ta sakar masu ledar turaran jijin tana turo baki hadi da gyara hijabinta
TAUFEEK ya girgiza kai cike da haushi ya ce" idan na kuma gannin kafarki a bangarena tabas sai na san yada na yi da ke, ke kam Hajia sai addu'a kuma, kar na kuma ganninki a wajena dan tsaf kike iya zige min mata , ku ji hijab har kasa kamar wata Malama , kuma da yake cewa turaranki dadi yana nufin kaurinsa idan kika turarawa mutun har ya yi wanki basa fita Ni koma kar ki biyo mu meye kike saka takalmi?"
Alhusain ya zarro ido yana fadin" kai da Maman Baba kake? Lalle baka da kunya, kuma bestyn kake kira matarka a gaban Hajia? Sai ta bi mu ai nasiha zamu yiwa matanka nasiha kuma da manya ta fi , mutumen kawai Hajia ai babu malamin da ya kaita kake wani yi mata rashin kunya"
Hajia ta ce" Gaya masa, gaya masa dan nan, Ni banma san me na masa ba da magaribar nan yace ba zan bi shi ba, wai kar na je bangarensa ai dole na je yaron nan ko dan na ringa masu nasiha, wai Khausarar ce yace matarsa? Nan fa yace min na masa auren dole Ni na manta ban fada mata ba dazun na taho mu je in sanar mata yanzu"
Wani irin cin birki TAUFEEK ya yi ya dawo yana nuna mata falonta ya ce" Koma, koma kin ji? Je ki cikin dakin in je in dawo , koma hajiata kar a shiga tsakanina da ke yan uba su ci galaba a kanmu, Ni fadan nan da muke yi ma gwara ki mana turare ta yiwu ba kalau ba"
Hajia ta yi ram da hannunsa ta ce" Kaima ka fara tunanin ba kalau ba ko? Ku je zan zo da safe in mana turare dan gaskiya bana tunanin ko lafiya ku je, Husaini na gambo Allah ya sa a sauka a jirgi lafiya ka saka hular sanyi saboda mura ka kuma tabatar ka yi addu'a ka ji? A kuma ringa yin jijin nan dan yana maganin iska sosai"
Alhusain a dole ya ringa dariya harda zama yana tsokanar Taufeek
TAUFEEK ya yi murmushi ya yi gaba yana fadin" Maragaici in ka gama ka sameni "
Alhusain ya daga murya yana fadin" ko Hajia bata fada ba Ni zan fada mata auren dole aka maku!"
Murmushi ya yi ya karasa bangarensa, shi kuma Alhusain maimakun ya mike ya bi shi su shiga ƙafarsa ƙafarsa sai ya yi zamansa saman kujera fara wajen shukoki kasancewar akoy hasken fitila ya dannawa matarsa kira wace idan suka fara fira ya tabata ba zasu gama da wuri ba bale ta san zai taso in an jima ta kama tambayarsa me yake so me zata masa da sauransu dan ba zai shiga ƙafarsa kafar aminin nasa ba bai san me zasu tarda ba, ko ba komai gidan mutun mai aure ba'a shiga kai tsaye haka ba
A lokacin da TAUFEEK ya tura falon ya shigo sai da ya dan zubawa falon ido ya lalubo wajen kunna fitila ya kunna
Falon ya karewa kallo sai kuma ya dan gyada kai, lalle an taba matar gidan, watau yau fitilarma Hajia Yumna bata kunna ba bale a yi tunanin tardo kanshi ko wata tarba irin nata ( masha ALLAH, ya zamto ko yayane mace idan mijinki ya zo ya samu wani yannayin da bai saba gani ba ya gane, ama ba a hade masa tunani ba kulun gidansa a hargitse kamar juji baya gane fari bale baki, du iya shegen Yumnah mijinta ya gane yau matarsa a sama take dan takan saka kanshi ta kuma girka koda na cikinta kadai ne)
Haurawa ya yi ya fada dakinsa ya shige bayi direct bayan ya ajiye karamar wayarsa, gaba daya yau bai dauki babar ba, dan kuwa koda yace masu na zai fita aiki ko kasuwa ba ya san sunna iya nemansa, Alhusain kuwa ya san ba zai shigo ba sai ya tabo shi dan haka suke yiwa junna , dabi'arsu ne, hasalima du tsakaninsu bai fi a irga ba suka shiga falon junna, sukan hadewarsu su sha firarsu ne a waje idan sun zo inda iyalansu suke basa sakin kari a yi ta zuba shirme ba kamun kan nan na wasu abokan mijin
A nutse ya yi wanka sosai da sabulun wankansa na ruwa mai sanyin kanshi sannan ya fito da tawul yana jin dakin nasa wani iri dan yau bai samu turaren wuta ba,
Wani yadi ya fitar mai tsari marar hayaniya ya saka a saman kannanun kayansa tamkar wanda zai fita anguwa sannan ya samu turare ya fesa sosai yadda ya saba kafin ya fito a nutse ya fara shiga dakin Yumnah da salama
Bakin gadonta ya sameta rike da kofin kwalba cike da madara da nido sai dan karamin cokali tana sha
Tunda ta amsa salamarsa ta kalle shi sau daya bata kuma kallonsa ba ta maida kanta cikin abinda take sha gabanta na dokawa hankalinta na neman tashi
Dan murmushi ya saki ya karasa bakin gadon ya zauna ya sake dubanta a tausashe ya ce" Ina yini Yumnahna"
Yumnah ta lumshe idannuwanta hawaye ya bale mata, a hankali ta fashe da kuka
Ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya janyota jikinsa ya rungumeta yana taping din bayanta kadan kadan, a hankali ya furta" Its ok Yumnah, ya isa haka kin ji?"
Yumnah ta ringa sauke ajiyar zuciya tana jin yadda kirjinta ke dokawa
Ya rab shin yaya zata yi da ranta? Ta yiwu a ga laifinta, tana yiwuwa a ki yi mata uzuri, sai dai ba zata iya ba kowa hakuri a kan abinda take ji ba, ita ta san ba laifi take aikatawa ba, kuma mijinta ya isa ta yi kishinsa
A sanyaye sosai ta furta" yayanmu....., Na kasa hakura, yaya zan yi in iya hakura?"
Sosai ya ji tausayinta ya kama shi, a tausashe ya cirota a jikinsa ya kama hannayenta yana kallonta ya ce " babu abinda zai kusanta ki da samun nutsuwar zuciya irin addu'a, sannan idan har bakya so ku zauna a waje daya kina da ikon zaba domin Musulunci ya zo mana cewa sai idan mace na so a hadata da abokiyar ZAMANTA ake haɗawa ......"
Da dan sauri ta kure lebensa da kallo, lokaci daya take ta tunanin maganarsa, hakan na nufin a fida Khausar daga wannan gidan da wannan banzar kakar rasa take ita a barta daga ita sai Hajia tana hannata rawar gaban hantsi? Ba zai yiwu ba, idanma Khausar ta yi nesa kennan ba ranar rabuwa tsakaninta da mijinta? Ba zai yiwu ba!
A hankali ta girgiza kanta ta ce" Ka barta a nan, kar a kaita ko'ina ta zauna a nan din"
TAUFEEK ya dan zubawa yannayinta ido, sai kuma ya dan lumshe idannuwansa yana rike da hannun nata ya ce" Shikenan, ama ina so ki kwontar da hankalinki ko dan abinda yake tare da ake, idan kin ji hankalinki zai tashi kuwa ki yi ta yin addu'a in sha Allah zaki ji sauki a ranki, Yumnah ban karra aure dan bana son ki ba believe me"
"Yayanmu, ka karra aure ko aka aura maka ita? Ka daina cewa ka karra, ka daina ɗorawa kanka abin nan Please" Yumnah ta fada tana sake duban fuskarsa
TAUFEEK ya zuba mata ido, yannayin na so ya fara damunsa fa, gaba daya kamar wace bata gane yarensa
A nutse ya saki hannunta ya mike ya karasa wajen tufafinta ya dauko mata hijab baba ya karaso ya mika mata
Amsa ta yi ta saka tana jiran karin bayani dan ta san ta yiwu fita zasu yi sai ta ji ya ce" *NI NE NA KARRA AURENA, BA AUREN DOLE KO NA HADI AKA YI MIN BA, MU JE HUSAIN ZAI MAKU SALAMA*"
Tamkar ya caka mata mashi ta ji a kirjinta
A raunane ta bi bayansa da kallo har ya karasa ya bude zai fita ta ji karrar bude kofar dakin da take kyautata zaton na Khausar din ne, dan haka da sauri ta taho ta riko hannunsa cikin nata harda rabun masa a Jikinsa a lokacin da suke bayyana a gaban Khausar wace ta fito hannunta rike da kaskon turaran wutar da ta sakawa dakinta bayan ya kama sosai ta ji tana ra'ayin sakawa a falon sai ta zuba wadatace ta dora hijab saman doguwar rigar yadi mai santsi dake jikinta ta fito dan kaiwa falon idannuwanta suka sauka a kansu
Wani irin abu ta ji ya caki makogwaronta, a hankali ta bi talabar da TAUFEEK ya yiwa Yumnah da kallo kafin ta dauke kanta tana tabe baki wanda tabe bakin tsaf a cikin idannuwansa ta juya bata ce masu ufan ba ta fara yin gaba a nutse ya sauka kasa turaran wutar nan na tashi ta karasa falon ta ajiye ta juya da nufin komawa sama TAUFEEK da ya hanna kansa Binta da kallo ta karfi da yaji cike da basarwa ya ce" Kar ki koma ki tsaya ku gaisa da Husain"
Yana gama fada ya fice a falon gaba daya, ita kuma ta ja ta tsaya tana kallon kofar da ya fita kirjinta na bugawa da wani haushinsa da take ji wanda ta tabata na abinda ya mata da safe ne ba komai ba
Yana fita Yumnah ta koma sama da sauri ta Kunno nata turaran itama ta sauko da shi, tana shirin ajiyewa ta dauke na Khausar din suka shigo Taufeek a gaba shi a baya bakin Husain da salama
Idannuwan TAUFEEK ne suka sauka a kan kasakan turaran wutar, a ransa ya ayana'To fah'
Su duka suka Amsa, Khausar ta yi kamar bata ga abinda Yumnah ta yi ba ta maida dubanta kan Husaini tan murmushi ta ce" Yau dai ga Besty, yaushe a gari?"
Yumnah kuwa sai ta wuce dan kawo masa ruwa a lokacin da Husain ke fadin" Aa a yi haka? Hajia bestyn besty ai ba zaki gane Ni ba jiya kai a lulube ana kukan ba za'a zo gidanmu ba bayan mu din nan mun riga mun rike kuma sai hakuri"
Da dan mamaki ta dago dan kallonsa jin bayaninsa sai ta ga TAUFEEK na kallonta, shi kuma sam bai wani tsareta da kallo ba magana dai yake yi normal , danma sun saba ne a da ya zamto a yau ya dan tsokaneta, basu taba irin haka da Yumnah ba
Kasa cewa komai ta yi ta sada kai cike da jin nauyi
Yumnah ta ajiye masa jus ta koma saman kujerar dake dan kusa da TAUFEEK ta zauna hankalinta a kan mijinta tana jin Husaini na mata godiya, ama kuma bai bude ba ya dai dauka ya rike a hannunsa , ita kuma a ranta tana ayana' Ni da ke a ga wanda zai fi samun shiga a fadar TAUFEEK!'
(Shi fa wani son, Allah ne ke halitarsa a ran bawa, ba dan an cika kyau ko isa ko matsayi ba, a'a, wani son kai dan adam sai ka ga mema aka gani na so din ne? To halitta ce da Allah ke halitarwa ya kuma hada da wanda ya ga ya dace, Allah ka sa mu so domin ka, mu kuma ki domin ka)
[7/24, 10:04 AM] +234 816 049 3429: 💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 5️⃣4️⃣
*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*
1: Duk karyar kada
2: Yar mahaukaciya
3: Neman na kaina
4: Bani da zabi
5: Bak'a ce
6: Kutkale
7: Makauniya ce
8: Mage
9: Duk nisan jifa
10: Idan ka raina inda kake
11: Dutse
12: Alkalamin kadarata
13: Bani da zabi
14: Dakika Biyar
15:Wata kokowar
16: Aure yakin mata
17: Ni zan ladabi
18: Daga tafia daukar soja
*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
A sanyaye Mama ta ce" Ka san yanzun ko babu abinda ya daga mata hankali abin na tashi, dan dai bai kai na yau ba dan idan ya tashi da na bata maganinta ta samu barci yake wucewa shi yasa baka Sannin ya tashinma"
Hajia Nawarah dake zaune a ranta gani take yi harda rashin godiyar Allah a wajen mijin nata da matarsa da kuma dansa, , ita dai bata jima sosai tare da su ba ama ko ita ta san cewa zuwa yanzu ai shekarun Hajia sun kai wajen ciwace ciwace irin na girma masu zafin nan
da ace bata samun kulawama da tuni ta kwonce ai, dan dai ga kulawa, ko abincinta ba irin na kowa bane, jikanta ya dora doka ko tuwon laushi za'a tuka mata da irin abincin masu diabete ake yi mata, sigan bangarenta na masu diabete ne, kai komai da ka sani yana taka tsantsan da shi yana kuma hankalce da shi baya yarda ko da wasa ta yi wasa da lafiyarta, sannan a dole ta saba da sport rawata kaffafuwanta dan a lokacin da ya ga ya dace ya sakata tafiyar shine ke fitar da ita cikin anguwa da duku duku sunna tafe sunna fada har Mai kwanoni shima yake binsu dan wani lokaci har dariya suka bata ita kam a ranta ta ayana' Rai dai ana sonka sai an rabu da kai, du abinku Hajia ai yanzun tana hararan kabari, du kaunar ku da ita kuwa ba zaku hanna ba'
Hajia dake sauraron zancen itama ta budi baki a matsayinta Na matar gida dadadiyar da ta rigayi kowace ta ce" To Elhaji ciwon zamani sai an tankwaloshi, ana gudunsa yana bin mutun bale masu ciwon hawan jinnin nan an ce ba'a cika so sunna yawan fada ba, Allah dai ya ba Hajia lafiya baiwar Allah du ta yi wani iri"
Elhaji ya amsa da amen, ya maida dubansa kan TAUFEEK wanda bai furta masu koda A bane
Jim kadan nurse da ta je da kayan aune aunen jinnin Hajiar ta dawo da result
Bata tsaya ba ta shige ta kaiwa doctors da Khausar dake zaune daf da gadon Hajiar tana rike da hannunta daya tana tofa mata addu'a dayan kuwa yana ɗauke da karin ruwan da doctors ya jona mata
Sunna gama gannin komai Doctor ya umarce su kan sunna iya tafia
Ya zamto shine karshen fitowa sai Khausar dake bayansa rike da wasu takardun da ya bata da kansa haka kuma kaf likitocin sun yi mamakin gaannin Khausar din da Hajia dan babu wanda ya san matarsa take haka kuma basu san ko members din family din Professeur din bace
Su Baba ya fara tsayawa ya kwontawa da hankalin cewa ta samu barci da sauki kamar yadda likitoci ke sanarwa wa'inda ba likitoci ba
Sannan ya dawo wajen da TAUFEEK ke tsaye daf da Mama ya amshi result din Hajiar ya mika masa sai ya dora da fadin" BP dinta ya yi kasa sosai ne, haka kuma sigan jikinta ya yi kasa fiye da misalin mai cuta irin nata, ga kuma ciwon kan da zazabi, mun saka mata maganinta na da wanda ya shafi siga din, ama na hawan jinnin na saka mata sabon treatement dan wancen din inaga ya fara sakin jikinta ne , zazzabin kuwa na saka karin ruwa da allurar saukar da ciwon kai da kuma na zazzabin wace zamu ringa saka mata du tsakanin awa shida, sai dan tari wanda in sha Allah shima zamu saka nasa maganin idan wannan ya daidaita, yanzu zamu ajiye nurse din da zata zauna kusa da ita dole wace zata ringa kula da hawan jinnin nata kowani lokaci har mu ga yannayin saukarsa, in sha Allah zata samu lafiya Sir "
Taufeek ya hadiyi dan yawun dake tsakanin harshensa da makogwaronsa , a hankali ya ce" Zan zauna da ita Doctor"
Doctor ya dan dube shi, dama ya san yakan iya cewa shi zai zauna da ita ama kuma nurse din da za'a saka ta zauna kusa da Itan anya zata iya aaikinta yada ya dace kuwa? Dan idan yana waje sukan rikice ne wani lokacin idan ana gudun kar a yi laifin nan ake aikata laifin ba'a sani ba, dan haka sai ya ce" I'm sorry prof da ka yi zamanka a office idan ya so sai komai ya ringa samunka a cen ko kuma ka ringa saukowa kana komawa dan likitar ta samu filin yin aikinta a nutse"
Khausar dake tsaye dan nesa da su rike da takardun ta budi baki a sanyaye duda ta san ba itace da ɗaukan wannan decision din ba , ama sai ta kasa hanna kanta fadin" Doctor, Please zan zauna matsayin nurse din tare da prof in sha Allah "
Doctor ya dan kalleta da mamakin yadda ta iya fadin haka a gaban TAUFEEK kanta tsaye
Tashi daya ya nuna ba zata yi ba dan ba ita ta saba kulawa da ita ba
Shi da kansa likitan ya fadi haka ne dan baya so ta jawa kanta fada, dan likitocin ba sunne suke da ikon yin hakan ba, uwa uba Khausar ba likitar jinya bace takardarta ya wuce nan
A hankali Taufeek ya dakata daga nufin nufar wajen Baba ya juyo a dakensa ya ce" zata iya zaman , *SHE IS MY WIFE*" Daga nan ya karasa yana fadawa Baba cewar su je gida kawai shi yana nan , kuma sun san harkar asibitinsa ba'a zama a yi jinya, shi dai zai zauna Khausar kuwa zata yi jinyar, dan ya hada kan matansa su juya baya son rigima da hayaniya a kai
Likitan kuwa sosai ya yi mamakin jin Khausar matar Doctor ce, sai dai bai tsaya ya wani nuna mamakin nasa a fili ba ya yi gaba yana fadin " Madame bismillah mu je na baki dukkan abubuwan da ake mata da takardar "
Khausar kam tunda ya fadi cewa ita matarsa ce sai ta ji dama ba a gaban Doctor din ba tace zata zauna, sai ta ji kunya da nauyin su Mama da suka ji maganar, ta bi likita shina cike da jin nauyisa ta je ta amso magungunan
Ko da ta dawo ba kowa ta shige dakin ta kai komai ta ajiye ta juyo inda yake zaune rike da hannun Hajia yana kallonta
A nutse ta dauko kujera ta ajiye daf da shi a hankali ta samu kanta da dora hannunta saman nasu a hankali ta dan matsa nasan kadan sannan ya dan bubuga a hankali ta ce" in sha Allah, zata samu sauki, ka kwontar da hankalinka Please"
TAUFEEK ya juyo yana kallon fuskarta, a hankali ya dago hannunta ya kai gefen fuskar tasa ya shafa gefen fuskar nasa da hannunta na dama yana kallonta kasa kasa ya ce" Allah ya sa "
Daga nan Khausar ta yi shiru suka ci gaba da kula da Hajia da dukkan motsinta
Sosai take barci mai daɗin gaske, sunna nan direba ya kawo suturar TAUFEEK wanda ya yi kira ya saka Yumnah ta dauko masa sannan ya fada mata ba sai ta zo ba dan ba barin jinya ake yi ba domin ta nuna tana son ta zo din itama ( wani lokacin, idan da rabo , mai hali irin na Yumnah na cenzawa idan ya samu abokin kwaikwayar halayar nasa mutun ne mai aikata aikinsa domin Allah ba dan a yabe shi ba ko dan ya saka dan uwan nasa jin haushi da kishinsa ba.)
Office dinsa ya je ya yi wanka ya cenza sannan ya shigo masu da abinci
Sallah kadai ke fidashi, Khausar kuwa tunda ta shige bata fito ba dan idan bayin ne akoy komai a ciki, kawai dai kayan jikinta take jin sun kai cenzawa dan kuwa ita rage acn nan ta yi sosai ta kuma kashe panka dan TAUFEEK har fifitu yake yi wai zafi ita kuma ta nuna tarin da Hajia ta fara in ta farka cikin sanyin nan da mura zata tashi,
A haka har aka fito daga sallar isha i, zuwa lokacin sosai jinnin Hajiya ya daidaita sai dai kasancewar bata farka daga barcin da take sha ba ba za'a iya tantance irin aikin da magungunan suka yi mata ba, ama ko a yannayin saukar numfashinta da sauki sosai
A hankali ya mike daga daf da Hajiar ya zubawa bayi ido
Kasa hanna kansa shiga ya yi a hankali ya bude ya shiga yana wani irin fatan da bai dace ya yishi ba a zuciyarsa a matsayinsa na abokin Khausarar Aba
Allah ya taimaketa tana tsaye tana alwallah ne, sai dai duda haka ta wanke pant dinta kennan ta shanya bayan ta yi wanka sama sama sannan ta yi bruch ta maida rigar da take yin datinta yanzun sosai a ranta guda ba wani dati da ta yi ta shiga yin alwallah hankali kwonce dan tunda take nan ta ga babu wanda ya shigo bale a ga paant dinta
Da sauri ta kai dubanta inda ya zubawa ido, a rikice ta kwalalo ido ta budi baki zata yi magana ya tako da saurin da bata yi zato ba ya janyota jikinsa lokaci daya ya dago kanta ya hade bakinsa da nata ya shiga kising cikin saurin da ya saka ta jan numfashinsa ta hadiye a huhunta sannan ya sake juyawa da ita ya hadeta jikin bangon nan a hankali hannunsa na damkar cinyarta ya ki bata damar kwace bakinta sai da ya gaji dan kansa sannan ya saketa yana fitar da numfashi da sauri da sauri ya janyota jikinsa ya sake rungumeta tsam har sai da ta kwontar da kanta dan dole a kirjin nasa tana sauke numfashi
A hankali ya dan yi kasa da bakinsa daf da kunnenta
Cikin kwarewa a aikinsa ya ringa sinsinar kunnen nata yana dan sauke hucin numfashinsa a nan, kasa kasa sosai ya ce" Ba'a magana a bayi, kin ga kin saka na maki abin nan da bakya so ko?"
Khausar ta dago da sauri ta zubawa fuskarsa ido, a rashin shiri ta ce" Kai TAUFEEK walahi da gangan ne ba gashi ba ka yi maganar ba?"
TAUFEEK ya dan zarro idannuwansa da hannunsa ya mata alamun ta yi shiru mana kafin ya nuna mata pampon wai ta yi abinda ya dameta tana yi
Ajiyar zuciya ta sauke ta koma ta bude ruwan ta daura alwallar tana kiyayewa kallonsa dan gudun kunyar dake nukurkusarta ta kayar da ita har ta gama cikin dabara ta janye pant dinta ta dauki hijab dinta ta nade shi a ciki da nufin in ta faki idonsa zata maido ta shanya ta yi gaba sai turo baki take yi ta bude bayin ta fito shi kuma yana baya yana kwasar ganima wa idannuwansa yana kashe kwarlwatar idonsa
Idannuwanta ta mutsitsika tana sake dubansa daga zaunen da ta kama ta zaunar da kanta da kanta ta sake rage girman idannuwanta tana dake tabatarwa kanta abinda take gani ta dauke kai ta ce" Uhum ikon Allah, dubun munafukai dai ta cika, dama karya fure take bata ya'ya, to Ni du wanda ya kuma min iskancin kukan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 36 Chapter of 47