsa kiran TAUFEEK dake sanar mata zai biyo ya bata katinta da zata bayar dan ta nace sai da ta buga mata kati na gayata ta samu ta wuce a gidan da kyar tana sauke ajiyar zuciya
Motar ta kurawa ido bayan ta ja ta tsaya a kofar gida, ance ta je ta shigo da shi ne, sai dai bata tunanin in har zata iya karasawa wajen motar cen dake tsaye ko ba zata iya karasawa ba, uwa uba yau anguwar dinke take tak da jama'a yan matan ne da samarinsu, tsofafin ne ana firar dare dai haka, kuma a hasken farin watan da ya haske anguwar tarin bolar dake zube ko'ina ta hasku tarrr haka itama ta hasku cikin farin hijabinta harma aka fara dan tsunguri tsoman ana raraba maganar cewa ta yiwu wanda ya saba zuwa ne ko kuwa menene wannan? Ciki harda yan matan da suka sha kwaliya suke kannan bayanta sosai sunna zaune a nasu gefen sun zubo ido sunna son gannin ya fito ya shiga cikin shigarsa ta kamala da tarin kwarjininsa kamar yadda ya saba, sai dai yau har yanzu babu fito daga motar ba
Tana kokarin neman layinsa ta ga ya bude motar ya fito, hakan ya sa ta dan sake matsawa kadan jikin garun ta sada kanta
"Barka da warhaka Hajia Kausar" ya fada da muryarsa mai sanyi kamar yadda ya saba yi mata magana
Cike da kunya ta dan dube shi, sai ta ji inama zata iya rage tsayinta koda basu zo daya ba ta dan gota shi kadan? Sai dai har ga Allah bashida tsayi ko kadan Mujaheed, dan dai yanada dan fadinsa ga tumbinsa kuwa a cikin manyan dinkinma ana gannin yadda ya yi gefe abinsa
Dan rage tsayi ta yi ta gaishe shi sannan ta sanar masa ance ya shiga ciki
Kwarai ya ji dadin haka, dan hakan ya nuna masa yana iya samun karbuwa wajen iyayenta, domin in har aka baka dama ka shiga cikin gida to fa ana da niyar dubanka ne
Har kasa ya duka ya gaisar da Mama dake labe daga daki sannan ya zauna saman tabarmar da aka shinfida masa, ita kuma ta labe daga fan lungun dakin su Mama tana ta aukin murza hannayenta
Su aisha sun gaishe shi sun kuma kawo masa ruwa sannan suka basu waje
Shiru wajen ya dauka, tamkar bata taba magana da shi a waya ba, kanta a kasa sai zufa take yi, haka yannayin da take ta motsa jikinta na alamun rashin sabo da zama irin haka da namiji ya bashi mamaki
Murmushi ya yi ya ce" KAUSAR, alhamdulilah, na godewa Allah da ya nuna min wannan rana, ina ta fata na ganta da raina da lafiyata, sai gashi na ganta, KAUSAR ni di ba yaro bane, inada mata biyu da Y'ayana bakwai, kamar yadda kika ganni a shagon gidanmu shagon mahaifina wannan itace sana'ata, watau ni dan kasuwa ne, a gaskiya ban cika jan neman aure ba dan in har na nuna ina so din nakan fito a mutun a bani na kilace, ni dai na ga kin min kuma ina sonki da aure, dan haka me kika ce ne ke
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 47