Share this page
sun je kauye ai koyon aiki na wata uku uku, ama gawar har suka yi suka gama biyu aka yi rasuwar itama ta zo an tafi da gawar ne Gannin matar ta shiga ya saka ta bi bayanta sannan ta ja ta tsaya daga dokin kofar tana sake sada kanta Karasawa matar ta yi bayan ta gaishe da likitan dake zaune yana ta aiyukansa sannan ta mika masa takardar dake hannunta "Hajia rauda idan kin san aiki kika kawo min kima juya da abinki" ya fada yana duba takardar Yar dariya ta yi ta ce" Wane ni docter, bakuwar wajen oga ce" Da sauri ya dago dan son gannin inda bakuwar take, wace ya yi tsamaninta dunda sanyin safiya harma yake zaune har zuwa yanzu a asibitin saboda ita bayan aikin dake gabansa Shima kallon da Hajia Rauda ta mata ya mata, sannan ya kalli Hajia Raudar da dan mamaki, sai kuma ya cire kansa Kasancewar dazu kasa kasa suke yin magana, yanzunma sai ya mata kasa kasan ya ce" Yaya zamu yi kennan? Zuwanta nan a wannan lokacin zata take abinta ne dan tana bakuwa daga oga?" Hajia Rauda ta girgiza kai ta ce" Ai ka san ba haka, kuma shi ya koya haka, ba maganar ta gida a aikin asibiti, so hukunci ya hau kanta kawai " Kai ya gyada ya nuna mata rigunnan da aka warewa Khausar din, da safar hannu da takalmi kwaya biyu sannan ya ajiye takardun a nan saman table din ya ci gaba da aikinsa Rigar daya ta bude ta mikowa Kausar tana fadin" Maza cire hijabin nan ki saka rigar ga takalmin mu je" Kausar ta amsa da hannu biyu gabanta na faduwa , ta cire hijabin? Da sauri ta debe hijabin cikin gagawa ta saka rigar fara kar budadiya sosai wace ta kusan yi mata daidai ama wajen cinyoyinta sai ta dage sosai Cikin sauri ta saka takalmin sannan ta saka safar hannun tana sake gyara hular dake kanta a cikin zuciyarta tana tunanin lalle akoy aiki a gabanta Hijab din ta dauko da niyar mayarwa Hajia Rauda ta kalleta da mamaki ta ce" Kina ji? Abubuwan da zan fada maki su zamto na farko na kuma karshe da zamu tatauna a kansu Na farko ga takarda da zaki cike ta bayanin dalilin da ya saka kika zo a lati , na biyu wannan zane zane na hannayenki ba naki bane yanzu dan aiki kika zo koya, na uku hijabin irin wannan ba na aikinki bane, idan kin zo ki tabata kin saka dan karamin hijab wanda ba zai hannaki aiki ba, sai kula da dukan aikin da aka baki a kan lokaci kin fahimta?" Kai take gyadawa da sauri tama rasa me zata ce Matar ta karbe hijabin suka fito daga Khausar sai hular nan suka nufi wani office din Nan Allah ya taimaketa matar ta bata baby hijab , tana sakawa ta kuma janyota suka nufi wani dakin da yar hayaniya ta yi yawa Sunna zuwa suka tarar da abinda Khausar ke iya kira tashin hankali, domin accident ne aka yi du an shanshanya mutane Sai dai abin rikicewar zuciyar shine wanin ya samu karaya ne kashi a fili, wanin a inda yake jini ne ya bata wajen , uwa uba wanda ya samu kunna a barin jikinsa Tsintsiya da abin gugar da aka miko mata aka nuna mata wajen mai kunnar dake yashe shima ana duduba shi cewar maza ta je ta kimtsa wajen dan ya bata shi ta rike jikinta na rawa hancinta na jin karnin jinni, idannuwanta na kallon jinni da ciwo, tun tana iya jurewa wajen wanke gadon har abin ya kai wuyanta ta shiga sheka amai tamkar zata amayar da hanjin cikinta, sai dai abin mamaki masu jinyar mararsa lafiya kawai suka iya nuna mata kamar sun damu, babar likitar nan aiki take ba kama hannun yaro ana ta raraba mararsa lafiyar har sai da ya zamto ba kowa a dakin na farko ta juyo kanta ta kama kafadunta ta mikar da ita tsaye tana kallonta cikin ido ta ce" Sai fa kin kama jikinki, sai kin wanke idannuwanki, dan inda aka kawoki ana kaunarki aka kawoki, domin nan ba zaki fita ba sai kin goge iya gogewa a aiki, ama fa kin ga rama? Sai kin rame, sai hankalinki ya tashi, domin wani abin idan kika gani zaki sha kuka kamar ranki zai fita, ki jure kawai , ki jure kawai haka aikinki ya gada, ki gama wanke jinin nan tas, ki shiga dakunan cen biyu summa ki wanke sosai su fita sai ki zo cen wajen office din Samira ki tsaya ki yi pansema" Daga haka ta wuce ta bar Khausar daga ita sai ita a dakin nan Ido du a waje hankali a tashe Du yadda ta hasasowa kanta tana iya haduwa da tashin hankali abin ya zarce haka, tun tana gane yannayin lokaci har ya shige mata ta daina fahimtar dare ya yi ko har yanzu a cikin wunin ranar ake Juwa ke dibanta du idan ta motsa ama ta gaza zama bale ta kwonta Yinwa take ji tun bayan yin amanta, ama a hankali yinwar ta disashe ta daina jinta Idan ta ga an nufi sallah sai ta je ta yi a irgenta sun gabatar da sallar isha ama shiru ba'a salameta ba Ido ya gama yi mata zuru zuru ya mutu murus kwalin da ta saka du ya jeme da kukan da ta yi Tun tana tunanin ranar zata kare ta tafi ko ta daina irga gawa har ta dawo idan ta ga an rufe sai ta yiwa mamacin addu'a a zuciyarta, ama idannuwanta sun gaza daina kuka Tana tsaye, kaffafuwanta sun sage, tana tare da wasu likitocin da take masu kallon kamar wa'inda basa jin komai a gaban jikinsu kamar ba mutane ba? Sunna kai kawonsu ba alamun gajiya a tatare da su tamkar su din basa jin gabai na jikinsu Ita dai bata ga lokacin da suka tsaya cin abinci ba, dama dama dazun da 5a shiga sake wanke fuskarta ta ga wani namiji a tsaye yana tura wani abin a bakinsa ama bata san abinci ne ko menene ba A yanzun da suke tsayen ta gama yankewa cewar a yau fa ta yiwu karshenta kennan kanta a kasa ta ji Hajia Rauda na magana cewar ta dauko hijabinta ta tafi gida, kar ta manta gobe karfe takwas na safe ya mata a nan idan ba haka ba zata hadu da punichment mai tsauri, sannan ta tafi da takardar rubuta dalilin yin latinta yau Bata taba tsamanin idan akace Khausar jeki gida zata ji kamar ance Khausar shiga aljannah bane sai yau Wani irin salama da zazabin dadi ya sauka a zuciyarta Irin yadda take sauri ta nufi office din ta dauko baban hijabinta ta saka a saman kayan aikin ko takalminta bata tuna ba bale ta cire rigar da aka bata ta saka ta yi aikin Salama ta masu ta fice tana tunanin ai bama zasu kuma ganninta ba bale su kasheta, Hajia Rauda kuwa ta yi murmushi a ranta ta yana' Ta yiwu da gangan chef ya turoki a lati dan ya ga yadda zamu maki, na tabata in kika fada masa zai yarda cewa muna aikinmu ba shiririta muke yi ba' Da sauri ta fito daga Emrgncy din ita kadai sai shasheka take ta shiga tunanin abin hawa Idonta idon mai tsaron kofar nan sai ta ga kamar wanda ya yi murmushi, tuna cewar murmushin me zai yi ya sakata dauke kanta a ranta tana tunanin yinwar da ta fara tuna mata cewar akoyta fa ce ta fara sakata gani gani a hanya Ta fara tafiyawa kennan wata watsetsiyar mota ta parker gabanta kadan Niyarta ta dan dakata motar ta wuce sai ta nemi abin hawa sai gannin Aisha ta yi ta fito daga motar tanna yar dariya hadi da fadin" Likita bokan turai, Aunty an fito?" KHausar ta dan zuba mata ido, ta kifta a hankali tana kallonta , murya a raunane ta ce" Aisha kece?" Aisha ta yi mata wani kallo jin tana tambayarta ko itace, sai kuma ta kamo hannunta ta janyota tana fadin" Zo mu je, yaya TAUFEEK ne ya zo daukarki, tun dazun Baba ya kasa hakuri ya tabo shi, shine ya je ya kwatantawa Baba yanzun fa sai an yi hakuri dole an jure , wai harda gadi zakina yi akace ko me? Kingama sai da muka biya butique din nan baba muka siyo maki hijabai masu yawa walahi wai a saman rigar aiki ake sakawa inji shi" Bude mata gaba ta yi tana mata alamun ta shiga mana, Khausar ta bude baki murya na rawa ta ce" Aisha yinwa nake ji" sai ga hawaye sharrrrr sun fara bin kumatunta A hankali TAUFEEK ya labe fuskarsa yana sakin murmushi Aisha kuwa da mamaki ta ce" Kai aunty, dari uku fa kika zo da ita ai ya ci ace ta isheki , Mama fa ta ajiye maki doyarki " Khausar ta samu ta shiga motar da kyar tana share hawayenta ta ce" Ni nama manta da kudin nan, kin ga abin hawa ne fa nake nema idan na je Aba ya biya, ba zan iya wannan aikin ba, a yau wankin jinni na ringa yi da gadajen da aka rasu, Aisha rasuwa biyar aka yi a gabana ana rufewa ana fita da su, Aisha an yi karaya kashi a fili aka hade aka dinke ina kallo, tunda na shiga ban zauna ba a tsaye nake, ko ruwa ban sha ba babu wanda ya bani, ki duba ki ga yadda jikina ke rawa, idan na yi sati a wajen nan ni na san ramar da zan yi ko mai cutar s wanda baya daukan magani sai ya fini kyan jiki, walahi TAUFEEK ba zan iya ba, sai in mutu, kamar wanda suke jirana? Kamar wace na masu laifi, wai dan na zo a lati ka ga harda takardar na cike dalilin zuwana a lati bayan ba laifina bane, TAUFEEK ba zaka taba iya aikin Asibiti ba, na rantse maka sai ka summa kai da baka son wahala ko ta rana ce bale irin wannan, TAUFEEK gawa gawa kamar me, ashe haka ake mutuwa? Kai da baka saba ba ai na san bama zaka iya ba" Da kyar ya iya hanna kansa dariya, bale da take hawaye ka'in da na'in Ceinduith din da ya siyo ya juya ya dauko ya miko mata da ruwa ama ba masu sanyi ba masu dumi dumi yana gimshewa kadan ya ce" Amshi dan fara shan ruwan kadan sai ki ci" Ruwan ta dan rike, jin bashi da sanyi ta dube shi fuska har yanzu a raunane ta ce" Besty, ruwan ba mai dan sanyi sanyi?" Kai ya gyada mata sannan ya tayar da motar dan karma tace zata sayi mai sanyin , a irin yadda cikinta ya shaki abubuwan da bata taba shaka ba in ta fara shan ruwa mai sanyi da yawa zata sha, in kuwa ta sha da yawa cikin zai kule ne ya kama ciwo Haka ta ringa tura abincin nan kafin su karasa gida Sunna zuwa ya dubeta fuskarsa ba alamar dariya ya ce" Gobe, idan Allah ya kaimu ki shirya da wuri ki tafi a kafa, jikinki zai saba ne da wahalar , ba maganar wai kin daina zuwa kin fahimta" Da mamaki take kallonsa, shi dan bai ji abinda ta ji bane, koda yake dama haka zai ce mana shi da shine ta tabbata bama zai iya tsayuwar minti ashirin ba , tsafma zai ajiye karatun asibitin tunda dama su suke so ya yi ba shi yake so ba Motar ya kunna yana sake dan haske ta Mujahid dake parker ya mata alamun ta fita mana Fita ta yi tana turo baki ta yi baya kadan har ya tayar ya yi gaba Harga Allah bata gane motar waye gaba da gidan kadan ba sai da ta tsinci murya kasa kasa da tsayinta haka ana fadin" Watau Motatace ba zaki shiga ba sai ta Elhaji TAUFEEK? Khausar wannan kawance da Elhaji TAUFEEK zan iya rabashi kuwa? Ina nufin idan kika zama matata kin san ai ko magana haramta maki zan yi da shi tunda ba muharaminki bane!" Da zafi zafi yake maganar, har kamarma yana huci gaskiya Da farko tsoratama ta yi, sai da hasken farin wata ya dale mata sankonsa ta yarda cewa shine Dan rage tsayinta ta yi tana gaisar da shi, da kula sosai da mutuntawa ta ce" Yah Mujaheed barka da warhaka, ban san zaka zo yau ba ai" Baki ya dan tabe cike da kishi ya ce" Yaya zaki yi ki sani kin kashen waya ama k8n kunnawa Elhaji, Khausar gwarama ki ba maganata mahinmanci , ko dai ke din ba matar karamin mutun irina bace?" Mamaki madaukaki ya kamata, wai me yake damun bawan Allahn nan ne yau? Ji fa wasu magangannu kuma fisabililahi, me yake faruwa da shi ne haka?, Gajiyar dake tare da ita kadai ta isheta, kanta ciwo yake yi haka gaban jikinta, dan haka a tausashe ta dan sake risinawa dan bata son tana saman nan yana kasa walahi, ta fi so ta ringa rage tsayinta sosai in dai zasu yi magana ta ce" *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣0️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A sanyaye sosai ta ce" Dan Allah ka yi hakuri Elhaji, a nan ban ga abin bacin rai ba sam, wayana tana gida yau tunda na tafi wajen aiki ban zauna ba sai yanzu da Aba ya saka ya daukoni, TAUFEEK fa dan uwana ne ba wani abu da zai taba shiga tsakanina da shi, dan Allah kar hakan ya saka ka fara wasu tunani a kan zumuncina da shi, domin shi din ya min halaci kuma yana cikin yi min " Maimakun sanyayawarta, tausasawarta, da kalamanta naa fahimta su dan ganar da shi inda ta nufa sau ya ga ta karra rufa TAUFEEK, to in bama wulakanci ba shi zata duba tace wai TAUFEEK dan uwantane? Na ina? Tare numfashinta ya yi ya ce" Ba sai kin nunan kin gaji kina son shiga gida ba, dama kulun a gubdure kike in ina gefenki, ki sani dan ya fini kudi ba yana nufin zai iya yin kyauta fiye da tawa ba, ko a gari ni an sanni in ina neman aure har gida bake ba budurwar, kema kun katsenine tun farko domin da kun barni da yanzu ba haka kike yawo ba sai a motar kanki, kuma da na cireku a gidan nan na maida ku wanda ya fi shi, nima ina iya yi maki halaci sosai Khausar dan ina sonki, bara na tafi na barki ki huta idan na dawo ma yi maganar, ki yi tunani sosai a kan maganata ta Elhaji, ni kam bana son tarayarku!" Da ido ta raka shi har ya bacewa ganninta Zuciyarta ta ji ta sake cinkushewa sosai har kamar zata kifa daga tsayen da take Da kyar ta lalubi gidan ta shige da salama kasa kasa, Idannuwanta suka sauka a fuskar Aba dake sake fadada fuskarsa da murmushi yana fadin" Oyoyo ga bokan turaina, ga autana, ga shalelena, ga masu yaki da allurana nan" A hankali ta ja numfashi tana kallon fara'ar dake kan fuskar mahaifinta, a sanyaye ta shagwabe fuskarta ta sake kifta ido, sai ga abinda ba zata iya rikewa a gabansa, da mama, da TAUFEEK ba, watau hawaye, Mama dake lekenta ta koma tana dariya dan ta san in ta fito abin kamari zai yi har ta mangareta, domin Aisha ta fada masu a dane take , a sama take sosai har tace wai ba zata koma ba, shi yasa Abansu ya kori kowa ya shinfida tabarma da ruwa da abincinta dan ya san in ta dan fara jajen dole a bukaci ruwa dan a dan jika makoshi a kuma ci abinci dan a sake samun karfi kadan, fatansa dai ta sauka da wuri dan ya fita ya siyo nata panadol ta dan hadiya, ko jikin ya dan saku Tabarmar ta karaso tana cire takalmin kafa ciki ta yar a nan ta haye tabarmar tana kallon abanta Sai kawai ta sheke da kuka harda tafa hannaye ta ce" Mahamadou Rasululahi sallalahu alaihi Wasallam Abana haka ake mutuwa? Ba accident ba, ba gobara ba abana gawa biyar biyar abana, wayo allahna abana kashi a fili, abana ashe aikin asibiti da kace ba zan iya ba inada saurin kuka na maka gardama haka ne?, Ai kam na yarda yanzun ba zan iya ba, gwarama a sakani wajen koyon dinki na koyo na ringa yiwa yan anguwa inda samun na sakawa a bakin salati" Aba dake ta amsa salatin da ta yi da kula sosai ya ce" Asha, asha asha, to in ba autar Aba ba rasuwa ai kulun yinta ake yi, kuma kin san mafi yawancinta daga babar asibitinku ake fitar da ita, kin san gari ya girma ba yau ba al'uma ta cika, kuma harda kauyuka, idan lokaci ya yi dole a amsa kiran mai sama , Allah dai ya sa mu cika da kyau da imani, ni abinda nake sha'awa a aikin asibiti har nake tsayuwar dare ina kai kukana wajen Allah ya nunan irin ranar nan tarin ladan da kuke samu, yau a kawo maka marar lafiya ka masa sannuma lada ne bale ku da zaku cencana ku bi ku wanke jinni ku gyara waje, Allah ya sa sanadiyar shigarki aljanna ne wannan hanya Khausar dina" Tsuru ta masa tana kallon yannayinsa Kasa kasa ta ce" Abana, wai da cewa na yi fa an fasa aikin , tunda na je ban ci komai ba fa ina ta aiki ina ta aiki kamar in summa, wai da cewa na yi mu yi shawararmu da kai sai ka cewa Mama ka soke aikin asibiti ba zan koma ba ko Abana?" Shima ya rage muryar sosai ya ce" kina nufin dan kawai kin dan wanke jinni kin ga gawa shikenan har kin karaya? Bayan kece mai kokarin a gidanma kaf? To da kike cewa fata kike ki fara aiki ki siya min babur in kika fasa da me zaki siya min kennan? Da kike cewa keke zaki koma shekara nawa zaki dauka kafin ki koya kuma ki dawo ku layu da su maman ummi wa za'a ba dinkin wa za'a hannawa? Ta yiwuma ke sai dai ki ringa dinkan jalabiya kawai a gidan, ni dai ina so ki yi aikinki abinda wahalar ta dan lokaci ce, na wata uku ne fa kawai, kamar gobe ne, kuma abincin da komai ni zan ringa kai maki fa, daga kasuwa zan je na kai maki sai in dawo, ni zan ringa rakakima fa" Wani irin fadawa da ta yi a tunani sai ka tausaya mata ka kuma yi mamakin du girmanta shekara kusan ta ashirin da takwas ama mahaifinta ya yi mata wayo a dan kankanin lokaci, koda yake dama Khausarar aba ba dai rashin wayo ba A sanyyaye ainun ta ce" Aba, ina jin tsoro, kuma akoy wahala sosai" Da kula, zuciyarsa cike da tausayinta da tarin tunanin inama zai iya hannawar, da ya hanna, sai dai ya san abu ne da ba zai yiwu ba, du irin shekarun da ta dauka tana karatun nan Allah ya fitar mata da hanya ai wahala jurewa za'a yi kawai, dan haka ya ringa karfafa matya gwuiwa da kula yana nuna mata cewar ai wahala bata kisa, kuma Wajen nan da aka kaita zata matukar jin dadi zuwa gaba domin zata koyi aiki ne hannunta ya kware sosai har sai ta zama abin alfahari ga kowa da kowa A cikin hirarsu ne yake mata maganar Yaya aka yi Mujaheed ya zo ya yi ta zama? Nan ta sanar masa basu yi zai zo ba, wayartama a gida ta bari, harma ta fada masa abinda Mujaheed din yace A gabanta dai Aba bai nuna komai ba karshema saka ya yi ta shige wanka tana fitowa ta gaisa sosai da mamansu sannan ta shuge dakinsu, kafin kace me wannan barci ya yi awon gaba da ita A lokacin da Aba ya shiga daki sosai ya nunawa Mama damuwarsa da damuwar yarsa, Mama ta bashi baki cewar idan aka jure yanzu abin zai wuce, dama aikin asibiti aiki ne mai girman gaske, dole za'a sha wahala idan ba'a saba ba, ama a hankali komai zai daidaita Numfashi ya fitar zuciyarsa na masa wani kaikayi,, abin ke sukarsa har kamar zai amayar ya sanarwa mahaifiyarsu ama kuma ya rike a ransa A maganar Khausar maganar Mujaheed ta matukar daga masa hankali Anya akoy zaren mutunci a yarensa kuwa Shi zai fitar da su daga gidan nan ya kaisu wani, da ta bashi dama da tana hawa motar kanta? Me kennan? Gaba daya sai zuciyarsa ke son gannin haka a matsayin cin fuska ko sharar fage dan ya kangarar da zuciyar yarinyarsa, idan har mai kwadayi ce maganarsa na iya sakata yiwa abin wata fahimta daban, shi bama maganar rabuwarta da TAUFEEK ya tsaye masa a rai ba, dan ya san dama idan har ta yi aure ba kowanu namiji bane zai

Chapter 14 of 47